Showing 24001 words to 27000 words out of 104561 words

Chapter 9 - Exiled Prince Book 3 Hausa Novel Complete

Meerah   

13 Dec 2024

381

di na wannan abun " ta kai karshen ta yi kuka

cikin rudu Moussa ya ce mata " baby wai me ya same shi ne , ni fa ina zaune kawai a ka ce min an kawo Malik Hospital kuma da allamun ba ya cikin hayacin shi "

" Poison ya ci "

" inallillahi wa'ina illaihi raji'un , baby garin yaya haka ta faru ? " Diya ya fada da dan karfi

marairaice mishi fuska ta yi kamar za ta yi kuka ta ce " yaya Moussa ni ma ban sani ba , kawai mu na shan fruits ne , sai da na ce mishi kar ya hadiye amma bai saurare ni ba , gashi yanzu su na neman su raba ni da shi , yaya Moussa don Allah ka sa a kamo wanda ya yi mishi haka " ta kai karshen hawaye na zubo mata

bayan salati ba abun da Diya ke yi , ya ma rasa abun da zai ce , ya za a ce da ga fitowar shi da ga fada har sun samu damar iya kashe shi
cak ya tsaya ya na zaro idanu ya ce " kenan bayan Miram da Mohammed akwai wanda ke son ganin bayan Malik ? "
ya tambayi kan shi cikin zuciyar shi , Miram da Mohammed da su ka kashe yanzu ya a ka yi su ka samu damar shirya wannan abun dole akwai wasu kenan

ya na dawowa da ga duniyar tunanin shi kawai ya ga Inaya har ta bar wajen ta nufi part din MALIKAT INAS
bai yi kokarin tseda ta ba , sai ma juyawa da ya yi ya nufi Hospital ya koma dan ya ga Malik



▪ROUKSAR



tsaye ta gaban Damba da ke faman dariya , sai matse fuska ta ke da allamun ba ta jin dadin dariyar shi

sai da ta gaji da sauraron shi sannan ta ja tsaki ta nan kauda kai ta ce " don Allah dariyar nan ta isa haka , na ce maka mu na cikin matsala kai k..... "

ba ta kai karshen maganar ta ba ya katse ta da cewa " ki bar ni na yi dariya ta mana , wannan shi ne a ke kira ka kashe maciji ba ka sare kan shi ba , Malik ya na konce rai hannun Allah , amma kin yi mistake guda , da ba ki kashe yarinyar nan ba , amma duk da hakan ba mu fadi ba , in dai Malik ya mutu kafin aljanun ta su Ankara ba abun da za su iya yi "

" Damba ban gane abun da ka ke nufi ba , ni plan din na ka ne duk ba na ganewa , ka ce ka na son zama Malik , amma ka ce na kashe yarinyar nan , ko na kashe ta ba za ka iya hawa mulkin ba saboda ba ita ce Malik "

" Rouksar , ba za ki gane ba , zomo me wayo ta kunnuwa a ke kama shi , wannan yarinyar da ki ke gani , ita ce garkuwar Malik in dai ta na raye ba abun da zai iya samun shi , ko so nawa za a yi kokarin kashe shi ko da kuwa rayuwar shi na tsakiyar gadar Siraji sai yarinyar nan ta medo shi duniya , in har ya tsalaka ta kuma shikenan ba abun da za iya yi "

cikin rudu Rouksar ta ce mishi " ban gane abun da ka ke nufi ba "

wani dan karamin tsaki ya yi kafin ya ce " ina nufi wannan damar mu ce , indai ya mutu ba za ta iya medo shi ba , ba abun da za ta iya yi "

wani dan karamin murmushi Rouksar ta saki kafin ta ce " in dai haka ne to ka kontar da hankalin ka , cikin daren nan Malik zai mutu , dan babu mutuman da zai iya shan poison di na , kuma ya yi rai "

cikin nitsuwa Damba ya katse ta da cewa " ko da kuwa poison din ki bai cika shi ba , ni zan je na Kamala shi , yanzu abu guda na ke bukata wajen ki , wanda zai tabbatar min hawa Mulkin Saudiya babu tangarda "

da murmushi a fuskar ta ta ce mishi " ina sauraron ka "

da hannu ya mata allamun ta matso , ba musu ta karaso dab da shi ta tsaya
a hankali ya dan sunkuyar da kan shi ya kai bakin shi saitin kunnen ta ya yi mata rada

a dubu dari Rouksar ta ja da baya ta na zaro idanu ta na wani nunfashi sama sama
" Yadda kowa zai yi tunanin halin da Malik ke ciki ne ya sa zuciyar ta bugawa har ta shiga doguwar suma " Damba ya fada da dan karfi saboda bayan da Rouksar ta yi

girgiza mishi kai ta yi a tsorace ta ke ce mishi " Aymane ba zan iya ba , Da ni da ita duk mutuwa za mu yi "
TO FA 🤔🤔🤔🤔 WANE AYMANE DIN ? BA DAI WANDA KE SHIRIN AUREN RIANNA BA ?

wani dan karamin tsaki ya yi kafin ya sa hannu ya zame haramin da ya rufe face din shi
😱😱WLH AYMANE NE , WAIT KENAN TUN FARKO SHI YA YI KOKARIN KASHE MALIK TUN YA NA AMIR 🤔🤔🤔 NI FA KAI NA YA FARA RUFEWA KAMAR DAI BA NA NAN A KA YI WANI CHAPITER DIN LABARIN NAN , BARI DAI MU CI GABA

cikin wata murya cike da isa ya ce mata " ba abun da zai same ki matsoraciya kawai " a hankali ya juya ya daura hannu saman bishiyar bayan shi ya ce mata " cikin nan za ki boye shi , babu wanda ya taba zuwa wajen bishiyar nan tsawan shekaru sama da dari , tun Malik Zayd bin Saud na raye bishiyar nan ke cikin masarautar nan kuma babu wanda ya taba tunanin bishiyar micece bare har su ce a fitar da ita , duk wani sihiri da na yi cikin masarautar nan cikin wannan bishiyar na ke boye shi , kuma a ciki za ki boye ruhin MALIKAT AL'UMU "

girgiza mishi kai Rouksar ta yi da sauri kamar za ta yi kuka ta yi taku guda baya ta na fadin " a'a Aymane , ba dan ka na son zama Malik za ka saka rayuwa ta cikin hatsari , Damba in kuma a ka je wani ya fitar da ruhin ta da ga cikin bishiyar nan ka fi kowa sanin abun da zai faru da ni "

wani dan karamin tsaki ya ja kafin ya ce mata " ba shawara na ke ba ki , umarni na ke ba ki , ba shawara ba "

da sauri ta ce mishi " Aymane son da ka ke yi wa kujerar Malik yanzu har ya kai za ka iya saka rayuwa ta cikin hatsari , I'm your little sister "

ba ta gama rufe bakin ta ba ya kai hannu ya damko wuyan ta ya matse da karfi ya na zaro idanun nan na shi da kyau ya ce mata " tun lokacin da na shigo duniya , da wannan kudirin na shigo ta , kalma ta farko da ta fara fitowa da ga baki na shi ne zai na zama Shugaban Saudiya baki dayan ta , wlh ba ke ba ko da sarki Abdoul Mujeeb ne zai fito da ka cikin kassa dan dakatar da ni wlh sai na meda shi inda ya fito , da tun farko ba ki bata min shiri na ba da yanzu ni ne zaune saman kujerar Malik , in ki ka ce ba za ki yi abun da na saka ki wlh da hannu na zan kashe ki , ban damu ba da ke yar uwa ta ce " ya na gama fadar haka ya tura ta gefe ta fadi wanwar a kassa ta jan nunfashi da karfi

ta na faduwa ya koma kassan bishiyar nan ya zauna ya ja haramin shi ya rufe fuskar shi , ya ce mata " na ba ki nan da kwana uku "

da sauri ta dago kai ta mike zaune , idanun ta sun koma jazir , cikin disashashiyar murya ta ce mishi " Damba , ba zan iya ba , tsawan shekaru nawa yanzu ban yi irin wannan aikin ba , kai ma ka sani idan a ka samu matsala da ni da MALIKAT AL'UMU tare za mu mutu "

" to ku mutu mana , sai me ? Zan kawo miki duk wani abu da za ki bukata for catching her soul , da ga shi na yi miki alkawari zan mayar da ke Daular Ottoman " ya na gama fadar haka ya bace bat a wajen ya bar ta nan zaune

ya na barin wajen ta saki wani dan karamin kukan kura ta na fadin " why ? gaskiya ba zan iya ba , ban shirya mutuwa ba , wlh yanzu zan yi wa Diya magana ya sa a mayar da ni gida "

ba ta gama rufe bakin ta ba ta jiyo Muryar Aymane ya na fadin " in dai ba ki yi abun da na saka ki ba , ko kin koma sai na medo ki "

Dum ta ji zuciyar ta ta buga ta zaro idanu ta na kallon wajen , babu shi kuma a wajen Muryar shi ce kawai
yau ta tabbata duk abun da ta ke tunani kan Aymane ya wuce haka , ai ba shiri ta tashi da gudu ta bar wajen



▪INAYA


zaune ta ke cikin parlourn MALIKAT INAS ta yi zugum waje guda sai ruwan hawaye ta ke yi
kamar da ga sama ta ji an dafa shoulder din ta
a hankali ta sauke ajiyar zuciya kafin ta juya ta ga wanene ya dafa shoulder din ta

nan take ta saki kuka ta fada jikin Nesrine ta rungume ta
a hankali Nesrine ta zauna geffen ta , ta rungume ta tsam a jikin ta ba tare da ta ce mata komai ba

sai da ta gaji da kukan ta sannan ta dago da ga jikin Nesrine ta na cewa " Nesi , yanzu ma su na neman su na raba ni da shi "

cikin sigar rarrashi Nesrine ta ce mata " Ki yi hakuri kin ji Auta ? in sha Allah mutuwa ce kadai za ta raba ki da yaya Zayd ba dai mutum ba "

ba ta ce mata komai ba ta ci gaba da kukan ta kamar baby
a hankali Nesrine ta kai hannu saman face din Inaya ta fara goge mata hawayen ta ta na fadin "idan ba ki daina kukan nan ba , ba zan fada miki abun da ya kawo ni ba "

a hankali Inaya ta rage sautin kukan ta , ta na fadin " Fada min to ina sauraron ki "

wani kyawatencen murmushi Nesrine ta saki kafin ta ce " I think i'm pregnant , kin kusa zama Aunty "

cak Inaya ta tsaya da kukan ta , ta na zaro idanu ta na kallon Nesrine
nan take ta saki wani kyawatencen murmushi har da wata yar karamar dariya ta rungume Nesrine da sauri ta na yar karamar dariya , kamar ba ita ba ce yanzu ke kuka

wata yar karamar dariya Nesrine ta yi kafin ta ce mata " ke malama sake ni , ban tabbatar ba , yanzu na ke shirin yin test din "

da sauri Inaya ta sake ta ta na cewa "Tashi tom mu je likita mu yi test din "

a hankali Nesrine ta juya ta kai hannu bayan ta ta dauki pregnancy Test din da ta shigo da shi , ta nunawa Inaya ta na cewa " kin ga ba sai mun je likita ba , two minutes kadai sun isa mu yi Test din "

da sauri Inaya ta ce mata " To ya a ke yin wannan shi kuma ? "
daga mata gera guda Nesrine ta yi ta na cewa " tasso mu je ki ka gani " ta kai karshen ta na mikewa tsaye

da sauri Inaya ta mike su ka fara takawa a tare su ka nufi corridor su ka shiga bedroom din Inaya
su na shiga Nesrine ta ce wa Inaya ta jira ta za ta shiga toilet yanzu ta fito

ba musu Inaya ta nufi bakin gadon ta , ta zauna Nesrine kuma ta nufi toilet ta shiga

ta na Shiga Inaya ta kai duban ta saman bedside drawer , nan ta ga Wayar ta ajiye saman bedside drawer
a hankali ta kai hannu ta dauki wayar , ta kunna ta
nan ta ga ruwan Text din a ka turo mata kuma duk Malik ya turo mata su

a hankali ta shiga karanto Text din daya bayan daya , duk kalaman Soyayya ne ya ke zaune ya turo mata wasu kawai I love you ne a ka turo , duk da su na tare a part din shi amma da ya dauki wayar shi first thing da ya ke yi shi ne ya tura mata Text

a haka har Text din su ka tafi dan sun kai hundred , kuma duk kalaman soyayya ne ya ke ta zuba mata , ni dai ba zan iya karanto muku text din ba sirrin su ba ruwa na

kawai sai ta tsinci kan ta da sakin wani cool murmushi ta na ci gaba da karanta text din

ta na a haka ta ji Nesrine ta fito da ga cikin toilet , a hankali ta kashe wayar ta ajiye saman bedside drawer sannan ta mike ta nufi Nesrine ta na fadin " Ya ne ? me ya ba da ? "

marairaice fuska Nesrine ta yi kamar za ta yi kuka ta karaso cikin dakin ta na dan karamin tsaki
da sauri Inaya ta ce mata " Nesi ki fada min mana , wlh har na kagu na ji "

" to malama sai ki daina kaguwa "

" shikenan shikenan na ji , yanzu ki ka fada min " Inaya cike da shagwaba

wani karamin murmushin geffen fuska Nesrine ta yi , ta na cewa " it's positif "


❤⚘ E X I L E D ⚘❤ P R I N C E ⚘❤


(LOVE MEETS POWER ) 👑🔥





( A heart touching love story , Romance , injustice & destiny )





STORY & WRITTEN BY : MEERAH ⚘🕊






BOOK ________3 👑✌






P A G E 9 🌹🕊





wata irin kara Inaya ta saki har da tsale , ta na nufi Nesrine da gudu ta rungume ta ta na dariya kamar wata mahaukaciya

da sauri Nesrine ta ce mata " ke malama yi a hankali kar ki ji min ciwo "
a hankali Inaya ta sake ta , ta na fadin " Sorry , sorry , sai na fadawa Mama , mu je mu fada mata don Allah " Inaya ta fada cike da zumudi

noke mata kafada Nesrine ta yi ta na fadin " sai na fara fadawa Sweetheart kafin kowa ya sani " ta kai karshen ta na kauda kai

dan tabe baki Inaya ta yi ta na kallon ta ta ce " sannu ma su sweetheart , to sai ki yi sauri ki fada mishi , dan na samu na yi wa mama Albishir , da yaya Abdoul "

" yawwa Auta , wai ina yaya Abdoul ya ke , na yi wajen one week ban gan shi ba , kuma part guda mu ke "

" ban gane ba , part guda ku ke , kuma ki ce kin yi wajen one week ba ki gan shi ba "

" No ba ki gane ba , kamar part biyu ne a cikin bangaran namu , so shi ya na cikin part daya , mu kuma cikin gudan , ban san in da ya ke tafiya ba ko na je neman shi ba ya nan "

wani dan karamin murmushi Inaya ta saki kafin ta ce " Nesi , ina ga yaya Abdoul din mu ya fara soyayya shi ma "

hararrar ta Nesrine ta yi ta na fadin " ke ba na son shirme , yaya Abdoul din ne ki ke cewa ya fada soyayya , da wa kuma ? "

daga mata kafadu Inaya ta yi ta na turo dan bakin nan nata allamun ba ta sani ba
wani dan karamin tsaki Nesrine ta yi kafin ta kai hannu ta zungure ta a kai ta na cewa " ke dai wlh Allah ya shirya ki "
" Ameen " ta fada ta na yar karamar dariya
🤔🤔BARI DAI MU LEKO ABDOUL NA JI SHIRU KWANA BIYU



▪ABDOUL



konce ya ke saman bed din shi , ya na sanye da short da Singlet Sky blue dukkan su
ya na rike da wani book a hannayan shi ya na karantawa , ya saka earpieces a kunnuwan shi , da ga gani ka san hankalin shi na cikin book din hannun shi

ya dan dauki lokaci a haka kawai ya ji an kwace mishi book din hannun shi
a razane ya juya ya kali saitin da ya ga an kwace mishi

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login