Showing 102001 words to 105000 words out of 207756 words

Chapter 35 - Bakar Inuwa Book 1 Hausa Novel Complete

17 Dec 2024

623

ya ɗauka spoon yana mai ƙurama abincin ido kamar mai son gano muninsa ko daɗinsa.
      Ramadhan mutum ne mai tarin nutsuwa akan komai. Girman kai da yawan mutane ke kallonsa da shi yasa komansa zaka iya masa kallon yanayinsa da isa ne irin ta waɗanda suka isa. Cin abincin yake tamkar bayaso, duk da ma yafi maida hankalisa ga nama. Sai da yay nisa da cin abincin harma ya kusan gamawa da naman ciki (wayaga kure🤣), sannan ya ɗan ɗago ya dubi Raudha da hankalinta ke akan tv.
      “Bismillah”.
   Ya faɗa a daƙile kamar an masa tilas.
      Juyowa Raudha ta ɗanyi ta kallesa, dan batai tunanin da ita yake ba. Da ido ya mata nuni da abincin, hakan ya sata itama kallonta ya sauka akan kwanon naman. Batare da tasan tayi ba ta ɗan tura baki gaba alamar sai da ka cinye naman.
     “An gaya miki duk mutuncin da nake da mutum ina masa ƙyautar nama ne”.
       Raudha tai saurin janye idanunta jin ya mata fassara daban, ga dariya data taho mata a bazata tanata ƙoƙarin kare bakinta da hannu, domin son kore tunaninsa tai sauri cewa, “Ni ama ƙoshe nake, nagode”.
       Kafaɗa ya ɗan ɗaga da taɓe baki irin na I don't care. Daga haka ya ɗan ƙara abincin ya ture yana goge bakinsa da tissue da ambaton Alhmdllhi.
    Bayan Raudha ta gama tattare kwanikan da nufin kama gabanta ya dakatar da ita.
     “Ɗauka min abu a cikin bedside drawer ɗin can.”
    Babu musu tabi umarninsa. Bedside ɗin da taga ya kalla ta nufa. Ta buɗe drawer ɗin wajen, takardu kawai ta gani, dan haka ta kwasosu ta dawo. Koda ya amsa sai ya buɗe file ɗin da suke ciki ya zaro guda ɗaya ya turota gabanta akan centre table ɗin. Ɗan dakatawa tai da ga kwashe kwanikan da take, ta kalli takardan sannan ta ɗan ɗago ta dubesa dan neman ƙarin bayani. Hankalinsa akan sauran takardun yake. Ƙundunbala tai ta ɗauka ta duba, jikinta ne kawai ya kama rawa, ta ɗago ta kallesa, ta sake maidawa ta kalli takardar. Tayi haka yafi sau biyar, dan ta rasa abin faɗa. Ruɗani ta shiga ko farin ciki ne yay mata yawa?, abinda ta daɗe da fidda ran samu, abinda zuciyarta ta daɗe da jaddada mata yay mata nisa... Cikin wani irin slow ta zamo a kujerar ta durƙushe gabansa hawaye na sakkowa saman kumatunta a hankali. Tabbas da ace bashi ɗin bane yau a gabanta babu abinda zai hanata daka tsalle ta rungumesa...
          Ƙafafunsa dake harɗe ya ɗan motsa yana mai zuba mata mayatattun idanunsa. Farin cikin data tsinta kanta a ciki ya hana tasirantuwar kallon nasa gareta.
       _“Ina roƙon ALLAH ya azurta zuciyarka da tarin farin ciki fiye da wanda ka sakani a yanzu. ALLAH ya baka ikon sauke nauyin al'umma dake kanka, ya kareka da duk wani abin ƙi na zahiri dana ɓoye. ALLAH ya ɗauraka a saman maƙiyanka kai da zuri'arka baki ɗaya. ALLAH ya cika maka burikanka na alkairi ya ƙyautata maka da sakamakon aljannah a ranar da ita kaɗaice abar kishirwa ga kowanne irin rai”._
      Tunda yake, tunda yazo duniya, ko yace tunda ya mallaki hankalin kansa a rayuwa, wani mahaluki bai taɓa masa makamanciyar addu'ar nan ba. Saboda shi mutum ne da idan yay alkairi baya taɓa zama a wajen dan jiran a gode masa ko a yabesa. Baya son yawan yabo a gaban ido, yayi imani da yana iya sakama mutum fara aikin riya, dan yabo na saka shauƙi a zuciyar wanda akaimawa da tunzurawar shaiɗan a wani lokacin. Ya lumshe idanunsa a hankali na kusan mintuna biyu. Sai kuma ya buɗesu a kanta. Komai baice ba sai nuni da yay mata da hannu alamar ta koma saman kujera. Batai musu ba ta miƙe ta koma, kwalin tissue dake a centre table ɗin yasa ɗan yatsa ya turashi gabanta.
        Anan ɗin ma bata musaba ta zara ta goge fuskarta tas tana haɗiyar zuciya. Tsahon wasu mintuna ɗakin ya ɗauka shiru, sai jan numfashinta kaɗan-kaɗan irin na wanda yay kuka. Tsam ya miƙe daga inda yake zaune, hakan yasa Raudha sake maida kanta ƙasa saboda kunyar wandon jikinsa. Duk da ya fahimci hakan sai bai maida kai ba, ya taka a hankali ta bayan kujerar da take zaune, kamar zai wuce sai kuma ya tsaya a dai-dai saitinta.
         A bazata, cikin rashin tsammani Raudha taji saukar numfashinsa ta gefen fuskarta, alamar ranƙwafowa yay ta bayan kujerar. Sosai ta daburce, jikinta ya fara tsuma dan tun asali ta riga ta sakama ranta tsoron kusanta kanta da wani namiji saboda kare kanta daga faɗawa tarkon lalacewa, ta wani gefen kuma mamakinsa na sake dilmiyata a ruɗani, dan abubuwan da yake matan basu tai tsammani ba, basu ta hanga cikin idanunsa kafin aurensu ba, bata tunanin shima ɗin su yay mata tanadi, to miya canja shi? Kodai yana zargin akwai masu son amfani da ita domin cutar da shi? Kodai?.. Kodai?... Harma ta rasa lissafin da zatayi saboda tasirin da saukar numfashinsa ke mata a dokin wuya yana tada mata tsigar jiki da yamutsa jinin jikinta.
         Ramadhan da ke lure da yanayin nata, ya basar abinsa, dan kuwa da gaske tunanin Raudha na kamanceceniya da wani ƙulli dake a ransa tun farko. Koya faɗa ko karya faɗa tabbas zuciyarsa bata yarda da ita ba kafin yau, shiyyasa yake binta matakin da ya tsara domin tabbatarwa (Humm da alama wajen gwaji za'a gwaje shugaba ƙasa😉lol).
      Cikin magana kamar raɗa yace, “Miye tukuyci na?”.
       Hannayenta ta matse cikin juna, dan yanda yay maganar cikin kunnenta tsigar jikinta ba ƙaramin yamutsawa tai ba, ga yawu kaɗan ya rage ya sarƙe mata numfashi. Taso jan jikinta gefe sai dai ya hana hakan ta hanyar zagayowa gefen damarta, kasancewar har yanzu a ranƙwafen yake sai yay mata runfar da ko numfashi ta kasa saki da ƙarfi. Gara ɗazun kujera ta musu katanga, yanzu ko hanunsa ma ɗaya idan tace jikin kujerar zata manne a kansa zata kwanta, ta gaba kuma ya tare ko ina. Sai kawai taji ƙwalla sun sake ciko mata ido. Maganar take sonyi amma ta kasa, sai laɓɓanta ke ɗan motsawa kaɗan-kaɗan.........✍


*_Ku garzaya AREWABOOKS ta link ɗin dake sama farkon page, domin samun pages fiye da wanda kuke gani a WhatsApp⛹🏻‍♀️⛹🏻‍♀️😘_*



*_ZAFAFA BIYAR (5) ZAZZAFAR TAFIYA🔥🔥👇👇👇_*


*1*~ *_KUFAN WUTA_*🔥
_Safiyya Huguma_

*1*~ *_BAQAR INUWA_*💥
_Billyn Abdul_

*1*~ *_RAYUWAR MACE_*💅
_Hafsat Rano_

*1*~ *_MASARAUTA_*💪
_Miss Xoxo_

*1*~ *_NOOR ALBI_*❤‍🔥
_Mamuhgee_



Guda 1👉300
Guda 2👉400
Guda 3👉500
Guda 4👉700
Guda 5👉1k


*_ZAKU BIYA KUDINKU ANAN👇👇_*

Bilkisu Ibrahim Musa
1487616276
Access bank

Number shaidar biya👇🏼

*_09032345899_*


*KATIN MTN*👇👇

09166221261
__________________

*_JAMA'AR JIGER zaku iya biyan kuɗin littatafan ZAFAFA BIYAR kuma ta nan👇🏼_*



Guda daya=300F
Guda biyu=400F
Uku=500F
Hudu=700F
Biyar=1000F


*ZAKU TURA KATIN WAYA NA (MOOV ko AIRTEL) ZUWA WANNAN NUMBER,TARE DA SHAIDAR BIYA*👇🏼

+227 95 16 61 77



*_TEAM ZAFAFABIYAR🔥🔥🔥🔥_*

_____________________


*_BAƘAR INUWA...👇🏻_*


Da ɗumi-ɗuminsa💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻

Please
*_Follow me_*
*_Share_*
*_Comments_* akan abinda ya shige maka duhu.

_AREWABOOKS, dan zaku dinga samun sabbin pages galla-galla akan lokaci insha ALLAH. Maza garzaya ka karanta naka hankali kwance. Ka kuma yi following ɗina ko dan kar ayi babu kai, da a baka labari gwara ka bayar🥰🥰🤝🏻👇🏻_


*YADDA AKE BUƊE ACCOUNT A AREWABOOKS*

Bayan kaje play store ka ɗakko ya sauka a kan wayarka. Za'a cike Form ɗin kamar haka: -

*Enter your name:* (Cikakken sunanki)

*Enter your mail:* (Email ɗinki)

*Enter an username* (Sunanki)

*Enter your password:* ( misali 12341234)

*Confirm password:* (misali 12341234)

Sai a taɓa *Sign Up* shikenan an buɗe account a ArewaBooks💃🏻😂.

*Continue with Google* - Idan kana da gmail/email akan wayarka kawai Continue with Google za'a taɓa zata buɗe maka account a ArewaBooks kaitsaye.

*Register* - Shine cike form domin buɗe account a ArewaBooks.


*_AREWABOOKS LINK kai tsaye_*

https://arewabooks.com/book?id=620032232dff83519bbad5a3


Masu iPhone

Zaku iya bibiyar shafinmu
https://arewabooks.com

*_Kuzo mu haɗa ƙarfi da ƙarfe domin gyara tafiyarmu. Koba komai ɗan uwanmu ne bahaushe ya zauna ya tsara ya kuma buɗe App... Ɗin domin cigabanmu da jin daɗinmu. Wannan abin alfaharine_.*


*_MARUBUTA DAKE NEMAN ƘARIN BAYANI KO MASU KARATUN MA, ZAKU IYA NEMANMU TA WANNAN NUMBER_*

+234 903 177 4742


_Alkairin ALLAH yakai gareku masoya a duk inda kuke, tare da fatan alkairi muna sonku irin trillions ɗin nan😍😘😍🥰😍😊_.




*_ALLAH ka gafartama iyayenmu😭🙏🏻_*
[6/24, 7:59 PM] NANA: *_Typing📲_*







*_BAƘAR INUWA👉🏻AREWABOOKS👇🏻_*

https://arewabooks.com/chapter?id=62b5bb45fa0b02c20d2788dd


*_Episode 25_*


.........Shi dariya ma ta bashi, amma sai ya dake abinsa, duk da ya fahimci kusancinsu ne matsalarta yaƙi kuma janye jikin nasa.
      “Kin zama kurma ne?”.
Da sauri ta girgiza kanta, tana ɗan matse jikinta waje guda..
   “Mikake so?”.
       Ta faɗa da rawar harshe.
Karan farko ya saki wani guntun murmushi dashi kansa a ƙarjinsa kawai yaji abinsa. Sai kuma ya miƙe da ga kanta ya taka zuwa kujerar gefenta ya zauna. Wayarsa dake faman vibration ya ɗauka, a yanda yake magana zaka fahimci mai muhimmanci ce, sai dai kuma ɗan walwalar dake kan fuskar tasa ya ida ɓacewa gaba ɗaya. Sunan Maa da taji ya ambata ya tabbatar mata da gimbiya Su'adah ce, kusan mintuna uku ya ajiye wayar batare da ta bashi damar yin wata kwakwkwarar magana ba. 
    Lip ɗinsa na ƙasa ya tura cikin baki da ƙarfi ya shiga taunarsa, yarasa miye manufar Maah ɗin na zuwan su Lubnah gidan su zauna. Abin takaicin ma a yanzu harda sharaɗin kar'a kuskura a ajiye mata yara a sashen baƙi. Dolene yaci uban yaran nan gwargwadon iko a wannan karon, dan zai saka musu ido sosai tare da abinda ko tace suzo zasuce a'a
        
                ★Ganin yanda yanayinsa ya canja zuwa ɓacin rai sosai ya saka Raudha da zuciyarta har yanzu ke kai kawo ɗan duban agogon ɗakin. A ɗan ɗarare ta ce, “Zanje nayi salla, magrib tayi”.
            Komai baice mata ba, sai dai ya kafeta da ido tamkar mai son gano maganin takaicin da Maah ta cusa masa yanzu a jikinta.
       Kanta ta duƙar ƙasa, wani ɓangare na nasihar Anne da Mummynsu na mata kaikawo a zuciya. _(Idan kin gansa cikin fushi, koda bake kika ɓata ransa ba ki faɗa masa magana mai daɗi da zata kore fushin nasa koda bazai saurareki ba. Idan har kika gusa a wajen zai maida hankali ga maganarki kuma fushinsa ya kwaranye, kimarki ta sake girma a idanunsa har yaji wataran kece kikafi kowa cancanta daya tunkara da matsalolinsa)._ Ɓoyayyen numfashi taja a hankali, zuciyarta na sake tunzurata akan gwadawa koda bazai kulatan ba. Kallonsa taɗan sata, ganin yanda ya lumshe idanu yana faman taunar lip data fara fahimtar ya zame masa ɗabi'a yasata haɗiyar busashen yawun da ya tokare maƙoshinta.
       _“A kowanne lokacin haƙuri shike kwaranye abinda zuciya bataso ba. koda ɗacinsa yafi ƙarfin ƙwaƙwalwa”._
        Raudha ta faɗa cikin matuƙar dauriya da ƙundunbala. Bakuma ta jira amsa ba ta kwashi kwankan da admission latter ɗin da ya bata ta kama hanyar fita a ɗakin cikin sassarfa, zuciyarta na luguden daka kamar zata fito. Dan sam batai tunanin zata iya faɗa masa maganar data faɗa ɗin ba yanzu sam.
         A hankali ya buɗe idanunsa da suka canja launi ya zuba mata, harta fice a ɗakin bai iya koda motsawa ba. Abu biyu ke masa kaikawo a rai. _Mamakinta_ da kuma _Ƙarfin halinta_.

         Raudha kam koda ta koma ɗaki bayan ta idar da salla admission ɗin ta sake ɗauka ta duba sosai, sai lokacin ta sake samun damar fara tsallen murna dariya na suɓuce mata da hawaye a lokaci guda. Inama tanada waya ta kira Mummy ta sanar mata, kai harsu Fatisa da Abbansu ma da duk saita faɗawa.
     Bata sake bi takan Ramadhan ba, sai dai ta kasance cikin ɗunbin farin cikin daya bata a wannan dare. Washe gari batai ganda ba ta shiga kitchen da taimakon mama Ladi da kuku suka shirya breakfast, dan bata san yau ma ba fita zaiyi ba. Ɗaki ta koma tai kwanciyarta dan murna bata bari tai barcin arziƙi ba jiya da dare. Sosai tasha barci, dan sai wajen sha biyu ta tashi. Wanka ta shiga bayan ta kimtsa ɗakin, tana tsaka da shiryawa ta samu saƙo daga mama ladi cewar tanada baƙi. Yin baƙi yanzu ba baƙon abu bane a gareta, dan haka ta canja akalar shirin nata datai niyya da doguwar rigar jallabiya ta sanya lass.
        Tuni Mama tambaya ta musu masauki da tarbar data dace da su, dan kuwa aunty Hannah ce matar vice president da wasu hamshaƙan mata su kusan shidda. Tabbas duk sun girmeta da finta wayewar rayuwa. Amma itama zama da Mama ladi da Mama tambaya ga huɗubar Bilkisu Da Anne data samu, ga wadda su aunty Hannah suka saka a mata tunkan ta shigo gidan yasa zuwa yanzu indai dressing ne baza'a nuna mata komai ba. A ɓangaren nutsuwa kuwa dama kowa yasan Raudha Alhamdulillahi bata da matsala tanan. A gefe kuma duk abinda ya haɗa da aunty Hannah *_TAKUN SAƘA_* take masa, dan karku manta a fuska Raudha yarinyace mai haƙuri, sai dai su aunty Hannah basu taɓa tunanin murɗaɗɗen haline da ita a baɗini ba.
          Da sallama suka shigo falon guards ɗinta da mama tambaya da mama ladi na take mata baya. (Tabbas Raudha first lady ce da jinta yafi ganinta). Ta kai zaune fuskarta ɗauke da ƙayataccen murmushi, ƙasan zuciyarta ɗauke da addu'a.
       “Mom barkanku da zuwa”.
Ta faɗa idonta akan Aunty Hannah dake mata kallon mamaki. Dan wani ƙyau da cikar kamala Raudha ta sake mata har da ƙiba. Ga wani buɗewa da taga idonta ya ƙarayi. (Da alama yarinyar nan tasan namiji zuwa yanzun) Aunty Hannah ta rayama ranta dan a tunaninta sanin namiji ga ɗiya mace shike sake buɗe kanta da idanu. Murmushi ta saki na basarwa ta amsa Raudha ɗin cike da tsantsar kulawa.
      “Oh my baby kodai nayi jika ne? Irin wannan ƙyawu haka?”.
    Kunya ce ta kama Raudha, amma sai ta dake ta saki murmushi kawai batare da tace komai ba. Sauran matan dake ɗan darawa suka shiga faɗin ashe munada gagarumin biki kuwa. Nanma dai komai Raudha batace ba, sai murmushin dake fuskarta da har yanzu bai gushe ba. Har suka taɓa ɗan barkwancinsu kuma bata tsoma baki ba, dan dukansu a haife sun haife ta, mutum ɗaya a cikinsu zata iya kira da yaya dan ita bata kaisu shekaru ba.
        Bayan sun ajiye barkwancin nasu a gefe aka gaisa a mutunce, Raudha bata bada wata ƙofar da wani aciki zai amfani da ƙarancin shekarunta ya kawo mata raini ba koda a magana ne. Aunty Hannah ce tai mata bayanin dukansu matan ministoci ne, sunzo ne domin yin godiya a gareta da miƙo gaisuwa ga shugaban ƙasa.
     Raudha ta ɗan jinjina kanta, cike da nutsuwarta da salon jin kai da aunty Hannah ke ganin kamar Raudha ta fara take binsu da kallon ƙasan ido. Sai da taja kusan mintuna biyu kafin ta fara magana.
      “Muma muna godiya da ziyara, ALLAH ya bar zuminci. Shugaban ƙasa kuma zaiji saƙon gaisuwarku”.
       A kaikaice aunty Hannah ta ɗan waro ido waje, ta shiga ƙyaftama Raudha idanu amma sai Raudha ta basar da ita tamkar ma bata lura ba. Ganin haka aunty Hannah ta miƙe tana faɗin, “Ya kamata kuɗan taɓa wani abu ko, bara uwa da ƴa su zuge labule”.
       Murmushi duk suka saki, dan tuni ta riga ta gama baza musu alaƙar dake tsakaninta da Raudha, kuma kamanin da suka gani tsakaninta da Raudhan ma ya sake tabbatar musu da haka. Kamar Raudha bazata miƙe ba, sai kuma ta tashi a nutse suka nufi ɗaya da ga cikin bedroom ɗin dake a falon.
        Suna shiga aunty Hannah ta damƙi hanun Raudha ta maida ƙofar ta datse. “K kinada hankali kuwa? Kinsan su waye waɗan nan matan?” Kafin Raudha tace wani abu ta cigaba da faɗin, “To ki saka hankalinki a jikinki waɗan nan duk zasu iya sayen garinku hutawa ne da kayan cikinsa. Kin wani zauna kina musu yatsina da jan aji dan sunce suna son ganin shugaban ƙasa”.
      Raudha da ke binta da kallon mamaki ta ce, “Amma Mom shugaban ƙasa dake office yanzu ta ina zan kaisu wajensa? To ko a gida yake ma ganin shugaban ƙaramin abune Mom?”.
     Aunty Hannah dake hararta ta ce, “K wawuya kina kwana da mutum a gida ɗaya amma baki san komai nasa ba. Abban Samha ya sanarmin sai monday zai fita office yana gida. Wai kuwa ma kina aikin da muke buƙata a gidan nan ko zaman samun canji waje da canja kayan da Asabe bata taɓa saka makamantasu ba kika tsaya”.
     Sosai maganar aunty Hannah na ƙarshe ya soki Raudha fiye da komai, amma sai ta danne tama saki murmushi. Takuma ƙi cewa komai.
      Wani irin takaici ya turniƙe zuciyar aunty Hannah, jitai kamar ta shaƙe shegiya ta huta. Dan ita ba hangen Raudha zata iya cin amanarsu take ba, zuciyarta kawai tana bata dan Raudha ta shigo daula ne take son fara raina mata wayo da tunanin tana dai-dai da ita.....
         Ganin aunty Hannah ta lula duniyar tunani Raudha tai tunanin maido da ita, dan ta fahimci fiddoma aunty Hannah ainahin kanta a yanzu ba nata bane. Cikin murmushi da nuna ɗoki tace, “Mom dama fa wlhy inata son ganin wani a cikinku, ya samarmin makaranta fa”.
       Firgigit aunty Hannah ta dawo hayyacinta, sai kuma ta saki murmushi da faɗin, “Kai Alhmdllhi da wannan labari, naji daɗi dan yayi abinda ya dace. Dama da batun nan nazo a raina, dan ya kamata ace kema zuwa yanzu kin fara fiddo kanki wa jama'a sosai, bawai ki kume cikin gida ba kamar kowace mace. Karfa ki manta ke first lady ce, ki masa maganar ya baki office ki fito duniya tasan ƙoƙarin ki...”
      Cikin mamaki Raudha tace, “Mom office kuma?”.
      “Eh office! Ko kina nufin haka zaki cigaba da zama ƙumshe a cikin gida

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login