Showing 81001 words to 84000 words out of 111128 words
motarsa suka gaisa cikeda k'aunar juna.
Ya Hamza ya ce, "lallai gida yafara kar6ar bak'i irin wannan hayaniya.
Dariya sukayi gabad'aya, ya ishaq ya ce, " tokumu k'arasa ciki..
Cikin falon suka nufa suna 'Yar hirarsu da dariya.
Na ce, "masha ALLAH, biki ya kankama Dan falon yad'an cika da bak'i wad'anda suka iso yau, ga hayaniyar yaransu ya ishaq daketa wasa da yara sa'anninisu bak'i.
Su bobo suka rissina suna kwasar gaisuwa, kowa kallonsu yake cikeda sha'awa, bayan gaisuwa aka ta6a 'Yar hira da tsokanar juna, shidai bobo banda murmushi babu abinda ya iya, dama haka yake ko tsokanarsa kakanni sukeyi iyakarsa murmushi, amma baya iya maida murtani, saidai 'yan uwansa idan suna kusa su kare masa.
Yanzuma wata 'Yar tsohuwa ke tsokanarsa, ta ce, " mai sunan Alhaji wai kaidai kana nan babu canji?, maganama wahala take maka bare dariya?.
Nanma murmishi kawai bobo yayi kamar yanda yasaba baice komaiba.
Ya sulaiman ya ce, "Hajiya iya aii maganar Abdulmaleek tsada gareta saikin saya da kud'i.
Yo sule mizanyi da maganarsa nikam barema na siya, wannan sai matarsa dai amma baniba.
Dariya suka saka gabad'aya falon.
Bobo Yakama gemunsa nagayu yana shafawa fuskarsa cikeda murmushi, ganin zasu saka rayuwarsa gaba yamik'e ya haye saman benen, aiko suka rakashi da dariya, ya ishaq ya ce, " Hajiya iya kinga kin koreshi?.
Isahaqa ai dankar yayi maganane yatashi, nibansan halinwa mai sunan Alhaji yakwasoba?, tunda nake ban ta6a ganin muskilin mutum irinsaba, mifa zan iya k'irga maganarsa mai tsawo danaji atsawon rayuwata, mutum kulum dund'un dunkum, sai murmushi shima idan ya gadamar yi.
Dariya aka sakeyi, su ya Hamza suka mik'e suna dariya, suma sama suka haura, cikin dariya da zolaya ya Hamza ke kiran Dund'un Dunkum! Kana inane?.
Bobo dake zaune kusada Ammi yaturo bak'i gaba, ammi kingansu ko?, wlhy nasan dani suke.
Murmushi Ammi tayi kafin tabashi Amsa su ya sulaiman suka shigo d'akin suna dariya dacigaba dakiran dund'un Dunkum.
Ya Hamza ya kalli bobo haba Dund'un Dunkum ya munata kira kaki amsa mana?.
Hararsu yayi cikin sigar wasa, ya ce, "halan faratun tsohurcan ce tafad'i sunan nan?.
Ammi dake k'unshe bak'i tana dariya ta rankwashi kan bobo, mukarram k'aniyarka wace faratun?..
Uhhhchch bobo yafad'a Dan zafi yana dafe kai, wayyo Ammi ALLAH da akwai zafi.
aidama dankaji zafin namaka tayi maganar tana k'ara kai masa wani rankwashin.
Da Sauri ya kauce, su ya ishaq suka saka dariya, gefe bobo Yakoma yana turo bak'i kamar wani k'aramin yaro, sai shafa Inda Ammi ta rankwasheshi yakeyi.
Sudai su ya hamza dariya suketa masa.
Ana cikin haka Appa yashigo d'akin da sallama, duk cikin dariya suka amsa harda ammi, Amma banda bobo dake gefe zaune ya shagwa6e fuska.
Tofa dariyarmi kuma akeyi uwa da 'yayanta?, Appa yafad'a yana zama abakin gadon Dan duk su ya Hamza suna ak'asan kafet ne zaune.
Bak'i bobo Yakuma turowa ya shagwa6e fuska kamar zaiyi kuka, Appa nifa sukema dariyarnan.
Kai kai kowa ya saurara, yazaku tasamin babana a gaba kuna dariya?, haba Ammi harda ke?. Babana zonan naji miya faru?..
Tasowa bobo yayi yazo yazauna kusada k'afafun Appa, yad'ora Kansa bisa cinyarsa, Appa yasaka hannu yana shafa kan bobon dayawani narke kamar yayayye.
Babana mikayi ake maka dariya haka?.
Appa ba Hajiya iya bace tacemin wai Dund'un Dunkum shine suka tasani gaba da dariya, ita kuma Ammi Dan nacema Hajiya iya 'Yar fara shine tarankwasar min kai, kumafa kaina harya fara ciwo.
Shima Appa sunan yabashi dariya wai Dund'un Dunkum, amma saiya gimtse saidai yayi murmushi, yacigaba da shafa kan bobo kaga mukarram d'ina barsu duksai na Rama maka, kowa saimun za6i suna sannan musaka masa.
d'agowa bobo yayi yana dariya shima, aii Appa harnama tanadi sunan dazan saka musu sai ranar deener zan fad'a idan za'a gabatar da manyan yayye yakare maganar dayimusu gwalo.
Appa yasaka dariyashida Ammi, sukam su ya ishaq kowa ya tsaya da dariyarsa suna hararar bobo Dan sun San zai iya aikatawa sarai.
Ya sulaiman ya ce, "haba bobon Ammi garadai kafad'a anan komai ya wuce.
Hum'im ban yarda da wayonba a can zan fad'a dankuji ehe.
Kaga sulaiman barsa yafad'a d'in , ALLAH yakaimu muma aisaimu fad'a, muce INA yayansu Amarya Dund'un Dunkum.
Appa ka gansuko?, bobo yay maganar cikeda shagwa6a.
Yanzunkam kowama saida yadara harsu aunty Rasheda dake k'ok'arin shigowa Dan gaida Appa, dama duk suna tsaye tun d'azun sunajin diramar family d'in, kowa sai kunshe bak'i take tana dariya dankar ajisu, zuwa yanzun sun kasa rik'eta Dan haka suka sheke da dariya suduka suna shigowa cikin d'akin.
Ya Hamza ya ce, "ALLAH bobo kaji kunya, wai yaushene zaka daina shagwa6ar nan takane?, Rahma kina fama gsky.
K'asa Rahma tayi da kanta tana dariya, Dan maganar ya Hamza tabata kunya.
Bobo ya kalli Rahma dake dariya tana to she bak'i da hannu, ba k'aramin birgesa tayiba.
Safna ma dai yau ba abarta abayaba Dan dariyar takeyi, ba k'aramin birgeta shagwa6aar bobo tayiba.
Saida aka tsagaita da dariya su Rahma suka gaida Appa, ya amsa fuskarsa wasai.
Mik'ewa su Aunty Sameera suka fara da zummar Fita su basu waje.
Appa ya ce, " a'a INA zakuje kuma?, kuzauna ayi hirar zumunci asamu ladan juna, komawa sukayi suka zazzaauna cikeda kunya da k'aunar sirikan nasu masu kamala da dattako.
Hira aka cigaba dayi cikin farinciki har aka kira sallar magriba kowa ya mik'e mazan suka wuce masallaci, sukuma kowa yayi alwala sukayi agida.
Basu dawoba saida akayi isha'i.
Safna dake la6e ajikin motoci tayi saurin rik'o rigar bobo.
Da Sauri yajuyo dansan ganin waye?, ganin Safna yasashi saurin zare ido, ya maida kallonsa gasu ya ishaq yaga babu Wanda yajuyo harma sun shige falo, hamdala yayi azuciyarsa dabasuga aika aikar da Safnar tayiba.
Juyowa yayi yana kallonta fuska a gimtse ya ce, "sakarmin Riga.
Babu musu tasaki Dan gizagon fuskarsa yabata tsoro, ta marairaice fuska kamar zatayi kuka ta ce, kacika "alk'awari.
Yagane mitake nufi amma dukda haka saiya yatsine fuska ya ce, " alk'awarin mi?, ke nifa kin addabawa rayuwata.
Safna ta marairaice fuska saiga hawaye sharrrr, ta ce, "bobo kana wulak'antani saboda ALLAH ya jarabceni da Sonka ko?, pls ka taimakeni ka taimaki rayuwata, wlhy sonka zai kasheni Abdulmaleek, bana iya barci, Sonka yana neman haddasa k'iyayya tsakanina da 'Yar uwata, Dan ALLAH karda kayadani Abdulmaleek wlhy Sonka zai halakani, inasonka INA Sonka fiyeda son dAnakema kaina..... Takasa k'arasawa saboda kuka dayaci k'arfinta.
Shikam tsayawa kawai yayi yana kallonta, zuwa yanzu tafara basa tausayi, jiyayi zuciyarsa tana shawartarsa daya taimaketa koda da nasihane k'ila tagane ta farka daga nannauyan barcin daya d'auketa.
Yad'an lumshe idanunsa yabud'e akanta, kinga tashi yafad'a cikin muryarsannan mai dad'i da amo.
Safna ta tashi tsaye tana share hawayen fuskarta.
A can ciki kuwa saida su ya sulaiman suka zauna sannan sukaga babu bobo.
A'a INA Abdulmaleek ya tsaya?, cewar ya ishaq.
Kasansa shida baba mai gadi yanzu haka yana can.
Ammi ta ce, "Rahma jeki kira mijinki yazo yaci abinci tukunna saiya tafi suyita hirar.
Akunyace Rahma tamik'e, zata fita Appa yafito shima daga d'akinsa, ya kallesu ya ce, " a'a INA mukarram d'in?.
Gashi can antafi kiransa wajen baba mai gadi.
To Aida kun k'yalesa babu dad'i suna hira kuma akatsesu, shima bazaiji dad'iba malam salen, daga yau kar a k'ara haka kunji?.
Insha ALLAHU Appa baza'a sakeba suka had'a baki wajen fad'a.
Rahma kam tana fita domin kiran bobo, harta kusa tsakkiyar gidan saita hango safna da bobo tsaye safna tana masa murmushi, badai ta hango fuskar bobo ba Dan ya juyasaiata baya, Dan haka batasan shi miyakeyiba, amma wata zuciyarta tana shaida mata shima murmushi yakeyima safna, tsayuwar sojan badakkare tayi, bata gama farfad'owaba ta hangosu sun nufi hanyar lambun gidan, jitai hawaye nabin kumatunta, yaukam abinda take zargi ya tabbata, inhar bobo da Safna ba soyayya sukeyiba a6oye mizaisasu ware kansu alambu kuma arin wannan lokacin?.
Ta share hawayenta tareda cije le6enta da k'arfi, juyawa tayi takoma cikin gidan, ta daure ta ce, "yana tareda baba suna hira awaje.
Appa ya ce, " kinga Rahma barsa kawai, idan sun gama yazo yaci abincin.
Jinjina kai tayi cikin ladabi ta ce, "to Appa."
Amma azuciyarta saitace aibama saiyaci abinciba soyayya zata k'osar dashi, d'akin su khairiya tashige tashiga bathroom tasha kukanta San ranta, zuciyarta sai tafarfasa takeyi Dan bak'in ciki, jitake gaba d'aya yau tatsani bobo dakomai nasa.
Haka tasha kukanta, bata fitoba saida taji aunty ummy na kwala mata kira tazo suci abinci, wanke fuskarta tayi tafito tana murmushin yak'e, ganinan aunty ummy wani abune yashigarmin ido shine nake cirewa.
Ayya sannu yafita ko?.
Eh ya fita aii ruwa naita sakawa.
To sannu, muje muci abinci ko.
To kawai tace mata suka fito falon k'asa inda kowa yake har Ammi, mazan ne kawai babu suna sama tareda Appa.
Aunty Sameera ta ce, "a'a INA safna wai?.
Da sauri Rahma ta ce, " tana waje tana waya, aii muci abincinmu kawai wannan ba yanzuba, idan tafara waya sai ALLAH.
Dariya sukayi gaba d'aya, aunty rasheeda ta ce, "wlhy kubarta ta soye abinta, itama muje musha biki, tunda tak'i bobon mu, madai gani ko guy d'in nata yafishine haka?.
Babu Wanda yace komai saidai anyi dariya, harda Rahma datayi na yak'e, tasan sarai habaici aunty Rasheeda tayima Safna, amma bataga laifintaba tunda itama ga aunty Safnar can suna cin dunduniyarta itada mijinta datad'auki so ta d'ora masa ayanzun.
Hakadai sukecin abincinsu, Rahma tanacine kawai badan dad'iba, amma jitake kamar tana cin magani.
Safna da bobo kam suna lambu zaune, bobo ya d'aure fuska kamar bai ta6a dariyaba Dan ganin yanda Safna takafeshi da idanu tamkar zata cinyeshi.
d'an tsaki yaja yana kauda kai daga kallinta, ke kinga inada abunyifa nazo nan nazauna, kuma matata banaso taduba bata ganniba Dan haka miye maganar taki?.
Dukda maganarsa ta 6atama safna rai, musamman dayace bayaso matarsa taduba taga bata nan amma saita danne ta matso hawaye tana shashshekar kuka.
Hannu ya d'aga mata, kinga ba kuka na tambayekiba fa malama.
Share hawayenta tayi, ta durkusa agabansa guywa ak'asa tana cigaba da hawaye, Abdulmaleek pls kasamo mana mafita, nidai nasan kaima kana sona, idan zaka iya daurewa wlhy ni bazan iya jurewa ba ka taimaki rayuwata karta salwanta akan sonka.
Wani murmushin mugunta bobo yayi, ya ce, "tabbas ina sonki amma so na 'yan uwantaka, irin Wanda nakema khursiyya da khairiyya.
So na gsky irin na soyayya da tsan tsan k'auna da begen juna, mai ratsa jijiya da ruhi da 6argo mutum d'aya tak nakemashi, itace Rahma, my Nusfulhayat d'ina, farin cikina uwar 'yayana, sarauniya mai sarautar dukkan zuciyata da duk abinda ke cikinta.
Safna kamar yanda na gaya miki wannan zaman shine zai zama zama na k'arshe tsakanina dake, kuma itace zata zama magana ta k'arshe tsakanina dake wadda ta danganci wannan, zan baki shawara kuma zan miki nasiha, idan kin d'auka kin huta, idan kin watsar ke wahala, nidai ALLAH yagani nafita hak'k'inki amatsayina na d'an uwanki musulmi.
Zamansa yagyara yana mai k'ara tattara nutsuwarsa waje d'aya.
Cikin murya mai nuna muhimmancin maganar dazaiyi ya ce, "Safna!.
d'agowa tayi tana kallonsa amma bata tankaba.
Ya ce, "Safna ina d'aga mini k'afane saboda darajar Rahma amma nakula ke bakisan zuruba.
Zan baki shawara ta k'arshe atafiyamu Dan inaso mugudu tare my tsira tare..............
*_Luv you oll._*
*_(((S)))......2017_*
[11/12, 2:58 PM] mrs bilkisu: 👩🏻💻typing........
❣ *_ABDUL-MALEEK_*❣
_•{BoBo}•_
*_NA_*
_*Bilyn Abdul*_
_sadaukarwa_
*_Abba Gana_*
*_Batul mamman_*
*_Billy giro_*
6⃣3⃣
Ina mai baki shawara amatsayina na mijin k'anwarki, ki nutsu kinemi miji kiyi aure kidaina wahalar da kanki akaina.
Amatsayinki na wadda tayi kuskure abaya yakamata kiyi zaman gyarashi yanzu, sannan ki d'auki sona dakike ik'irarin kinayi ki jefar dashi gefe ki tsarkake zuciyarki, ki daina biyema k'awayen banza suna sakaki a hanyar hallaka na bin bokaye.....
Cikin matuk'ar mamaki Safna take kallonsa, azuciyarta ta ce, "a ina yasan wannan?.
Kamar yasan tunanin datake yayd'an murmushi tareda jinjina kai, yacigaba da fad'in kina mamakin ina nasani ko? Humm hakan babu inda zai kaiki wlhy saidai kiyita komawa baya arayuwarki, Safna babu abinda ke cutar da rayuwarki sai son zuciya, to son zuciya kuma facin zuciyane.
Na tabbata ALLAH ya jarabceki da sonane saboda hakan yazamarma masu hali irinnaki ishara.
Da'ace su Abba basuda Rahma dasunji kunya awaccan ranar dakika nuna musu basu isaba, saboda k'ok'arin kunyatasu dakikayi akan dalilinki mara tushe.
Shin alokacin kinada tabbacin sake ganina?, kokuwa idan kin ganni kinada tabbacin zan kar6i soyayyarkine?, amma saboda son zuciya kika bijirema iyayenki akaina, wannan itace jarabawa tafarko dakika fara fad'uwa arayuwarki.
Safna iyayenmu sunfi kowa sonmu Dan haka bazasu cutar damuba, idan baki saniba zan fad'a miki ayau, tunda nake banta6a za6ar matar aureba da kaina.
Matata ta farko ma iyayenane suka za6amin, dukda banasonta amma nayima iyayena biyayya nakar6i k'yautarsu da hannu bibbiyu, biyayyar danamusu ban bijireba sainaci riba, daga ni'ima har Rahma sunzamemin alkairi arayuwata, wadda na tabbata da auren soyayya nayi bazanci riba hakaba, kema na tabbata dakinma iyayenki biyayya dakinyi gamon katar da abinda kikeso, amma kinga sakamakon da bijirewar taja miki yanzu, saidai sharri shaid'an dana zuciya sun danneki kin kasa ganewa bare kiyi nadama harki nemi afuwar iyayenki.
To inamai tabbatar miki idan baki gyaraba haka zakiyita fad'uwa ak'asa, ki k'are rayuwarki a bibiyar tamu rayuwar, gashi mukuma kullum farincikine ke k'ara baibaye rayuwarmu saboda albarkar iyaye dake bibiyarmu.
_amatsayinmu na 'Ya'ya wad'anda iyayenmu sukasha wahala wajen haihuwarmu, rainanmu, karatunmu, tarbiyyarmu, basa son kukanmu, kulada lafiyarmu daduk wani motsinmu, amma ayayin damuka girma muka mallaki hankalinkanmu lokacin daya kamata mu share hawayensu, amma sai suka nemi wata alfarma agaremu muka bijire musu, saboda mu muna ganin mun waye su mutanen Dane, mukuma 'ya'yan zamani wad'anda boko tagina, shin kuwa muna ganin ALLAH zai k'yalemu kuwa?, aganina babu abinda 'ya'ya zasuyi aduniya su biya iyayensu akan hidima da d'awauniyar dasukayi dasu suna k'anana._
Akwai inda zaka iya bijirema iyaye kaci riba, shine idan sunce kasa6ama ALLAH, wannankam ba'a yarda kamusu biyayyaba.
Idanfa ta gsky da tsarin addini za'abi, iyaye akace suza6ama 'Ya'ya mijin farko, idan kuma k'addara ta gifta hartayi zawarci to wannan tanada 'yancin za6ama kanta akaro na biyu tunda ta mallaki hankalin kanta.
Safna kije ki tsugguna ga iyayenki kinemi gafararsu na tabbata insha ALLAHU ko yayane saikinji sona yaragu azuciyarki.
Inhar iyaye na fushi dakai tom dolene kaita tsintar kanka cikin asara, bafa zaka sami sassauciba harsai sun janye fushinsu akanka, tokema ki gwada ki gani insha ALLAHU zaki dace.......
Shashshekar kukan Safna ne yakatsemasa dogon bayanin daya d'akko, d'ago k'yawawan idanunsa yayi yana kallonta, ya ce, "ba kuka zakiyiba inhar nasihata tashigeki, nadama zakiyi, kuma ki d'auki hanyar gyarawa.
Cikin shashshekar kuka safna ta ce, " duk abinda kafad'a gsky ne, amma wlhy akowane dak'ika na rayuwata k'ara sonka nakeyi, narasa yanda zanyi nacireka araina, ina sonka so bana wasaba.
Tabashi tausayi kwari da gsk, Dan haka cikin taushin murya ya ce, "kiyi hak'uri Safna, kimik'a lamarinki ga ALLAH shine zai taimakeki, na tabbata shaid'an nak'ara hura wutar sonane azuciyarki Dan kawai yaraba zumincin dake tsakaninki da 'Yar uwarki, Yakuma cigaba da 6atar dake acikin duhuwa kikasa rok'ar gafarar iyayenki bare harkici riba a rayuwarki.
Zan tayaki da addu'a ALLAH yacire miki sona azuciyarki kema yabaki miji nagari maisonki fiye da komai amadadina, nabaki kwana uku kije kiyi tunani kuma kiduk'ufa da addu'a Nina zan tayaki.
Jinjina kai Safna tayi cikin sanyin jiki, ga hawaye sha6e sha6e afuskarta, yazaro farin handky d'insa daga aljihu sai tashin k'amshi yake yabata.
Hannu biyu tasaka takar6a tareda fad'in ngd ya Abdulmaleek, ALLAH yabiyaka da mafificiyar nasara, yasakama rayuwarka da mafificin alkairi.
Jinjina mata kai yayi tareda lumshe idanunsa fuskarsa d'aukeda murmushi Wanda bata ta6a ganin irinsaba daga gareshi.
Itama mayar masa da murmushin tayi, tashare hawayenta da handky d'in.
Gaba tayi yana binta abaya gabad'aya saiyaji tabashi tausayi Dan baiyi tunanin zatayi sanyi dawuri hakaba.
Cak safna tatsaya tanabin mutanen Dake tsaye da kallo a harabar gidan d'aya bayan d'aya.
Da Rahma suka fara had'a ido, tunda take bata ta6a ganin 'Yar uwarta Rahma hakaba, ta tamke