Showing 57001 words to 60000 words out of 104589 words

Chapter 20 - Tubali Book 2 Hausa Novel Complete

Unknown   

21 Dec 2024

186

ta damu da shigar riga da wandon dake jikinta ba, kaitsaye ta nufi falon, kanta sanye da hulan sanyi, sai kuma wani bedroom shoe mai kyau.
Riga da wandon dake jikin nata kuwa, bak’aramin bayyana shape dinta sukayi ba, duk da cewar Suna da kauri, amma sunyi mata kyau sosai, Dan saita fito kamar irin y’an matan turawa dinnan, domin saboda tsabar zaman waje d’aya, har wani yellow da ja skin dinta yayi tsabar fari.

Ahankali ta bud’e kofar dakin ta fito.

Tana fitowa kuwa yana sauke idanunsa akanta.

Saurin yin kasa da kanta tayi, tare da karasowa cikin falon.

Shikuwa tun fitowarta ya kasa d’auke idanunsa, daga kallonta saidai fuskarnan tasa babu alaman Murmushi.

Ahankali ta zauna akan carpet, tare da nannad’e k’afafunta.

Rayyern din kuwa Ganin ta zauna ak’asan san ne, yasa shi gyara zamansa, tare da kwantar da murya cikin ladabi yace.

“Abba gatanan na shigo cikin gidan.”

Yana gama fadin hakan ya mik’a mata wayan.

Ai kuwa kaman jira take har hannayenta, na rawa wajen amsar wayar.

Tana karawa akan kunnenta, tayi Sallama.

Abban ne ya amsa mata, cikin kulawa da kuma sakin rai yace.

“Jannart ya kike ya gida, fatan komai da komai lafiya.”

Ajiyar zuciya ta sauke cikin tsananin jin dadi, tace.

“Lafiya k’alau Abba yasu Mamy, Ramadan da Baba Maud’o.”

“Duk Suna lafiya, gama Mamyn naku anan kusa bari na bata.”

Cikin jin dadi Jannart din ta jinjina kai, Jin Mamy ta karb’i wayanne kuma yasa ta karyar da wuya, cikin muryar shagwab’a tace.

“Ina wuni Mamy.”

“Lafiya kalau Jannart dinmu, wallahi munyi kewarki sosai, fatan dai kina nan lafiya.”

Mamyn ta tambayeta cike da kulawa, hadi kuma dajin dadin samun Jannart din.

“Nima nayi kewarku sosai Mamy, nayi kewarku sosai da sosai garin ba dadi sam Mamy, Ina Ramadan?”

“Ramadan yana can wajen aiki, kullum saiya tambayeki.”

Mamyn ta fad’a tana nazartar kalmar Garin ba dadi sam da Jannart ɗin ta fadi, shadar zaman doya da manja sukeyi kenan.

Jannart kuwa Kai ta kwantar kana cikin sanyi, tace.

“Ayya Mamy kice ina gaishe sa, Idan kunyi waya da Riyyam nsra ma kice ina gaishesa.”

“To Jannart Insha Allah zasuji, amma Ina dai babu wata matsala kam?”

Kai Jannart din ta d’an sunkuyar, cikin tausasa murya tace.

“Eh Mamy babu komai.”

“Masha Allah haka akeso ai, amma dai kina kulawa da sanyi, Dan naji ance sanyin garin daban yake dana kowacce k’asa.”

“To Mamy.”
Jannart din ta amsa, daga hakane kuma sukayi sallama da Mamyn, sosai Jannart taji dadin wayar da sukeyin, musamman taji zuciyarta tayi sanyi.

Acikin kaso 50 na damuwarta duka sun kau, dama matsalarta kewa ne kawai.

Ahankali ta zare wayar akan kunnenta, tare da mik’o masa.

Idanunsa dake alumshe ya bud’e tare kuma dasa hannu ya karb’i wayar.

Itakuwa Jannart maida kanta k’asa tayi, tare da sauke idanunta akan yatsun k’afarsa, wanda taga yana d’an motsa su Ahankali.

Idanu tad’an zubawa yatsun nasa, bakinta kuwa Ahankali yake motsi da alama, wani abu take son fad’a.

Rayyern dake zaune asamanta kuwa, Akasalance ya Kai dubansa gareta, karab kuwa idanunsa suka sauk’a akan saman kirjinta, kasancewar rigar da ta saka din mai d’an fad’in wuya ne, shi yasa saman kyawawan breast dinta suka bayyana.

Janye idanunsa gefe yayi, tare da maida kansa ya kwantar ajikin kujera.

Itakuwa Jannart d’agowa tayi ta kalleshi, Ahankali ta d’an had’e hannayenta waje d’aya.

Cikin daddad’an murya da kuma sanyin yanayi, mai kama da rok’o tace.

“Ummmm... Dan Allah kakiramin Abbana!!!”

Ta k’are maganan cikin seizing voice, lokaci daya kuma Idanunta suka kawo ruwa.

Yanayin yanda yaji sauti da Amon muryar nata ne, kuma ya saka shi bud’e idanunsa, tare da Kallon cute face dinta.

Ahankali ya mik’o mata wayar, ba tare kuma daya ce komai ba, ya maida kansa.

Itakuwa Jannart cikin jin dadi ta mik’e tsaye, da wayartasa ahannunta kaitsaye ta nufi dakinta.

Tana shiga kuwa tayi dialing numbern Abba Kabir.
Cikin sa’a kuwa bugu biyu wayar ta shiga.

Rayyern kuwa Ganin ta shiga daki ne, ya sashi tashi shima ya wuce nasa d’akin, bayan yayi al'wala ne kuma ya wuce masallaci.

Jannart Kuwa tanajin Abba Kabir ya d’aga kiran, ta kara wayar akan kunnenta, lokaci daya taji tamkar zatayi kuka, cike da matsanancin kewa, batare da ta iya amsa sallaman da yayi mata ba tace.

“Nayi kewarka sosai Abbana.”

Daga can b’angaren Abba Kabir kuwa, Jin muryar Jannart d’insa ya sashi lumshe ido, shima cike da tsananin kewa hadi da jin dadin, kiransa da tayi yace.

“Muma haka Jannart dina, munyi kewarki sosai, ya Mascow din, fatan duk kuma nan lafiya.”

“Lafiya K’alau Abbana, yasu Aunty Dijat dasu Hafeez, Allah nayi kewarsu sosai, har ma da Daddy na.”

Ta kare maganan cikin shagwab’a.

“Duk suna nan lafiya Jannart, suma kuma sunyi kewarki, Ina Rayyern din?”

Abba Kabir din ya tambaya, Dan waigawa bayanta tayi, kamar Wacce takesa ran ganinsa sai kuma tace.

“Yana lafiya Abba.”

Kai Abba Kabir din ya jinjina, cike da jin dadin jin muryoyin juna, haka suka sha hirarsu, bayan sun kammala wayar ne kuma ta tashi tayi Sallah.


Shikuwa Rayyern bashi ya dawo gidan ba, saida yayi sallan Isha, Koda ya shigo cikin falon, zama yayi akan sofa tare da d’aukan, abincin daya shigo dashi ya danci kad’an.

Bayan ya kammala cin abincinne kuma ya mik’e tsaye, direct dakinsa ya wuce, yana shiga ya soma rage kayan dake jikinsa.

Wani fari kal din towel ya d’aura akan waist d’insa, tare da nufar toilet kaitsaye.

Duk da cewar yana jin gajiya sosai ajikinsa, amma hakan bai hanashi yin wanka anutse ba, yana fitowa daga wankan direct gaban dressing mirror d’insa ya nufa.

Wani d’an k’aramin towel ya d’auka, tare da soma goge jikinsa dake jik’e da ruwa, sosai gargasan jikin nasa suka kwanta lub, ga wani hasken fatarsa daya sake bayyana.

Body lotion kawai ya shafa ajikin nasa, sai kuma turarensa mai dadin kamshi, bayan ya gama shafa mai dinne kuma, ya saka wani wandon boxer ajikinsa.

Duk da sanyin da ake yi kuwa, haka ya nufi kan gadonsa ya kwanta, batare da ya saka riga ko rufe kyakkyawar surar jikinsa ba.

Kwanciyar rub da ciki yayi tare da jawo laptop dinsa, ya soma dannawa.

Acan b’angaren Jannart kuwa, Koda ta idar da sallan nata, kwanciya tayi akan gado, zuciyarta cike da nishadi, saboda duk wani damuwan dake zuciyarta ya kau, yau tayi waya da Abbanta da kuma su Mamy, taji komai yayi mata wasai.

Gyara kwanciyarta tayi, juyawan da zatayi ne kuma Idanunta suka sauk’a, akan wayar Rayyern da ta ajiye akan bedside drawer dinta wayar na kawo haske alamun kira.

Da sauri ta d’an dafe goshinta, saboda ita gaba daya ma ta manta da batun wayar.
Sanin da tayi cewar zai buk’aci wayarne, kuma yasa ta tashi daga kwancen, wasu takalman ta saka tare da miƙa hannu zata jawo wayar.
Garin hakane ta amsa kiran.
Juyo fuskar wayar tayi da niyar taga wake kira sai taga ashema ta amsa kiran.
Sabon number ne, da sauri ta kalli rubutun dake ƙasan number Ethiopia ta faɗa cikin nazari, alamun daga can kiran yake.
Kiran na gab da sinkewa ta amsa da addu'ar ko Riyyam-nsra ne,
Da sauri ta kara wayar a kunne jin muryar Riyyam-nsra yana cewa.
“Asssalamu alaikum, Hamma Rayyern”.
Cikin sakin fuska da jin daɗin tace.
“Wa alaikassalam Riyyim”.

“Lahh My Aunty”.
Riyyam-nsra ya faɗi cikin jin daɗi da so da mutuntaka.
“Na'am Riyyam-nsra yasu Mammy da Zaytoon.”

“Duk suna lfy, mu Aunty nayi kewarku, kullum ina son in kiraku bani da number ku Hamma Radaman ɗan wulaƙanci sai yau ya turo min”.
Hanyar fita ta nufa tare da cewa.
“Allah sarki autan Mammy i miss u so much wlh”.
Cikin jin daɗi yace.
“wlh na fiku kewa gaba ɗaya yanzu Ethiopia ta daina min daɗi ma yaseen”.
Ya ƙare mgnar yana shiga falon Mammynsa.
Ita kuwa Jannart
murd’a handle din kofar tayi ta buɗe kana ta fito kaitsaye ta nufi dakinsa.
Suna masu ci gaba da mgn da Riyyam-nsra.

Ahankali ta murd’a handle din k’ofar d’akin nasa, tare dasa K’afarta ciki.
Cikin wani irin yanayi t...!
By
*GARKUWAR FULANI*
Sassayan numfashin ta fesar kana.
Tasa k’afarta na dama acikin d’akin, wani irin sassanyan kamshi daya daki hancinta ne, ya sata lumshe Idanunta tare da, turo kanta cikin dakin bakinta d’auke da sallama.

Sako kanta acikin dakin da tayi ne kuma, yasa idanunta sauk’a akanshi, inda yake kwance sanye da boxer ajikinsa, sai kuma laptop d’insa daya saka agaba da alama, wani aiki mai muhimmanci yakeyi.

Da sauri ta juya tare da kawar da kanta gefe, saboda wannan ne karo na farko acikin rayuwarta, da ta fara Ganin namiji haka dagashi sai yar finkilar boxer.

Rayyern kuwa dake kwance jin sallama, da kuma motsinta ne ya sashi jan blanket ya d’an rufe cinyoyinsa, tare kuma da juyowa ya kalleta.

Tsaye take amma ta kawar da kanta gefe, sannan tasa duka hannayenta akan kirjinta, da’alama kuma sanyin dake cikin dakinne yayi mata yawa.

“Meye?”

Ya fad’a yana me tsareta da idanunsa, saboda tunda suka zo bata tab’a shigowa cikin d’akin nasa ba sai yau.

Tsayuwarta ta d’an gyara tare kuma da juyowa ta fuskancesa, saidai bata yarda ta sake ajiye Idanunta akansa ba.
Cikin sanyin muryarta da akullum, take fitar da wani irin daddad’an sauti tace.

“Dama wayarka ake kira shine na kawo ma.”

Ta k’are maganar tana me d’an matsowa jikin gadon, a hankali saboda mik’a masa wayar.

“Gashi.”
Ta fad’a adai-dai lokacin da ta iso kusa dashi.

Hannunsa ya mik’a mata, still yana daga kwancen batare daya tashi ba, cikin wata irin murya yace.

“Give me.”

Mik’a masa wayar tayi, kasancewar ta sunkuyar da kanta k’asa ne kuma, yasa ta sauke Idanunta akan, wasu kwantattun gashin dake kwance akan kirjinsa, wanda kuma sudinne suka taho har zuwa, saman cibiyansa, gashi ne masu kyau da laushi, duk da cewar basu da yawa amma sun k’awata, farar fatar jikinsa sosai.
Tsaida idanunta tayi akan saman mararsa, wanda tananne gargasan sukafi yawa, kuma sun kwanta lub lub gwanin ban sha’awa, Kallon gashin jikin nasa ne kuma yasa, ta kasa sakar masa wayar da take mik’a masa.

Tana son gashin jiki sosai domin abun yana yi mata kyau, musamman awajen Namiji, duk da cewar ta saba kanin na legs din, Ya Junaid kasancewar ya saba zama da gajerun wanduna, amma bata tab’a ganin kyawawan gashi kamar na Rayyern din ba, saboda shi nasa har wasu shining sukeyi.

Rayyern kuwa dake mik’a mata hannu, Idanunta ya kalla saboda yaga ta kasa sakar masa wayar.

Ganin yanda take Kallon jikinsa ne kuma, ya sa shima ya kalli jikin nasa, saboda atunaninsa ko wani abun ta gani.

Fahimtar da yayi cewar hairs d’insa take kallone, kuma ya sashi dawo da kallonsa gareta, Cikin yanayin gajiyawa da Kallon nata yace.

“Wai duk wannan Kallon kam na menene Malama? ko cinyeni kikeson yi ne, Dan nasan zaki iya ko dai naci miki bashin wani abune kike kallonsa a jikina?.”

Maganan nasa daya fad’a ne yasa tayi saurin yin k’asa, da kanta tare da sakar masa wayar, lokaci daya kuma taji wani irin kunya ya lullub’e ta, saboda Sam bataso hakan ya kasance ba.

Jin ya karbi wayarne kuma yasa ta juyawa, da sauri ta fice daga cikin dakin.

Rayyern kuwa bakinsa ya tab’e, tare da bin bayanta da idanu, kasancewar tana tafiyar nata cikin sauri ne kuma yasa, duk wani gab’a dake jikinta motsawa, musamman big hips dinta way’anda suke da shape na burgewa, duk da cewar rigar bacci ne ajikinta, amma hakan bai hana hips din nata bayyana ba, saboda rigar jikin nata yana da santsi, ga kuma dogon gashin kanta daya sauko har bayanta.

Saurin kawar da idanunsa daga kan hips din nata, yayi tare da maida kansa ya ajiye akan pillow, akaron farko na rayuwarsa da yaji zuciyarsa na tsananta, bugawa akan wani abu na daban.

Idanunsa ya d’an lumshe tare da sauk’e Ajiyar zuciya.

Wayartasa ya kunna tare da duba mai kiran nasa, Ganin new number ne kuma ya sashi share kiran, saidai ko minti 1 ba’a rufa ba, wani kiran ya sake shigowa, Ganin kiranne kuma ya sashi d’agawa tare da kara wayar akan kunnensa.

Daga can b’angaren Riyyam yace.

“Hello Hamma Rayyern Riyyam-nsra ne.”

Ajiyar zuciya Rayyern din ya sauk’e, saboda Jin muryar Riyyam din, cikin muryarsa dake nuna d’an yanayin kasalan dake tattare dashi yace.

“Riyyam yakake yasu Mammy.”

“Lafiyanmu k’alau Hamma Rayyern, saidai nayi kewarka sosai, Mammy da Zaytoon sunce na gaisheka, kuma Hamma Rayyern mafa tuntuni nake cewa, Hamma Ramadan ya bani numbern ka, amma sai jiya ya turomin.”

Riyyam nsra din ya fad’I haka cikin tura baki.

Rayyern kuwa sanin halin surutun Riyyam dinne, yasa shi gyara kwanciyarsa tare da cewa.

“Ina Mammy?”

“Ga tanan.”
Riyyam din ya fada yana bawa Mammyn wayan, saboda dama tana gefensa.

“Assalamu Alaikum Rayyern.”

Rayyern dake kwance jin muryar Mammy, ya sashi tashi ya zauna, cikin sakin fuska ya amsa mata sallaman tare kuma da gaisheta.

Mummy kuwa cikin jin dadin jin muryar Rayyern din tace.

“Ya Mascow da kuma Surukata.”

“Lafiya lau Mammy, itama kuma tana lafiya, Zaytoon fa?”

Rayyern din ya tambaya.

Murmushi Mammy tayi kana cikin jin dadin kulawarsa agaresu tace.

“Zaytoon tana lafiya, saidai kasanta kasa ce sarkin bacci, har tayi bacci da na had’aku kun gaisa, yasu Mamynku da Ramadan, fatan duk suma Suna lafiya.”

“Lafiya lau Mammy, d’azu munyi waya dasu, Ramadan kuma yana can yanata zumudi, saboda an bashi mata, kuma naji anacewa aurensa kafun Azumi.”

Rayyern din ya fad’a yana me gyara zamansa, saboda hakanan Idan yana waya da Mammyn yakejin sakewa.

Mammy kuwa jin abunda ya fad’ane yasa cikin farinciki tace.

“Masha Allah gaskiya na tayasa murna, Allah Ya sanya alkhairi yasa ayi damu.”

“Ameen Mammy zaku zo biki ko?”

Yayi maganar kamar Wacce tazo masa afuzge, wanda kuma abunda ke cikin zuciyarsa ne ya fito fili, saboda haka kawai yakejin yana son Ganin matar ido da ido.

Daga can b’angaren Mammy kuwa murmushi tayi, cikin kuma danne damuwar dake ranta tace.

“Insha Allah zanzo mana Maud’ona Idan angayyace ni.”

Murmushi Rayyern din yayi tare da lumshe idanunsa, saboda yana jin dadi aduk lokacin da matar takirasa da suna Maud’o.
Cikin sakin rai yace.

“Mammy zaki zo mana, ai basai an gayyaceki ba saboda kema mai iya gayyatan wasu bakinne daban.”

“Hakane Maud’o Allah ya kaimu lokacin, ya kuma bamu Aron rai da lafiya, bari na barka saboda naga dare yayi, nasan awajenka ma nitsawan daren yafi haka.”

Mammyn ta fad’a cikin sakin rai.

Rayyern kuwa kansa ya jinjina, kamar Mammyn tana gabansa kuwa yace.

“Ameen Mammy saida safe, ki gaishemin da Zaytoon.”

“Zataji Insha Allah.”

Mammyn ta amsa masa, tare da zare wayar akunnenta ta kashe.

Shidinma Rayyern ajiye wayar tasa yayi, tare da komawa ya kwanta, kana ahankali ya lumshe idanunsa.

Acan b’angaren Jannart kuwa tana komawa, d’akinta kwanciya tayi tare dajan babban blanket ta rufe jikinta.

Lub tayi akan gadon tana mejin kunyan, ka mata da Rayyern din yayi tana Kallon jikinsa.

Hannayenta tasa ta rufe fuskarta.
Dan sai taji tamkar har yanzun tana gabansa ne.
Tana ahaka bacci b’arawo ya d’auketa.

*Washegari*
Yau d’in ba kamar kowacce rana ba, domin tunda ya tashi yayi sallan asuba bai sake komawa bacci ba.

6:30 am dai-dai ya gama shirya kansa cikin wasu, tsadaddun suit masu kalan light orange, suit ne masu masifar kyau da tsada, wanda suka bayyana kyawu da kwarjininsa.

Black shoe na sau ciki ya saka ak’afafunsa, tare da d’aura agogon WW a hannunsa.
Yayi kyau matuk’a musamman da ya zamana, sajen dake kwance akan fusuka kawo breakfast din da yayi order.

Amsar breakfast din yayi ya ajiye, saboda bashi da enough time ne kuma, yasa ko tsayawa ci baiyi ba, haka yasa kai ya fice sai baza kamshi yake.
Direct Babban JSC MEDICINA CLINIC MASCOW Hospital din ya nufa, domin acanne yau za suyi meeting din nasu, kasancewar kuma abunda zasuyi din nada yawa, shiyasa duk suka fito da wuri.

10:00 am dai-dai Jannart ta bud’e k’ofar d’akin nata ta fito zuwa falon.

Sanye take cikin wani straight gown mai kauri, Wacce ta kama jikinta ta zauna d’amas, sai kuma hulan sanyi da ta saka ta rufe gashinta dashi, ak’afarta kuwa wani safa ne, wanda da ‘alama yana tare mata sanyi sosai.

K’arasowa tsakiyar falon da tayi ne kuma, ya sanyata lumshe Idanunta.
Badon komai ba kuwa saidan k’amshin turarensa, da ya mamaye cikin falon, domin duk da cewar ya jima da fita amma kamshinsa na nan.

Lumsassun Idanunta ta d’an bud’e ahankali, tare da neman waje ta zauna akan d’aya daga cikin kujerun falon.

Ledan abincin daya ajiye mata din ta d’auka, tare da bud’ewa , ga mamakinta kuma yau din, chips and ketchup ne sai kuma hadin Salad da lemon tsami.

Taji dadin hakan sosai saboda dama ta gaji, da ire iren abincin kasar, wannan dalilin yasa sosai taci abincin bayan ta kammala ne, kuma ta Kai sauran ragowan kitchine, tare da dawowa falon, tv ta kunna cikin sa’a kuwa ta samu wani, tasha suna haska film mai kyau.

Komawa kan tree seater tayi, har za ta kwanta ne kuma sai idanunta, suka sauk’a akan sachet din maganin Rayyern din, dake ajiye akan kujeran.

D’aukan sachet din maganin Tayi, tare da d’an jujjuyasa saboda Ganin da tayi, saura guda biyar ne kawai ya rage maganin ya k’are.

Bayan ta duba sunan maganin ne kuma ta maidashi ta ajiye, Ahankali ta kwanta akan kujeran tare da mik’e k’afafunta, kana ta maida hankalinta duka akan tv’n.

Tana nan kwance kuwa bacci ya d’auketa, batare da ta shiryawa hakan ba.

*Nigeria.*

Abdull ne ya turo k’ofar babban falon nasu, ya shigo hannunsa rike da jakan makarantarsa.

D’an tsayawa yayi daga bakin kofar yana me Kallon, Momynsa wacce take zaune jigum acikin falon, ta d’aura hannayenta bisa kan k’uncinta.

Kansa ya d’an sunkuyar k’asa, lokaci d’aya kuma yaji hawaye sun cika idanunsa, badon komai ba kuwa saidan sanin damuwar dake, zuciyar kowannensu daga Cikin gidan.

Maida kofar falon yayi ya rufe, tare da karasowa ya zauna ad’an nesa da mahaifiyar tasa.

“Momy.”
Ya kira sunanta murya asanyaye.

Saurin d’agowa Momyn tayi saboda sam bata ji shigowar nasa ba.

“Na’am Abdull ka dawo.” Momyn ta amsa asanyaye.

Idanu Abdull din ya zubawa Momyn nasu kana cikin sanyi yace.

“Nasan akan me kike damuwa Momy, nasani akan b’atan Aunty Jannart ce, nima kuma akwai wannan damuwar acikin zuciyata, kullum dashi nake kwana nake tashi, har yau nakanji wani iri, Idan na tuna cewar wai Aunty Jannart ta b’ata, b’atan da har yau ankasa samota, tayaya hakan zata kasance Momy? Nikam nasani wasu ne kawai suka sace Aunty

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login