Showing 171001 words to 174000 words out of 207756 words
nannauyan numfashi ya sauke da girgiza kansa, sai kuma ya saki murmushi tausayin ɗansa na ƙara ratsa masa zuciya. Mikewa yay ya fice sashen mahaifansa. Acan ya samu har su Yafendo suna hirarsu cike da farin ciki kamar yanda suka saba.
Bappi dake shan fura ya ɗan tsura masa idanu cike da nazarin ɗan nasa. Sai kuma ya ɗauke kansa. Ita kanta Anne idanun nata a kansa suke, dan tun shigowarsa ta fahimci akwai damuwa tattare da shi. Bayan ya gaishesu Inna ke faɗin, “Bashari lafiya kuwa na ganka kamar mai damuwa?”.
Ɗan murmushi yay mata yana furzar da huci. Sai kuma ya gyara zamansa sosai yana fuskantarsu. “Lafiya lau Inna, kawai nazo nayi magana da ku ne in ba damuwa”.
Yafendo tace, “Faɗi kanka tsaye Bashari mike faruwa?”.
Jin Anne da Bappi basuce komai ba ya sashi dubansu, sai dai yanda suka maida hankalinsu garesa suma ya sashi sauke ajiyar zuya. “Ba komai bane dama akan Ramadhan ne da wannan auren nasa.”
“Ba mun wuce wannan babin ba mi kuma ya faru?”.
Bappi ya faɗa yana kallonsa fuska a tsuke.
“Kayi haƙuri Bappah, bawai na dawo da hanun agogo baya baneba. Kawai ina son muyi wani abune dan ALLAH saboda wani nazari dana zauna nayi.” batare da ya jira cewarsa ba ya cigaba da faɗin. “Ni da ku duk munsan waye Ramadhan da kuma kammu, amma jama'ar gari da Ramadhan ke mulka har yanzu basu gama sanin waye shi ba. Auren Ramadhan da yarinyar nan Ameenatu dududu watanni na bakwai muke a ciki yanzu, ko shekara bamuyiba. Aurene da yasha soke-soke da kace nace a idanun mutane da bakunansu dalilin tazarar da su suke hange da mu babu ita a zukatanmu. Shin ya kuke tunani idan akace yanzu an fiddo maganar ƙara auren Ramadhan wa duniya, kuma da ɗiya irinsa mai irin matsayinsa kuma ƴar uwarsa sannan mai dukkan kishiyar abinda akai cece kuce Ameenatu bata da shi a baya?. Dama ance munyi haɗin auren Ameenatune da Ramadhan saboda mu gyara masa siyasarsa ace yana son talaka gashi harya auri ɗiyar cikinsu. To yanzu wannan auren nasa da har yanzu bamu gama sanin kansaba ake masa shiri na tashin hankali bama tunanin cikkakkiyar amsace ga ƴan ƙasa da abokan hamayya?. Ba ina fargar damu bane dan tunanin kar Ramadhan ya rasa kujera a zaɓe nagaba. Ina fargar damune domun kare mutuncin kammu dana Ameenatu yarinyar kirki da batajiba bata ganiba, hakama ina kare kunyar da zamu daurama bayin ALLAH da suka goya da bayanmu suka kuma tabbatar da tsarkake abinda mukayin badan sakamakon mu a hanunsu yake ba, sai dan bana son mu cire hope ɗin mutane akan mulkin Ramadhan. A yanzu Su'adah tazomin da wannan invitation card ɗin” ya ajiye iv ɗin gaban Bappi. “Bappah ka dubafa ka gani, events kusan goma ne anan aka shirya wanda ake fatan duniya ta gani ta shaida za'ama Ramadhan auren gata bama ƙasar NAYA kaɗai ba. Bayan kuma mu a wannan gidan duk bama hakan tun auren ƴaƴanmu na farko, sannan ko'a yanzun ma bawai shine kaɗai auren da za'a ɗaura ɗin ba”.
Tsitt falon yay bayan Pa yayi shiru. Sai dai tsananin ɓacin rai ya bayyana ga fiskokinsu bayan duk sun ga katin da tarin bidi'oin dake a ciki. Anne da idanunta suka fara cika da ƙwalla tace, “Anya kuwa Ramadhan ma yana cikin hayyacinsa? Bana son zargi sam a rayuwata ballema dana san dai Su'adah mahaifiyarsa ce babu yanda za'ai ta cutar da shi....”
Murmushi Pa yayi, cikin kunar rai yace, “Idan ita bata cutar da shi ba ai anyi amfani da ita da son zuciyarta an cutar da shi Anne. Bara yau na fito na sanar muku gaskiyar lamari akwai sihiri tattare da Ramadhan, sam abinda yakeyi ba'a cikin hankalinsa yakeba..”
Salllami falon ya ɗauka da sautin kukan su Yafendo. Yayinda Bappi ya tsurama ɗan nasa ido duk da shima ya jima yana wannan zargin. Pa yaja numfashi mai cike da takaici. “Karku wani damu kanku ni hakan yamun daɗi ai, maybe a dalilinsa Su'adah zata dawo cikin hankalinta tasan abinda ke mata ciwo. Na jima da fahimtar hakan amma bana son kowa ya nemawa Ramadhan magani dan ALLAH har sai anzo gaɓar daya dace...”
Da sauri Inna ta katse Pa, “Baka da hankali Bashari. Taya za'abar yaro a baƙar inuwar sihiri? Kenanfa kusan duk abinda yakeyi baima san yanai ba! Kai nifa ina mamakin canjawar yaron nan lokaci guda. Har takai yanzu zaizo gidan nan amma bamu sani ba. Barinsa cikin wannan tashin hankalin ai matsalane, sai ya iya shafar mulkin da yake kai ko kai baka san hakaba”.
Karon farko Bappi ya saki murmushi, cikin takaici yace, “Sadiya kenan wannan na nawa kuma. Badan ALLAH ya bashi chief of staffs na ƙwarai mai amana da tsoron ALLAH ba ai da tuni halin da Ramadhan ke ciki ya bayyana a cikin mulkin nasa. ALLAH dai ya ƙyauta. Ni yanzu inaga kai Basheer faɗi dalilinka muji, idan mai yuwuwane saimu riƙe. Idan bazai yuwuba a sake shawara”.
Kai Pa ya jinjina masa. “Bappi abinda yasa na roƙeku kar'a nema masa magani saboda dalilai uku ne zuwa biyu. Na farko ina son Su'adah ta gane kuskurenta akan Ameenatu, na biyu ina son ta gane wacece ƴar uwarta Asma'u. Na ƙarahen da bakinta nake son ta bayyana dana saninta a kansa. Dan haka ina roƙonku yin wannan aure a sirrance. A ɗaurashi a sirrance iya wakilansa da wakilan yarinyar. Akuma hana kowanne biki da suka shirya da an ɗaura aure ya dauka matarsa su wuce kawai, sauran dokokina a kansa sai bayan ɗaurin auren ne”.
Shiru falon yayi kowa na nazari, bayan shuɗewar wasu mintuna Bappi ya fara jinjina kansa alamar gamsuwa. “Kamar hakan duk yayi gaskiya. Sai dai Jannatu mi kuke gani ku?”.
Anne dake ta danne kukan dake taso mata ta haɗiye da ƙyar. “Dattijo hukuncinka ai namune. ALLAH yasa haka shine mafi alkairi”.
Da amin duk suka amsa. Daga haka suka cigaba da tattauna abinda ya dace............✍
*_Ku garzaya AREWABOOKS ta app ɗin dake a play store, domin samun pages fiye da wanda kuke gani a WhatsApp da zaran kinyi Searching littafin BAƘAR INUWA ⛹🏻♀️⛹🏻♀️😘_*
*_ZAFAFA BIYAR (5) ZAZZAFAR TAFIYA🔥🔥👇👇👇_*
*1*~ *_KUFAN WUTA_*🔥
_Safiyya Huguma_
*1*~ *_BAQAR INUWA_*💥
_Billyn Abdul_
*1*~ *_RAYUWAR MACE_*💅
_Hafsat Rano_
*1*~ *_MASARAUTA_*💪
_Miss Xoxo_
*1*~ *_NOOR ALBI_*❤🔥
_Mamuhgee_
Guda 1👉300
Guda 2👉400
Guda 3👉500
Guda 4👉700
Guda 5👉1k
*_ZAKU BIYA KUDINKU ANAN👇👇_*
Bilkisu Ibrahim Musa
1487616276
Access bank
Number shaidar biya👇🏼
*_09032345899_*
*KATIN MTN*👇👇
09166221261
__________________
*_JAMA'AR JIGER zaku iya biyan kuɗin littatafan ZAFAFA BIYAR kuma ta nan👇🏼_*
Guda daya=300F
Guda biyu=400F
Uku=500F
Hudu=700F
Biyar=1000F
*ZAKU TURA KATIN WAYA NA (MOOV ko AIRTEL) ZUWA WANNAN NUMBER,TARE DA SHAIDAR BIYA*👇🏼
+227 95 16 61 77
*_TEAM ZAFAFABIYAR🔥🔥🔥🔥_*
_____________________
*_BAƘAR INUWA...👇🏻_*
Da ɗumi-ɗuminsa💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻
Please
*_Follow me_*
*_Share_*
*_Comments_* akan abinda ya shige maka duhu.
_AREWABOOKS, dan zaku dinga samun sabbin pages galla-galla akan lokaci insha ALLAH. Maza garzaya ka karanta naka hankali kwance. Ka kuma yi following ɗina ko dan kar ayi babu kai, da a baka labari gwara ka bayar🥰🥰🤝🏻👇🏻_
*YADDA AKE BUƊE ACCOUNT A AREWABOOKS*
Bayan kaje play store ka ɗakko ya sauka a kan wayarka. Za'a cike Form ɗin kamar haka: -
*Enter your name:* (Cikakken sunanki)
*Enter your mail:* (Email ɗinki)
*Enter an username* (Sunanki)
*Enter your password:* ( misali 12341234)
*Confirm password:* (misali 12341234)
Sai a taɓa *Sign Up* shikenan an buɗe account a ArewaBooks💃🏻😂.
*Continue with Google* - Idan kana da gmail/email akan wayarka kawai Continue with Google za'a taɓa zata buɗe maka account a ArewaBooks kaitsaye.
*Register* - Shine cike form domin buɗe account a ArewaBooks.
*_AREWABOOKS LINK kai tsaye_*
https://arewabooks.com/book?id=620032232dff83519bbad5a3
Masu iPhone
Zaku iya bibiyar shafinmu
https://arewabooks.com
*_Kuzo mu haɗa ƙarfi da ƙarfe domin gyara tafiyarmu. Koba komai ɗan uwanmu ne bahaushe ya zauna ya tsara ya kuma buɗe App... Ɗin domin cigabanmu da jin daɗinmu. Wannan abin alfaharine_.*
*_MARUBUTA DAKE NEMAN ƘARIN BAYANI KO MASU KARATUN MA, ZAKU IYA NEMANMU TA WANNAN NUMBER_*
+234 903 177 4742
_Alkairin ALLAH yakai gareku masoya a duk inda kuke, tare da fatan alkairi muna sonku irin trillions ɗin nan😍😘😍🥰😍😊_.
*_ALLAH ka gafartama iyayenmu😭🙏🏻_*
[7/7, 1:32 PM] NANA: *_Typing📲_*
*_Episode 59_*
.........Bayan kwanaki biyar da wannan magana Bappi ya shirya da kansa yaje har masarautar Bina sukai magana da mai-martaba, sai dai bai sanar da shi ainahin dalilinsu game da sihiri dake tare da Ramadhan ba. Ya nuna masa suyi hakanne kodan gudun abinda zaije ya dawo ga mutanen ƙasa akan kallo da fasararar da zasuma al'amarin. Da yake mutum ne mai fahimta kuma yayi matukar yarda da Bappi a take ya amince ya kuma gamsu. Sai dai ya tsuke bakinsa ko fulani bai tunkara da zancen ba.
Haka shirye-shirye ya cigaba da gudana har biki ya rage baifi saura kwanaki takwas ba. Su gimbiya Su'adah nata shirye-shiryen fara sanarwa a gidajen redio da television Pa ya dakatar. Cikin ɓacin rai ta nema dalili yace idan lokaci yayi zata sani ai. Acan bangaren mai-martaba ma ya dakatar da Fulani da Adda Asmah, dan koda mijinta ya tsawatar shi da yake ya zama mijin tace batajiba, saima tujara data zuba masa gwargwadon iyawa shiko ya sanarma mai-martaba da dama shine ya bashi umarnin shima.
Wannan abu ya cuɗa musu zuciya. Babu kunya Gimbiya Su'adah harda kai karar Pa gaban su Bappi. Anne zatai magana Bappi ya girgiza mata kai, yace Gimbiya Su'adah taje zaiyo magana da Pa. Sai dai har yau da ya rage saura kwanaki biyar basuji komai daga bakin Bappin da suka san zai iya yiwa har mai-martaba magana ya janye sharaɗin daya sharɗanta akan duk wanda yay wani abu babu umarninsu a bakin auren Fulani ne. Tashin hankali kennan da ba'a saka masa rana. Domin kuwa wannan furuci na mai-martaba ya matuƙar birkita kowa a cikinsu har Ramadhan ɗin kansa da Gimbiya Su'adah ta kira a waya ta sanarma komai lokacin yana office. Da wannan ɓacin ran ya tabbatar mata zai shigo gidan da dare dama Bappi nata damunsa da son ganinsa ya sharesa.
*_GOVERNMENT HOUSE_*..
Yau kam da wuri ya shigo gida saboda son zuwa Taura house da anyi magrib. Raudha najin shigowar motocinsa kuwa ta mike daga falo inda suke zaune suna tattauna tsare-tsaren bikin Bilkisu da ayanzu ta zame mata ƙawa dan dama bata da su sai school mate kuma ita iyakarta a gaisa babu aminiya. Saurin riƙota Bilkiau tai ta zaunar. “Ni banga amfanin wannan wasan ɓuyan da kike da shi ba, kiyi zamanki dan ALLAH karma ya samu kafar rainaki dan zai ƙara aure ko ya zata wani kishinsa kike ma”.
Kamar Raudha zatai kuka sai dai komai batace ba ta koma ta zauna ɗin. A haka Ramadhan ya shigo ya samesu.
Akan Raudha ko ya fara sauke idanunsa, itama anyi sa'a kallon nasa take. Lokaci ɗaya zukatansu suka harba cikin bugu mai tsanani. Raudha da taga ya rame mata a ido sosai sai dai ya ƙara haske da ƙyau ta fara janye nata idanun fuskarta na nuna wani yanayi mai wajalar fassara. Shiko ido ya ɗan tsura mata tamkar mai nazari ko kuma yau ya fara ganinta. Sosai ya ga ta ƙara masa girma da cika. Dan duk da ciwo da take fama da shi a watan nan baki ɗaya saita kara buɗewa tai ƙiba da girma. Sannan komai nata ya ƙara girma ga haske tayi sosai mai tafe da wani sirrintaccen ƙyawu da duk hassadar mai hassada bai isa mata kallo guda ya ɗauke ido ba.
Kansa ne yaji ya sara masa. Yay saurin janye idanun a kasalance, sai kuma yay ƙoƙarin barin wajen kamar da ƴar sassarfa dan ko gaisuwar da Bilkisu ke masa bai amsa ba. Ƙofar ya maida ya rufe tare da jingina a jikinta lokcin da ya iso bedroom ɗin nasa. Ya ja ajiyar zuciya da sauke nanauyan numfashi idanunsa har sun kaɗa sunyi jajur. Ya jima a wajen tsaye kafin yaja kafafunsa da ƙyar zuwa toilet, agogon kawai ya cire ya sakarma kansa shower. Sai da yay sharkaf daga shi har kayan dake jikinsa sannan ya ragesu yay wanka....
Raudha da dama a cikin yanayi. dauriya take zaune a wajen ta miƙe da gudu tabar wajen hanunta toshe da bakinta. Da sauri Bilkisu ta bita har cikin toilet data shiga. Amai ta shiga kwarawa tamkar zata amayar da hanjin cikinta. Hankalin Bilkisu ya sake ɗagawa matuƙa ta riƙe Raudha. Sai da komai data ɗanci ya fita tas sannan aka samu lafiya. Bilkisu ta tamaka mata ta gyara jikinta da wajen suka fito tana jera mata sannu.
Cikin sauke numfashi a wahale tana kaiwa kwance ta ce, “Kai aunty B ƙamshin turare nan na Yaya babu daɗi”.
Sosai Bilkisu ta zaro idanu waje, sai kuma tace, “Kutt Aunty Raudha ƙamshin _Boucheron_ ɗinne baida daɗi? Anya kuwa kin shaka dai-dai?”.
“Ni wlhy lafiya lau na shaƙa, kuma dai tun yashe muke zaune a falon na ƙamshin komai bai dameni ba sai daya shigo ne ƙamshin turaren nan mai kama da ka.....”
Da sauri Bilkisu ta ruƙe mata hannu tana dariya, “Uhmm to lallai Taura grandchild bai zo da wasa ba.”
Sam Raudha ba wani fahimtarta tai ba. Bakuma tabuƙaci ba'asin mganar ba tama lumshe ido dan barci ke ɗan figarta ga kanta daya fara ciwo.
*_TAURA HOUSE_*
Cikin matuƙar bayyanar tashin hankali Ramadhan ya ɗago yana duban Bappi da ya gama masa jawabi. A take idonsa ya rufe yama manta da wanda yake tare.
“Gaskiya bazai yuwuba Bappi, duk ma wada yake tunanin sharɗanta hakan ya janye dan ba yarda zanyi ba. Tayama kamar ni za'ace a ɗaura aurena a sirri sai kace wani funafunci? Na muku biyayya na amince da zabinku kukai yanda kuke so nima dole a barni nai yanda nake so akan nawa zaɓin. Sannan maganar events banajin akwai ɗaya da za'a janye a ciki, ba sai kun dinga nuna hassadarku da adawa aka dangin mahaifiyata zan san kun isa da ni b.....”
Ji kake “tauuuu!!” Wani bazafaren mari ya sauka a saman kuncin Ramadhan har sai da ya kifa kamar zai faɗi. Pa da yake a fusace zai ƙara masa Bappi ya dakatar da shi. “No Basheer barsa barsa. Kai Ramadhan mu kake faɗama muna adawa da hassada da dangin uwarka!!”.
Har yanzu hanunsa a saman kuncinsa dan da gaske marin yay matuƙar ratashi. Cikin ƙanƙanin lokaci ya sake birkicewa gaba ɗaya, idanunsa suka rufe ruf. “Idan ba hassada ba a gayamin mi kuke musu? Kun rabani da su komai sai ku, tun ina 2years a rabani da uwata tayi kawaici ta bar muku amma hakan baisa kunga haƙurinta da kawaicinta ba. To wlhy daga yau ku sani ta ƙare, idan kuma kunce a'a to muzuba mu gani!!”.
Ya ƙare maganar cikin ƙaraji da nufar hanyar fita.
Da sauri Pa ya miƙe cikin wani irin fushi yay kansa shima. Sai da Bappi yay azamar riƙo hanunsa yana girgiza masa kai. Duk yanda Pa yaso yin magana Bappi ya hana shi, ganin yanda jikinsama ke rawa sai kawai ya rungumesa yana shafa bayansa murmushi na subuce masa na tsantsar zafin da yakeji a ransa. Da wahala kaga fushin Bappi. Mutum ne mai yawan fara'a da dattako, akoda yaushe fuskarsa ɗauke take da murmushi. Duk abinda kaga faɗansa akai an ƙuresane.
*_GOVERNMENT HOUSE_*
Baƙaramin faɗuwa gaban Raudha dake zaune a gado tana karatu yayi ba. Babu haske mai yawa a ɗakin. ta zabi tai zaman karatu ne kafin lokacin da zata tashi ganawa da UBANGIJI ne. Ta zaro manyan idanunta akan Ramadhan daya shigo a tsananin fusace. “Innalillahi.....” har ƙarshe take ambata a jajjere harya iso inda take, wata irin muguwar damƙa yayma gashinta dake daure a tsakkiyar kai da hanunsa....
“K!! Har kin isa saboda aurenki a hanani yin yanda nakeso akan auren wadda zanyi? Wacece ke? Mikika taka?!.. Wato kinje kin kai munafunci garesu dansu hanani, to ai in gaya miki babu ubanda ya isa. Yau zan tabbatar miki ke ɗin ƙaramar mara kunyace kuwa wlhy...”
Kuka sosai Raudha keji jikinta na tsananin rawa. Ta shiga yarfa hannayenta duka biyu kuka mai ƙarfi na ƙwace mata ganin yana kunce belt ɗin wandon jeans ɗin jikinsa. Abu biyu ta kawo a ranta. Duka ko abinda yay mata ranar, dan haka tai yun ƙurin ceto rayuwarta sai dai hakan ya gagara. Dan tuni ya damƙota ya jefa saman gadon har sai da bayanta ya amsa dan azaba.......
★★★
Ihun Raudha ya matukar tada hankalin Bilkisu da ke ɗaki har barci ya fara daukarta. Ta fito a waje zuwa ɗakin sai dai ta samesa a kulle. Bugawa ta shigayi tana kiran sunan Raudha. Sai dai wata shegiyan ashariya da batasan Yayan nasu ya iyaba sai yau ya mulmulo mata daga ciki. Ai babu shiri tabar wajen a guje. Sai dai koda ta koma ɗaki wayar Anne ta kira. Tana dagawa ta fashe mata da kuka da fara zayyana mata abinda ta sani.
Sosai hankalin Anne da Bappi ya tashi, dan sun san ba kamar yanda Bilkisun ke tunanin Ramadhan dukan Raudha yake ba. Su sun san illolin daya dingama Amnah idan irin wannan ɓacin ran mai tsanani ya riskesa. sai dai suna ƙoƙarin rufe hakan ga kanensa idan ka cire Mardiyya da Safina dakan san wasu a wani lokutan.
Hankali a tashe tsoffi nan suka baro gida a daren nan tare da Dr Hauwa da suka taso itama ta waya suka nufo government house. Dan Dr Hauwa ce ma da kanta taja motar.
Lokacin da suka iso Ramadhan ya riga ya gama illata Raudha har jini ya ɓalle mata. Tunda ya fito a hargitse Bilkisu na son shiga tanajin tsoro. A durkushe suka sameta bakin ƙofar tana kuka. Tana ganinsu ta faɗa jikin Anne ta rungumeta.
“Anne ya kasheta, wlhy ya kasheta Anne!!”.
A tsawace Bappi yace, “Yana ina!?”.
Cikin kuka Bilkisu ta sanar masa ya koma dakinsa. Hakan ya bama Anne da Dr Hauwa damar shiga. Bappi kuma