Showing 93001 words to 96000 words out of 104561 words

Chapter 32 - Exiled Prince Book 3 Hausa Novel Complete

Meerah   

13 Dec 2024

404

barci " ya fada ya na nuna mata Nayel da ya yi barci a cikin hannunshi
murmushi mai dan sauti ta yi kafin ta ce " ba dole ba , ya na cikin hannun Daddyn shi dole barci ya dauke shi "

bai ce mata komai ba ya ci gaba da kallon Nayel , sai zuba mishi surutu ta ke amma ba ya ma jin ta tuni ya tafi duniyar tunanin shi



▪AFTER TWO DAYS



wani katon waje ne cike da chairs red color dukkan su , su na kallon wani hall
a saman hall din akwai wata doguwar table shinfide da wani tissu white color , an jera drinks kala² a sama da Mic guda 11 a gaban kowace kujera , amma na gaban farar chair din nan ya fi kawatuwa
, bayan table din akwai wasu chair guda biyar a geffen , biyar a geffen hagu sai wata babba fara kal ta alfarma a tsakiyar su

wajen duk zagaye ya ke da Sojoji , kowane rike da gun ya daure fuska , ga wasu yan JARIDA zazzaune saman chairs din nan , sai wasu manyan cameras wajen hall din nan

cen na hango Diya zaune saman kujerun da ke saman Hall , da Rafik , da General Abdallah , Idris da Hussein a geffen dama , a geffen Hagu ma akwai wasu biyar zaune saman chair din da allamun wadanan su kuma ministers ne

wajen ya yi tsit ba ka jin komai
su na a haka Malik ya shigo wajen ya na sanye da wasu suit Farare kal ma su mugun kyau , ya saka wasu sneakers farare kal a kafafun shi , ya daure wanan smooth hair din nashi a baya , ya na taku cike da Izza wasu sojoji guda uku na biye da bayan shi

ya na shigowa wajen kowa ya mike tsaye , har su Diya , nan take kowa ya shiga yin tapi , dan duk mutanan wajen ba karamin dadi su ka ji ba ganin shi

a haka har ya karaso saman hall din nan , ya nufi chair din Fara , da sauri wani soja da ke tsaye baya ya karaso zai janyo mishi chair
a hankali Malik ya daga mishi hannu , ba musu ya koma ya tsaya
hannu ya sa janyo chair ya zauna , sai da ya zauna sannan kowane ya koma ya zauna su na kallon shi

cike da nitsuwa ya fara magana cikin wata zazzakar murya ya na fadin " Assalamualaikum wa rahmatullah wa barkatuhu , My name is Nawfel Hicham Bin Jaabar , na ji dadin ganin yadda ku ka hallaci wannan zaman , kafin mu fara abun da ya kawo mu , zan so mu bude taron nan da addu'a , mai girma Rafik , bismillah " ya fada ya na dan kallon Rafik

ba musu Rafik ya mike tsaye ya fara jero musu addu'o'i su na amsa mishi da Ameen , sai da ya kammala sannan ya koma ya zauna saman chair din shi

ya na zama Malik ya ce " Alhamdoulilah , na san kowa a wajen nan ya san matsayina a cikin kassar nan tamu mai albarka , na san kuma kowa ya san abun da ya faru last seven months da ba nan , bayan hawan Aymane Bin Abdoul Mujeeb kujerar Malik , da farko zan so na gabatar da sakon ta'aziyata ga ahalin da su ka rasa 'ya'yansu , ina me kara ba ku hakuri , in sha Allah wannan shi ne na karshe da izinin ubangiji , Tabbas ni na hakura na sauka da ga kujerar Malik , amma ba wanda ya yi tunanin Abun da Malik Aymane zai aikata , a lokacin da na samu labarin abun da ke faruwa a cikin masarautar na yanke shawarar dawowa dan na rushe wannan bakin mulkin nashi , kuma cikin yardar ubangiji na yi nassara , ga duk al'umar Saudiya da ke sauraro na a wannan lokacin , zan so ku sani , ni Malik Nawfel HICHAM bin JAABAR na dawo kan kujerata ta Malik , kuma in sha Allah zan ci gaba da kula da kassar Saudiya kamar yadda mahaifina Malik HICHAM BIN JAABAR ya kula da ita bisa gaskiya da kyakyawar zuciya , da ga yanzu duk wani mai laifi za a yanke mishi hukunci dai'dai abun da ya aikata bayan kwakwaran bincike , mai gaskiya kuma a ba shi gaskiyarshi , duk wasu makarantu da a ka rufe za a bude su , a ci gaba da bawa yaranmu karatun da ya dace , da ga Maza har zuwa Mata , I'm sorry ba ni da isashen lokacin sauraron tambayoyin ku , amma ministers za su amsa muku , ina yi wa kowa fatan al'heri , Allah ya mayar da kowa gidanshi na lafiya , Thanks a lot "

ya na gama fadar haka ya mike , da sauri su ma yan JARIDA su ka mike su na kokarin su nufe shi amma sojoji sun tare su , a haka har Malik ya sa kafa ya fice wajen ,
ya na fitowa sai saman wasu dankareren motoci ma su nunfashi duk black , cike a wajen , na yi kokarin kirga motocin amma gaskiya na kassa sai ka ce companyn buga mota dan wajen cike ya ke da motoci
ga kuma motocin sojoji kamar su ci kan su , ga kuma sojoji cike da harabar wajen 200 ma Albarka , kowane rike da gun

Malik na fitowa duk sojojin wajen nan su ka tsaya cak waje guda , da sauri wani ya nufi wata dankareriar mota Fara kal dan duk cikin motocin nan fara guda tak na gani sai motocin yan JARIDA , a haka sojan nan ya sa hannu ya bude mishi gidan bayan motar

hannu ya kai cikin aljihun wandon shi , ya fiddo wasu glass bakake ya saka a idanun shi , maimakon ya shiga motar nan da soja ya bude mishi
kawai sai ya raba ta geffen ta ya wuce , ya ci gaba da tafiyar shi ya nufi hanyar fita wajen , duk inda ya wuce sai sojojin nan sun daga kafa su na sara mishi

ko sannu bai ce musu ba , a hankali ya dago hannun ya cire button din Jacket din suit din , ya fida jacket din ya yadda a kassa ba tare da ya tsaya ba
ya kai hannu ya fido kassan farar shirt din shi da ya soke cikin wandon shi , ya kai hannu cikin dayan aljihu ya fiddo wata bakar face mask , ya saka , ya sa kafa ya fice wajen shi kadai

duk mutanan wajen sai da su ka yi mamaki baki sake , sun ma rasa abun da za su yi , su bi shi ko kuwa ? kawai dai sun tsaya su na bin shi da kallo har ya fice

bangaran Malik kuwa kai tsaye hanyar Daular Saudiya ya nufa da kafa , duk inda ya wuce sai ya jiyo Muryoyin mutane su na ta yabon shi , dan taron da su ka yi yanzu on live ne kowa ya na kallo
ba karamin dadi ya ke ji ba jin yadda mutane ke yabon shi , wasu na jefa mishi Albarka , wasu na jero mishi addu'a kai abun dai Masha Allah , ya amshi sunan shi na Malik dan kowa cikin garin Saudiya ya shaide shi

ya na tsaka da tafiyar shi kawai ya karaso wajen wani plaza , cak ya tsaya ya na bin plaza din da kallo , ya na nan yadda bai sauya ba , lokacin guda ya saki wani cool murmushi ya na kallon plaza din dan a wannan wajen ne ya hadu da Diya for the first time

a haka dai ya ci gaba da tafiyar shi hannayanshi na cikin aljihun wandon shi , har yi dan nisa kawai ya jiyo Muryoyin wasu samari da ga bayan shi su na fadin " ranka shi dade ! " su ka fada da karfi

cak ko ya tsaya , kafin ya ci gaba da tafiyar shi ba tare da ya juyo ba
ya na haka kawai ya ga wasu samari guda hudu a gaban shi kamar sun fado da ga sama sun tare mishi hanya
daya da ga cikin su ya na ce " ku yi hakuri mun tsayar da ku , ni sunana Adel , tun mu na wancen layin ne mu ka hango ku , to na cewa abokai na mai martaba Malik ne , amma sun ki yarda , shi ne mu ka biyo ku dan mu tabbatar "

a hankali Malik ya dago musu hannu ya nuna musu kunnenshi kafin ya yi musu kwatancen shi kurma ne kuma makaho , ba zai iya magana ba

" wayo , ba ka gani kuma ka ke tafiya kai daya ? ina dan jagoran ka ? dama dama yanzu akwai security a masarautar da tuni an yi gaba da kai " daya da ga cikin su ya fada

a hankali ya girgiza musu kai allamun ba shi da
Adel ne ya kalli abokanshi ya ce " kun ga , bari mu raka shi ni da Hadi , kun ga zirga²r da a ke a masarautar nan ya dawo kamar da farko , kar a je mota ta buge shi , ku/ku koma shop , ba za mu jima "

ba musu biyun su ka raba ta geffen Malik su ka koma inda su ka fito
su na barin wajen wanda ya yi magana da farko ya riko hannun Malik ya na fadin " mu tafi "
ba musu Malik ya bi shi su ka tafi tare da wanda ya kira Hadi

sai sun karaso wajen da a dakwai kwana sai su tsaya su tambayi Malik wace kwana za su yi ,
sai ya girgiza musu kai ya na nuna musu gaban su allamun su ci gaba

ba musu su ke yin hanyar , a haka har su ka karaso bakin kofar Daular Saudiya , ba tare da sun kawo komai a ransu ba

sai da su ka zo dab da kofar shigar sannan Malik ya kwace hannunshi ya na fadin " okay , na gode sosai da rakiya , rike wannan " ya fada ya na cire face mask din shi ya daura saman hannun hadi

sannan ya cire glass din shi ya daura saman hannun dayan ya na fadin " na gode , amma na san hanya , zan ci gaba da ga nan , see you next time " ya kai karshen ya na shiga Daular ya bar su nan sun yi sumar tsaye

sai da ya shiga sannan ya su ka juyo su ka kalli junan su baki sake su na zaro idanu , wata yar karamar kara su ka saki da dariya a tare kafin Adel ya ce " sai da na ce muku Malik ne amma ba ku yarda ba "

wani dan karamin murmushin geffen fuska Malik ya saki dan ya jiyo abun da ya ce , da ga haka ya ci gaba da tafiyar shi har ya iso part din MALIKAT HOUDA

bakin shi da sallama ya shigo parlourn MALIKAT HOUDA , nan ya tardo ta zaune tare da MALIKAT AL'UMU da mama da Nesrine , MALIKAT AL'UMU na rike da Nayel , MALIKAT HOUDA kuma ta na rike da Junior ( 🤣🤣🤣✌ gaskiya sai dai mu kira shi da Junior dan ni mutum guda na bawa wannan sunnan wato MALIK NAWFEL HICHAM BIN JAABAR , MY NUMBER ONE 🤣✌ )

bai ce musu komai ba ya nufi corridor ya shige , kai tsaye bedroom din da Inaya ke ciki ya nufa dan dama ita ya zo nema

ya na shiga ya gan ta konce tsakiyar gado , ta dunkule waje guda , idanunta na bude
da sauri ya nufi gadon dan a nashi tunanin wani abu ya same ta , ya na isa ya zauna a baki ya na fadin " my Cutie , me ya faru ? ciwo ki ke ? "

a hankali ta dawo da kallon ta gare shi , ta saki wani dan karamin murmushi ta ce " yanzu fa na tashi da ga barci , ko one minute ba a yi ba da na bude ido "

a hankali ya sauke ajiyar zuciya kafin ya ce " to me ya faru ? ko wani abu ki ke so ? fada min zan je na kawo miki "

girgiza mishi kai ta yi ta na fadin " yaya Zayd ba na bukatar komai a yanzu , kawai ina son na huta , jikina duk a mace ya ke "

a hankali ya sunkuyar da kai ya manna mata kiss saman forehead ya na fadin " okay my Cutie , konta ki huta , dama na zo na fada miki ran Friday za mu tafi Makkah , da ga nan mu koma gidanmu na US "

wani dan karamin murmushi ta saki murya a sanyaye ta ce " da gaske yaya Zayd , za mu tafi Makkah ? "

gyada mata kai ya yi a hankali ya na cewa " har Madina sai mun biya , da ga nan mu tafi Dubaï mu yi shopping sannan mu komawar US "

a hankali ta lumshe idanunta ta na sakin murmushi , ta na a haka ta ji saukar lips din shi saman kumatunta ya manna mata kiss sannan ya mike ya na fadin zai dawo zuwa anjima
gyada mishi kai kawai ta yi ba tare da ta ce komai ba
da ga haka ya sa kai ya baro bedroom din
har zai fita parlourn MALIKAT HOUDA ta yi saurin ce mishi " da ka tafi da ita ma zai fi , ka zo ka wuce mutane ko sannu babu "

slowly ya juyo ya kalle ta ya ce " ke dai tsohuwar nan kin shiga rayuwata wlh , sai na yi maganin ki nan gama , kar ki damu ki na gani zan zo na dauke ta na tafi da ita ai dama tawa ce ba taki ba , ci gaba da shiga harkata sai na rataye ki , tsohuwa kawai " ya kai karshen ya na juyawa ya fice abun shi

baki sake MALIKAT HOUDA ke kallon shi , har sai da ya fita sannan ta dawo da kallonta kan MALIKAT AL'UMU da ke rike da jikanta ta ce " kin dai ji abun da yaron ki ya ce ko ? kuma ba ki ce mishi komai ba ?

wata yar karamar dariya MALIKAT AL'UMU ta yi ta na fadin " to mamie ya zan yi ? na isa na shiga tsakanin mata da mijinta , um um ku yi dramar ku cen nawa ni dai kallo kawai "

a tare duk mutanan wajen su ka yi dariya har ita MALIKAT HOUDA , ba karya tun lokacin da Malik ke karami ya saba sosai da MALIKAT HOUDA , dan bayan ita babu wanda ya ke yi wa wassan kaka da jika , ita ma bayan shi ba wanda ta ke yi wa irin wannan wassan , jinin su ne ya hadu tamkar ita ce kakar shi ta gaskiya bayan ba shi da hadi da ita




❤⚘

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login