Showing 132001 words to 135000 words out of 207756 words

Chapter 45 - Bakar Inuwa Book 1 Hausa Novel Complete

17 Dec 2024

1243

ɗin shugaban ƙasa da yake gidan yasa bai samu wata matsala ta shigaba. A ɓangaren Raudha shigar mutunci tayi dogon hijjab harda niƙaf, tafukan hanunta kawai kake iya gani hakan yasa bayan Mama ladi babu wanda yasan da fitarta.
          Taji daɗin kasancewar ta a wannan makaranta da ta daɗe da fidda ran ganin kanta a ciki. Babban farin cikinta kuma department ɗinsu ɗaya da Rumaisa da Basma. Fadila ce kawai take daban dan abinda take karanta yanada banbanci da su Basma. Suturta jikinta ya matuƙar ɓoyeta ga kowa sai su Basma da suka sani. A nutse komanta ya gudana a wannan yani cikin kwanciyar hankali da farin ciki. Har a waya ta kira Asabe tai mata addu'ar fatan alkairi. Hakama M. Dauda ta kirashi sai dai Larai ta ɗaga cikin masifa tace baya nan. Ko jira su gaisa bataiba kuma ta kashe wayar. Murmushi kawai Raudha tayi dan halin matar baban nasu ba sabon abu bane a wajenta.

      Ƙarfe huɗu da wasu mintuna su Basma suka kawota gida, sai dai basu shigoba suka juya. Yunwa takeji sosai dan har wani dishi-dishi take gani saboda ta fita ko karyawa batai ba. Kuma har taje ta dawo ruwa kawai tasan tasha. Sam batai tunanin samun Ramadhan a gida ba tunda tasan yana office, dan haka kai tsaye ta wuce ɗakinta. A daddafe ta watsa ruwa ta canja kayanta zuwa doguwar riga mara nauyi, sai hula data saka da Slippers ta fito. Ba komai a dining, ita kuma tacema mama ladi kar ai komai sai dare tunda itama bata gida hakama bilkisu. Taɗan riƙe ƙugu da hanunta dake riƙe da wayarta, ɗayan kuma tana murza goshinta dake mata ciwo ta ciki kaɗan-kaɗan tabbacin yunwa da rashin isashen barci na damunta.
      Rasa inda zata kama ya sata kiran Mama ladi a waya ta sanar mata ta dawo. Sai kuma ta kai zaune cikin kujera cike da rashin ƙarfin jiki tana shafa ciki da ɓata fuska. dan da gaske yunwa takeji fa irin ta fita hankalin nan. Minti goma ba'a ƙulla ba sai ga mama ladi da basket na kayan abinci, ai tunkan ta ƙaraso inda take ta sauke ajiyar zuciya da faɗin, “Wayyo mama gaskiya kina sona”.
      Ƴar dariya mama ladi tayi tana ƙarasowa gareta. Cike da girmamawa ta ce, “Barka da dawowa ranki ya daɗe ai bansan kin shigoba wlhy”.
     “Bamma jimaba mama, dan ko mintuna talatin bana zaton nayi, dan na fara wanka ne shiyyasa. Kamar kinsan da yunwa na dawo gidan”.
       “Ai nasan za'a rina, tunda naga kun fita baki karyawar kirki ba. shiyyasa na tashi na haɗa miki wannan karki dawo ba'a kammala abincin dare ba”.
     “Nagode sosai mama ALLAH ya saka da alkairi”.
    Cike da jin daɗi mama ladi ta amsa mata. ta tsiyaya mata kunun tsamiya daketa ƙamshi dan ta fahimci Raudha naso sosai, zata zuba mata sauran abinci ta dakatar da ita. “Mama bara nasha wannan tukunna dai to”.
     Cikin ƴar dariya mama ladi tace, “Yunwar dai bata kai ko'inaba ma kenan to”.
     Dariya kawai Raudha tayi itama tana saka sugar. Mama ladi ta miƙe tana faɗin, “Bara na barki kici abinci naje kitchen muga mi za'a girka kar adalin shugabamu ya dawo da wuri. Amma mi za'a girka masa da kema kanki?”.
        A cikin zuciya Raudha tace (shi wannan mina sani zaɓinsa inba nama da fura ba) a fili kam sai tace, ko tuwon alkama za'ai masa ne, sai a haɗa da farfesun kayan ciki asa yaji da ɗan yawa dan yana mura..... Kodaima mama ku jirani naci abincin zanzo kitchen ɗin kawai”.
       “To shikenan a fito lafiya”.

    A nutse Raudha ta cigaba da shan kununta hankalinta nakan wayarta tana karatun wani littafin hausa da Bilkisu ta tura mata. Bayi take ba, amma yanda Bilkisu ke zuga littafin ya sata fara dubawa shekaranjiya. Sai kuma kamar wasa labarin ya tafi da ita ta nutsu a karatunsa. Dan ita bama tasan bayan marubutan dake buga littafi ba akwai na online sai yanzu. Kodan bata da wayar ne shiyyasa. Kuma ko sanda suke hutawa bata damu da waya ba shiyyasa bata taɓa maida hankalinta ga nasu Fatisa ba, amma tasha jin suna sauraren littafi a waya ta zata na masu bugawa ne da ake karantawa a gidan redio.

          Yunwa ce ta hana barcinsa tasiri shima. Duk da dai babu laifi ya ɗanyi tunda gashi har makara sallar la'asar yayi. Da ƙyar ya tashi zuwa toilet ya ɗan watsa ruwa duk da zazzaɓi dake jikinsa ga ciwon kai. A kallo guda zaka fahimci murar ta sake masa rugu-rugu dan saman hancinsa ya ƙara jaa sosai abinka da fari. Hakama idanunsa sun kumburo fiye da jiya fatarsu tai jajur. Ga shi dama baiyi wani barci isashe ba da daddare. Sama-sama ya shafa mai ya saka wando da riga masu ɗan kauri na kamfanin adidas harda hula a jikin rigar, sai dai bai ɗora hular a kansa ba ya saketa saman bayansa. Slippers ya zura cike da dauriya ya fito falon hannayensa duka a aljihun wandon, gara ya samu ko tea ya sha kozai samu nutsuwa ta wani ɓangaren. Tun daga nesa idonsa ke kanta, yayinda sam ita batasan dashi a wajen ba dan gaba ɗaya hankalinta ya tafine akan littafin da take karantawa mai suna *_SIYASA KO ƘABILANCI?_* na (marubuciya Bilyn Andull ƴar ƙasar Nigeria). Labarin ya matuƙar ɗaukar hankalinta saboda kamanceceniyarsa da tsarin da mijinta kamar yake kai a yanzun.
        Tafiya yake a hankali kamar baya so, saboda rashin ƙwarin jiki harya iso inda take, ya kai zaune a kujerar 3seater ɗin da take zaune sam bata fargaba. Sai da ya kai kwance ya ɗaura kansa bisa cinyarta tai saurin ɗagowa a zabure dan tsabar firgitar ganin kan mutum bisa cinyarta a baza .
       “Shut up!”.
Ya faɗa da yanayin tsawatarwa ganin zatai ihu sai dai muryar a ɗashe take fita da sanyi-sanyin dushewarta a dalilin mura da damuwa. Hannu Raudha tai saurin ɗaurawa a bakinta, sai kuma ta lumshe idanunta zuciyarta sai lugude take a ƙirjinta kamar zata faɗo.
       “Sai shegen tsoro”.
Ya sake faɗa a hankali yana lumshe idanunsa da harɗe hannayensa a ƙirji ya miƙar da ƙafafunsa har bisa hannun kujerar da ƙyau. Raudha da sanin shi ɗinne baisa ta dai-daita ɗari bisa ɗari ba ta buɗe idanunta a hankali ta sauke bisa sumar kansa da ko ba'a faɗa ba kasan tana cin kuɗi kodan ƙyallin da takeyi duk da kasancewarta irin sumar baƙaƙen fata mai tauri da cika.
      Cinyarta ta ɗan motsa cikin ɓata fuska, a ganinta adalilin miye wannan taɓara da zaizo ya kwanta mata cinya babu gaira babu dalili. Motsa ƙafafun nata ya sashi buɗe idanunsa sai suka shige cikin nata da take hararar masa kai. Da sauri ta kauda kanta gefe da gyara yanayin fuskarta tace, “Ina yini”.
     Kamar koyaushe yanzun ma bai amsa ba, sai dai ya zare hanunsa guda daga saman ƙirji ya kamo haɓarta ya dawo da fuskarta yanda take. Cikin sake tsuke fuska ya ce, “Hararata kikeyi?”.
      Idanu Raudha ta ɗan zaro. “Ka rufamin asiri, ni yazanyi na hahareka?”.
     Kamar zaiyi magana sai kuma ya saki fuskar da maida hannayensa a ƙirji yana faɗin, “Inma kin hararenin ne iyakarki hararar, kuma duk matar dake harar mijinta dai kinsan aljanna sai dai ta gani dajin ƙamshi a maƙota”.........✍


*_🚶🏻🚶🏻🤣Da alama dai shugaban ƙasa Ramadhan ya koma wa'azi😂😜🤭_*


*_BAƘAR INUWA...👇🏻_*



Da ɗumi-ɗuminsa💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻


Please
*_Follow me_*
*_Share_*
*_Comments_* akan abinda ya shige maka duhu.

_AREWABOOKS, dan zaku dinga samun sabbin pages galla-galla akan lokaci insha ALLAH. Maza garzaya ka karanta naka hankali kwance. Ka kuma yi following ɗina ko dan kar ayi babu kai, da a baka labari gwara ka bayar🥰🥰🤝🏻👇🏻_


*YADDA AKE BUƊE ACCOUNT A AREWABOOKS*

Bayan kaje play store ka ɗakko ya sauka a kan wayarka. Za'a cike Form ɗin kamar haka: -

*Enter your name:* (Cikakken sunanki)

*Enter your mail:* (Email ɗinki)

*Enter an username* (Sunanki)

*Enter your password:* ( misali 12341234)

*Confirm password:* (misali 12341234)

Sai a taɓa *Sign Up* shikenan an buɗe account a ArewaBooks💃🏻😂.

*Continue with Google* - Idan kana da gmail/email akan wayarka kawai Continue with Google za'a taɓa zata buɗe maka account a ArewaBooks kaitsaye.

*Register* - Shine cike form domin buɗe account a ArewaBooks.


*_AREWABOOKS LINK kai tsaye_*

https://arewabooks.com/book?id=620032232dff83519bbad5a3


Masu iPhone

Zaku iya bibiyar shafinmu
https://arewabooks.com

*_Kuzo mu haɗa ƙarfi da ƙarfe domin gyara tafiyarmu. Koba komai ɗan uwanmu ne bahaushe ya zauna ya tsara ya kuma buɗe App... Ɗin domin cigabanmu da jin daɗinmu. Wannan abin alfaharine_.*


*_YADDA ZAKA SIYA LITTAFI A AREWABOOKS_*👇🏾👇🏾👇🏾👇🏾👇🏾

*Recharge* - inda ake shiga domin saka kudi cikin account.

*Balance* - Zai nuna kudin account dinku da zaku iya sayayyan littafai cikin kasuwar ArewaBooks.

*Credit/Debit Card* - Hanyar farko kuma mai dadi wajan Recharge din account dinku.

A inda (Enter your amount) za'a saka kudin da akeson Recharge din sai a taba "Proceed". Zaibude muku inda zaku saka bayanan katin banki, kuna gamawa kudinku zaishiga account dinku kaitsaye (instant).

--------

Akwai wasu hanyoyin saka kudi a ArewaBooks account kamar:

*Bank Transfer*
*Airtime Transfer*

Saidai su ba kaitsaye bane (instantly) sai ArewaBooks ta tabbatar da Transfer din, amman bayakai 1hour za'a gansa a Balance.


*Bank Transfer* - kamar yadda akwai bayani a sama da kuma account number ArewaBooks.

_Account No_ - *1220077999*
_Account Name_ - *Arewa Books Publishers*
_Bank_ - *Zenith Bank*

Bayan anyi Transfer dinne sai a cike wannan Form din:

Amount Paid: - Nawa aka tura?

Name used for transfer: - sunan da aka saka wajan turowa

Transferred time: - lokacin da aka turo

Name of bank: - sunan bankin da aka turo dashi

Deposit date: - ranar da aka turo

Sai ayi SUBMIT.

*Airtime Transfer* - muna bada shawaran ayi amfani da *Debit Card* kokuma *Bank Transfer* akan *Airtime Transfer* , amma idan yakama babu mafita saishi tau muna amsar:

MTN,
9Mobile
Glo
Airtel

Amma kamar yadda akayi rubutu a sama afara tuntubar ArewaBooks a WhatsApp domin akwai percent da ake cirewa na canji(convert) kafin kudinka yashiga Balance.

*WANNAN SHINE BAYANAN*



*_MARUBUTA DAKE NEMAN ƘARIN BAYANI KO MASU KARATUN MA, ZAKU IYA NEMANMU TA WANNAN NUMBER_*

+234 903 177 4742


_Alkairin ALLAH yakai gareku masoya a duk inda kuke, tare da fatan alkairi muna sonku irin trillions ɗin nan😍😘😍🥰😍😊_.




*_ALLAH ka gafartama iyayenmu😭🙏🏻_*
[7/1, 8:00 PM] NANA: *_Typing📲_*







*_BAƘAR INUWA👉🏻AREWABOOKS👇🏻_*


https://arewabooks.com/chapter?id=62bd9379f0fb62def3120ded

*_Episode 44_*


.........Yanda yay maganar kamar bashiba yasa Raudha ɗan taɓe baki da marairaice fuska. “Ni dai tunda banyi ba ai Alhmdllhi”.
      Bai tanka mata ba, sai dai ya sake buɗe idanu yana kallonta. Sosai zuciyarta ke gudu a ƙirjinta dan ta fahimci abinda yake kallon. (Oh ita Raudha taga takanta, mima ya kaita fitowa ba hijjab ko mayafi?) ta ayyana a zuciyarta a fili kamar zatai kuka.
        “35, 32, 38... Uhhm da alama zaki iya....”
Saurin buɗe ido tayi jin ta ɗan zama kanta na son ganin kuma mi yake ma lissafin numbers haka? Da cewa zata iya. Saurin son zame masa kai tayi a ƙafarta sai ya ɗan mintsini cinyarta. “Hi kokin manta sadaki na biya malama. Stay quite ko kiji a jikinki”.
         Daina motsa ƙafafun tayi, sai dai tasa hannu ta kare ƙirjinta tana tura baki dan ta fahimci lissafin seize ɗinta na ƙirji, ciki, hips yake yi. Ji take inama ƙasa ta tsage ta shige kawai ta huta dan kunya. Ita kam al'amarinsa yanzu ya daina bata mamaki sai dai tsoro.
        Ganin yanda ta kare ƙirjin nata ya sashi ɗan yamutsa fuska da taɓe baki. “Yarinyar nan anya kuwa bazaki lalatani ba. To banda son lalatani inda na dosa daban inda kika dosa daban tabbacin abinda ke ranki kenan”.
             Ji Raudha tai mizai hana kawai ta saki kuka ta huta, kafin ta lalubo abinyi ya tashi zaune cike da ƙarfin hali yana gyara zamansa sosai a gefenta dab. Fuska a yamutse idonsa ƙyam a kanta yace, “Da alama yarinyar nan zaki tsufa da wuri, dan ƙiba zakiyi bata wasa ba mtsoww nidai an cucan..” ya ƙare maganar da ɗaukar kofin kunun da take sha. Zamansa ya gyara tamkar bashi ya gama zuba zancen ba ya kai kofin bakinsa bayan ya ƙarema abinda ke cikin kofin kallo ya fahimci kunun tsamiya ne da Anne nayi, kuma Alhmdllhi yana matuƙar son sa.
          Yunƙurawa Raudha tai zata tashi dan ya gama dabaibaiyeta a cikin cakwakiyar kunya ya dakatar da ita. “Amma gaskiya baki da tausayi Ameenatu! Haka akace ki kula da miji idan baida lafiya!?...”
      Yanda ya ƙarasa maganar da saki wata wahalalliyar atishawa da jin sunanta a bakinsa ya sakata dakatawa. Zuciyarta da ɗan fargaba ta dubesa dan tun dama yazo wajen ya fara magana da ɗumin dataji kamar a kansa daya ɗaura jikinta take tunanin yana lafiya kuwa? Sai dai tsokanar magana daya ɓige da mata yasata ture tunanin. Dubansa tai cikin ƙarfin hali, ganin yanda fuskarsa tai jaa musamman saman hancinsa, sai kuma idanunsa da ya buɗe suka haɗa ido suma sun sake koɗewa fiye da jiya alamar babu lafiya. Saurin kauda nata tayi tausayinsa na ɗarsuwa mata a rai, dan tun fil azal haka take da saurin jin tausayin mutum koda mugune (akwai lokacin da aka taɓa kama ɓarawo a makwaftansu, gashi dai itama haushinsa takeji saboda ya taɓa haurawa gidansu yay sata. Amma yanda aka dinga jibgarsa sai itama taita kuka tana roƙon a barsa ya tafi).
      A bazata taji ya damƙi hanunta ya kai saman goshinsa da ya ɗauka zafi sosai har tanajin harbawar jijiyoyin wajen. Cikin tsoro da tausayinsa da ya bayya a cikin idanunta ta buɗe baki zatai magana sai dai ya rigata. Cikin taushi da sanyin murya da batasan yanada su ba.  “Ki bani abinci naci kiban magani”.
        Tausayinsa sosai ya sake kamata. Cikin damuwa da sake sanyaya muryarta itama mai sauƙin faɗi tace, “Murance har yanzun?”.
        Idanunsa daya ɗan maida ya lumshe ya sake buɗewa. Sai kuma ya kwanto kansa kan kafaɗarta yana faɗin, “Kin damu da nine balle ki sani? An baki amanata kin kasa riƙewa”. Nanma zafi taji jikinsa. Tai saurin rumtse idanu kunya na sake dabaibayeta da dariyar maganarsa (wai an bata amanarsa. Bama itace aka bashi amanarta ba) Tasan ya kamata tun a jiya data fahimci ya dawo da mura tabi shawarar Bilkisu na kai masa magani. Amma ganin kamar Bilkisu ta manta sai itama ta share batun dalilin abinda ya sake harmutsasu na faɗan ƙauyen Kauci. Dai-dai tana janye hanunta a goshinsa yace, “Kiramin Anne”.
           A sanyaye tace, “Amma za'a tayar mata da hankali ai”.
     Komai bai ceba ya ɗaura hanunsa saman cinyarta idanunsa a lumshe ya hau laluben wayarta. Saurin riƙe masa hannu tai a ɗan firgice jin yanda yake lalubeta kamar da gayya.
        “Ki daina fassarani da abinda bashi nake nufi ba, ni waya nake nema”.
       Duk da idonsa a rufe yay maganar hakan bai hana Raudha ƙyaɓe fuska ba da tsuke ta. Sai dai batace komai ba ta tura masa wayar ta dunguri hanunsa datai saurin saki a nata. Shima komai bai sake cewa ba ya ɗauka wayar ya ɗaura bisa hanunta. Murya babu wasa yace,
      “Kiramin Anne”.
Badan taso ba tabi umarninsa tai kira number Anne ɗin. Sau biyu tai wringing aka ɗaga, a hanunsa ta ɗora wayar dan ita kam bata san mizatace da Anne ɗin ba. Shima komai baice mata ba ya tashi da ga kafaɗarta ya kwantar da bayansa a kujerar yana kai wayar kunnensa. Dai-dai Anne na ambaton sunan Raudha cike da kulawa....
       “Anneee!”.
Ya kira sunanta cikin katseta. Ɗan jimm tayi kafin tace, “Ramadhan!”.
     “Uhhyim”
Ya amsa yana sakin atishawa cikin rashin ƙarfin jiki. A take Anne ta rikice, dama tun jiya ta tsargu a muryarsa da suna waya. Amma koda ta tambayesa sai ya nuna mata lafiyarsa ƙalau.
       “Baka da lafiya ko! Haba Ramadhan abin nan kasa a ranka harya kwantar da kai haka?”.
      “Anne cool down mura ne tun a uk nataho da shi”.
   Sanin wahalar da shi da mura keyi ya saka Anne sake shiga damuwa. Cikin ƴar rikicewa tace “Haɗani da Aminatu”.
        Maimakon bama Raudha da akace sai cayay “Anne ni dai kizo dan ALLAH, ko kuma na taho nan”.
      Murmushi tayi mai sauti, ita kanta tasan badan raino irin na uwa taima Ramadhan ba tabbas a taɓare zai tashi. Sai dai batai sakancin masa rainon kaka ba ta tsaya kansa da tarbiyyarsa tamkar uwa, kai ko uwarsa batajin idan da a hanunta yake zai samu tarbiyya makamanciyar wadda yake a yanzu. “To naji bani Aminatu nace”.
     Fuska ya tsuƙe yana ɗorama Raudha wayar a kunne sai kuma ya tashi zaune ya ɗauka kunun ya cigaba da sha badan yana masa daɗi a baki ba, saboda gaba daya baida appetite.  Gashi kuma yaji tasa sugar sai dai baiyi ƙarfi ba shiyyasa bai damu ba tunda yana ɗan sha wani lokacin duk da yana wahalar da shi idan akai rashin sa'a...
         Cikin damuwa Anne take amsa gaisuwar Raudha. Kafin ta ɗora da roƙo akan Ramadhan ɗin. “Ameenatu kiyi haƙuri nasan bazaki barsa cikin ciwo ba amma dan ALLAH ki kula dashi sosai kinji. Ramadhan nada matuƙar rauni akan ciwo bai da juriya, ga rakin tsiya. Dan gaba ɗaya shafkewa yake tamkar yaron goye musamman mura da bata masa kamun wasa. Wajigasa take matuƙa ga wannan ma naji kamar ta masa ƙarfi sosai halan baisha ko magani ba tun jiyan?...”
     Cikin ɗan in ina da kunya Raudha tace, “Eh Anne gaskiya inaga bai sha ba, dan yau tunda safe ya fita a gida”.
       “Amma garin yaya haka ta kasance Aminatu?”.
    “Uhm..uh...m Anne jiyanne ransa ɓace ya kwana saboda abinda ya faru a ƙauyan can, daga baya ma kulle kansa yay a ɗaki”.
     Sosai Anne ta sauke numfashi mai nauyi tunda tasan halin kayanta idan ransa ya aɓaci. Alhmdllhi ma an samu canji bai

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login