Showing 39001 words to 42000 words out of 127542 words
takaici,daga nan itama a bata shawara baza ta dinga addua da kanta ba sai a fada malamai,idan kuma an sawa mutum cuta dole sai da malamai za a warke daga nan idan an warke baza a hakura ba anga hanya shike nan sai aci gaba da kai bukatu.
Malam ya zauna ya nuna shi na Allah ne yana ta kawo aya da wa'azi ta yarda dashi malamin kirki ne baya shirka ashe a daki shi kadai yana can yana rafka Sabo yana bautar Aljani yana shirka wa Allah,gasu nan abinda akeyi kenan yanzu,ko yar karamar sana'a mutum ya fara sai ya fada malamai Sabo da yanzu masu hassada za fara masa binne binne a wajen na layoyi,dan a hanashi ci gaba,wani container zai siya kafin ya hada ta wai sai kaga har anje an masa binne binne ciki,abin haushi yanzu har gonaki na kauye akeyi,da anga gonar wane tayi kyau sai aje ayi maka kulunboto ta lalace kar a samu abin kirki,kar dai aci gaba.
Abin haushin kaga mace bata ci gaba wata ma ragwargwajajjiya Amma in kaji tana lissafin malamai abin sai ya Bada mamaki,kuma dai bata ci gaba ba tana nan yanda take sai baya ma da taci,a dinga hakuri da lamarin Allah mata,wasu ma su suke dauko HIV wajen bokaye su sawa mazan ace miji ne,wasu ayi amfani da ruwan ni'imarsu,aji tsoron Allah mata da Maza musulmi,shirka Babban laifine kar a mutu anayi wlh wuta har abada ba sassauci ba rangawame.
Idan ma kinayi ki roki Allah ya rabaki da shirka ki daina,duk rabonka bai wuce ka,abinda zaka samu shi zaka samu a duniya ba wanda ya Isa ya hana ko yasa.
Maimuna anyi kiba an kara haske anyi kyau sosai tana juya Hashim dinta domin magungunan mata take sha tana gyara jikinta,bata shirka iya maganin gyaranta take siya sai yanda take kunna Hashim dinta yana like mata,Zainura matar Ubale tana da kishiya anyi mata Amarya ta siyi me kwado dan mukulli,Zainura tasa Ubale baya sha'awar kowa sai ita,kishiyarta Asiya sam Ubale baya sha'awarta duk ranar kwananta,sannan ta siyi maganin sawa a tsohuwar rijiya na malkakar miji,itama Asiya taje takanas ta siyo me dan mukulli,duk ranar kwanan ko wacce sai ta kulle Ubale,ranar kwanan Zainura sai Asiya Tace Bismillahi na kulle Ubale,shike nan bazai sha'awar Zainura ba yanzu,Haka itama Ranar kwanan Asiya sai Zainura ta daga nata tace Bismillahi na kulle Ubale sai ta saki karfe fas shike nan,gaba daya sun hana Ubale sha'awar ko wacce cikinsu,ko wacce ta kulleshi,sunyiwa kansu sun cuceshi kuma.
Kwana Uku da gama shagalin kauyen,Salma yanzu ta iya girkin gargajiya da yawa komai ta iya,haka Umma tana koya mata dabarun mata idan sunyi aure,dole take sata tana amfani da ruwan zafi da gayyen magariya tana tsarki dasu,har wasu tsumin tana dan bata irin na yan mata Sabo da lafiyarta ta zauna daram tare da maganin infection na ciwon Sanyi da dawwamar da Ni'ima a jikin mace.
Na'im yana zaune yana duba wani littafin musulunci ya rufe fuskarsa da littafin Amma a zahiri ba karatu yake ba idonsa ya leko ta yar kafar littafin yana ta faman kallon Salma,ji yake kamar ma ya jawota jikinsa ya maidata cikinsa su zauna har abada,
Salma tana wankin kayansu da nata da nasa tana kallon abinda yakeyi idonsa har ya canja kala Sabo da jarabar Na'im, Salma ta kalleshi suka hada ido ta saki murmushi me tsada da birgewa,dimple nata ya loba,Umma na kallonsu ta tashi cike da kunya ta fada kitchen tana aikin abincinta,Salma ta dago masa hannu da kumfa a hannunta,dariya ya mata tare da yafito ta wai tazo,sanye take da English wears riga da skert sun mata kyau,cikin lafiyarta ta jan hankali da birge me kallo ta karaso wajensa ta tsuguna megidana gani,Na'im yaji wani sanyi,ya kalleta tare da mika mata tafin hannunsa yace mu danyi kadan kafin Malam ko Umma su gani,Salma tace me fa? Yace dan sabon mu danyi kadan Malam yace Sabo ne taba mace ba muharramarka ba ko?Salma tace eh,why not yau na taba kadan mu danyi kadan? Salma tace gaskiya hakane mu me mukeyi ma na Sabo ai mu salihai ne,to mutane da dama suna ganin basa aikata Sabo ko me sukeyi ai kadan ne,baka sani ba da kadan din sai yafi me yin babba a wajen Allah,Allah Sa mu dace.
Salma ta mika masa Hannun ta me santsi da laushi shima Na'im haka ya hade hannun waje daya gam yana murzawa Salma tana lumshe ido,yana kare mata kallo kamar me,da kyar ta kalleshi a kunyace yace me kike ji?da dadi?Salma ta rumtse idon kunya tace uhm...wani zir..zir...Kamar tafiyar tsutsa a jinina,A hankali Na'im yace nima haka,Malam ya mana auren ko?,Salma ta daga kai wai ae idan ya dawo ka fada masa tunda idan anyi aure ai zamu iya rike hannu da rungumewa ma Na'im yace hakane bari ya dawo je ki karasa aikin ya sake mata hannu ta koma wajen aikinta shi kuma yaci gaba da kallon abarsa,Salma tace au munyi Sabo to muyi istinghifari,sai ko kowannensu ya fara astaghafirillah wa atubu ilaih a hankali suna ta mus..mus..da baki.
Da dare Na'im yaje har dakin Malam suna tare da Umma ya sanar masa cewar ayi musu aure shi da Salma,Malam yace nafika son na hada wannan auren Amma ban san ko Salma ta taba aure ba taya zan hadaku azo a shiga matsala,Salma tana labe a jikin kofar harda goge hawaye anki yarda ayi musu auren,ta leka ta jikin labile tare da cewa Malam ni ban taba aure ba fa,Malam yace taya kika sani tunda bakwa tuna baya?Salma tace koma na taba auren ni wlh ko memory na ya dawo ni bana son wancan mijin nawa na farko wannan nake so Muhammad dashi zan zauna.
Malam yayi dariyar Manya sannan yace to ni dai Bazan daura ba sai Kwakwalwarku ta dawo dai dai.
Na'im kamar zaiyi kuka ya mike ya bar dakin,yana fitowa Salma ta tareshi harda janshi can wajen zauren kofar gida tace yanzu dai kayi hakuri tukunna muga abinda Allah zaiyi,ka daina fushi kar kasa damuwa ko ina da aure dole dai kai zan aura in dai muna raye,mene abin damuwa kuma? Na'im yayi shuru yana jin yanda take kwantar masa da hankali ba shiri ya jawota jikinsa cikin duhu ya rungumeta kam suna jin kamshin juna,bakinsa ya saka cikin nata suka fara kiss so deep Salma ta kara kankameshi a jikinta,sai kuwa suka ji motsin Malam zai fito daga daki zai je toilet,da sauri a tsorace suka saki juna Salma tayi waje kofar gida tunda 8pm na dare ba a dade da yin Sallar Isha ba,Na'im kuma yayi cikin gidan suka ci karo da Malam,yace ina kaje kuma Muhammad?yace wani...wani...uhm.....wani na duba ko zan ganshi akwai abinda yace zai fada min,Malam yace anya kuwa kana da gaskiya Muhd? Murmushin rashin gaskiya yayi yana sosa kai yace Ba komai fa,Ina Salma? Malam ya tambaya amma Na'im yace tana dakinta tace bacci zatayi yanzu.
Malam yace to to madalla ya shige bayi,Da Sauri Na'im ya leka cikin kasa da Murya yace shigo yana toilet, Salma ta shigo da gudu ta fada bedroom dinta tana dariya ta haye Gadonta ta fara baccin karya,Malam na fitowa Na'im yace Malam zo kaganta har tayi bacci ma Ashe,kuji rainin hankalin Na'im,Malam yace ai na yarda daku kyaleta Allah tashe mu lfy ya shige dakinsa.
Washe gari kuwa Umma ta tafi cikin birnin Katsina wajen kanwarta,Malam yana gona,Salma da Na'im kadai ne a gidan suna aikinsu tare kamar yanda sukeyi komai tare,Na'im ya kalli kirjin Salma yace ina son wannan abu naki,me?Salma ta tambaya,hannu ya kai saman boobs dinta da niyyar nuna mata,ta bige hannunsa tare da harararsa da wasa tace kai shiii dodo ne shishi ne,ba a tabawa,Na'im ya tintsire da dariya yace ni yaro ne zaki ce min wai dodo ne,Salma ma dariya tayi tace to kamashi dodo, indai wannan zai kamani to naji dadi cewar Na'im,Iskanci ne fa Salma ta furta,ashe Na'im ya haddace Kalmar zai fadawa Malam gaskiya watarana yana son Iskanci ayi masa aure.
Salma ce ta fara magana cike da nutsuwa serious muyi Sauri mu tuno baya ayi mana aure mu huta kaga idan bamu tuna ba Malam bazai mana auren ba,kullum ni ina kokarin tunawa da dare Amma har yau na kasa tunawa wlh,Cewar Na'im
Wasa wasa sai ga Salma da Na'im sun kwashe wajen wata tara a gidan Malam Magaji basu tuna komai ba.
Ranar Juma'a da dare Salma ta kara zuga Na'im ya koma ya fadawa Malam ayi musu aure,ta kara labewa a jikin labile tana ji,Na'im kalar tausayi yayi zaiyi kuka yace pls Malam ayi muna auren nan mana,Umma tace nima ina bayanku kawai ayi musu wlh nan gaba in sun tuna idan da matsala sai a warware,Malam yace sam basu da hankali bazai daura ba shi dai,kuma Bada yawunsa ba,Na'im yayi tunani ya samo reason dinsa budar bakinsa yace Malam ni dai ina son Iskanci tunaninsa sunan Breast ne hakan wai yana so,Malam ya hangame baki tare da ware hannu ya cillowa Na'im zagin manya dakuwa,ya kara masa ambola yace gidanku Muhd baka da hankali,Malam ya zauna yayi iya kokarinsa na ya fahimtar da Na'im me kalmar Iskanci ke nufi a Hausa Amma sai Na'im yace ai shi din yake so iskancin dai shi yake so,Umma ma tayi bayani kamar bakinta zai ciwo Amma Na'im yace ni dai ina so na zama dan iska tunda shi nake so,Malam sunga dai bazai gane ba kawai sai ma kunya da yake basu Suka ce ya tashi ya tafi,Kafin ya tafi ma saida ya kalli Malam yace ina son Iskancin Salma ni dai,Malam yace to dan ubanka wlh ka sake ka taba ta sai kaci gidanku Allah zai kona ka.shi dai Na'im yayi ficewarsa abinsa.
Malam yace naga ta kaina idan yaron nan yayiwa yarinyar wani abu,ni ya zanyi dasu yanzu idan tana da auren wani fa,kuma aure ba sanin iyayensu wlh Bazan iya ba.
Umma taji haushin Malam tace shike nan wlh alhaki a kanka su fa yanzu kwakwalwarsu a juye take komai zasu iya aikatawa bana son a samu matsala Malam mu zo muna danasani dan Allah ka daura musu auren nan,ni wlh ga raguna guda biyar a gidan Kanwata zan siyar na Bada sadakin,Malam yace ni ance miki bani da kudin ne?ko kyashi nake? Ranar dai sai da sukayi fada Da Umma da Malam tace sai an daura aure Malam yace a'a.
Na'im kuwa yana fitowa idonsa cike da kwalla saura kadan ta zubo shi kadai yasan me yake ji na Sha'awa kuma Salma kadai yake jin hakan a jikinsa.
Salma tana rakube a Bango taji ba nasara yau ma sai sharce Hawaye take ita dai Son Na'im kasheta zaiyi ma ta sani.
Na'im ya karasa kusa da ita yace nasan Solution ki bari sai gobe dole Malam yayi mana auren nan,7:30muke shigowa daga Sallar Isha to gobe kawai ki tsaya a zaure Bazan je masallaci ba a gida zanyi Sallah,Salma ta mike cike da kuri irin shegiyar nan an samo mafita tace za a gani ne wlh sai Malam ya san mune yan zamani mu muka san Zamani, we no dey carry last tayi kwafa. har kofar Bedroom nata Na'im ya rakata tare da riko hannunta yana wasa da yatsunta Salma jiki ya dauki Harama da niyya fa anyi shuru tayi lakato har ya sata a kirjinsa tare da rungumeta kamar suna Aljanna haka suka ji,da kyar ya saketa saida ta tuna masa da Umma ko Malam sannan ya mata kiss a goshi ta shige daki tare da yin juyi ta fada saman Bed dinta na jin dadi,Na'im kuwa yana haurawa saman Bed sai pillow ya jawo tare da rungumewa kam kamar shine Salma yana ta faman murmushi tare da Tafiya tunani Amma baya tuna komai sai rayuwarsa gidan Malam Magaji,haka ma Salma abin yake.
Sharhi fans
AsmaBaffa
[1/14, 5:14 PM] Sis Asma: 🏉KAMARSU CE DAYA🏉
71-75
Official
By
AsmaBaffa
Khadija A Hamza,Salisu Aisha,Fatima Abdullah,Naja'atu Aleeyou,Queen kk,Mom twins,Hadiza Hussaini and Agas wannan page naku ne Ku kadai Masoya.
Mrs.M.D.Argungun Ina godiya ina posting zanga comment naki tnx once again.
Mummy abin nata harda rashin tawakali ma domin yanzu har sambatu takeyi kala kala,yau tana kwance ta rame tayi baki kamar ba Mummy ba kowa ya ganta sai ya tausaya kamar Na'im ne kadai danta,Su Irfan har basa son ganinta Sabo da zuciyarsu karyewa takeyi,duk wanda ya shigo sai dai ta dinga Na'im kaine? Na'im dina ya dawo?Na'im zo na shafaka naji,abin gwanin tausayi surutu iri iri.
Dada ta dawo gidan da zama tana kula da yarta,haka dangi ana zuwa musu jaje da duba Mummy, yau Dada ta shigo dakin sai ko Mummy tana daga kwance Hawaye na sintiri a idonta ta fara Na'im kaine?ka dawo? Zo ga Mummy naka,Salma kake so?zan aura ma ita,duk inda ta shige za a nemota,Dada tayi tsalle gefe tare da cewa yau na shigesu da wannan yarinya ni yau me zan gani haka?kashe kanki zakiyi Sabo da rashin karbar kaddara,sabo da rashin tawakali,da mutuwa yayi fa sai kema ki bishi,yara nawa gareki baza ki godewa Allah ba sai shashanci,Mummy ita dai ba ruwanta tana ji ance ma da mutuwa yayi fa ta saka kuka wiwi harda gunji tana ni gwara na mutu na huta,gwara na shiga daji,Irfan duk sun tsaya can gefe ransu ya jagule,Aisha kuwa kuka itama take taya Mummy,tana tausayin Uwarsu,yanzu Aisha babu jin dadin rayuwar da za tafi shaye shaye,an daina lez ma gaba daya ta daina komai yanzu to gida ba lfy,dama komai jin dadi ke sawa ayi,Irfan kuwa shi ke komai duk business na Na'im shi yake rike komai bashi da time ko kadan,Hunaif ma ya zage a wani part din,kullum Irfan idan yaje Office companies na Na'im sai ya zubar da Hawaye,haka sauran ma,Hunaif kuwa Hospital din shike kula dashi na Na'im idan yaji ana neman Doctor Me Imani sai zuciyarsa ta karye ya zubar da Hawaye,ace sai dai kaninsa,nan ya tambayi me Na'im kewa patients ne suke damuwa dashi haka ana Jimamin rashinsa?Suka ce ai kaf patients indai shi ya dubaka to komai girman cuta kyauta za ayi maka aiki,nan Shima Hunaif duk Ranar da ya shiga asibitin shi ba Doctor ba amma Idan wasu Doctors sun duba zai zabi da yawa a musu komai kyauta yanda Na'im keyi yace idan ya mutu Allah haskaka kabarinsa,idan kuma yana raye anyi Sadaka Allah bayyana shi da gaggawa.
Aisha kuwa Watarana tana zuwa Embassy ta sanar musu duk halin da ake ciki fa ba a ganshi ba,wayoyin Na'im da System nasa duk Irfan ke Amfani dasu wajen Aikinsu.
Dada dai taga Mummy idan sunyi sake haukacewa zatayi kawai ta fara taimako da adduoi Amma abin kullum ci gaba yake,Irfan yace kawai a kaita asibiti ta zauna acan kar brain nata ya samu matsala.
Nan aka kai Mummy asibiti ana kula da ita ko yaushe,Dada na wajenta su Aisha suna hanya kullum har dare asibiti ya koma kamar gidansu ma.
Mummy tana dan jin sauki yau ma ta mike zatayi Sallah ta kalli kudu,Dada tace hauka kike ne?ga gabas nan,nan ma Mummy a kalli Arewa abinta zata fara Sallah da kyar aka samu ta daidaita abin ba dadi dai.
Salma da Na'im soyayya sai abinda yaci uban da,kullum Karuwa take a zukatansu kamar su hadiye juna, Malam Magaji ya siyawa Na'im waya me kyau yar dubu ashirin Tecno sabuwa dal,suka siyi sabon layi yasa,nan Salma ta karbo wayar Rahina suka tura hotunansu na Sallar taushe,Kullum sai sun dauki hotuna kamar hauka a wayar nan duk wanka sai sunyi selfie,Umma da Malam tun suna shiga har sun daina ana yin hoton dasu,har video suke daukan kansu idan sun fita yawo a garin,Yauma Umma ta aikesu a siyo mata Kubewa danya da dankalin Hausa,sun fita sai hira sukeyi suna tafka muhawara akan kalmar Soyayya da kauna,Salma tace na fika iya yaren nan fa So shine Love fa,Kauna kuma fa? Yace kauna...kauna ya tafi tunani ya kasa tunawa,Salma tace ahaf shine dai so,sanda kayi min kiss din nan jiya kasan sunansa?to soyayya mukayi fa,Na'im yace hakane soyayya?ke baki santa ba dalla,ai so shine soyayya ake soyawa,Salma ta langabe kai tace ohhh...na gane a kasko ko?yace kwarai ke baki ganewa ne har yau,tace to ai gwara da ka ganar dani kaga yanzu na gane,Ko dai mu tambayi Rahina? Na'im yace nop komai sai mun tambaya tunda muna ganewa mu daina tambayar kowa tace to.
Tunda Na'im yake bai taba zagi ba na ashar amma a kauyen nan ya iyata,daga shi har Salma basu san zagine ko ba zagi bane su Kalmar ma dariya take basu,sai suyi ta narkawa junansu ita suna video a waya,Salma ta daga waya sama yace Dan bura Uba shege suka kyalkyale da dariya,Salma ma ta fada masa,idan Umma ta aikesu har gajiya take da jira Sabo da hira da sukeyi da jarabar daukan hoto da video.
Suna dawowa Umma ta rufesu da fada tace daga yau na daina aikenku tare ba inda Dayanku zaibi daya,ya Isa na gama abinci Amma kuna can kuna daukan hoton Banza da wofi.
Saida suka bawa Umma hakuri ta daina musu masifa.
Tunda Na'im yace Salma zata jirashi a zaure yau kimanin 3days kenan basuyi komai ba akan Malam ya musu aure,waya ta dauke musu hankali sun manta da zancen nasu,Na'im garin danne danne ya gano yanda ake searching abu a Google nan ma Google yaga ta kansa shi da Salma duk kudin Malam suke karbewa suna Sa kati suyi ta searching Words