Showing 84001 words to 87000 words out of 104561 words

Chapter 29 - Exiled Prince Book 3 Hausa Novel Complete

Meerah   

13 Dec 2024

403

katse shi da cewa " ka ga don Allah ka ba mu waje mu yi mu wuce wajen , a sani na ka kashe ko a kashe ka shi ne tsarin wannan fadan , dan haka ka wuce ka ba mu waje "

" za ka iya tafiya Rafik " Malik ya fada cikin sanyin murya
gyada mishi kai Rafik ya yi kafin ya juya ya karbi Sword din da ke hannayan Azim da ke tsaye bayan shi

ya mikawa Aymane guda , sannan ya mikawa Malik guda ya na fadin " Allah ya ba mai rabo sa'a " amma cikin zuciyar shi Malik kawai ya ke yi wa addu'ar samun nassara , da ga haka ya bar wajen ya koma wajen da a ka shiryawa ma su kallo

ya zauna saman chair din shi geffen MALIKAT AL'UMU , ya na zama ko Aymane da Malik su ka fara fadan su

a hankali MALIKAT AL'UMU ta juyo ta kalli Rafik ta ce " Rafik , wai fadan minene su ke yi ? "

wani dan karamin murmushi Rafik ya yi ya na fadin " ranki shi dade , wanda ya yi nassara shi zai hau kujerar Malik "

" Wanda bai yi nassara kuma fa ? " MALIKAT INAS ta fada

dan jinkirtawa Rafik ya yi kafin ya ce " mutuwa zai yi "

a tare su ka ce " inallillahi wa'ina illaihi raji'un , ka na nufin idan Malik bai yi nassara ba kashe shi Aymane zai yi ? "

a hankali ya gyada mishi kai ya na fadin " ina jin tsoron hakan ranki shi dade , addu'a kawai za ku yi Allah ya ba shi sa'a , idan Aymane ya yi nassara za mu shiga babban tashin hankali dan babu wanda zai iya yin jayaya da shi a kan kujerar Malik "

kalmar shahada MALIKAT AL'UMU da INAS su ka shiga jerowa , kenan kashe musu yaron su za a yi in dai bai yi nassara ba , nan take zuciyoyinsu su ka fara bugawa da karfi
a hankali MALIKAT INAS ta juya ta kalli su Malik dai'dai lokacin da Aymane ya samu Malik a damtsen shi na dama ya yanke shi nan take ya fara zubar da jini har ya gangaro saman takobin hannunshi

da sauri Inaya ta rumtse idanunta , ta na kauda kai gefe
a hankali RIANNA ta riko ta , ta na fadin " ko mu koma ciki ? "
girgiza mata kai Inaya ta yi ta na fadin " a'a Aunty RIANNA "

da to kawai RIANNA ta amsa mata kafin su ci gaba da kallon su Malik

wata yar karamar dariya Aymane ya yi lokacin da ya ji wa Malik ciwo a hannu ya na fadin " ya ,har ka gaji ? still yanzu ma mu ka fara "

a hankali ya kai hannun shi na hagu ya riko sword din , dan ba karamin rauni ya samu ba , ba zai iya ci gaba da fadan da hannun damar ba

wata yar karamar ajiyar zuciya ya sauke kafin ya nufi Aymane , shi ma Aymane da gudu ya nufo Malik
sai dai kafin ya kai ga daga takobin shi , Malik ya juya ya ba shi baya ya caka mishi sword din shi a ciki har sai da ta fito mishi ta baya

da sauri Malik ya juyo ya yi baya ya na kallon Aymane da ke zubar da jini ta bakinshi

wata nanauyar ajiyar zuciya duk mutanan Malik su ka sauke MALIKAT AL'UMU da INAS su na yi wa Allah godiya cikin zuciyoyinsu

da sauri Inaya ta mike tsaye ta na kallon Malik ta ce " ka cire mishi kai ! " ta fada da karfi har sai da hankalin kowa ya dawo gare ta

Malik na jin hakan ya tuno abun da ta tabba fada mishi lokacin da ya ce wa Aymane su yi duel din na ya cire mishi kai ta haka ne kawai zai mutu

tuno hakan ne ya sa shi nufar Aymane da sauri zai zame takobin shi
sai dai kafin ya karaso ya ga Aymane ya zare takobin da kan shi ya tilla gefe ya na sakin murmushi
" ka kashe ni , amma ba za ka iya ja da shi ba " Aymane ya fada jini na fitowa da ga bakin shi

kafin Malik ya yi taku biyu , kawai ya ga skin din Aymane ta koma green scales na fito mishi kamar irin na maciji , idanunshi su ka koma irin na maciji

bayan kalmar shahada ba abun da mutanan wajen da Malik su ke yi
su na kallon Aymane da ya fara girma , ya na girma , ya na girma , ya koma dankareren maciji tsanwa shar , girman shi ya yi biyun macijin da Rouksar ta zama a word room

wani irin razanannan kuka macijin nan ya yi tongue din shi na fitowa waje
duk mutanan wajen sai da su ka saki kara , ma su tserewa na yi , ma su suma na yi
MALIKAT INAS , MALIKAT AL'UMU da Rafik , RIANNA , Diya , bayan kalmar shahada ba abun da su ke yi

da sauri General Abdallah ya kalli Sojojin shi da ke tsaye cen a geffen ya daga musu murya ya na fadin " Fire ! "

da sauri Su ka fiddo gun su ka fara harbin macijin nan , amma ko ajikin shi , bullet din sai faduwa kassa su ke yi
wutsiyar shi kawai ya sa ya buge duk sojojin da ke wajen su ka yi cen gefe su ka fadi
shi dai Malik ya yi sumar tsaye bayan kallon macijin nan ba abun da ya ke yi , sai kalmar shahada da ya ke karantawa cikin zuciyar shi , ya na kallon macijin nan cikin ido dan shi ma macijin Malik ya ke kallon

ya na tsaye a haka kawai ya ga........




❀⚘ EXILED PRINCE ⚘❀

( LOVE MEETS POWER ) πŸ‘‘πŸ”₯




( A heart touching love story , Romance , injustice & destiny )




STORY & WRITTEN BY : MEERAH βš˜πŸ•Š


【THE ROYALTY LOVE β€πŸŒΉγ€‘



【 BOOK ________3 πŸ“šβœπŸ’Œ 】





_______________________β™‘β™‘β™‘β™‘β™‘β™‘β™‘β™‘β™‘β™‘β™‘β™‘______________________




ο½› P A G E ________ 27 βœπŸ’•πŸ”₯}






ya na tsaye a haka kawai ya ga Inaya kamar ta fado da ga sama tsaye a gaban shi , kayan jikin ta duk sun koma baki kirin , gashin ta ya yi black sosai , ga shi kuma ya yi kwari kamar an yi kitso , idanunta sun koma bakake kirin ko digon fari babu , har wani bakin hayaki ke tashi da ga saman rigar ta da gashin ta , wani abun mamaki kuma cikin jikinta ya bace bat kamar ba ta taba yi ba

a hankali Malik ya bude baki ya na shirin magana ya ga wani haske ya fito da ga jikin ta ya yi cen gefe dan nesa kadan

wata irin muguwar bugawa zuciyar shi ta yi
wata Inayar ce kuma daban , amma wannan kayan jikin ta duk farare ne , har gashin kan ta fari ne kal , idanunta sun koma farare kal har wani haske su ke yi kamar torch , ita ma dai cikin ta a shafe ya ke babu allamun pregnancy a tattare da ita

cikin wani harshe da ban san irin shi ba mai sanye da bakaken kaya ta cewa dayar " Abyad ki koma , idan wani abu ya same ki dukka mu uku ba za mu rayu ba "

girgiza mata kai Abyad ta yi ta na fadin " Aswad , ba za ki iya yin fada da shi ba ke kadai , ki bari na taimaka miki "

" Ki fara fitar da Malik da ga wajen nan " Aswad ta fada

gyada mata kai kawai Abyad ta yi , kafin ta tako da gudu ta nufo Malik da ya yi sumar tsaye , ta riko hannunshi ta bace bat tare da shi

sai ga ta tsaya gaban su MALIKAT AL'UMU rike da Malik
sakin hannunshi ta yi , ta na shirin juyawa ya riko hannunta ya na fadin " Cutie , kar ki tafi "

a hankali Abyad ta juyo , ta kwace hannunta a hankali , wannan karan da harshen Hausa ta ce " kar ka damu ba abun da zai same ta , ka zauna a nan , idan wani abu ya same ka , ita ma za ta cutu "

ta na gama fadar haka , ta yi taku uku baya , ta na fuskantar su , ta fara motsa lips din ta a hankali

a hankali wani farin hayaki ya fara tashi tsakanin su , ta dago hannun ta , ta fara yin sama da shi , shi ma hayakin nan ya fara yin sama

sannan ta daina motsa lips din ta , ta sauko hannun ta kafin ta juya da gudu

ta na juyawa Malik ya tako da sauri ya na fadin " Cutie ! " , sai dai ya na iso wajen hayakin nan ya yi baya da sauri ya ji kamar ya bugi bango

a rude ya tsaya ya na kallon hayakin nan , ya mika hannun shi , kawai sai ya ga ya tabo abu kamar ya taba bango
cikin fitar hayaci ya fara kai wa hayakin nan bugu , ya na fadin " Cutie ! Cutie ! " da sauri Diya ya riko shi ya na fadin " Ka kontar da hankalin ka , ba abun da zai faru da ita

bangaran Abyad kuwa , kai tsaye geffen Aswad ta dawo ta tsaya ta na fadin " ya za mu yi da shi ? "

a hankali Aswad ta yi sama da hannu ta , sai ga wata katuwar Sword baka kirin ta fito a ciki , ba tare da ta kalli Abyad ba ta ce mata " kar ki damu , zan yi maganin shi "

ta na gama fadar haka ta nufi macijin nan da gudu
da sauri ya juyo da wutsiyar shi zai kai mata bugu , kawai sai ta bace bat
sai ga ta tsaya a bayan shi , ba tsaya bata lokaci kawai ta caka mishi sword din hannun ta a baya

wani irin razanannan kuka macijin nan ya yi , a dubu dari ya sa wutsiyar shi ya buge ta , wata yar karamar kara ta saki ta na yin cen gefe ta fadi

" Cutie ! " Malik ya fada da karfi ya na zaro idanu lokacin da macijin nan ya buge ta , sa karfi ya shiga kai wa hayakin nan bugu amma ina , ba kuma zai iya zagaye shi ba dan hayakin ya raba masarautar biyu , babu ta hanyar wucewa

lokaci guda Abyad ta bace , sai ga ta tsugune geffen Aswad ta na fadin " ba ki ji ciwo ba ? "

" a'a " Aswad ta fada ta na kokarin tashi

da sauri Abyad ta mike tsaye , ta na kallon macijin nan ya na kokarin cire sword din Aswad da ke bayan shi

a hankali ta mika hannunta , kamar da ga sama wata farar bow ta fito cikin hannunta
a hankali ta kai dayan hannunta , ta fara jan zaren bow din nan kamar ta na shirin tilla kibiya
sai da ta ja shi har karshe kafin ta saki , kawai sai na ga wata farar Arrow ta fito ta nufi macijin nan da mugun gudu ta soke shi a jiki

wani marayen kuka macijin nan ya saki dan ba karya ya ji zafin hakan
lokaci guda Abyad ta bace bat , ta koma gaban macijin , ta kara jan bow din nan ta harba mishi kibiya , ta sake bacewa ta koma bayan shi , ta harba mishi wata arrow a baya , yanzu ma ta sake bacewa ta koma dayan geffen ta sake harba mishi arrow , sai da ta harba mishi har guda hudu kafin bow din hannunta ta bace

wani marayen kuka macijin nan ya saki , kafin ya nufe ta gudu , duk da ya galabaita dan har idanun shi sun fara rufewa , jikin shi ya yi sanyi

ya na isa ya sa wutsiya , kafin ta bace , ya matse ta a cikin wutsiyar shi ya daga ta sama , ya buga ga kassa da mugun karfi har kura na tashi

da mugun gudu Aswad ta tasso , ta nufi Abyad ta Zube saman guyiwowin ta , ta talabo ta , ta na fadin " Abyad , Abyad , ki na ji na ? "

murya a disashe ta ce " ina jin ki , ba abun da ya same ni "

da sauri Aswad ta mike tsaye , cike da bacin rai , ta bude baki ta yi wata razananiyar kara ta na kallon macijin nan
nan take wata bakar guguwa ta tashi da karfi ta fara mamaye macijin nan , a hankali Aswad ta daga kafa ta shiga cikin guguwar nan , ta tsaya cak waje guda

a hankali ta mika hannunta , da sauri Sword din ta da ta caka mishi a baya ta fito ta koma cikin hannun ta
wata razananiyar kara macijin nan ya saki lokacin da sword din ta fita da ga jikin shi

da sauri ya nufi Aswad cike da bacin rai , sai dai kafin ya iso gare ta , ta bace bat cikin guguwar nan

cak ya tsaya ya na juyi ya na kuka ya na neman Aswad
sai da ya share one minute a haka , babu Aswad
ya na a haka ya ga kawai ta fito da ga cikin guguwar nan cen sama dai'dai tsawon shi , kamar an tillo ta , ta daga sword din ta sama ta raba macijin nan gida biyu har jininshi ya watsun mata a fuska

nan take ya fadi kassa rabi ya yi gefe , rabi ya yi dayan gefe
non take gudun guguwar nan ya kara , sai kururuwa ta ke yi wani razanannan sauti na fitowa da ga ciki

sai da ta yi wajen good one hour ta na wannan sautin kafin ta bace bat tare da macijin baki daya

wata nanauyar ajiyar zuciya Abyad ta sauke ita da Aswad a tare , ta tashi da gudu ta nufi Aswad
wani dan karamin murmushi Aswad ta saki kafin ta bude mata hannayan ta , ta na isa ta shige jikin ta

a hankali farin hayakin nan da ta tare su Malik da shi ya fara yin kassa har ya bace shi ma

ya na bacewa ko sai ga Inaya tsaye a wajen , ta na sanye da kayan ta na farko , idanun ta sun komo dai'dai har wannan katon cikin nata

a hankali ta fara bin wajen da kallo ta na tambayar kanta me ta ke yi a nan

cen ta hango su Malik tsaye , sun yi cirkoΒ² su na kallon ta babu ko kiftawa sun ma rasa abun da za su ce , da a ce wani ne ya ba su labarin abun su ka gani yau , da wlh sai su ce mishi ba shi da hankali , amma da idanunsu su ka gani , kowa ya shiga yi wa Inaya ayar tambaya ban da Malik

ta na ganin shi ta saki wani cool murmushi ta fara takawa a hankali ta nufe shi
ya na ganin ta fara takowa ya sauke wata nanauyar ajiyar zuciya
har zai daga kafa kawai ya ga ta tsaya cak , kawai sai ya ga wajen da ta ke tsaye ya jiqe kamar an watsa mishi ruwa

wata irin muguwar murdawa cikin ta , ya yi mata har sai da ta saki wata razananiyar kara ta na dafe shi da hannayan ta

a dubu dari Malik ya yi kanta ya na fadin " Cutie , me ya faru ? "

amma ko jin shi ba ta yi sai kara ta saki , ta nunfashi sama sama
da sauri su MALIKAT INAS su ka nufe su dan sun ga allamun kamar naquda ce ta ke , ga shi kuma ta zubar da ruwa hakan na nufin haihuwa za ta yi

MALIKAT INAS na karasowa wajen Malik ta ce mishi " mu kai word room , haifuwa za ta yi "

dum ya ji gaban shi ya fadi , tun kafin wani ya yi magana , ya sa hannayan shi biyu ya dauke ta cak sai kara ta ke saki ya nufi word room da ita
sai cije lips din shi ya ke dan ba karamin zafi hannun shi na dama ya ke yi mishi ba , ga shi ko sai zubar da jini ya ke

amma a haka ya daure ya nufi word room da ita , tun a reception ya shiga kwallawa su doctor kira
dama cikin word room din akwai mace likita me karbar haihuwar matan masarautar
da gudu wata nurse ta tafi office din ta , ta kira ta
ta na fitowa ta cewa Malik " yi sauri ka shiga da ita dakin cen " ta fada ta na nuna mishi wani daki

da sauri ya nufi dakin , har su MALIKAT INAS sun bi bayan shi , doctor ta ce musu " a'a ku tsaya a nan , shi ma yanzu zai fito " ta kai karshen ta na nufar dakin da Malik ya shiga
ba musu kowane ya zauna saman waiting chair , kowane da addu'ar da ya ke yi cikin zuciyar shi

bangaran Malik kuwa , ya na isa cikin dakin kawai ya kontar da ita saman gadon jinya dai'dai lokacin da doctor ta shigo ta na fadin " za ka iya fita " ta fada dai'dai lokacin da wasu nurse guda biyu su ka shiga da gudu

har ya juya zai fita ya ji ta riko hannunshi
da sauri ya juya ya na kallon ta , a hankali ta girgiza

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login