Showing 78001 words to 81000 words out of 111128 words

Chapter 27 - Abdulmalik Bobo Part 1 Hausa Novel Complete

20 Dec 2024

770

ad'aure zakuje lahira Dan daku ake mulkarmu ak'asarnan.
Dariya Ammar yayi ya ce, "masheranci aii kaima ad'auren zakaje indai hakane.
Can abakinka d'an fatan tsiya sai anjima.
Yanke wayar sukayi suduka suna dariya.
Harzai ajiye wayar saikuma yafasa yakira Rahma.
Tana zaune afalo ita kad'ai tana kallon wani India film, takalli wayarta dake wringing, ganin sunan dake a screen d'in yasakata murmushi, *_Nurulk'albee_*, d'auka tayi muryarta can k'asan mak'oshi tace amincin ALLAH ya tabbata agareka ya *_Nurulk'albee._*
Wata sassanyar ajiyar zuciya bobo yasauke, murya akasalance ya ce, " kema amincin ALLAH ya tabbata agareki my *_Nusfulhayat_*. Ina fata kina cikin k'oshin lafiya da kuzari?.
Alhmdllh sai godiyar ALLAH kam.
Wani k'asaitaccen murmushi yasaki Wanda hartanajin sautinsa akunnenta, ya ce, "nagodema ALLAH da kika kasance cikin k'oshin lfy, kinga kenan yau za'a kar6e ni 100/100 abani kulawa ta musamman awajen barci.
Kamar tana gabansa tafara buga k'afafu cikin shagwa6a ta ce, " nidai a'a wlhy inajin tsoro kuma har yanzu wajen akwai zafi.
Yanda take masa magana cikin shagwa6a yasaka jikinsa yin sanyi, k'ara lafewa yayi acikin kujerar yana shak'ar kamshin turarensa dana office d'in, yakuma narke murya can k'asan mak'oshi haba my Angel kedai kincika tsorone kawai, amma yau kwana hud'u ace haryau anajin zafi?, kodai ana gudunane?.
Hannu tasaka tarufe fuska wai ita kunya kamar tana gabansan, nidai Dan ALLAH kabarmin wannan maganar banaso.
'Yar sassanyar dariya yayi harda shashsheka wadda tasaka Rahma shagala tana saurarensa, ya ce, "shikenan idan nadawo gida zamuyi aii, kafinma nadawo kisaka d'iyarki tayi barci, ummuch๐Ÿ’‹ yamannama wayar kiss, batareda yajira amsartaba ya yanke Kiran.
Lumshe ido Rahma tayi tana murmushi, afili ta ce, ''kai maza sai'a barsu sudai ko kunya basaji?.
Shimadai a can murmushi yayi, yamik'e yana had'a takardu, yad'auki k'atuwar rigarsu ta lauyoyi tareda hular yarik'e sannan yad'akko siririn farin Gil's d'insa yasaka yafice domin gabatar da shari'a...............











*_luv you oll_*.
*_(((S))).........2017_*
[11/12, 2:58 PM] mrs bilkisu: ๐Ÿ‘ฉ๐Ÿปโ€๐Ÿ’ปtyping........

โฃ *_ABDUL-MALEEK_*โฃ
_โ€ข{๐Ÿ…ฑ๐Ÿ…พ๐Ÿ…ฑ๐Ÿ…พ}โ€ข_


*_NA_*
_*Bilyn Abdul*_

_sadaukarwa_
*_Abba Gana_*
*_Batul mamman_*
*_Billy giro_*

*_masu karatu bara namuku gulmar Xoxo da 'Yar ficika,๐Ÿ˜Ž hummm Xoxo cedai Xoxo cedai da Yar Ficika, saimukaje gidan Hafsat Rano aka kawo mana gasashshiyar kaza da lemo๐Ÿ—๐Ÿน๐Ÿพhummm ina gaya mukudai, shikenan dai shikenan dai, sai.....๐Ÿ™Šum bara nayi shiru kar zarah Bukar da hajja sufad'a musu gobe su sassambad'i k'eyata alungu๐ŸŒ, kekuma Rano saura kifad'a eheโ™€๐Ÿ˜._*
_๐Ÿ˜‚luv you so much, my sweet sisters, Hafsat xoxo, Hafsat Rano, 'Yar Ficika & Zarah Bukar, hajjace, Ayusha ilyasu, gaisuwa agareku dafatan Alkairi._
๐Ÿ˜˜๐Ÿ˜˜๐Ÿ˜˜๐Ÿ˜˜๐Ÿ˜˜๐Ÿ‘Œ๐Ÿผ.

6โƒฃ1โƒฃ

*_5:12pm_* bobo yamik'e tareda harhad'a takardun dazai buk'ata agida, yacire laptop d'imsa daga caji yasaka a jakka, bayan yagama had'a komai yakashe kayan wutar office d'in sannan yad'auki rigarsa ta lauyoyi ya sak'ala ahannu, yarataya jakar aikinsa akafad'a yafito.
Da sauri Kamilu yataso yana fad'in oga kafito?.
Nafito kamilu, zan wuce gida kuma.
Kamilu ya washe baki tareda kar6ar key d'in hannun bobo ya kulle k'ofar, fitowa sukayi har wajen mota yarakishi, Dan tuni sakatariya Madeena tana gida, k'arfe hud'u da rabi yake sallamarta ita.
Saida yashiga motar sannan yad'ago yana kallon Kamilu, to kashigo muwuce mana Dan naga garin kamarma hadarine.
Dariya Kamilu yayi yabud'e mortar yashiga yana fad'in oga ai damunar tafara kankamane, nanda 'yan satittika zakaga ruwa yafara wadata.
Murmushi kawai bobo yayi danyasan surutun Kamilu baya k'arewa, ahankali yake Murza kan motar yana kuma sauraren karatun alkur'anin dake tashi amotar cikin k'ira'ar shriek Abdurrahaman sudes, har k'ofar gida yakai Kamilu yamik'a masa kud'i yana fad'in gashi asaima uwargida kaza.
Cikin washe baki Kamilu yakar6a yana godiya, wannan dalilin yanasakashi k'ara ganin kimar ogan nasu, kwatakwata bashida k'yankyamin talaka bare girmankai irinna alhazan birnin nan, gashida alkairi kullum baya gajiyawa.
Har bobo yafice daga anguwar Kamilu natsaye yana kallonsa, saida ya6acema ganinsa sannan yashiga gida cikeda farinciki.
Ganin hadarin nak'ara tasowa yasaka bobo k'ara gudun motarsa cikin 'yan mintuna k'alilan ya Isa gida, guri yasamu yay parking sannan yakwashi tarkacensa yanufi ciki, zuwa sannan anfara yayyafi.
Rahma tana kichin Dan k'ok'arin had'a abincin dare taji ana kwankwasa k'ofa, fitowa tayi da hanzari dakuma tunanin wanene haka? Acikin hadarinnan.
Batayi gaggawar bud'ewaba saida ta ce, "wayene?.
Jin haka yasa bobo niyyar tsokanarta, ya mak'e murya kamar mace ya ce, " nice hafsat Xoxo budurwar bobo.
Gabantane yafad'i gakuma wani k'ululn bak'inciki aranta, cikin masifa ta ce, "ai bayanan saiki koma sai sanda yadawo kizo.
Pls madam ki taimakeni ruwafa na jik'ani.
Yo ya kasheki mana, Rahma tafad'a ak'ufule tareda juyawarta kicin.
Magana yasakeyi yaji shiru, ga ruwa yafara jik'ashi, da Sauri yanufi baya yaduba ko k'ofar kichin abud'e take ta baya, yana turawa tabud'e, yashigo da hanzari Dan tasowar wata iska mai sanyi.
Da sauri Rahma tajuyo dansan ganin waye, ido tad'an zaro waje Dan mamaki, sannu dazuwa tayi maganar a cunkushe Dan tuna abundana yafaru yanzu tsakaninta da Xoxo.
Dariya tabashi danganin kishi k'uru k'uru kwance afuskarta, amma saiya gimtse ya ce, " yawwa.
K'arasowa tayi inda yake tsaye takar6i jakarsa da rigar, sai wani kakkauda kai takeyi.
Lfy kuwa?, naganki haka?.
Lfy lau tafad'a tana nufar cikin falo.
Binta yayi da kallo yana murmushi, zame rigar suit d'insa yayi danta d'an jike yaja kujerar dake kicind'in ya zauna yana cire takalminsa.
Rahma tadawo kichind'in ganinsa azaune yasata binsa da kallon mamaki, dukda yaji shigowarta amma bai d'agoba saida yagama cire takalmin yad'ora k'afarsa fara Sol Asama.
Rahma ta ce, "azuciyarta, hummm jik'afa kamar ba'a takata ak'asa........
Bobo yad'ago shima yana kallonta, nikam Nusfulhayat wana ganin ak'ofar falo tsaye kamar mace?.
Baki Rahma taturo gaba, ta kauda kanta gefe, nima bansaniba.
Ido yazaro waje bakisanibafa kikace?, datazo batayi Knocking bane?.
Hawayen datake mak'alewa suka zubo akumatunta, cikin shagwa6a ta ce, " bakai tazo nemaba, kuma ta ce, "budurwarkace ita.
Yaso ya shek'e da dariya amma saiya dake, yamik'e da Sauri yana fad'in amma kika barta awaje ruwa na dukanta, yanzunan cute sokike kifara korarmin 'yammatane?, kwasar takalmansa yayi ahannu yawuce cikin falon.
Rahma taduk'e kanta ajikin cabinet d'in kicin tana kuka.
Shikam bobo d'akinsa yanufa yana 'Yar dariyar farincikin ana kishinsa Ashe?, kayansa yacire yafad'a wanka.
Itakam Rahma saida taci kukanta ta more sannan tad'ago tacigaba da girkin, jitake dama batayi MASA girkinba, tsaf ta kammala komai tajere a dinning sannan tagyara kichind'in tsaf.
Dubanta takai ga agogon falon, ganin lokaci yayi nisa tanufi d'akinta ta tatada Nawal dake barci Dan magriba ta k'arato, hannunta taja zuwa bayi tawanke mata fuska sannan suka dawo falo tabata ruwa.......hummm ni shinema yau ko ruwan ba'a baniba bare akula dani, maganar bobo tadaki dodo kunnenta.
Da Sauri Nawal takwace hannunta taje tarungumeshi tana fad'in my papa oyoyo.
Shima d'aukarta yayi yad'aga sama, my baby INA kika shigane bangankiba?.
Papa barci nakeyi yanzu momyna ta tadani magriba tayi.
Oh 'yargatan momynta yafad'a yana sumbatar kumatun yarinyar.
Rahma dai tana tsaye tana kallonsu cikeda sha'awa, hannunsa yasa yakare fuskar Nawal sannan yad'agama Rahma gira, kauda kai tayi tanad'an murgud'a baki.
Ya ce, "Niko?.
Nidaifa banceba ehe, itama tafad'a kamar badashi takeba.
Murmushi yayi sannan yadire Nawal, baby sauka nasha ruwa tunda an hanani.
Da d'an gudu Rahma taje gaban firij tad'akko ruwa da cup takawo MASA.
Bobo yayi dariya tareda fad'in ashedai ana tsoron kishiya.
Gaba tayi tashige d'akinta tana tura baki, shikuma yazuba ruwa a cup yasha yana dariya.
Nawal ta CE, " papa yaushe zamu tafi gidan Ammi?, gobene bikinsu aunty khursiyya.
Saida ya shanye ruwan sannan ya ce, "jekiyi sallah idan nadawo masallaci zan sanar miki.
d'akin momynta tanufa shikuma yadoshi hanyar fita, yabud'e sannan yad'an lek'a, ruwa akeyi sosai Dan haka yahak'ura yajuya d'akin Rahma dansuyi jam'i.
Shigar tasa tayi daidai da fitowar Rahma daga bayi, da alama alwala tayi, baice da ita komaiba ya gyara shimfid'ar sallayar, itama ganin haka yasa tagane abinda yake nufi.
Yana gaba suna baya itada Nawal yajasu jam'in magriba.
Bayan sun idar Rahma ta d'akko alkur'ani tana koyama Nawal, shima yana zaune yana kallonsu cikeda jin dad'i, har lokacin sallar isha'i yayi suka mik'e domin gabatarwa.
Saida yamusu doguwar addu'a sannan kowa yamik'e suka fito falo.
Bobo yazube saman kujera yana fad'in wash ALLAH na, Nawal tazauna kusadashi my papa bakada lafiyane?.
A'a baby nagajine kawai....... ga abinci fa....Rahma takatse musu zancen tana kallonsu.
Fararen idanunsa yad'ago yana mata wani shu'umin kallo, ta kauda idonta daga kansa shima saiya ta6e baki.
Nawal tamik'e shikuma ya ce, "nidai nagaji bazan iya hawan dining ba.
Yanda yay maganar ashagwa6e saiyabama Rahma dariya, dinning tanifa tana murmushi, komai saida suka sakko dashi tsakkiyar falon.
Tana niyyar zuba abincin taji ya ce, " kihad'amana a filet d'aya kawai, batace k'alaba tacigaba da zuba abincinta, bayan tagama ta tatura gabansa.
Gyara zamansa kawai yayi yafara cin abincin atsanake, Rahma azuciyarta ta ce, "guy d'innan komai yahad'a, cin abincinsama abin kallone.
Hakadai suka gama cin abincin anutse, daganan aka koma kallo, Nawal najikin papanta kwance yana shafa kanta ahankali.
Tuni barci yad'auketa, yakalli Rahma dake kwance a 2sita tana game da wayarta, momyn Nawal zoki d'auketa tamin barci ajiki.
Mik'ewa Rahma tayi domin d'aukar Nawal amma saiya jawota ta zauna akusadashi, hannunta yarik'e gam sannan yashiga k'ok'arin janye Nawal daga jikinsa cikin dabara.
Rahma ta turo baki gaba, yatsu biyu yasa ya d'alli bakinta, da sauri tasaka hannunta awajen Dan zafi, cikin shagwa6a ta ce, " wayyo bakina.
Habawa yarinya nagafa kamar kinfara rainani, bobo yay maganar yana matseta ajikinsa.
Shinwai ni sa'ankine?.
Da sauri Rahma ta ce, "a'a dantaji zafin d'allar mata baki dayayi. Ya ce, " to miye kiketa wani kumbura fuska?, nifa babu komai kaina yake ciwone.
Ayya my Angel sorry, namiki kamu?.
Kai tad'aga masa alamar eh.
Ahankali ya kwantar da ita acinyarsa, maimakon yamata kamunkai saitaji bakinsa akan nata, tabud'e baki zatayi magana yasamu damar zira harshensa......

๐Ÿšถ๐Ÿปโ€โ™€baya najuya musu karsuce nacika saka musu ido.
Saida aka d'auki tsawon lokaci sannan na juyo Dan inada tabbacin komai ya kammala.
Raham nagani tana cusa kanta acikin bobo suna dariya, da alama wani abun yafad'a mata taji kunya.
Ya ce, "kinga tashi muje mu kwanta, mik'ewa tayi cikin jin kunya, ta d'auki Nawal takai d'akinta, kayan barci ta canja mata itama ta canja, tana k'ok'arin hayewa gado saiga Bobo yashigo sanye cikin kayan barci shima.
Kallo d'aya tamasa ta kauda kai, shima baibi ta kantaba yamatsa kusada Nawal yamata kiss akumatu sannan yaja bargon yarufeta yana fad'in saida safe d'iyar albarka.
Itadai Rahma batace komaiba Dan harta kwanta agefen Nawal, jitayi anyi sama da ita, tafara wutsil wutsil da k'afafu wayyo ya Abdulmaleek kabarni barci nakeji, nidai yau bazanbar Nawal ita kad'aiba, pls kabarmu mu kwanta.
Bai sauraretaba har yakaita d'akinsa yadire agadon, tana k'ok'arin tashi yasa k'afa ya danneta, wayoyinsa yad'auka ya kashe sannan shima yahaye gadon yakwanta tareda jawota jikinsa.
Itakam tuni tafara kuka zuciyarta cike fal da tsoro, jin yafara mata abinda hankalinta bazai d'aukaba tafara kuka tana zame zame.
K'ara matseta yayi ajikinsa yana k'ara rud'a jikinta da sakwanni wad'anda sukeyin tasiri ajikinta da zuciyarta, amma kuzarinta na k'ok'arin turesu domin ku6tar kai.
Ina mutumin naku baiko saurara mataba Dan tuni jikinsa da ruhinsa sun Lula duniyar begen aika aikar dayakeyi, da zafifi yake aikamata sak'wannin soyayyarsa, kafin tafarga yad'auki hanyar mallakarta daga ita har zuciyarta Dan tuni itama tabada kai dukda d'unbin tsoro da fargaba dasuka kanainaye ilahinrin lungun da sak'on zuciyarta.

_Hummm masu karatu nima bara naja camryn ๐Ÿšถ๐Ÿปโ€โ™€k'afafuna nanufi wajen angona kuma sarkina mamallakin zuciyarta da ruhina_ *_{Abdus'salam)_* d'ina adon zuciyata๐Ÿ˜˜๐Ÿ˜‚.


_washe gari_
Hummm yaukam na iso amakare Dan natarar har Rahma tagama tsaftace ko ina na gidan, takuma had'a breakfast mairai da lafiya.
Zaune na isakesu a dinning suna karyawa, Rahma da bobo dasun had'a ido saisu sakarma juna murmushi, bobo kam harda d'aga mata gira, takan kauda kai tana murmushi Dan gudun kar Nawal tafahimci wainar da suke toyawa.
Bayan sunci sun k'oshi suka mik'ewa tareda yin hamdala ga sarkin sarakuna mai k'yauta da k'ari.
Bobo yad'auki jakar aikinsa ya rataya, yaukam sanye yake cikin wani farin yadi mai laushi, Wanda akaima ado da bak'in zare, rigar dakad'an tawuce d'uwawunsa amma yayi d'as aciki kamar kazauna kayita kallonsa,
_Hummm karkuma ka kalla k'ilu tajawo bau, Rahma ta ce, "kana kalan mata miji๐Ÿคฅ, my Xoxo ki kalleshi kad'an keda Rano_o๐Ÿ˜Ž.
Rahma tasakama Nawal jakarta abaya sannan tad'auki d'an kwandon abincinta suka fito, itama Rahma sanye take da shadda ruwan k'asa mai turuwa zani da Riga, tasaka farin hijjabi har k'asa Asama.
Saida suka fara sauke Nawal a school sannan Bobo yad'auki hanyar gidan Appa.
Juyowa yayi ya kalleta hayateena awajefa zan saukeki dannayi latti.
Itama kallonsa tayi sannan ta kalli agogon motar ta ce, " k'arfe 7:34am yanzu".
Eh nasani, sonake naje office dawuri yau, nayi duk aikin dazanyi zuwa 4 nadawo gida mukasance tare.
Hannu Rahma tasa tarufe fuska tana 'Yar dariya, ALLAH kana bani kunya.
Murmushi yayi idonsa atiti ya ce, "tom nadaina baki kunya Nusfulhayat d'ina mai kuka, yaya Dan ALLAH kabini ahankali, daddyn Nawal wlhy yauma a kwai zafi, wayyo ummina kizo ki cecen...........
Bata bari yak'arasaba tasaka MASA kukan shagwa6a.
Ohh sorry my cute nadaina fad'a, cikin dariyar shak'iyanci yay maganar.
Maigadi yabud'e masa gate yashiga, ko gama tsayawa da motar baiyiba tafice tayi cikin gida.
Binta kawai yayi da kallo yana murmushi, afili ya ce, "wato idan ka auri yarinya k'arama tana maka ta6ara kaima saika zama ta6ararre, ya shafa sajensa daya kwanta luf, yad'an lumshe ido yana fad'in ALLAH yak'arama ANNABI daraja da fadila da Wasila.
Rahma kin mallake *_Barrister Abdulmaleek Aliyu Abdulmaleek hamshak'i_* gaba d'ayansa da komai nasa, kin mantar dani damuwata gabad'aya, ya ALLAH kak'ara mana soyayyar juna, kakuma nisanta shaid'an daga garemu.

Na ce, " Ameen bobon Rahma.

Fitowa yay shima yanufi cikin gidan, babu kowa afalon sai kamshi dake tashi da sanyin AC.
Shiru yay atsaye yana nazarin gidan, sallamar Baba hansai mai Aiki yasakashi juyowa, ta ce, "a'a Alhaji kaine agidan.
Murmushi yamata sannan yarisina ya gaisheta, baba hansai masu gidan basu tashi bane?.
Khairiyya da khursiyya sun tashi tun d'azu, amma banga Ammi ba gsky.
Okey bara to nawuce office kawai saina dawo.
To Alhaji bazakaci komai bane?.
Ahhh baba nidanake da mata, ai tuni nafita agandu.
Dariyar jin dad'i baba hansai tayi, ta ce, " to madallah Alhaji, ina Nawal da mamanta?.
Nawal na makaranta, mamanta kam tana nan cikin tare mukazo, kud'i yazaro a aljihu yamik'a mata yafice.
Itakuwa tarakashi da k'yawawan addu'oi.

Rahma kam koda tashigo taga falon babu kowa saita wuce d'akinsu khursiyya, cikeda ihun murnar ganinta suka tashi suka ruk'unk'umeta, akan gado suka zube suna dariya.
Daga nan hira suka farayi.
fitar bobo badad'ewa safna tafito daga bayi, dama tana wanka sanda Rahma tashigo.
Rahma ta gaisheta, da k'yar ta amsa, itakam batabi takantaba Dan abunda su khairiyya suke nuna mata ya d'auke hankalinta.
Khursiyya ta ce, "aunty Rahma wai waya kawokine?."
Ya Abdulmaleek mana Rahma tafad'a tana dariya.
Kai yana ina?.
Inaga yakoma Dan yace dama bazai shigoba sauri yakeyi.
Ajiyar zuciya Safna ta sauke aranta ta ce, "yagama guje gujensa yazo yasameni daram.
Sudai su Khairiyya dabasusan tanayibama hirarsu suketa zugawa suna kwasar dariya kamar wasu k'awaye.................




*_๐Ÿ’ƒ๐ŸปTaka rawar gani akalla kome kayi kanka duniyace, mai jimirin zama cikinta, shike zuga kansa d'an magori._*

(zancenka haka yake nura m inuwa๐Ÿ˜Ž).











*_luv u oll_*
*_(((S)))........2017_*
[11/12, 2:58 PM] mrs bilkisu: ๐Ÿ‘ฉ๐Ÿปโ€๐Ÿ’ปtyping........

โฃ *_ABDUL-MALEEK_*โฃ
๐Ÿ…ฑ๐Ÿ…พ๐Ÿ…ฑ๐Ÿ…พ


*_NA_*
_*Bilyn Abdul*_

_sadaukarwa_
*_Abba Gana_*
*_Batul mamman_*
*_Billy giro_*

*_yau gaisuwar da shafin duk nakune sister Fertymerh xarah & Nafi Anka, alkairin ALLAH yakai muku aduk inda kuke, bilyn Abdul na gaisheku tareda bobon Rahma._*
_I Luv you manya manya๐Ÿ˜˜๐Ÿ˜‚_
6โƒฃ2โƒฃ

Sai wajen k'arfe biyar su bobo suka dawo gidan, kamar had'in baki suka dawo kusan lokaci d'aya suduka hud'un, bayan kowa yafito daga

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login