Showing 9001 words to 12000 words out of 111128 words
Safna kam abubuwa sun cakud'e danta tsaya kaida fata batason auren, anbuga anbuga tak'i, anyi lallashin abanza, hardai takai yau ya Shaheed ya zaneta amma abanza, Dan tace wlhy aka matsa mata zatabar gidan.
Hankalin Abba yatashi sosai, yarasa mafita, gashi har anfara shirye shiryen biki, Dan gobe za'a kawo lefe............
*_Luv u oll fan's d'in aunty bilyn Abdul._*
[11/12, 2:15 PM] mrs bilkisu: π©π»βπ»
β£ *_ABDUL-MALEEK_*β£
_{Bobo}_
_Story & editin_
*_Aunty Bilyn Abdul_*
βπΏ _Written_
*_Marak'isiyya_*
_hak'in mallaka_
*_Aunty Bilyn Abdul_*
_sadaukarwa_
*_Abba Gana_*
*_Batul mamman_*
*_Bily giro_*
1β£5β£&1β£6β£
Tana kwance agadonsu tana sharar kuka Rahma tashigo, da sauri tak'arasa gaban gadon tana fad'in haba aunty Safna yakamata kibar kukannan haka, ko sokike kizo kanki yana ciwone?.
Safna ta tashi zaune dolene nayi kuka Rahma kinajindai yanda ya Shaheed yace aure babu fashi, wlhy nikuma bana sonsa....
Rahma ta katsemata zancen da fad'in toni aunty Safna ganinake tunda bawani kike soyayya dashiba kawai kiyima su Abba biyayya mana. Tunda kinsan bazasu cutar dakeba.
Safna takamo hannun Rahma tarik'e gam kamar tana gudun kar'a kwace mata ita, ta ce, "Rahma bazan 6oye mikiba, zan gaya miki dalilin bijirema su Abba.
Wlhy sati hud'u dasuka wuce zuciyata tayi tuntu6en kamuwa dason wani bawan ALLAH, a makarantarmu muka had'u kuma wlhy ina bala'in sonsa, kullum sainayi mafarkinsa.
Lokaci k'an k'ani guy d'in ya sace zuciyata, nikam nad'auki aniyar nemoshi duk inda yake, inaji ajikina shine uban 'ya'yana, yanzu haka nabada kwangilar nemosa, shiyyasa duk abindasu Abba zasuyi saidai suyi bazan yarda amin Auren doleba.
To amma aunty kina ganin kinyi dai dai kenan?.
Da Sauri tad'aga mata hannu kinga baneman shawara nakeba, nabaki labarin sirrin zuciyatane kawai, Dan haka sauraramin, ragamar rayuwata ahannuna take Dan haka bazan yarda azalunceniba inaji INA gani.
Ainaga kema kin isa auren, miyasa Abba bazai aura masa keba saini?, idan kinajin banyi daidaiba toke kice su aura masa ke, nikuma abarni da Wanda nakeso, danhaka tashimin anan banason shishshigi da k'wala kai afaranti.
Haka Rahma ta hak'ura dukda k'ok'arin datakeyi na fahimtar da yayar tata muhimmancin biyayya ga iyaye, da illar bijire musu, amma firr Safana taki'i saurarenta, daga k'arshema abin fad'a yaso yazamar musu.
Rahma tabata hak'uri ta tashi tafita.
.*.*.*.*.*.*.*.*.*.*.
Bikifa ya kankama, bak'i harsun fara sauka, ayau kuma za'a kai lefe Dan haka matansu ya Is'haq duk suna gidan.
Akwatuna har goma sha biyu nagani baje afalo, dangi anata d'agawa ana jinjina kai dayaba k'yan kayana, Appa da babban yayane sukayi lefe, ya sulaiman yad'auki nauyin duk wani abincin daza'aci, ya Hamza kam suna 6angaren cashiya, shine yahad'a faty za'ayi dina da daddare bayan an d'aura aure ankawo amarya.
Ammi ta had'a mother night ana gobe d'aurin aure.
Suma su khairiyya da matan su ya hamza ba'a barsu abayaba sun had'a Sisters day washe garin d'aurin aure da safe kafin ayi walima.
(Nace hummm kaga bikin d'an gata).
Ango kam babu abinda zaiyi saidai gyaran gidansa, Dan za'a canja MASA fenti da abundan ba'a rasaba tunda andad'e babu kowa agidan, "tun bayan rasuwar Ni'ima daya Shiga rud'ani kamar yayai hauka yasa Appa ya tattaroshi yamaido gida kusadasu.
Kayan lefe kam sunyi masha ALLAHU saidai mak'iyi aunty Rashida matar ya is'haq tafad'a tana fesama kanta turare.
Dariya suka shek'e da ita suduka, aunty Sameera matar ya Hamza ta ce, "k'yaface haka aunty Rasheeda tunda kina ragema amarya turare.......
To aii gara kafesa, k'ila idan amaryar tazo wannan mijin nata maikama da soja ya hanaka fesawa.
Dariya suka kuma shek'ewa da ita harda tafawa kamar wasu k'awaye.
Adai dai wannan lokacin kuma Bobo yashigo falon shida ya Hamza.
Ahankali suka fara tsagaita dariyar tasu, ya Hamza ya ce, " kukuma lfy?, miya sakaku dariya haka?.
Aunty Sameera ta maimaita musu abinda yafaru, dariya ya hamza yayi, bobo kam saiyayi murmushi yana kallon aunty rasheda dake dariya, ta ce, "ka kafeni da ido konayi k'aryane?.
Kauda Kansa yayi yana murmushi, ya ce, " aunty Rasheeda kenan, kisanifa saikin biyama matana turarenta babu d'aga k'afa.
Nanmadai dariya akayi, Aunty ummy ta ce, "lah bobo dama kanason auren nan amma idan anyi magana kaita wani basarwa?.
Okey da kin d'auka banasone aunty ummy?, tsaya kiga ikon ALLAH bayan d'aurin aure zakisha mamaki Romeo zan zama.
Dariya sosai sukeyi harda ya hamza da Ammi dake sakkowa daga saman Appa.
Shikam bobo d'akinsa yashige yana murmushi.
Bayan sunyi dariya mai isarsu suka koma tsokanar bobo ya Hamza yana kare masa, danshi tunda yashige d'aki yak'i fitowa.
.*.*.*.*.*.*.*.*.*.*.*.*.
Alhmdllh yau lefe ya iso gidansu Safna, anyima 'yan kawo lefe tarba ta girmamawa, kowa ya kalli lefen saiya jinjina kai, Dan kayane masu k'yau da birgewa.
Sund'an dad'e agidan sannan suka tafi cikeda tukuyci na girma.
Cikeda zumud'i Rahma tashiga d'akinsu, Safna tana zaune tana chart da baseera daketa k'ara zugata wai karta yarda da wannan auren, *boy ya ce, " yana gab da samo mata bobonta.
Murmushin jin dad'i taketa zabgawa, k'arar rufe k'ofa da Rahma tayi yasa Safna d'agowa, Rahma tak'araso gurinta tana washe baki, aunty Safna kinga kayan lefenki kuwa jar ubancan kai, wlhy kamar basusan ciwon kud'iba.
Baki safna ta ta6e sannan tagallama Rahma harara yarinyarnan na kula kemafa kanki da motsi, banace kidaina jingina aurennan danibane Dan uwarki, kakin yakamata kitaya farinciki Dan lefennan nakine baniba kam, saikuma tayi wata 'Yar dariya Rahma lefena yana nan zuwa daga Bobona, k'ilama sannan kinada ciki hhhhhjhhhh ta shek'e da dariya harda rik'e ciki.
"Na ce, " hummmmm".
Rahma kam girgiza kai kawai tayi, tana mamakin halin kafiya da dagiya irinna Safna, tanayin Abu kamar batada ilimin addini, ALLAH ya k'yauta tafad'a afili tana ficewa ad'akin.
Amin safna tafad'a ita tana Raka Rahma da harara.
Ran Abba a 6ace yake, sai safa da marwa yake afalonsa, gobe d'aurin aure amma Safna ta tsaya kaida fata bata son aurennan, yau Uncle Abubakar sau biyu yana dukanta shida ya Shaheed amma tace Sam batasan zancenba, daga k'arshema kayanta tahad'a waizata bar musu gidan.
Ya Shaheed ne yashigo falon Abba da sallamasa, Abba ya amsa yana mai tsurama Shaheed d'in ido kamar yau yafara ganinsa, ya Shaheed ya rissina ya gaida Abba sannan ya zauna ak'asa kan kafet.
Shima Abba saiya nemi waje ya zauna.
Ya Shaheed ya sauke numfashi Kansa ak'asa ya ce, "Abba dama wata shawarace nazo da ita.
Ina jinka Shaheed Abba yafad'a da hanzari.
" Hummm Abba inaga tunda Safna tak'i har yanzu, dataje tamana abin kunya inaganin kawai mubarta, inhar zasu yarda kawai abashi Rahma.
Abba yazaro ido waje, Shaheed baka ganin Rahma batayi k'ank'antaba!?.
Abba batayi k'ank'antaba, tafa gama secondary, kuma yanda nasan Rahma da hakuri da biyayya bazata bijirema umarninkaba kamar yanda safna tayi, nasan zata yarda ta auri Abdulmalik indai Rahma ce......
Dai dainan Rahma tashigo falon, tiren dake hannunta ya su6ce, abinda ke ciki yazube jikinta sai rawa yake saboda jin furucin ya Shaheed na k'arshe.
Ya Shaheed ne yamik'e da sauri yakamota ya zaunar, cikin taushin murya ya ce, kiyi hak'uri Rahma kibi umarnin Abba kifiddashi daga kunyar mutanen daya tara, kikalli gidannan cike yake da danginmu, wasuma daga wani gari suka taso, kituna d'unbin mutanene da Abba ya gayyata wad'anda zasu halarci taron d'aurin aure gobe idan ALLAH ya kaimu.
Rahma kema kinason Abbanmu yaji kunya?, kamar yanda Safna tayi, jibi kiga yanda hankalin Abba yake atashe akan abinda baifi k'arfiba daga garemu.
Rahma tad'ago kai takalli mahaifinsu dashima su yake kallo, gabad'aya fuskarsa ta canja, Abbansu muntum mai sauk'in kai da hak'uri amma yau 6acin rai ya maidashi wani iri, ita saitagama kamar yarame.....
Ya Shaheed yad'an ta6ata, da sauri takalleshi, ya ce, "baki aminceba kema ko?.
Yanda ya Shaheed yay maganar saiya bata tausayi shima, ahankali ta jinjina kai, cikin kuka ta ce, " nayarda yaya wlhy na amince zan fidda Abba kunya... Shashshekar kuka tahanata k'arasawa."
Cikin farin cikin ya Shaheed ya rungumeta, Abba kuma yarungumesu gaba d'aya.
Sai albarka suke saka mata da addu'ar fatan alkairi, itakam tana kuka tana sharar hawaye.
Abba yakira Appa ya sanar masa komai bai 6oye masaba.
Appa ya ce, "babu wani damuwa da Safna da Rahma duk d'ayane tunda daga tsatso d'aya suka fito, shima yayta sakama Rahma albarka.
Abba yaji dad'i sosai, sukayi sallama.
Ummi ma Abba yakirata tazo d'akin, jin abinda yafaru yasa ta rungume 'yartata cikeda farinciki dakuma saka mata albarka, saidai gefen zuciyarta tana tausayin Rahma, aganinta nawa Rahmar take, amma babu yanda zasuyi, sun tara d'unbin mutane wannan ne kawai mafita agaresu Baki d'aya.
Fatanta ALLAH yasa mijin nata yakasance mai kula da tausaya mata, Dan Rahma tanada rauni sosai, dukcikin 'yayansu babu Wanda yakai Rahma hak'uri, daga ita sai ya Muneer, sune suka d'ebo halin mahaifinsu Sak, na Rahma ma yafi nasa, Dan Rahma akwai hak'uri, kuma yaran gidan duk sunfita k'yau sosai.
Rahma ba fara bace amma tanada d'an haskenta daidai gwargwado, zamu iya kiran rahma tsaka tsaki batada tsawo bakuma gajera bace, tanada d'an jiki Dan 'Yar lukutar ummi ma da akece mata, idan akafad'a tayita kuka bataso, tanada k'yanta daidai gwargwado (saidai Safna tafita k'yau nesa ba kusaba), Abu mafi d'aukar hankali ajikin Rahma shine idanunta, wasu irin idanu Rahma take dasu masu hasken tsiya da girma kamar suffar kwai, duk yanda ran Rahma ya6aci basa canja kala saidai su k'ank'ance.
ALLAH yabama Rahma baiwar juya idanu, gasu masha ALLAHU da girma, sau dayawa idanun Rahma kan fisgi hankalin mutane kanta Dan danan tashiga ransu Dan ita mutumce mai saurin Shiga rai, indai zaka zauna da ita saita shiga ranka.
Wannan kenan.π€Έπ»ββππΌ
.*.*.*.*.*.*.*.*.*.*.*.*.
Labaridai ya isa kunnene Bobo "wai Amarya bata sonsa", amma abin bai bashi haushiba sosai, tunda dama shima ba auren yakesoba, Dan haka da yarinyar tasoshi da karta soshi duk uwar ubansu d'aya ko akwalar rigarsa, shi dama wadda za'a bashi yanzu d'in ta ce, " itama bataso, da wlhy har k'yauta zai mata.
Na ce, "hummmm.........
β€β€β€β€β€β€β€ *_masoya kumuje zuwa yanzufa aka fara gashi suya sai ran sallah_*πππΌ
[11/12, 2:16 PM] mrs bilkisu: π©π»βπ»
β£ *_ABDUL-MALEEK_*β£
_{Bobo}_
_Story & editin_
*_Aunty Bilyn Abdul_*
βπΏ _Written_
*_Marak'isiyya_*
_hak'in mallaka_
*_Aunty Bilyn Abdul_*
_sadaukarwa_
*_Abba Gana_*
*_Batul mamman_*
*_Bily giro_*
1β£7β£&1β£8β£
Kafin la'asar zazza6i yarufe Rahma, tana d'akin Abba kwance ak'udundune, ya Muneer yashogo da Dr kaleed har cikin falon Abba.
Abba da kansa yashiga d'akinsa yatasoda Rahma daketa rawar sanyi, saman kujera ya zaunar da'ita Doctor yashiga aikinsa, babu wata matsala Alhaji 'Yar damuwace kawai Dr Kaleed yafad'a.
Abba ya ce, "to Dr babu wani taimako da za'ad'an bata kenan?.
A'a zan mata allura da magani tad'an samu barci, insha ALLAHU daga nan zuwa yamma zata koma Normal, yanzudai idan namata allurar tad'an samu koda tee ne tasha saitasha magani tayi wanka da ruwa maid'an sanyi ta kwanta, insha ALLAHU normal zata tashi nanda anjima.
To madallah Dr mungode sosai.
Babu damuwa Alhaji aii aikinane.
Babu 6ata lokaci Dr yayma Rahma duk abinda yadace, ummi tabata shayi tad'ansha kad'an tabata magani Wanda tashashi da k'yar Dan Rahma akwai tsoron allura da magani, bataso ko kad'an allurarma saida lallashi akayi.
Bayan tasha maganin ummi ta taimaka mata tayi wanna a bayin Abba, kaya aka d'akko mata tasaka takuma kwanciyarta a gadon Abba sai barci.
Hummmm wai ina Safna?.
Tana nan acikingidan kuma labari yakai mata, ancanjeta da Rahma, Dan haka tadage tarink'a tsallen murna ita taci nasara, shikenan zata mallaki bobonta nanda lokaci kad'an, har ruwa tazuba k'asa tasha Dan dad'i.
Cikeda farinciki takira Baseera ta guntsa mata, murna sosai ta tayata harda jinjina da yaba k'ok'arinta na dagiya.
Bayan sungama da baseera takira zeenat itama, zeenat ta ce, " wlhy Safana kin tafka babban kuskure a rayuwarki, na tabata nangaba saikinyi Dana sani Mara iyaka, son zuciya yasa kin bijirema iyayenki akan Wanda baima San da zamankiba, ke kanki bakisan Inda yakeba yanzu, bakida tabbacin zai kar6eki kobazai kar6i soyayyarkiba, wlhy kidaina biyema hud'ubar baseera zatayita kaiki tana baroki a tashar wahala ne......
Safna ta k'atseta atsawace, kee!!! Dallah malama yimin shiru, nakiraki nafad'a mikine danki tayani murna ba surutun banzaba, aiikin banza kawai mtsowww taja tsaki tana yanke wayar.
"Daga can Zeenat ta girgiza kai tana fad'in ALLAH ya shiryeki Safna, amma zakiyi nadama wlhy na tabbatar."
Babu Wanda yakumabi takan Safna shagalin biki akacigaba da gudanarwa, itama tafita harkar kowa agidan lamuran gabanta kawai takeyi harda yima Rahma dariyar mugunta.
Na ce, "hummmm.
.*.*.*.*.*.*.*.*.*.*.*
Bobo ya lalubo wayarsa dake wringing daga aljihun jins d'insa, ido yad'an zaro tareda kallon Ya Sulaiman dake duba yarinyar da akaima fad'e.
Lfy kuwa bobo?.
Tab ya Is'haq ne kasanfa sunacan suna jiranmu..... K'ara kiran da akayine yasa Yakuma kallon wayar, ya is'haq d'innedai, d'agawa yayi tareda yin sallama.
Abdulmalik wai kuna inane kaida sulaiman?, ya Is'haq yafad'a daga can.
Wlhy muna asibiti wajen yarinyarnan amma gamunan zuwa Ku k'ara hak'uri.
Tom yakamatafa kuyi sauri Dan akwai abubuwa agabanmu masu yawa.
Gamunan yanzunan insha ALLAHU.
yanke wayar yayi tareda dawo da kallonsa kan ya sulaiman, ya Sulaiman yakamatafa muje kasandai masifar babban yaya, muk'arasa kafin ya k'ulu.
Gsky ne muje kawai aii nagama harma takoma bacci.
Bobo yad'an lek'a fuskarta, ya ce, " baiwar ALLAH, wlhy rashin maganar yarinyarnan yana damuna, yakamatafa ace iyayenta sunsan halin datake ciki.
Hakane gsky to amma yazamuyi? tunda bamusan idan takeba, saidai mucigaba da addu'a. Idan kuma tak'ara samun lfy mubi shawarar Ammi mumaidata wajenta kawai.
To shikenan bobo yafad'a yana fitowa.
Waje yanufa shikuma ya sulaiman yashiga office Dan ajiye kayan hannunsa.
Babu dad'ewa yafito, mota yashiga Inda bobo ke zaune a mazaunin direba, bobo yatada motar suka fice daga asibitin.
.+.
Gidansu Safna kuwa anyi shirin kamu Wanda aka had'a a babban harabar gidan nasu, saidai matsalar amarya babu lfya tana d'akin Abba kwance tana barci.
Hafsat matar ya Shaheed ta kalli ummi, ummi to yanzu yaza'ayine harfa dangin angon sun iso ga babu amarya, dama Safna zata mana alfarmar yanzu kawai saita zauna amadadin Rahma d'in.
A'a barta kawai hafsat, nibanamaso muna saka Safna acinkin sha'anin bikinnan, takalli agogon dake hannunta, hafsat inaga bari kawai atada Rahma d'in dukda dai bata dad'e da kwanciyaba.
A'a ummi abarta kawai likitafa ya ce, tana buk'atar Hutu, gashi dangin ango since k'arfe tara akwai mother Night, yakamata tasamu ishashshen barci kafin sannan, yanzu bari nayima Basman aunty Yahanasu magana saita shirya tazauna amadadin amarya tunda kusan kansu d'aya.
Yauwa hakama yafi, dama gasu suna kama ba laifi.
Haka suka saka Basma aunty yahanasu k'anwar ummi tashirya tsaf tamkar amaryar, idanma baka saniba saika d'auka Rahma d'ince Dan suna matuk'ar kama, idanuwa kawai Rahma zatafi Basma.
Dahaka aka gudanar da kamu Wanda yak'ayatar da dangin ango, su khairiyya da khursiyya dasu aunty Rasheeda sai zuba lik'i suke wa amarya, Dan basusan ba amaryarsu bace.
Dahakadai taro yatashi gab da magriba Alhmdllh.
Duk shagalinnan da akeyi Safna tana d'aki kwance abinta, da barcima takeyi kid'an da'aka sakane yasa tatashi tana mita da tsaki anhanata barci wai, wayarta ta d'auka takira *boy danneman k'arin bayani akan aikin data bashi.
Ya ce, "mata yana nan yana k'ok'ari.
Tana yanke wayar takira Baseera sukaita labarinsu Rabi duk akan bobone.
Na CE hummmm.
.*.*.*.*.*.*.*.*.*.*.
Su bobo suna isa gidan suka Tatar da ya Is'haq da ya Hamza zaune aharabar gidan, harda wasu samari wajensu bakwai, cikin samarin danginsune, ya Hamza yana cikinsu sunashan shafta.
Ya Is'haq kam yana gefe zaune saman mota Dan bakomai yake Shiga cikinsuba kasancewarsa babba.
Bayan bobo yayi fakin suka fito, wajensu ya Hamza suka k'arasa, hannu sukaita bama matasan samarin ana musabahaπ€.
Bayan sun gama gaisawa Bobo yanufi Inda Ya Is'haq yake.
Hannu yabashi shima suka gaisa.
Ya ce, "kunje kun wani mak'ale a asibiti tamkar kun manta da abinda me gabanku.
Sorry babban yaya, bobo yafad'a yana had'e hannayensa waje d'aya alamar tubaππ».
Dirowa ya Is'haq yayi, to yazanyi idan ban hak'uraba ma.
Motocine suka fara shigowa gidan, bobo yabisu da kallon yana fad'in wannan gayarfa daga ina?....
Daidainan ya Hamza da ya sulaiman suka k'araso garesu.
Ya Hamza ya ce, " daga gidan amaryarka suke, sun halarci kamune.
Baki bobo yad'an ta6e ya Hamza miye kuma kamu?.
Kafin ya Hamza yabashi amsa aunty Rasheeda da aunty ummy suka k'araso, aunty sameera dasu khursiyya suna biye dasu.
Bud'a aunty Sameera tarangad'a akunnen bobo, yay saurin toshe kunnansa, saida tagama sannan ya kalleta fuska a shagwa6e, kai aunty Sameera dodon kunne zaki kashemin?.
Dariya suka shek'e dashi suduka, yayinda aunty Rasheeda tafara fesama bobo turare mai shegen k'amshi, kaima ankamaka kamar yanda mukaje kama amaryarka.
Dariya su ya Sulaiman suka saka danganin yanda bobo ya kwa6e fuska tamkar