Showing 48001 words to 51000 words out of 104589 words
horaswa da sukeji dashi a kasar.
Basu k’ara jaddada kyawun asibitin ba kuwa, saida suka shigo babban dakin ganawan manyan likitoti, wanda aka yi masa tsari na daban kuma na musamman.
D’akin taron da komansa ya kasance na glass, cike yake da manyan likitoti way’anda suka zo daga k’asashe sassan daban daban na duniya, kowanne likita kuwa ya amsa sunansa likita, wanda kuma sunzo ne dan k’arawa junansu sani.
Koda suka shiga cikin d’akin taron amutumce suka gaisa da junansu, anutse kuma kowanne ya zauna akan kujerar dake lik’e da sunansa.
Cikin girmama junansu, batare da wani babban cin k’asa ko addini ba suka soma gudanar da abunda ya kawosu.
Sosai suka b’ata lokaci wajen meeting, wanda ya d’aukesu sama da 6hours, domin tun 8:00 am suka shiga, basu fito ba kuma sai 2:00 pm dai-dai.
Nan ma bawai sun kammala bane, breaktime ne suka samu, wanda kuma hakanne ya baya musulman cikinsu daman yin sallah’n azahar.
Bayan sunyi sallan azahar dinne kuma, suka wuce wani cafe dake cikin hospital din, abinci mai kyau akayi saving nasu.
Saidai shi Rayyern bai wani ci sosai ba, duk da cewar baiyi breakfast ba yau din, amma hakan baisa yaci abincin sosai ba.
Bayan sun kammala cin abincinne kuma, suka sake komawa meeting din.
Basu suka fito ba sai sallan la'asar.
Koda sukayi salla kuwa, sashin da sabbin na'urorin aikin su suka nufa nan akai ta gwada musu ko wanne da kuma aikinsa
Basu fito ba har sai 5:30 pm, gaba d’ayansu agajiye suke, duk da cewar dukansu sun samu k’arin haske akan abubuwa da yawa, amma gaba d’aya sun jigata, saboda zaman waje daya babu dadi.
Fitowarsu din kenan kuma, Rayyern ya kalli su Dr. Sulaiman way’anda duk gajiya ya bayyana atattare dasu.
“I hope all yours. understanding the meeting?”
Yayi maganan yana me gyara zaman suit din dake jikinsa da rike jakar laptop nashi wanda shiyasa baya son Usman P.A yayi nesa dashi.
“Yeah we understanding.”
Gaba d’aya suka had’a baki wajen amsa masa.
Kai ya jinjina cike da gamsuwa, dai-dai lokacin kuma taxi din da suka tara suka k’araso.
Rayyern kuwa juyawa yayi ya nufi motarsa, shi kansa agajiye yake ga kuma wani irin kasala dake saukar masa.
Kusan Atare suka fita daga harabar asibitin, shida su Dr. Sulaiman way’anda suka shiga cikin taxi.
Suna hawa titi kuwa suka raba hanya, inda su masaukinsu Brosko hotel Arbat l, direct hotel dinsu suka nufa, shikuwa Rayyern hanyar gidansa ya nufa.
Cikin nutsuwa yake driving dinnasa, Dai-dai yazo wajen HALAL Sapiens RESTAURANT ne kuma ya tsaida motar, tare da fitowa ya nufi ciki.
Takeaway na african dishes yayi, sai kuma na salad and Chinese dishes.
Yayi hakanne kuma saboda sometimes yafiso yana mixing food.
Gaba d’aya acikin tsarinsa ma babu Jannart, domin kuwa kwata-kwata ma ya manta da cewar yazo da MACE.
Bayan ya karb’i takeaway dinnasa ne kuma, kaitsaye ya koma mota tare da nufar gidan nasa.
Koda ya iso gidan acikin compound yayi parking motar, Ahankali yake tafiya yana me zare suit din dake jikinsa.
Hannunsa ya d’aura ajikin kofar, tana bud’ewa ya tura kansa ciki.
Ahankali ya sauk’e Ajiyar zuciya, tare kuma da ajiye ledan Halal Restaurant din dake hannunsa akan kujera.
Direct bedroom d’insa ya wuce, yana shiga kuwa ya rage kayan dake jikinsa, tare da wuce bedroom in 20mn yayi wanka.
Bayan ya fito ne kuma ya shirya kansa, cikin wasu Sabin kaya.
Wayarsa ya d’auka kana ya kuma dawowa cikin falon.
Zama yayi akan sofa tare da tank’washe k’afafunsa, Ahankali ya bud’e ledar Halal restaurant din.
Chinese dishes din ya soma ci, Yayinda ya maida hankalinsa gaba d’aya kan laptop din dake gabansa.
Daga can cikin left side bedroom din kuwa, Jannart ce kwance tayi lub akan gado.
Wanda zuwa yanzu kuma tayi matuk’ar jigata, saboda wani irin yunwa dake damunta, kasancewar rabonta da abinci tun jiya da safe, Domin ko acikin jirgi wani dan cake kawai taci.
Tun tashinta yau din kuwa babu abunda takeci sai ruwa.
Wanda zuwa yanzu har ruwan ya soma murd’arta.
Ga kuma wani shegen sanyi dake damunta.
Hannu tasa ahakali ta dafe Kanta dake d’anyi mata ciwo, her know tasan babu kowa acikin gidan, kasancewar d’azu ta fito, ta kuma gama dube dubenta amma sam bataga alaman bayan ita akwai wani rai agidan ba, har kitchine din dake cikin falon ta shiga wai ko, zata samu abunda zataci amma babu komai.
Hakan kuwa shi yasa koda tayi sallan la’asar ta dawo daki ta kwanta.
Duk yanda taso bacci ya dauketa kuwa abun ya kasa, saboda yunwa ya hanata sukuni.
Shikuwa Rayyern baiwani ci abincin sosai ba, ya mik’e tsaye, saboda yaga lokacin sallan magriba tayi.
Direct dakinsa ya koma ya d’auro alwala.
Koda ya fito car key d’insa ya dauka, tare kuma da ficewa daga Cikin gidan gaba d’aya.
Kasancewar yana dan gudu ne kuma yasa, tafiyar 13mn ne ya kaisa babban masallacin.
Yana zuwa kuwa ko mintuna 3 baiyi ba aka shiga sallan magriba.
Bayan sun idar ma haka ya zauna acikin masallacin, har saida akayi sallan Isha.
Acan gidan kuwa Jannart adaddafe tayi sallan Isha, saboda yunwan da take cinta aciki, bayan ta idar da sallan ne kuma ta sake dawowa falon.
Aikuwa cikin sa’a ta samu sauran abincin da yaci ya rage, zama tayi awajen cikin yunwa, batare kuma da tunanin komai ba ta jawo takeaway d’aya ta soma ci, sosai taci abincin har saida taji cikinta ya kama, kana ta bi da ruwa.
Tana gama cin abincin kuwa lokaci d’aya, taji wani irin kasala ya sauk’ar mata azabebben sanyin da takeji ya ɗan ragu kaɗan.
Ahankali ta mik’e tsaye tare da wucewa d’akinta, tana shiga kuwa ta fad’a kan gado, tare da jawo blanket ta rufawa jikinta, lokaci daya kuma taji wani irin bacci na fusgarta.
Shikuwa Rayyern bayan an idar da Sallan isha’n, kaitsaye hanyan gida ya nufo.
A hankali yayi paking kana ya fito tare da rufe motar, cikin yanayin gajiya, Bacci da kasala ya nufi cikin gidan,
hannunsa ya ɗaura tsakiyar kofar lokacin ɗaya ta buɗe, cikin lumshe ido ya kutsa kansa cikin falon.
Yana taku cikin alamun bacci, gaban santer table ɗin ya nufa dan ɗaukar System ɗin sa daya bari a wurin.
Da sauri ya ɗan zubawa ledodin kan table ɗin idanu,
“Yah salam”.
Ya faɗi tare dasa hannunsa ya dafe kansa.
Allah ya sani shi ya ma mance da ita gaba ɗaya sai yanzu da yaga ledodin da ya bari an sauya musu tsarin zama ta fado mishi a rai, a fili yace.
“Astagfirrullah ba ga irinta nanba na gayawa Abba yaki fahimtata, ni yaushema na kula da kainama bare wata da aka lika min gashi nan wlh na mance da ita”.
Ya ƙarashe mgnar yana k’arasa isowa gaban table din.
Yana isa kuwa idanunsa suka sauk’a akan ledan abincin daya bari, ga kuma wani takeaway dake gefe wanda aka bud’e.
Da dukkan alama kuma yasan itace taci abincin.
Kansa ya d’an girgiza tare da lumshe idanunsa, cikin d’an yanayin gajiya yace.
“Sune suka ja miki Allah ya gani ba laifina bane, na fad’awa Abba cewar ni bazan iya kula da wata mace ba, amma yasaka dole saida nazo da ita, zata takurani nasani, then ba Lallai na iya kulawa da cinta ba, cause nima ban kula da nawa cin ba.”
Ya ƙare mgnar yana mai
D’aga kafad’unsa yayi tare kuma da bud’e hannayensa alaman ko oho, bai sake bi takan takeaway dinba kuma ya wuce zuwa bedroom d’insa.
Yana shiga ya kwanta tare da buɗe laptop d’insa yana dan latsawa, ahaka har bacci ya d’aukesa.
Yayinda ab’angaren Jannart kuwa tuntuni ma, ita baccin ya d’auketa.
Washegari.
The same 7:00 am dai-dai ya gama shirya kansa, still cikin wasu tsadaddun suit, saidai colourn ya banbanta dana jiya, Domin yau din ash colour suit ya saka, sai kuma wani babban jacket mai kyau daya d’aura akai, musamman Dan tarewa kansa, masifaffen sanyin da akeyi.
Fitowa falon yayi cikin shirinsa na office tsab, zama yayi akan d’aya daga cikin kujerun falon, tare da zaro wayarsa yayi musu ordern abinci.
Laptop d’insa ya bud’e tare da d’an soma tattab’awa, yana nan azaunen kuwa yajiyo k’aran intercom, da’alama kuma order’n abincin da yayi dinne ya iso.
Ahankali ya mike tsaye tare da k’arasawa ya bud’e kofar, kaman yanda yayi hasa she din kuwa hakanne, domin abincin ne aka kawo, karb’a yayi kasancewar kuma free delivery ne, shiyasa shi juyawa ya koma ciki.
Zama yayi tare da bud’e takeaways din, way’anda yaga zai iya ci ya d’an tsakala, batare kuma da yaci sosai ba ya tashi, ya wuce zuwa HSCT centre hospital domin yasan yauma 8:00 am dai-dai zasu shiga meeting.
Fitannasa da kamar 17mn Jannart ta bud’e kofar dakin ta fito, sanye take cikin wani riga da wandon jeans, da sukayi matukar kama jikinta, kasancewar kayan masu kauri kuma shiyasa, basu wani bayyana surar jikinta sosai ba, uwa uba kuma kaurin nasu ya rage mata kaso 30 acikin d’ari na sanyin da takeji.
Ahankali ta k’araso cikin falon, sauk’e idanunta akan abincin da tayi ne kuma yasa ta sauk’e Ajiyar zuciya, domin kafun yanzu harta fara tunanin wuni da yunwa.
Zama tayi acikin falon tare da kunna TV plasma, Anutse kuma cikin kwanciyar hankali ta soma cin abincin.
Bayan ta kammala ne kuma ta kimtsa falon, tare da dawowa ta kwanta akan wata cushion, din da musamman akayi ta dan shak’atawa.
Acan b’angaren Rayyern kuwa yauma taron nasu ya dau zafi sosai, Dan yau din kamar karantar dasu akeyi, akan sikila ta yanda za’a magance ta, da kuma yanda za’a iya sanjawa mai d’auke da cutar jini.
Sosai kuma duk Doctors din suke enjoying abunda ake koyar dasu.
*Nigeria*
Mamy ce zaune acikin falon tayi shiru, saboda duk haka takejin gidan nasu babu dad’i, domin hatta Ramadan yanzu ba zama yakeyi ba, gaba daya hankalinsa, ya maidashi akan hospital dinsu, Idan ya fita baya dawowa saida yamma.
Abba da shigowarsa kenan, ganin yanda matar tasa ke cikin damuwa ne yasa shi cewa.
“Ruk’ayya.”
Ya k’ira sunanta atausashe.
Hakan kuwa shiya saka ta juyo ta fuskancesa.
“Tunanin me kikeyi haka?”
Abban ya tambaya yana me k’arasowa cikin falon.
Mamyn kuwa Ajiyar zuciya ta sauk’e, cikin dan yanayin sanyin dake dauke da kewa tace.
“Kewar su Rayyern da Jannart nake, gaba d’aya kwana biyun nan gidan duk babu dadi, ga Ramadan ba zama yake ba, dama ace Riyyam bai koma ba, to danasan abun da sauk’i, gaskiya nima yanzu kam na matsu ayi batun auren Ramadan, akawo mana Wacce zata na d’an d’ebe mana kewa.”
Mamyn ta k’are maganan cikin dan damuwa.
Abba kuwa murmushi yayi tare da zama akusa da ita, Cikin kulawa kuma yace.
“To in bandake da abunki Ruk’ayya gaki ga mijinki kuma wani kewa ne ya rage miki?”
Murmushi itama Mamyn tayi, kana cikin dan sakin fuska tace.
“Hakane amma nima ai inason kusanci da y’ay’ana matsayin kewar miji da ban ta yarama da ban ina son yarana.”
Ta ida mgnar hawaye na silalo mata da alamun akwai wani babban abin data tuna wanda ke damun rayuwarta.
Kai Abban ya jinjina tare da gyara zamansa cikin tausasawa yace.
“Badamuwa maganar auren Ramadan, yanzu muna jiran cewa daga wajen iyayen yarinyar ne, Insha Allah za’ayi bikinsu nan bada jimawa ba,
Sannan yara kuma keda Allah ya bawa Rayyern, Ramadan, ai saikice Alhamdulillah.”
Uhummm taja wani dogon numfashi tare da zuba mishi ido alamun tuni.
Shi kuwa Abba kai ya jinjina mata, tare kauda zancen da cewa.
“Amma niko tunda yaronnan Riyyam-nsra ya tafi kunyi magana dashi kuwa?.”
Murmushin Jin dadi Mamyn tayi, cikin farinciki kuma tace.
“Masha Allah,eh munyi magana dashi, washegarin tafiyarsa Ramadan ya k’ira ya kuma bani wayar mun gaisa.”
Kai Abban ya jinjina.
Dai-dai lokacin kuma Ramadan ya turo k’ofar falon ya shigo.
Akusa da Mamyn nasa ya zauna, bayan yayi musu sannu da gida ne kuma, ya sake dagowa ya kalli Mamyn nasa, cikin sanyi yace.
“Mamy kina ta zaune duk gidan babu dadi ko?”
Kai Mamyn ta jinjina masa alaman “Eh.”
Hakan kuwa shiyasa Ahankali ya d’an gyara zamansa, tare da cewa.
“Ai Mamy na fad’a miki cewar gidannan bazai yi dadi ba, matukar babu su Hamma Rayyern, duk gidan ya rame mun zama abun tausayi.”
Murmushi Mamyn tayi tare da kallonsa, domin ita ta gama sanin ayanzun me yake nufi, wanda kuma yanzu suka gama maganan abunda yakeso din da Abba.
Cikin son kawar da zancen nasa tace.
“Yauwa kiramin Riyyam nsra mana.”
“To.”
Ramadan din yace tare dayin dialing numbern Riyyam, bugu biyu ya d’aga, bayan sun gaisa ne kuma ya bawa Mamyn waya.
Mamy na amsa Daga can b’angaren Riyyam nsra yace.
“Wallahi I miss you so much Mamy na, nayi missing girkinku keda Aunty Jannart.”
Murmushi Mamy tayi kana cikin danjin dadi tace.
“Muma munyi kewarka Riyyam ya Mammyn ka da kuma Zaytoon?”
“Duk Suna lafiya Mamy yasu Abba, da Hamma Rayyern na, bani da numbernsa na k’asar Mascow.”
Riyyam din ya tambaya cike da kewa.
Mamy kuwa fuska asake tace masa duk suna lafiya,
Haka dai suka d’an tab’a hira kafun daga bisani sukayi sallama.
Acan Mascow kuwa, kamar dai jiya yau d’inma sai k’arfe biyar, su Rayyern suka tashi ataron nasu.
Ahanyarsa ta dawowa ne kuma ya biya, Halal Mascow on top restaurant ya saya musu abinci.
Koda ya dawo wanka yayi tare da dawowa, falon ya zauna, tashar CNN yake kallo, Ahankali kuma yake d’an cin abincin dake gabansa, wanda kwata-kwata shi yanzu ba wani dadin abincin yakeji sosai ba.
Bayan ya kammala cin abincinne kuma ya wuce masallaci.
Jannart din kuwa kamar jiya haka yau d’inma ta fito taci abinci, saidai bata wani ci sosai ba, drinks din kawai tasha ta koma ta kwanta.
Taso yin k’ira amma kuma tasan layinta, bazai yi amfani awannan k’asar ba sabida bata da kati ko asi, shiyasa ta hakura, gashi shi kuma tun ranan da suka zo ba ganinsa ma takeyi ba.
Wannan dalilin yasa kawai ta soma buga game, tana cikin yin game dinne kuma bacci ya d’auketa.
*Ethiopia.*
Riyyam-nsra ne zaune akan sofan, dake cikin katafaren falon Mammynsa, daga can gefensa kuwa Mammyn nasa ce, sai Kuma Zaytoon itama dake gefe.
Kakarsu Didi kuwa kwance take akan kujera.
Riyyam-nsra din ne kuma ya d’ago kansa, tare da jingina da jikin Mammynsa, cikin farinciki da kulawa yace.
“Mammy duk wani abun da muke zato da tunani ya tabbata, Mammy Nigeria tsatson mune, kuma jigonmu ce acan tushen farin cikinmu suke, wallahi Mamy ni harma naji na gaji da k’asar nan, inason komawa k’asata ta Haihuwa kuma k’asar mahaifina.”
Ya k’are maganan cikin wani irin bege me karfi dake fusgarsa.
Zaytoon dake zaune agefensa ne ta d’an langwabar dakai, kana Cikin sanyi tace.
“Har gwara kaima Riyyam kaje kaga k’asar, kaje ka ga abunda ni idanuna suka kasa ganemin kaje ka ƙamshin ƙasarmu ka shaƙi iskar ƙarmu.”
Idanunsa ya d’an lumshe kana cikin son bawa y’ar uwartasa k’arfin guiwa yace.
“Insha Allah kema zakije Zaytoon, auren Hamma Ramadan na tashi, Mamy zata je kema kuma zakiji harma da Didi, nikam naji dadin zama cikin ahalina, nayi farinciki sosai Ina kuma fatan kasancewa dasu har abada.”
Idanu Mammy ta d’an lumshe cikin kuma yanayin sanyi tace.
“Insha Allah Riyyam komai zaiyi dai-dai, watarana komai zai wuce mubi komai ahankali.”
Fuska Riyyam din ya d’an kwab’e, kana cikin salon shagwab’a yace.
“Mamy wani irin ahankali tsawon shekaru fa muna zaune ahaka, ayanzu kuma gaba d’aya komai ya tabbata.”
Gyara zama Mammyn tayi kana cikin kulawa tace.
“Riyyam nima inaji ajikina cewar watarana zanje, zuciyata ta zak’u akan naje din, saidai bansan meye zuwan nawa zai haifar ba Riyyam, duk wani abu da kake tunani ya wuce nan, har yanzu akwai k’ullin da bai gama warwarewa ba, amma nasa araina cewa Insha Allah zanje watarana, saidai kuma akwai buk’atar muyita addu’a, saboda Allah ya sauk’ak’a mana duk wani tsanani.”
Da “Ameen.” Duk suka amsa, kana daga nan kuma suka ci gaba da hirarsu.
Ahaka rayuwa taci gaba, aduniyar Rayyern da kuma Jannart, babu wanda yaga d’an uwansa tun zuwansu Mascow’n, wanda ak’alla yau kwanansu shida suna neman na bakwai kenan.
Ko yanzun kuwa Jannart dince ke zaune acikin falon, zaman nan tayi irin na tankwashe kafafu.
Yayinda take sanye da wani pencil jeans pink colour, da kuma wani t-shirt sai jacket mai nauyi da ta d’aura akan shigar tata.
Ahankali ta dan daga kanta sama, tare da kwantar da kannata ajikin kujera.
Yanayin zaman da tayi dinne kuma yasa, gaba daya duk wani shati na halittar jikinta ya bayyana, more especially breast dinta, wanda ko bra bata saka ba, gashi kuma rigar sanyin nata ya Dan bud’e kad’an.
Idan ka kalleta azahirance zakayi tunanin cewar bacci ne ya d’auketa ahaka, saidai kuma azahirin gaskiya bawai hakan bane, domin gaba daya tunaninta ya tafi ne izuwa Gida.
Ayanzu tunanin halin da Dadynta dasu Abdull suke ciki take, domin tasan koma yaya basa cikin yanayi mai dadi, gashi kuma tunda tazo k’asar batayi waya da Abba Kabir dinta ba ko su Mamy da Ramadan batayi mgn dasuba gaba ɗaya kewarsu ya dabaibayeta.
Ahankali ya turo k’ofar falon ya shigo, hannunsa rike da ledan restaurant da kuma suit d’insa.
Shigowarsa cikin falon kuwa shiya saka shi sauk’e idanunsa akanta.
D’an tsayawa yayi yana me kallonta, tun daga k’afafunta dake tankwashe, har zuwa kan lafaffen cikinta, da kuma kirjinta zuwa dogon wuyanta.
Idanunsa ya d’an k’urawa soft neck din nata, wanda yake dauke da dan siririn chain, sosai wuyan nata ke da kyau ga wani layi layi, Ahankali ya kuma dawo da kallonsa ga kirjinta.
Lokaci daya kuma cikin sauri ya janye, idanunsa daga kallonta.
Ledan dake hannunsa ya ajiye, tare da ci gaba da takowa ya k’arasa shigowa cikin falon.
Jannart kuwa jin alamun takunsa ne yasa ta saurin d’ago Kanta, karab kuwa Idanunsu suka sark’e acikin na juna.
Wanda hakan yasa taji zuciyarta tayi wani irin bugawa, lokaci d’aya kuma taji wani irin rauni ya lullub’e zuciyarta.
Ahankali tayi k’asa da kanta, tare da da hannu ta gyara zaman rigar sanyin ta.
Cikin wata irin sanyin murya mai dauke da shagwab’a tace.
“Sannu da dawowa.”
Idanunsa ya d’an lumshe
tare kuma da kawar da kansa, murya akasalance da kuma gajiya yace.
“Uhummm.”
Yanayin yanda ya amsa da Uhummm dinne kuma ya sata lumshe ido, saboda hakanan taji yanayin nasa na kasala, ya tada mata da tsikar jiki.
Ahankali Rayyern din ya soma tafiya, har yakai bakin k’ofarsa kuma saiya juyo, ya kalleta, wani abu yakeson ce mata, amma hakanan sai yaji bakinsa yayi nauyi kana shi kansa bai san me yake son ce matanba, hakan kuwa shiyasa kawai ya wuce daki.
Jannart kuw najin alamun ya