Showing 18001 words to 21000 words out of 104589 words

Chapter 7 - Tubali Book 2 Hausa Novel Complete

Unknown   

21 Dec 2024

157

ba tare da ya kalleshi ba.

Cikin sanyi yace.
“Eh dama gidansu Rayhana ce, sukace in tura”

A fakaice Abba ya kalleshi tare da cewa.
“Ka tura me?”
Kamar zaiyi kuka yace.
“Wai in tura manya na ayi mgnar aure in da gaske nakeyi, dan su gidansu daga yarinya ta gama Secondary School bazataci gaba ba, sai an aurar da ita taci gaba a gidan mijinta, to gashi ita Rayhana har taci gaba sabida, batun Hamma Rayyern baiyi aureba, shine sukace toh ai yanzu dai yayi auren sai ayi batun namun ko?”

Ya ƙare mgnar yana kallon iyayen nasu.
Mamy kam kai ta kauda tana mamakin zalama, irin ta Ramadan sam baya iya ɓoye maitarsa akan san aure.
“Wannan dai anyi jarabebben yaro”
Ta faɗa cikin ranta
Abba kuwa numfashi ya ɗan fesar tare da cewa.
“Toh su sukace ko dai kai kace?"
Da sauri yace.
“Su”
Kallonshi yayi tare da cewa.
“Banbancinka da Rayyern kenan Ramadan, kai kakan ɗan taɓa ƙarya shi kuwa duk ɗacin gsky zai faɗeta, yanzu da shine cewa zaiyi shine ya faɗa”
Da sauri yace.
“Toh Abba nine na faɗan.”
Mamy kam dariyar dake cintane ta dan subuce mata.
Ido ya ɗan zuba mishi kana yace.
“Wato kai dai ayi maka aure kake so ko?”
Da sauri yayi ƙasa da kansa.

“Toh ba damuwa tashi kaje zamuyi mgn da Baba Mauɗo.”

Wayyo Ramadan kamar ya mutu dan daɗi ai da sassarfa ya fito.
A falo ya tsaya kusa da Jannart cikin happy yace.
“My Aunty ki shirya kun kusa kai kayan aure.”
Da sauri Jannnart din tace.
“Kai haba dai iye, lallai kam abin nema ya samu kenan matar ma tsunci ta haifi kogi.”

Riyyam nsra kuwa Jujjuyawa yayi tare da cewa.
“Eh matar falke ta haifi sanda,
kai lallai akwai casu a ƙasar Kano”
Sai kuma suka bishi da ido jin ya kira Rayhana ya fara mgn da ita ya haura sama.
Murmushi Jannart tayi tare da cewa.
“Kai Riyyam wai kai baka gajiya da rawane?”
Dariya mai sauti yayi tare da cewa.
“Nida Hamma Rayyern duka ƙugunmu kamar roba yake Bama gajiya da karairayashi”
Harara ta ɗan cilla mishi tare da cewa.
“Ji sharri”.
Da sauri yace.
“Wallahi kuwa my Aunty”.
Cikin hararan wasa tace.
“A'a wlh kada kayi mishi sharri, wannan kuma da son jiki ma abu kaɗan ya kama raki yaushe zai iya jujjuyawa kamar yadda kake”

Dariyar Mamy da suka jine yasa, Jannart miƙewa da sauri ta nufi ɗakinta cike da kunya.
Ita kuwa Mamy tafiya takeyi tare da cewa.
“Gskyarki dai kare mijinki diyata”

Shima Riyyam dariya yayi tare da cewa.
“Aifa kam tana kareshi.”

Nan dai sukaci gaba da hira.

A can China kuwa gaba ɗaya wunin ranar a daki Rayyern yayi shi.
Koda ruwa bai sa a bakinsa ba,
sabida matsa mishi da cikinsa yayi duk bayan 10mnt sai ya lafa na tsawon 10mnt ɗin kana ya sake tashi.
Salla kwai ke tadashi, shima sai in ya samu ya lafa.

P.A kuwa haka ya wuni zirga-zirga a kansa.

Dare nayi kuwa ciwo yace Assalamu alaikum.
Ya tashi gadan-gadan.

Shi kuwa P.A yayi baccin gajiyan zirga-zirgan, da yayi yau din.

“Ya ilahi ya mujibadda'awati.”

Sune kalaman da bakinshi ke iya furta wa, yayinda gaba ɗaya jikinshi ke wani irin masifeffen karkarwa,
zuface take keto mishi tako ina tamkar wanda ake watsawa ruwa.

Juyi yakeyi a kan gadon yana mai yin duk wata addu'ar da tazo bakinsa.

“Innalillahi wa innailaihi rajiun".
Yayi addu'ar cikin wani irin azabebben numfashin, da yake ja tamkar ransa zai bar gangar jikinsa.
Kar-kar haka jikinsa ke rawa, so yake ya jawo wayarshi ya kira asibiti, amman ina ya kasa hakan sabida ko numfashinsa, in yaja kamar zai suma haka yakeji, cikin ya kulle yayi wani irin tauri da zafi.

A hankali ya mirgino dan matsowa zai jawo wayarsa, cikin akasi ya ture woyoyin duka biyu suka fadi ƙasa daga kan bedside drower.

Dai-dai lokacin kuma yaji cikin nasa yayi wani irin damƙa mai cike da azaba.
Wani irin duhune ya rufewa ganinsa.
A hankali yaji kamar gadon na jujjuyawa dashi...


P.A kuwa yanata baccinsa, sai asuba ya tashi, alwala yayi bayan ya fito yayi sallan asuba.
Sabida ganin kamar ya ɗan makara yasa Rayyern yayi ta tadashi kenan bai tashi ba.

Yana idawar ya fito falo.

Shiru ya tsaya tsakiyar falon.
“Bai tashi ba, ko ya fitane, bari in duba dai?”
Yayi mgnar zuciya yana mai nufar dakin.

A hankali ya dan ƙonƙosa kofar.
Shiru ba alamun mgn haka yasa ya kuma bubbugawa yana mai kiransa still shiru.

Dan tura ƙofar yayi tare da sallama a bakinsa.

Cikin yanayin firgici ya zaro ido tare da nufo kan gadon, sabida hango Rayyern ɗin da yayi a yashe bisa gadon tamkar matacce.
Cikin kidima ya haura gadon tare da ruggumeshi yana jijjigashi da kiran sunanshi da ɗan ƙarfi.
“Sir! Sir!! Sirrrrrr!!!!".
Ya ida kiran da ƙarfi cikin tsananin tashin hankali, domin gaba d’aya jikinsa ya sake yayi sanyi tamkar wanda ya mutu, sai iya cikinsa ne yake da ɗumi.
“Innalillahi wa innailaihi rajiun hasbunallahiwani'imanwakil Hamma Rayyern tashi".
Gaba ɗaya jikinsa rawa da karkarwar yakeyi.
Cikin tsananin tashin hankali ya debo ruwa ya yayyafa mishi amman ina.
Haka yasa ya buɗe ƙofar ɗakin ya fita da gudu.
Sauka kasa yayi.

Jim kaɗan sai gashi ya dawo da ma'aikatan hotel ɗin.
Kana da Driver'n' taxi.
ID card din Rayyern ya nuna musu.
Tare da Receipt's din kayayyakin da suka saya da kuma takardun Campany da matsayin nasa companies din da kasan cewarsa likita.
Haka yasa da sauri sukasa hannu suka ciccibeshi suka sauƙo aka sashi a mota, P.A ya shiga tare da jan marfin ya rufe kana Driver'n yaja.


Daga nan kai tsaye
Puhua International Hospital and clinic (PIH) Suka nufa.

A cikin motar kuwa cikin tashin hankali P.A ya kira. Dr Sulaiman yana ɗagawa yace.
“Dr Usman P.A ke mgna”.
Cikin kaɗuwa Sulaiman yace.
“Yesss na gane meke faruwa ne Usman”.
Murya a karye yayi mishi bayanin abinda ya faru ya ɗaura da cewa.
“Yanzu haka yana sume gamu a hanyar zuwa asibiti, yauwa gashi ma mun iso”
Yayi mgnar ganin sun shiga cikin asibitin.

Suna yin parking nurses Suka nufosu.
Da irin wannan gadajen ganin Ambulance ce kuma da tambarin hotel ɗin a jiki.
Suna isa driver'n na buɗe musu.
Da sauri P.A ya fito yayinda Sulaiman ke ce mishi.
Ina kun isa ka haɗani da Doctor ko nurse, duk wanda ka samu kana kada ka gayawa su Abba sai ya farfaɗo kaji ko Usman”.
Da sauri yace to kana ya fito.

Daurasa sukayi a kan gadon kana suka nufi Emergency room.
Yayinda tuni likitoci suka rufawa Nurses din dake tura gadon baya.

Da sauri P.A ya miƙawa daya daga cikin Nurses din wayarsa.
Ƙarawa a kunne tayi.
Kai take ta jinjinawa jin cikekken bayanin matsalarsa, haka yasa da sauri ta miƙa babban Doctor'nsu wayar.

Sosai Sulaiman yayi mishi duk bayani, wannan yasa suka fara bin matakan bashi taimakon gaggawa.
Bayan ya bawa nurse din wayar ta dawowa P.A da ita.

Wasa-wasa kusan awa uku ba'a fito da shiba,
hankali P.A yayi matuƙar tashi.
Sulaiman kuwa ya kirashi yafi sau goma.
Sosai shima ya karaya jin shiru ba'a fito da shi bane.
Yasa yace.
“P.A kira Ramadan ka gaya masa halin da ake ci, ni gsky abin ya bani tsoro”.

Cikin karaya P.A yace.
“To.” kana ya katse kiran.

Number Ramadan ya kira.
Shi kuwa Ramadan lokacin duk suna falon, sun gama karyawa kenan.
Kasan cewar jiya a asibiti ya kwana shiyasa yau zai wuni a gida duk da Monday ne.

Jin wayarsa na ringing ne ya kalli Jannart, dake kusa da wayar inda ya sakalata a caji.
“Waye ne”. Ya tambaya.

Dan leƙa fuskar wayar tayi tare da cewa.
“P.A ne”
Haka nan sai yaji zuciyarsa ta tsinke.
Mamy ma haka abin yake gareta.
Sai suka zubawa wayar ido gaba dayansu.
Riyyam-nsra ne ya ɗan jujjuya ya kallesu.
Yayinda sai kuma yace.
“Hamma Ramadan ka amsa mana”.

“Miƙo min wayar”.
Yace yana kalloshi
Da sauri ya miƙo masa wayar bayan ya amsa kira na biyu.
“Hello P.A ya akayi ne?”
Cewar Ramadan.

P.A kuwa Murya a sanyaye yace.
“Ramadan Hamma Rayyern ba lfy ciwon cikinsa ya tash...”

Da sauri duk suka juyo suna kallon Ramadan din daya miƙe tsaye yana cewa.
“Innalillahi wa innailaihi rajiun, hasbunallahiwani'imanwakil,
P.A, ina yake? Wanne hali yake ciki? Kuna ina yanzu? Bashi wayar!"

Gaba daya Ramadan din ya gigice.

Jin abinda yake faɗa ne kuma yasa Mamy miƙewa, jiki na rawa take cewa.

“Menene Ramadan meya faru da Rayyern? Ina yake bani wayar”.

Juyawa yayi cikin yanayi tashin hankali jin P.A na cewa.
“Muna asibitine Ramadan, a sume muka kawoshi tun safe, kuma har yanzu bai farfad’oba, nima kaina ban san halin da yake cikiba”

“Yah ilahi ya mujibadda'awati”.
Ramadan ya faɗa murya na rawa.
Mamy kuwa da sauri ta nufi side ɗinsu tana cewa.
“Abban Rayyern, Rayyern! Rayyern!!!”.
Da sauri Abba ya miƙe ya nufo kofar falon su.

Riyyam-nsra kuwa a main falon.
Gaba ɗaya jikinshi rawa ya fara.
Yayinda Jannart kuwa take binsu da kallo.
Shi kuwa Ramadan bin bayan Mamy yayi yana cewa.
“Abba Hamma Rayyern ciwon cikinsa ya tashi, tun jiya da dare yana sume har yanzu bai farfadoba, Abba ya zamuyi.”
Da sauri duk suka tsaya cirko-cirko a tsakiyar falon.

“Kira min P.A maza bani wayar”

Cewar Abba haka yasa Ramadan sake kiran P.A.
Bayanin da yayiwa Ramadan din shi yayiwa Abba.

Tashin hankalin da ba'a sa masa rana.
Jannart kuwa shiru tayi tana kallon Riyyam-nsra daya kira Mammy a waya yana gaya mata abinda ke faruwa yadaura da cewa.
“Mammy kiyi masa addu'a'n samun lfy kin san addu'arki gareshi bata da hijabi, Mammy yana cikin tsananin hali wuya bakiga yadda ciwon ke wahal dashi ba kamar zai ɗauke mana ransa”.
Ya ƙare mgnar murya na rawa hawaye na zuba.

Ita kam Jannart abubuwan sun raunata-ta.
Domin ganin hawayen Riyyam.
Dan ita haka Allah yayi idonta muddin taga hawaye idon wani to nata zai zubo, dan irin idon GARKUWA ne fareta.
Haka kuma tana da rauni abu kaɗan ke sata hawaye.
Bare kuma wannan al'amarin da tasan yana masifar sasu cikin tsananin tashin hankali.
Sautin muryar Abba tajiyo cikin rauni yana cewa.
“Rukayya ki dena yi mishi kuka, addu'arki yafi buƙata, Ramadan tashi maza dauki E-passport dinmu, Ka fara mana shirin tafiya.”
Ya ƙare mgnar suna fitowa main falon a jere.
Yayinda shima idanunsa sunyi jazir alamun tashin hankali.

Waje ya nufa.

Mamy kuwa zamewa tayi ta zauna bisa kujera hawaye na shatata tace.
“Yah Allah kaji tausayin wannan bawa naka, ka jikanshi ka yaye masa wannan azabar ka bashi lfy.
Ya Allah ka zama gatansa a kasar da ba ta saba bashi da kowa sai kai ya Allah”
Cikin raunin murya da sanyi ido na ciko da hawaye Jannart tace.
“Amin ya Allah, Mamy ki dena kuka kici gaba da yimishi addu'a”.

Riyyam ya kalli Ramadan da ya sauƙo yanzu da E passport a hannunsa.
Da sauri Riyyam yace.
“Hamma Ramadan bazakayi muku booking ta online ba ai yafi sauki.
Ka duba ka gani ina za’afi samun jirgin China da wuri Abuja ko Lagos kaga baka da nitsuwar yin tuƙi”.
Da sauri Jannart tace.
“Eh hakanfa zaifi”.

Hakan kuwa shi yasa Ramadan komawa zaune jiki, a mace ya fara bincike kan sifirin jiragen sama na kasa da kasa.
Cikin sa'a kuwa ya samu akwai jirgin zuwa China ta Abuja nanda kwana biyu.

Haka yasa ya fara hidimar neman visa nan take a wurin yayi komai.
Sabida yanzu duniya ta zama a tafin hannu.

A can harabar gidan kuwa.
Gaba ɗaya hankalin Baba Mauɗo yayi matukar tashi da jin wannan lbrin.
Hadi da Ari ma jikinsu yayi sanyi.

Suna nan Sulaiman ya shigo.
Bayan sun gaisane ya kalli Baba Mauɗo cikin kulawa yace.
“Ba komai fa, ya farfaɗo P.A ya ganshi ma, sai dai sun hanashi shiga dakin da yake”.
Toh abunka da nesa in kaji baka gamsuwa in ba gani kayi ba.

Koda suka shiga cikin gida.
Nan yayi ta kwantar musu da hankali.
Haka dai suka wuni a ranar da zulumi bini-bini su kira P.A.

Washe gari ma hakan suka wuni.
Toh da Yamma Ramadan ya tafi Abuja.
Dan Sulaiman da P.A sunce ba sai Abban yaje ba.
Tafiyar Ramadan yasan gidan ya ƙara zama shiru kamar ba mutane.

P.A kuwa shima har yau bai ganshi ba.
Sai da dare ne da ya sake zuwa asibitin sai gobe da safe yazo.
sunce ya koma masauƙinsu ne a cewarsu ma'aikatansu ke kula da maralafiya.


Ranar da Ramadan yazo Abuja da dare washe gari da safe.
Jirginsu ya daga zuwa kasar China.

Gab da magriba jirginsu Ramadan ya sauƙa.
Daga Airport ɗin kai tsaye Puhua International Hospital din yace mai taxi ya wuce dashi.
Cikin sa'a kuwa suna zuwa bakin gate din P.A na fitowa.
Nan ya sallami mai taxi shida PA Suka nufi ciki.
“Kayi sauri P.A ta ina zamu bi? Ya jikin nasa? Yana mgn?”.
Ramadan ya jerowa Usman tambayoyin.
Cikin sanyi Usman yace.
“Ko munje bazasu barka ka ganshi ba, amman sunce gobe da safe zamu ganshi. Sai dai in nuna maka dakin da yake ciki kawai."
Hakan kuwa akayi duk da kasancewar Ramadan likita basu barshi ya shigaba sabida wai ƙare a gidansa zakine.

Dole suka koma masauƙinsu.
Usman din yayi musu order'n abinci.
Bayan sunyi wonka sunyi sallane.
Suna cin abinci Ramadan ya kira Abba wanda lokacin suna tare da Baba Mauɗo nan ya ɗan ƙarfafa musu guiwa.
Kana ya kira Riyyam yace ya bawa Mamy waya.
Toh sun danji sanyi dai.

Washegari

Ƙarfe takwas dai-dai ta samesu tsaye a bakin dakin da Rayyern ɗin ke ciki.
Wanda yau kwana shi uju kenan a na hudu.
Bayan Doctor ya fitone.
Ya kalli Ramadan tare da cewa ya biyosa Office nasa.
Haka kuwa akayi.

P.A kuma yana tsaye a wurin
Tsawon kusan ,35mnt kafin Ramadan ya dawo jiki a mace.
A hankali yace.
“P.A mu shiga”.
Da sauri P.A ya mara masa baya.

Suna shiga suka hangoshi can kwance kan gado.
Lumshe ido Ramadan yayi sai ga wasu hawaye masu zafi sun zubo mishi.
Sabida tausayin Hamman nashi.
Shi kuwa Rayyern cikin yanayin mamaki yake kallon Ramadan tare da buɗe baki a hankali yace.
“Ramadan yaushe kazo”.
Hawaye na zuba yace.
“Jiya nazo Hamma Rayyern”.
Cikin tausayawa P.A yace.
“Sir ya jikin?”.

A hankali yace.
“Alhamdulillah”.
Ina hawaye Ramadan sun gaza tsayuwa, sabida ganin wani irin masifeffen rama da Hamman nashi yayi.
Cikin nan a ɗakale tamkar babu hanji a ciki.
Ya rame yayi fiyau.
Yayi wani irin sanyi ko mgn a hankali yakeyi.
“Abba ya gaisheka da jiki Baba Mauɗo yace inyi maka sannu in shafa masa kanka, Riyyam yanata kuka.
Mamy ma tanata kuka.
Aunty Jannart tace in gaisheka da jikin”.
Idonshi ya lumshe tare da cewa.
“Ayyah na samu sauƙi ai”.
A raunace.
P.A yace.
“Sir a hakan ne ka samu sauƙin?”.
Kai ya ɗan jinjina dan baida kuzarin komai.

Cikin sanyi yace.
“Visa'n mu ya kusa karewa ko.
Dama kwana ashirin da uku ne ko P.A?”.
Da sauri ya gyaɗa kai.
Cikin sanyi yace.
“Kaifa Ramadan?”.
Yana gyara masa pillow yace.
“Ƙafarka kafata ai”.

Kwanansu biyu a asibitin bayan zuwan Ramadan aka sallamesu.
Nan suka fara shirin dawowa.
Sun dai kashe kudi kam dan yanke kwanakin Ramadan.

Cikin sa'a kuwa suka samu jirgin Lagos.

Haka yasa suna sauƙa suka haɗo da kayansu da ya kai kwana bakwai da isowa.

Ƙarfe takwas na dare suka sauka a Lagos.

Sha ɗaya da rabi kuma jirgi ya debesu zuwa kanon dabo jallabar hausa.


A gida kuwa Abba da Baba Mauɗo.
Hadi da Riyyam mota ɗaya ne suka tafi Airport daukosu.


Jannart kuwa tun bayan sallan isha'i da ta fito.
Bata samu kowa a falonba ta koma dakinta

Ta kwanta tana Game har bacci ya kwasheta.


Sha biyu da rabi dai-dai suka iso gida.
Da sauri Ari ya buɗe musu gate.
Cikin kulawa Baba Mauɗo ya fito tare da matsawa gefe.
Kasan cewar dama a tsakiya sukasa Rayyern ɗin shida Abba.
Tallabeshi yayi sabida ganin kamar jiri na dibansa.
Cikin sanyi yace.
“Baba Maud’o zan iya dai”.

Da kulawa yace.
“A'a Rayyanu kaga yadda ka dawo kuwa cikin sati ɗaya”.
Isowar Ramadan ne yasa ya ɗan matsa yace.
“Ramadan tallabeshi.”
Cikin ƙarfin hali yace.
“Ka barni zan iya”.

Dole tasa aka barshi.
P.A da Riyyam kuma dama sunyi gaba da kaya tuni sun haura sama.
Ganinsu ne yasa Mamy fitowa da sauri.

Dai-dai lokacin su kuma suka iso kan barandar.
A hankali ya zauna bisa kujera tare da sauke nannauyan numfashi dan gajiya.
Cikin tsananin so Mamy ta matsoshi tare da jera mishi sannu.

“Sannu Babana. Ramadan meyasa bazaka taimaka mishi ba, kasan yadda allurar nan take mishi fa”.

A hankali ya fesar da numfashi tare da miƙewa tsaye yace.
“Mamy ba'amin allurar ba”.
Ya ƙare mgnar yana shigewa ciki.
Abba da Ramadan na biye dashi a baya.
Baba Mauɗo Kuma dasu Hadi sukayi baya.

A hankali ya fara take matakalan yana layi.
Ganin hakane yasa Abba rikoshi ya tallabeshi suka fara takawa
Fuska ya ɗan kwaɓe yana cewa.
“Zan iyafa”.

“Kaci gidanku Rayyern, bana son wannan taurin kan da ƙarfin halin dolen nan”.
Abba ya faɗa suna takawa.
Dole yayi shiru.

Suna shiga kai tsaye ɗakinsa suka shiga.
“Zan kwanta bacci nakeji”.
Ya faɗa yana kwanciya.

“Kada kayi bacci bari in kawo ma abinci”.
Cewar Mamy kai ya jujjuya tare da lumshe ido.

“Ku barshi sabida akwai mgnin dake ɗan sa bacci a magungunanshi.”
Cewar Ramadan.
Haka yasa suka fita suka bar Ramadan.
Abba da Mamy suka sauƙo.
P.A da Riyyam suka kwana dakin Ramadan.

Abba kuwa da Mamy a falonsu suka zauna suka fara tattauna wasu, mahimman abubuwan wanda dagasu sai mahalicci su suka san menene.

Washegari da safe.
Misalin ƙarfe shida Jannart ta fito.
Cikin wani tattausan material mai masifar kyau.
Ɗinkin doguwar riga yabi jikinta ya lafe.
Kasan cewarsa Royal blue, pink, yellow, and green sai ya zama kamar zanen dawisu kana yasa farar fatarta kara fitowa ras hips ɗinta sukayi cib-cib da rigar gwanin kyau.
Ta tubke jelan gashinta daya konta kan wuyanta.
Ɗan sisirin mayafi pink color ta yafa.
Sai ƙamshi take bazawa gwanin daɗi.

A hankali ta turo ƙofar falon.
Da sauri ta rusuna ganin Abba na saukowa daga sama.
“Abba ina kwana?”.
Cikin kulawa yace.
“Lfya lau Alhamdulillah ya gajiyan aiyuka".

Alhamdulillah tace kanta a sunkuye.
Kofar fita ya nufa.
Ita kuwa da sauri ta nufi.
Kitchine jin gidan ya kacame da kanshi Mamy nata hidima.

“Barka da safiya Mamy”.
Ta faɗa tana shigowa Kitchen din.

Da sauri Mamy ta juyo tare da cewa.
“Barka dai Jannart kin fito”.

Matsowa tayi tana cewa.
“Eh Mamy kawo in karɓa miki aikin”.
Ta ida mgnar tana son amsar ludayen.
Da sauri Mamy tace.
“A'a bari ma ai na gama ma”.

Toh tace tana ɗan matsawa tare da cewa.
“Mamy ya lbrin mai jiki?”.
Da sauri ta juyo tare da cewa.
“A'a na mancema ai sun iso jiya da dare.
Maza haura yana ɗakinsa jeki dubashi da jikin ko”.
Cikin yin ƙasa da kai tace.
“Ayyah ashe sun dawo”.

”Eh wlh kusan ƙarfe ɗaya suka shigo shiyasa ban gaya miki ba.”
Cewar Mamy.
Ita kuwa Jannart
“Ayyah”. Tace tare da tsayuwa.
Ramadan ne ya leƙo Kitchen din tare da cewa.
“Mamy Hamma Rayyern yace tea yake so. Akai mishi tun ɗazu ya gayawa Abba”.

Da sauri Mamyn tace.
“Toh ban saniba, Abbanku woje yayi da sauri”.

“Toh kawo in kai mishi, inaga ya mantane”.

“A'a bari ga matarsa zata kai mishi”
Mamy ta faɗa tana hada kayan tea ɗin akan tray'n.

Shi kuwa Ramadan juyawa yayi tare da cewa.
“Toh bari inje wurin Abba da P.A zamu wuce kai kayan campany”.

Sai kun dawo tayi musu tana mai mikowa Jannart ɗan madaidicin tray'n datasa komai a kai.

Amsar tray'n tayi cikin sanyi tace.
“Mamy ban san dakin shiba ai”.
Ta faɗa tanajin zuciyarta na harbawa.

Ita kuwa Mamy ba tare da ta kalleta ba tace.
“Kina haurawa sama na gefen dama shine ɗakinsa na hagu na Ramadan.
Kiyi maza ki kai mishi”.
Ta ƙare mgnar tana kallonta hakan ne yasa.
Ta juya a hankali ta fita Kitchen.

Tsakiyar falon ta fito tare da nufan steps din a hankali take daga kafafunta.
Haka nan taji zuciyarta na harbawa da

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login