Showing 99001 words to 102000 words out of 207756 words

Chapter 34 - Bakar Inuwa Book 1 Hausa Novel Complete

17 Dec 2024

647

buƙaci yayi, dan jininsa ya hau sama. Baiso zaman ba sam, sai dai babu yanda ya iya saboda Anne ta saka baki.
     Hutune da basai ƙasa ta san zaije ba, domin zai ɗan iya zartar da wasu ayyuka muhimmai da ga cikin gidansa. A ranar yinin farko Raudha batasan wainar da ake toyawa ba, tunda rabon ma ita data gansa tun randa ya dawo China, shima ta fito ne da dare ɗaukar ruwa sakamakon ruwan fridge nata ya ƙare ta shafa'a bata saka an zuba ba sukai kiciɓus da shi a falo yana haurowa daga stairs ɗin fadarsa. Taɗan daburce a lokacin, dan bataso ya ganta da kayan barcin jikinta ba. Ta shiga masa sannu da zuwa aɗan daburce, dan ga kunyar kaya gata tsareta da yay da idanu. Kusan mintuna biyu suna a hakan kafin yay wucewarsa bedroom ɗinsa ita kuma ta saki ajiyar zuciya ta koma ɗaki da sassarfa, ruwan da bata ɗauka ba kenan. Daga ranar kuma basu sake haɗuwa ba sai dai ta gansa a television.
        A ɓangaren su Basma kuwa washe garin daya dawo daga China duk suka koma gida saboda gimbiya Su'adah ta dawo, hakan sai ya saka Raudha a tsananin kewarsu da damuwa fiye da farko, dan tanajin daɗin zama da bilkisu da Basma ɗin. Su Lubnah kam tun randa ya maidasu sashen baƙi dama sai ta so ma suke ganinta, hakan ya kawo mata sauƙi sosai da cin zarafinsu.
       Bayan tafiyarsu sai ta koma bata da abokin zama sai Mama ladi, tun bata sakin jiki da mama Ladin sosai harta fahimci ƙyawawan halayenta itama. Dan cikin hikima take ɗorata akan abubuwa masu muhimmanci da suka shafi aurenta da zamantakewar mutane fiye ma da yanda Bilkisu ke mata. Kuma Alhmdllhi tana fahimta sosai tare da ɗaura ɗamarar ɗaukar komai.

       Kusan sha ɗaya na safe tana bedroom ɗinta Mama Ladi ta shigo bayan ta nema izini, dan tunda mama Ladi tazo gidan aikin mama tambaya ya koma iya falon ƙasa, dama aikinta kula da ɗakin Raudha da zama mai kusanci da ita fiye da kowa. Kawo mama ladi kuma ya nuna Raudha ta sake ta, hakan yama mama tambaya zafi, har takai ƙara wa iyayen gidanta su aunty Hannah. Amma sai suka lallasheta akan karta damu zasuyi wani abu.
         “Mama akwai matsala ne?”.
Raudha dake duba littafi ta faɗa fuskarta a sake tana duban mama Ladi data shigo bayan ta bata izini.
     Cikin girmamawa tace, “Ranki ya daɗe dama naga su Hajiya Anne ne gaba ɗayansu a gidan nan sai nake tunanin kamar dai babu lafiya”.
        Sosai ƙirjin Raudha ya buga, a ɗan tsorace tace, “Suna ina?”.
      “Basu shigo ta nan sashen ba. Ta can fadar shugaban ƙasa naga anbi dasu”.
      Tunda suka shigo gidan gwamnati bayan wanda sukai mata rakkiya da kawo lefenta su Lubnah ne kawai suka taɓa zuwa gidan a kaf zuri'ar Taura, dan haka Raudha ta tabbatar lallai babu lafiya da gaske. Tun lokacin da yabi da ita ta fadarsa lokacin da zasuje Taura house bai sake ba, amma tsabar ruɗewa batasan ta fita kai tsaye zuwa can ba bayan ta zumbula hijjab har ƙasa da yay mata matuƙar ƙyau kasancewar yanda komai na jikinta ya sake canjawa a yanzu saboda canjin waje da abinci.
       Tana kai ƙafarta step ɗin farko ta tsaya cak sakamakon riƙota da akai. Tsabar bugawa da ƙirjinta yayi batasan ta juyo gaba ɗayanta ba. Kasancewar yana gab da ita sai ta faɗa a jikinsa gaba ɗayanta.
     “Ya ALLAH”.
Ta faɗa a rikice tana son jan jikinta baya...........✍


*_Tsabar gata pags 2 na haɗe muku waje guda👩🏻‍🦯🥹🥹_*



*_Ku garzaya AREWABOOKS ta link ɗin dake sama farkon page, domin samun pages fiye da wanda kuke gani a WhatsApp⛹🏻‍♀️⛹🏻‍♀️😘_*



*_ZAFAFA BIYAR (5) ZAZZAFAR TAFIYA🔥🔥👇👇👇_*


*1*~ *_KUFAN WUTA_*🔥
_Safiyya Huguma_

*1*~ *_BAQAR INUWA_*💥
_Billyn Abdul_

*1*~ *_RAYUWAR MACE_*💅
_Hafsat Rano_

*1*~ *_MASARAUTA_*💪
_Miss Xoxo_

*1*~ *_NOOR ALBI_*❤‍🔥
_Mamuhgee_



Guda 1👉300
Guda 2👉400
Guda 3👉500
Guda 4👉700
Guda 5👉1k


*_ZAKU BIYA KUDINKU ANAN👇👇_*

Bilkisu Ibrahim Musa
1487616276
Access bank

Number shaidar biya👇🏼

*_09032345899_*


*KATIN MTN*👇👇

09166221261
__________________

*_JAMA'AR JIGER zaku iya biyan kuɗin littatafan ZAFAFA BIYAR kuma ta nan👇🏼_*



Guda daya=300F
Guda biyu=400F
Uku=500F
Hudu=700F
Biyar=1000F


*ZAKU TURA KATIN WAYA NA (MOOV ko AIRTEL) ZUWA WANNAN NUMBER,TARE DA SHAIDAR BIYA*👇🏼

+227 95 16 61 77



*_TEAM ZAFAFABIYAR🔥🔥🔥🔥_*

_____________________


*_BAƘAR INUWA...👇🏻_*


Da ɗumi-ɗuminsa💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻

Please
*_Follow me_*
*_Share_*
*_Comments_* akan abinda ya shige maka duhu.

_AREWABOOKS, dan zaku dinga samun sabbin pages galla-galla akan lokaci insha ALLAH. Maza garzaya ka karanta naka hankali kwance. Ka kuma yi following ɗina ko dan kar ayi babu kai, da a baka labari gwara ka bayar🥰🥰🤝🏻👇🏻_


*YADDA AKE BUƊE ACCOUNT A AREWABOOKS*

Bayan kaje play store ka ɗakko ya sauka a kan wayarka. Za'a cike Form ɗin kamar haka: -

*Enter your name:* (Cikakken sunanki)

*Enter your mail:* (Email ɗinki)

*Enter an username* (Sunanki)

*Enter your password:* ( misali 12341234)

*Confirm password:* (misali 12341234)

Sai a taɓa *Sign Up* shikenan an buɗe account a ArewaBooks💃🏻😂.

*Continue with Google* - Idan kana da gmail/email akan wayarka kawai Continue with Google za'a taɓa zata buɗe maka account a ArewaBooks kaitsaye.

*Register* - Shine cike form domin buɗe account a ArewaBooks.


*_AREWABOOKS LINK kai tsaye_*

https://arewabooks.com/book?id=620032232dff83519bbad5a3


Masu iPhone

Zaku iya bibiyar shafinmu
https://arewabooks.com

*_Kuzo mu haɗa ƙarfi da ƙarfe domin gyara tafiyarmu. Koba komai ɗan uwanmu ne bahaushe ya zauna ya tsara ya kuma buɗe App... Ɗin domin cigabanmu da jin daɗinmu. Wannan abin alfaharine_.*


*_MARUBUTA DAKE NEMAN ƘARIN BAYANI KO MASU KARATUN MA, ZAKU IYA NEMANMU TA WANNAN NUMBER_*

+234 903 177 4742


_Alkairin ALLAH yakai gareku masoya a duk inda kuke, tare da fatan alkairi muna sonku irin trillions ɗin nan😍😘😍🥰😍😊_.




*_ALLAH ka gafartama iyayenmu😭🙏🏻_*
[6/23, 8:36 PM] NANA: *_Typing📲_*







*_BAƘAR INUWA👉🏻AREWABOOKS👇🏻_*

https://arewabooks.com/chapter?id=62b35fdfcfb019e4836d06fe


*_Episode 34_*


..........Bai bata wannan damar ba, sai ma saurin riƙota da yay ya tallafe da hannunsa da ƙyau, dan ya tabbatar dabai mata hakan ba zata iya zamewa a samu matsala. Karan farko, a kuma lokaci na farko da hakan ta faru.
     “Relax”.
Ya faɗa cikin wata irin muryar data nema gusar da hankalin Raudha, maimakon ta samu nutsuwar daya ambata. Ganin ba nutsuwar zatai ba ya juyata ya jingina da jikin glass da akai kwalliyar stairs ɗin da shi. Sai dai har lokacin tana a jikin nasa. Numfashi taja da ƙyar, ta haɗiyi kakkauran yawun daya kasa gusar mata da bushewar maƙoshin data riski kanta a ciki, tsahon minti guda da wasu sakanni bai sake magana ba yana kallonta kawai, sai da ya ɗanga numfashinta ya dai-daita ya janye jikinsa a nata ya matsa baya kaɗan. Hannayensa ya zura cikin aljihu duka yana furzar da ƙaramar iska shima a bakinsa.
       “Miya faru?”.
Ya faɗa idanunsa na cigaba da yawo akan ƙyaƙyƙyawar fuskarta da har yanzu take a ɗan firgice. Kanta ta girgiza masa, ta lalubo amsa da ƙyar da ga ƙwalwarta zuwa harshe.
      “Ba komai, kawai naji ance su Anne sun zo ne”.
          Shiru baice komai ba, sai dai har yanzu idonsa kafe a kanta. Jin shirun ya sata ɗan ɗagowa da tunanin ko baya tare da itane? Duk da kuwa tanajin tasirin kaifin idanunsa a kanta. Janye idanunsa yay cike da basarwa ya maida downstairs duk da baya iya hango su Annen sai hayaniyarsu sama-sama.
        “Ni sukazo dubawa”.
Ya faɗa har yanzu idonsa a downstairs.
      Cikin subutar baki da waro idanu Raudha tace, “Baka da lafiya ne?”.
     Yanda tai maganar kanta tsaye, da waro idanunta farare tas ya matuƙar tada tsigar jikin sa. A gefe kuma taso bashi dariya amma sai ya gimtse. Takawa ya ɗan ƙarayi gabanta, ta matsa baya tana sake mannewa da glass ɗin. Hannunsa ɗaya ya ɗaura jikin glass ɗin gab da ita, ɗayan na cikin aljihunsa bai cire ba. Ya ɗan ranƙwafo kanta yanda har tana iya jin saukar numfashinsa a saman fuskarta.
     “Kin damu dani ne balle ki sani?”.
(Ya ALLAH) Raudha ta ambata a cikin ranta, dan kaɗan ya hana zuciyarta yin tsalle ta fito ta bakinta daga ƙirji.
     “D...dan ALLAH kayi haƙuri”.
Ta faɗa kamar zata fashe da kuka, duk da idanunta a rumtse suke.
    Karon farko Ramadhan ya saki wani ɗan guntun murmushi da lumshe idanu ya sake buɗewa a kanta, tare da sake kusanta fuskarsa da tata. A bazata ya sauke lips nashi a kan nata ya sumbata.
Gaba ɗaya ta waro masa idanunta baki a hangame jikinta na tsuma. Wata ƴar shaƙiyyar dariya yayi yana sake maida lips ɗin nasa saman nata ya tsotsa. Sai kuma ya janye ya ɗan ɗallesu da yatsansa manuniya har yanzu fuskarsa ƙayace da murmushin da bata taɓa sanin ya iya ba
“Ustaza ana so ana kaiwa kasuwa”
Ya faɗa cikin raɗa da ɗan rungumota jikinsa. Jin numfashinta kamar yana barazanar ɗaukewa ya sashi sake sakin murmushin mai faɗi ya janye jikinsa ga baɗaya ya bata iska. Aiko sai ga Raudha da sakin wata wawuyar ajiyar zuciya da ita kanta sai da taji kunyar kanta.
    Bai sake cewa komai ba ya nuna mata hanyar downstairs ɗin alamar suje. Kasa kallonsa tayi, bakinta kuma ya gagara furta komai balle tace masa wani abu, kai ji take ma kamar ta zama matatta dan bata gane komai😹🤭...

        Kusan gaba ɗayansu suka zubo musu ido lokacin da suke sakkowa. Duk da kan Raudha a ƙasa yake sai da taji kaifin idanunsu a jikinta. Dama gashi mai gayya mai aikin ya gama sukurkuta mata rayuwa a sama. Dan har yanzu zuciyarta bata bar luguden daka akan abinda ya faru ba.
       Anne, Bappi, Pa kallo guda sukai musu suka ɗauke zukatansu fes da farin ciki, hakama fuskokinsu ɗauke da murmushi. Gimbiya Su'adah ma dai a kallo gudan ta ɗauke idanunta cike da takaici da sakejin tsanar Raudha, dan ji take kamar ta kunna mata wuta ta babbaka banza. Hajiya Mufida da Hajiya Shuwa kuwa tsantsar kishi ne sosai a ransu. Yayinda sauran yaran mafi yawa babu komai a ransu sai ɗan abinda ba'a rasaba na ƴan ubanci da shakkar Ramadhan ɗin a tare da su. Sai ko su Lubnah dake zubama Raudha kallon tsantsar tsana a kaikaice.
      Rufaidah da Basma and Fadila suka taso suka rungume Raudha bakunansu kamar gonar audiga....

       Cikin nutsuwa Raudha ta kai duƙe gaban Bappi da Anne ta gaishe su. Fuskokinsu cike da fara'a dajin ƙaunarta suke amsawa. Suka ɗora da tambayar ya jikin mijin nata?. Kanta a ƙasa ta amsa musu kafin ta koma gaishe da Pa shima, shima dai ya amsa mata da kulawa yana tambayar jikin Ramadhan ɗin. Nanma dai kanta a ƙasa ta amsa fuskarta dai da ɗan murmushin girmamawa wanda yake sukar zuciyar gimbiya Su'adah matuƙa. Dan koda Raudha ta gaishe ta da ƙyar ta amsa. Bakuma ta tambayeta jikin Ramadhan ɗin ba. Dan a ganinta Raudha bata isa ba.
        Raudha dai ba kallonta take ba, sai dai a ranta tanajin shakkar uwar mijin nata da take hango ɗunbin tsana da ƙyamar da take mata ƙiri-ƙiri. Ta gaishe da su Hajiya Shuwa ma. Sukam cike da bariki suka amsa ma Raudha ɗin da kulawa suna tambayarta jikin Ramadhan. Sauran yara kuwa ta gaida wanda suka girmeta, yayinda su Lubnah suka basar da ita itama sai tayi kamar bata gansu ba ta wayance da amsama Anne tambayar da ta jeho mata akan Ramadhan ɗin na kula da shan maganinsa dai ko?.
        Raudha ta ɗan saci kallon inda ya ke zaune cikin kujerar dake gab da Bappi. Ido suka haɗa, tai azamar janye nata tana fafutukar nemo amsar data dace ta bama Anne.
       “Oh Anne, har yanzu dai kina ɗaukata wani baby doll na lura?”.
      Yanda yay maganar a ɗan narke ya saka Bappi da Anne darawa. Pa yay murmushi kawai, dan kowa yasan ƙaunar dake tsakanin Ramadhan dasu Anne sai dai ALLAH yasan iyakarta. Hanunsa Bappi ya kamo cikin nasa har lokacin fuskarsa da murmushi mai faɗi. “Gaskiya ka girma kam, kai da ke shugabantar babbar ƙasa irin NAYA ai ka wuce doll”.
       “Yauwa Bappi na dama nasan yanzu munfi shiri” Ya ƙara faɗa a narke.
              Mikewa Raudha da abin ya nema girman kanta tai, karon farko na rayuwarta ta koma sashenta domin bada umarnin shirya abinci. Amma rashin sanin yanda tsare-tsaren suke yasata neman mama tambaya. Mama tambaya ce tai mata bayanin wannan alhakin shugaban ma'aikata ne. Shine yasan tsarin aikin na kowanne ɓangare a gidan.
     Babu jimawa aka nemo mata shi. Ya iso gabanta cike da girmamawa duk da kuwa babban mutum ne. Amma mulki sha'aninsa daban ne ai. Ta masa bayanin abinda take buƙatar ayi. Ya tabbatar mata cikin girmamawar da harga ALLAH kunya take bata. Sai dai babu yanda zatayi tunda ga'a inda ta tsinci kanta bisa alƙalamin ƙaddara.

     Cikin ƙanƙanin lokaci aka kammala cika umarnin Raudha da tuni ta koma wajen su Anne. Duk da tasan basuzo da yunwa ba dai ta saka an shirya musu abubuwan motsa baki kala-kala domin karramawa. Sai fruits da kayan sha. Dan danan falon ya kaure da ƙamshin abubuwa. Har cikin rai Ramadhan yaji daɗin abinda tayi, hakama Anne ta sakejin ƙaunar yarinyar a ranta matuƙa.
      Kowa ya ɗan taɓa wani abu, idan ka cire gimbiya Su'adah dako ruwa bata kurɓa ba. Sai ma sake miskile fuska da tai tanta harare-harare. Sam Ramadhan baiji daɗin yanayin nata ba, gashi yasan haushinsa takeji tun akan abinda yay ma su Lubnah dan bai yarda sun haɗu ba tunda suka dawo da ga London. Sannu da zuwa ma ta waya yay mata duk da yaje Taura house ɗin har sau biyu a sirrance. Dan na farko ko Anne ma batasan yaje ɗin ba.

        ★★

  Bayan wucewar su Anne Raudha da tai musu rakkiya ta dawo, bata sameshi a falon ba, dan haka ta haura sama itama, a ranta tana ganin ya kamata shima ta haɗa masa wani abun tunda taga baici komai a abinda aka ajiyema su Anne ba. Tsaye ta samesa a falon saman yana amsa waya, ɗan dakatawa tai ya kammala sannan. Kanta a ƙasa dan har yanzu matsananciyar kunyarsa ce ke dawainiya da ita.
       “Naga bakaci komai ba, ko kana bukatar wani abu?”.
        Mikewa yay batare da yace komai ba. Dan hankalinsa ma gaba ɗaya yana kan waya da alama akwai abinda yake nema. Sai da ya ɗanyi nisa da ita yace, “Biyoni da shi ciki”.
     Ƙirjin Raudha ya harba ganin ya nufi hanyar bedroom ɗinsa, dan tunda randa ta kai masa kuɗin nan bata tunanin ta sake ko kallon sashen, balle tai sha'awar shiga ɗakinsa wataran. Cikin dauriya da bin umarni ta amsa da “To” tana mikewa ta wuce downstairs ɗin dan sama masa abinda zaici ɗin. Samun kuku da tai tare da mama ladi ya bata ƙwarin gwiwar haɗo abinda ya dafa na lunch wanda tasan zai masa daɗin ci matsayin mara lafiya, tasan dai mama ladi bazatayi sakacin da za'a cutar da shi ba a gabanta.
       Ɗauke da basket ɗin data shiryo abincin ta shigo falon, kai tsaye tabi bayansa duk da zuciyarta na lugude har yanzun. Sai da tai knocking sau biyu ta ɗan dakata duk da bataji motsi ba. Lokacin da'aka murza handle ɗin ƙofar sai da ta rumtse ido hanjin cikinta na juyawa. Ta ɗan zabura baya tare da daburcewa ganin da ga shi sai towel alamar wanka ya fito ma. Komai baice mata ba ya saki ƙofar ya juya ciki. Sam kasa shiga tayi, ta cigaba da tsaiwa a wajen har sai da yay magana.
     “Akwai dodo ne a ɗakin?”.
   Da ɗan rawar baki ta ce, “Am sorry”.
Bai sake tankawa ba hakan yasa cikin sanɗa kamar wata ɓarauniya ta shigo kanta a ƙasa. Wani irin mayatattun ƙamshin turare kashi-kashi suka fara rige-rigen afka mata cikin hanci. Ta ware manyan idanunta laɓɓanta dake motsawa a hankali na ambaton kalmar “Masha ALLAH”. Dan kuwa duk haɗuwa da tsaruwar ɗakinta da take gani sai ta gansa ba komai ba akan wannan, dan ma ta kasa kallon ko'ina yanda ya kamata. Amma duk da haka ɗaki ne kam da zaman lissafin tsarinsa ma ɓata lokacine. Abinda kawai za'a iya faɗa shine ALLAH ka gafarta mana ka azurtamu da aljanna maɗaukakiya.
       Da ƙyar Raudha ta iya ɗaga ƙafa ta ƙarasa ga wasu haɗaɗɗun royal chairs farare tas da adon pitch kaɗan-kaɗan ta ajiye basket ɗin saman centre table dake tsakkiyarsu. Ga wani lumbutsetsen Turkish carpet da laushinsa ba'a magana. 
      Ramadhan dake tsaye gaban mirror yana gyara jikinsa duk yana kallonta, a duk lokacin daya ganta a yanayin kunya irin wannan sai zuciyarsa tai ta kaikawo akan tambarin karuwanci da akace ahalinta na da shi. Yana son mace wayayya kuma mai shekarun dake gab da nashi, dan haka yake kallon mace mai ƙarancin shekaru ba'a tsarinsa ba, sai dai akan Raudha zuciyarsa ta fara kokwanto da saƙa masa kalmar wauta a ra'ayin nasa, duk da kuwa shi bazai iya cewa komai game da wani abu akan Raudha na so ko makamancin hakan ba.
        Ya ɗan yatsine fuska da ɗaukar t-shirt fara ƙal da ya ajiye ya saka a jikinsa, sai wando three quarter da baima gama kaimasa gwiwa ba shima ya saka cike da rashin damuwar Raudha na ɗakin. Kodan yaga ta juya masa baya ne oho masa.

        Sayun takowarsa wajen ya saka Raudha dake bin ɗakin da kallo har yanzu ɗauke idonta ta sake nutsuwa. Ya kai zaune a kujerar dake facing wadda take zaune, yanda baiyi magana ba itama batai ba, sai sakkowa da tai ɗan gabansa ta fara cire kwanikan da ga basket ɗin. Bayan ta bubbuɗe ta nema zaɓinsa akan abinda zai ci.
    “Duk wanda yay miki saka”.
Ya bata amsa a taƙaice hankalinsa nakan canja tasha a television. Ƙundunbala tai ta zuba masa wanda yay mata ɗin, bayan ta kammala ta koma ta zauna inda ta taso saboda tunawa da dokarsa ta ranar. Sai da ya shanye kusan 2minutes sannan ya ajiye remote ɗin

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login