Showing 75001 words to 78000 words out of 111128 words
ce, " Yar lukutar ummi kin k'ara kibafa, aunty baseera kema hadake ko?, Rahma tayi maganar cikeda shagwa6a.
Dariya sukayi tareda k'arasawa cikin falon, baseera da zeenat suka kalli juna Dan basuyi zaton bobo yana nanba.
Zama sukayi suna gaisheshi, baiko kallesuba ya amsa da lfy amma fuskarsa asake, mik'ewa yayi yana fad'in yakuke?.
Sukace lfy lau wlhy.
Fita yayi harabar gidan danya basu waje, dandanan Rahma tacika musu gaba da kayan ciye ciye, ta zauna suka gaisa.
Zeenat ta ce, "nibanji motsin mutuniyarba.
Wai aunty safna?.
Sukace eh.
Lah tana gidansu ya Abdulmaleek aii, a can takwana wlhy. Dama tunda naganku nasan zuwantane tunda Baku ta6a zuwaminba.
Dariya sukayi baseera ta ce, " a'a dama gunki mukazo ko zeenat, gyad'a kai zeenat tayi tana dariya.
Daganan hira sukashigayi, bayan kamar minti30 suka mik'e tareda alk'awarin suma zasu halarci bikinsu khairiyya d'in.
Godiya tamusu tarakosu har harabar gidan, bobo nasaman mota zaune, suka masa sallama sannan suka tafi.
Dirowa yayi daga saman motar idonsa akan Rahma, batayi auneba taji yad'auketa cak kamar jaririya yanufi cikin falon da ita.
Direta yayi saman doguwar kujera suna dariya, yakwanta tareda d'ora kansa saman cinyarta suna kallon juna, ya ce, "wad'an nanfa daga ina?.
K'awayen aunty Safna ne?.
Baice komaiba, saima ya kauda zancen da d'akko wani daban.................
*_"Dan ALLAH duk masoyina yamin addu'a acikin sallarsa, ALLAH yabiyamin buk'atata ta alkairi, yakuma azurtani da abundana nake buri na alkairi."_*
πππππ»ππ»ππ»
*_luv you oll_*
*_(((S))).......2017_*
[11/12, 2:58 PM] mrs bilkisu: π©π»βπ»typing........
β£ *_ABDUL-MALEEK_*β£
_β’{π
±π
Ύπ
±π
Ύ}β’_
*_NA_*
_*Bilyn Abdul*_
_sadaukarwa_
*_Abba Gana_*
*_Batul mamman_*
*_Billy giro_*
*_duk Wanda yasake d'aukar number ta yay amafani da'ita ta hanyar dabata daceba, dasakani a group d'in banza, ko turomin sak'on banza ta PC ALLAH ya Isa ban yafeba, nabarsa da ALLAH shine zai sakamin, tunda nayi magana harna gaji ank'i bari._*
ππππππ
6β£0β£
Wunin ranar gaba d'aya haka bobo da Rahma suka kasheshi asoyayya da tattalin juna, dukda Rahma tanad'anjin kunyar bobo har yanzu.
Ganin shiru basuzoba Ammi takira bobo tana tambayar ko jikin Rahmar ne har yanzu?.
Cikin Sosa kai na jin kunya ya ce, "a'a ammi taji sauk'i bamuzoba daine kawai, sai gobe idan ALLAH ya kaimu.
Murmushi Ammi tayi ta ce, " toshikenan ALLAH yakaimu goben tunda dai lfy Alhmdllh, ka gaishemin da ita
To Ammi zataji.
Rahma dake kwance ajikinkinsa ta ce, "ya Abdulmaleek ko kunya bakajiba Dan ALLAH.
Murmushi yayma tareda fad'in kunyar wa zanji?.
Ta Ammi mana.
Nanma murmushin yasakeyi batareda yace komaiba.
.*.*.*.*.*.*.*.*.*.*.*.*.
Shirye shiryen biki ya kankama sosai, hidima akeyi babu kama hannun yaro.
Rahma da bobo kan sai godiyar ALLAH, soyayyarsu suketa zubawa kamar babu gobe, amma dai baisake mata komaiba Dan yana tausayinta sosai, kuma bobo ba irin fitunannun mazan nan baneba, tattalikam tana shansa, azuciyarta har mamakin bobo takeyi Dan bata ta6a tunanin yanada sauk'i hakaba, ada tana masa kallon muskili masifaffe.
Amma yanzun data k'ara kusanci dashi saitaga Bahaka bane, dukda yanada fad'a amma sai anta6oshi yakeyi.
Safna kam abin duniya ya isheta, k'iriΒ² Ammi tahanata komawa gidansu Rahma, kayantama ranar gabad'aya bobo yakawomata gidan Ammi, bak'aramin 6aci ranta yayiba dantasan wannan Duk shirin bobone.
Yau tunda safe take tsumayensa amma yak'i zuwa gidan kamar yanda yasaba, suna zaune itadasu khairiyya dake had'a kayansu saboda daga gobe shagalin biki zai fara.
Kad'an kad'an saita lek'a window d'akinsu khairiyyar Dan daganan ana hangen Wanda zaishigo gidan, ta kalli agogon hanunta tareda yin tsaki.
Khursiyya ta ce, "aunty safna lfy kuwa?.
Murmushin yak'e tayi tareda wayancewa ta ce, " wlhy ya Abdulmaleek nake jira sonake nakar6i sak'o awanjensa.
Su khairiyya basu kawo komaiba aransuba sukace ayya k'ila yanacan yana shan sharafin soyayarsama, kinsan su ya Abdulmaleek sai addu'a, k'ila kuma bazaizo gidanba saiya tashi daga aiki Dan wataran haka yakeyi.
Dammmmm safna taji gabanta yafad'i, azuciyarta ta ce, "soyayya kuma?, wani kululun bak'in ciki yatokare mata mak'oshi ta had'iyeshi dak'yar, zamewa tayi takwanta visa gadon su khursiyya tana sauk'e ajiyar zuciya wadda su bama sukulaba hankalinsu nakan rigima akan wani wandon jins dakowa ya ce, " yanaso sukahau kokawa, can ALLAH yabama khursiyya sa'ar kwacewa daga hannun khairiyya ta sambad'a da gudu zuwa waje.
Itama khairiyya ta take mata baya tana fad'in wlhy baki isaba saidai kowa yahak'ura mu badashi, daidai zasushiga d'akin Ammi bobo yashigo falon da sallama.
Sanye yake cikin suit blue, komai na jikinsa blue ne amma banda belt da takalmi dasuka kasance jajaye, dressing d'in bak'aramin feeting d'insa yayiba, masha ALLAH.
hannunsa yatura cikin aljihun wandonsa yajingina da kujera yana kallonsu khairiyya daketa zagaye falon batareda sunkula dashiba.
Ganinfa bamasu gansaba yasakashi daka musu tsawa, kai!!! Wane irin iskancine wannan?, zaku maida mana gida filin polo?.
Can suka tsaya suna mazurai, yacire hannunsa daga aljihu ya nunasu Ku nakula kafin kubar gidannan saina ta6a lfyar jikinku?, dannaga wani tashen iskanci kukeji yanzu?, to ubanmiye ya had'aku?!!.
suduka saida sukad'an razana da tsawar dayayi, sukad'anja baya khairiyya ta CE, "Yaya wandonefa nad'auka shine ta kwace tagudo.
Tsaki yayi ya ce, " wandon nawaye?.
Da Sauri khursiyya ta ce, "nawanefa, itama khairiyya ta CE, " Yaya k'arya takeyi nawanefa.
Kansa yadafe Dan suna Neman samasa ciwonkai ma wlhy...
Ammi tafito ta ce, "miya faru kuma tom and Jerry?.
Suduka suka nufi Ammi suna mata bayani.....
Hannu Ammi tad'aga musu ta ce, " ainagaya muku kubar sayen Abu guda d'aya saboda gudun irin wannan ranar to gashinan kun saya kuma yanzu bawaje d'aya zaku kasanceba sannan kowa yanaso.
Khairiyya tayi kwalkwal zatayi kuka, Ammi tafasan Nafi son wandon kuma nace ta d'auki rigar nitabani wandon amma tak'i yarda.
Hannu bobo yamik'a ya ce, "kubani wandon....
Jikin khirsiyya na Rawa tamik'a masa, yana kar6a ya haura saman Appa batareda yasake maganaba.
Khairiya tafara hawaye tana hararar khursiyya Ammi ta ce, " wlhy ALLAH yabaku sa'a kunsandai halin mukarram sarai ba bak'oku bane, idan darabon saiya zaneku kuna a amare kukuka sani, idan kunason kanku da arzik'in toku kama kanku danni babu ruwana wlhy, tana gama fad'a itama tahaye saman Appa.
Jiki asanyaye suka koma d'akinsu, Safna ta kallesu tana fad'in kukuma lfy INA wandon?.
Baki Khairiyya ta turo ta ce, "bataja ya Abdulmaleek ya kwaceba.
Zumbur safna tamik'e tana fad'in yazone?.
Basu tanka mataba Dan duk haushinsa ya ishesu.
Itama bata saurari amsa daga garesuba tafito falon, jin k'amshin turarensa daya tafi yabari yasakata murmushin jindad'i, tasan yanzu yana wajen iyayensa danhaka tafito harabar gidan.
Ganin motarsa yasakata k'ara sakin wani murmushin, bud'e gaban motar tayi tashige Dan bai kulleba.
Shikam yanayanacan gaban Appa suna magana.
Appa ya ce, "Mukarram tunda Alhaji sunusu dala yabada hak'uri miyasa bazaka hak'ura dakaishi koti ba, bakamar yanda kayi niyya tun farko ba?.
Appa idan na k'yaleshi to bansan mizaimin agaba ba, badan ALLAH ya tak'aita wahalabafa nasan yaransa zasu iya kashe Rahma da Nawal alokacin nan, Amma shine yanzu zai dawo yana 'Yar murya wai ayi hak'iri, naga da ko magana baya maka amma dayake yanzu yasan miya shirya shine zaizo yay maka dad'in baki akan kahanani kaisa kotu?.
Hakane mukarram amma ni aganina duk bak'in halin mutum idan yay nadamar kuskure dayayi to yanada k'ayau agafarta MASA tunda ALLAH ma muna MASA laifi kuma idan muka rok'eshi saiya yafe mana, amatsayina na mahaifinka INA rok'ama alhaji sunusi gafara agareka da iyalanka, daga nan idan yasake yunk'urin cutar dawani namu saika d'auki matakin daduk yadace bazan hanakaba saidai na taimaka maka akan hakan.
Shikenan Appa zan yafe MASA to amma Alhaji Abdurrazak fa?, na tabbata tare sukayi k'ulle k'ullen sacemin mata da 'ya.
Eh nasani Dan yafad'ami. Shinema yazugashi akan suyi hakan, to amma wani nacin arzik'in wani aii, to shima Alhaji Abdurrazak yaci arzik'in Alhaji sunusi.
Shikenan Appa zanfad'ama Ammar karsu tura maganar kotu dama sonake agama bikinnan sannan mushiga kotu, tunda hakane zan fad'a MASA najanye amma akwai shari'ar damukeyi da Alhaji Abdurrazak akan kisan Barrister Lawan Usman D/tofa, da ake zargin su suka saka akasheshi akan wata shari'a daya tsaya da lauyansu kuma yasamu nasara.
Ranar dayaje office d'ina danyimin gargad'i kuma yaso tabbatar min dahakan saidai bodyguard d'insa yak'atseshi.
Ajiyar zuciya APPA yasauke ya ce, "a'a wannan bazan hanakaba kam Dan waccan shari'ar daban wannan daban Dan haka saidai nace ALLAH yabaka Nasara, Yakuma k'ara kareka daga Sharrin mak'iya da azzalumai, ALLAH yamuku albarka kaida sauran 'yan uwanka.
Ammeen Appa, bobo da Ammi suka amsa.
Daganan wani zancan suka d'akko.
Bobo yakalli agogo tareda mik'ewa, Ammi Appa bara nashiga Office time na wuceawa kuma inada shari'a yau k'arfe 11:30.
To ALLAH yabada nasara jarumin babammu.
'Yar dariya yayi yana k'ok'arin fita, to kugaidamin inna da Baba Dan bazan samu shiga wajensuba nayi latti.
To zasuji idan sun fito.
Ficewa yayi da hanzari, abakin k'ofa yaci karo da Idris tareda ya sulaiman zasu shigo.
Tofa kukuma daga ina haka?, bobo yay maganar yana mik'amusu hannu, gaisawa sukayi cikin musabaha.
Ya sulaiman ya ce, "yanzu nashigo muka had'u da idris zashi gaida su Ammi.
Bobo ya maida kallonsa ga idris, ya karatu idris?.
Alhmdllh yaya komai normal munata fama.
To ALLAH ya taimaka, ni bara nawuce nayi latti.
To ALLAH ya tsare yabada sa'a.
Ameen ngd.
Ya sulaiman ya ce, " yauwa idan katashi kuma Kannada lokaci plss kad'an biyo ta asibiti dama inason ganinka.
Okey babu damuwa saina shigo.
Okey saina ganka shima ya sulaiman yafad'a suna nufar ciki shida idris, shikuma bobo yafito.
Motarsa yanufa hankali kwance yabud'e yashiga yana fad'in masha ALLAH yanzu kuma sai office.
Idan ka gama dani ko?........
Da sauri bobo yakalli gefensa dan son ganin waye?.
d'aure fuska yayi tareda fad'in miyasa kina shigarmin mota?, wama yabaki izinin shiga?.
Wani murmushi Safna tasaki tareda k'ara lafewa cikin kujerar tana shak'ar k'amshin mortar da turaren bobo, tayi far da idanunta tana kallon k'yak'yk'yawar fuskarsa, aibasai anbani izinin shiga motar mijina ba, tayi maganar tana d'an d'aga gira.
Kauda kansa yayi daga kanta tareda k'ara had'e fuska, ke banason k'aramin iskanci fitarmin amiota.
Safna ta marairaice fuska harda hawaye, cikin muryar kuka ta ce, "Dan ALLAH ka saurareni wlhy magana nazo muyi kuma mai muhimmancice.
d'agowa yayi yakalleta haryanzu fuskarsa ad'aure take, ganin tana kuka saikuma tabashi tausayi, bayason mutum yashiga damuwa akansa, yad'an huro iska daga bakinsa tareda kallon jan agogon fatar dake hannunsa 8:45, batareda ya kalletaba ya ce, " nabaki minti5 Dan inada abinyi.
Hawayen fuskarta ta share ta ce, "wlhy minti5 yamin kad'an pls ka k'aramin.
d'agowa yayi yad'an kalleta saikuma ya kauda kai, saidai ki hak'ura kuma saina taso daga aiki Dan yanzu haka nayi latti, so idan nadawo zanzo nan saiki sameni amma ki tabbata magarki tanada muhimmanci, kuma ki tabbata itace magana tak'arshe dazata shiga tsakaninmu daga ita kifita arayuwata, ina d'aga miki k'afane saboda banaso nazama silar rushewar zumincin iyayenmu, sannan bazan iya wulak'anta jinin Rahma ba, dan itama bata wulak'anta jininaba.
Batareda yasake kallontaba yatada motarsa, ya ce, " sai anjima.
Jiki a sanyaye Safna ta bud'e motar ta fito, hakan yayi daidai da fitowar ya sulaiman da idris.
Suduka cikin mamaki suke kallon Safna da kuma motar bobon.
Bobo dake kallonsu ya sulaiman ta madubi yad'anja tsaki, dama abinda yake gudu kenan, ganin ya sulaiman kamar yanufoshi yaja motar da sauri yabar gidan Dan bayason tambaya, musammanma akan safnar.
Cak ya sulaiman ya tsaya yabi motar da kallo har bobo yafice daga gidan, kallonsa yadawo dashi akan Safna dake ida share hawayenta.
Rissinawa tayi tana gaisheshi sannan tara6a ta gefensa zata wuce.
Jimana ya sulaiman yafad'i yana kallonta.
Safna tatsaya harya k'araso gabanta suna fuskantar juna, lfy kuwa mike faruwa?.
Babu komai safna tayi magana muryarta nad'an rawa, shiru ya sulaiman yay yana kallonta da nazarin yanayinta, yad'an gyara tsayuwarsa yana sauke numgashi, ya ce, "keba yayar Rahma bace?.
Yayartace, cewar Safna.
To amma miya had'aki da Abdulmaleek? har kike kuka?.
d'ago ido tayi ta kalleshi, bazata iya kallon idonsaba Dan yana mata kamada na bobo, tayi shiru batareda ta iya cewa komaiba.
Ganin bazatayi maganaba ya ce, " to shiga cikin....
Da sauri tawuce batareda ko juyowaba.
Shima binta yayi da kallo cikin mamakin miye tsakaninta da bobo?, bai zargi komaiba Dan yasan bobo dodon matane, bazai ta6a zarginsa da fasik'anciba, amma tabbas akwai wata ak'asa tunda har bobo yafice daga gidan Dan bayaso suyi magana.
Yabud'e motarsa yashiga zuciyarsa cike da waswasi, shima ficewa yayi da zummar zai tambayi bobo inhar sun had'u.
++++++++++
a6angaren bobo kam yana fita office yanufa kai tsaye.
Sakatariyarsa ta gaishesa cikeda salo kamar yanda ta saba, babu k'arya yau wankan bobo yakasheta, datanada dama har pic zata masa.
Turare tad'auka tafesa tareda k'ara kallon kanta amadubi, komai daidai, tagyara zaman siket d'in material d'inta da rigar, shima mayafin aka sake salon yafawa sannan. Tanufi office d'in.
Masinja Kamilu dake la6e yana kallonta Dan yasan dolene indai oga yashigo saitayi gyare gyarennan ya tuntsure da dariya yana fad'in kai iska na wahalar da maikayan kara, kedai awahala zaki k'are yarinya, mutum kamar wannan aii kasan matarsama abar kalloce, tomizai tsaya kallo ajikinki wannan karfata.
Itadai Sakatariya Madeenaππ dabatasan masija nayiba tanufi office d'in cikin takun k'asaita da salon yanga irinta d'aukar hankali.
Bobo na zaune akan kujerarsa ta alfarma yana rubuce rubuce sakatariya tayi sallama.
Bai d'agoba amma ya amsa mata, yad'ora dafad'in waye yazo nemana?.
Lissafa masa tafarayi daga k'arshe ta ce, "ad'arare sai Alhaji sunusi da la..
Tak'are maganar da in ina.
Dukda haka bai d'agoba sannan baice komaiba itakuma baice tatafiba.
Araina na ce, " mulki kenan."
Yakai kusan minti 4 yana rubuce rubucensa saida yagama sannan yad'ago yana linke takardar.
Mik'a mata yayi, tamatso tareda rissinawa takar6a.
Yamaida bayansa yakwantar ajikin kujerarsa yana d'an lilawa kad'an, idonsa akanta ya ce, ke yanzu dakikayi shigar mutunci bakijin kinfi kima a idon mutane ba?, amma da ko kunya bak'yaji kisakko kananun kaya kina tallar jikinki ga jama'ar gari da sunan wayewa, wannan ba wayewa bace shashancine, ki kama kanki sai miji nagari yaganki yasoki, shigar banza babu abinda yake jawomuku sai mazan banza suyita bibiyarku dankoba 'yan iskanbane tofa kallon 'yan iska irinsu suke muku, ki kiyaye banason shashanci.
Kaita gyad'a duk kuma sai jikinta yayi sanyi, ta ce, "sir ngd ALLAH yak'ara girma da d'aukaka yatsareka daga sharrin mak'iya.
To amin, ALLAH yasa mudace yafad'a yana d'agowa daga kwanciyar dayayi akujera, yanuna takardar hannunta, wannan takardar kibama Kamilu yakai office d'in Barrister Kamal Abubakar, yatsaya yakaranta yabasshi Reply yakawo min.
Okey sir madeena sakatariya yafad'a tanad'an rissinawa cikeda girmamawa.
Hartakai k'ofa tajuyo sir baka buk'atar wani Abu?.
Kai bobo ya girgiza mata yana jawo laptop d'insa daga cikin jakka.
Itama ficewa tayi tana fad'in OK sir.
Tana fita ta tararda Kamilu zaune akujerar dake gefen tebir d'inta, fuska ta had'e dantasan gulmace ta kawoshi.
Ilaikuwa kallonta yayi yana 'Yar dariya, madee ince dai yau andace oga ya k'yasa?.
Harararsa tayi tareda fad'in ban saniba magananne ni dalla kar6i oga ya ce, " ka kaima sir Kamal, kuma kajira yabaka Reply ka kawo masa.
Mik'ewa yayi yakar6i takardar, to madee bara naje nadawo muyi magana, tunda har yanzu oga yak'i k'yasawa nisaina taya.
Wata uwar harara tawatsa masa, kaidai shashashane Kamilu, yoko mazan duniya sun k'are aibanga abinda zanyi da sakaren namiji irinkaba.
Tab yarinya aii ba'a fuska ake gane sakaran namijiba.
Tsaki tayi tareda mik'ewa wlhy zanje nafad'ama oga baka tafiba.
Da sauri yawuce a'a Madeena rufamin asiri Dan ALLAH, wannan zakin faman yanzu saiya hau kaina aii.
raka bayansa tayi da harara, taja tsaki tazauna tana mita.
Bobo yakalli wayarsa dake wringing ganin Ammar yasashi d'aukar wayar da hanzari, gaisawa sukayi tareda tsokanar juna kamar yanda suka saba.
Bobo ya ce, "dama kobaka kiraniba zan kiraka.
To miya faru angon Rahma?.
Murmushi bobo yayi, ya ce, " so inaga anjima zanshigo gidan saimuyi magana atsanake yanzu time d'ina k'urarrene nanda 'yan mintuna kad'an zanshiga wata shari'a.
Okey babu damuwa to saina ganka, nima inada ganawa da Governor nanda minti 10.
Hummm mutumina kuna sha'aninkufa, idan kukayi wasa duk