Showing 66001 words to 69000 words out of 104589 words
garin da kike, in baki shirya saya yanzuba Please kada mu wahal da juna ki bari sai kin shirya kafin kiyi min mgn.
đ€đ»đ„°đ Daga taku AYSHA ALIYU GARKUWA
*(GARKUWAR MA'AURATA)*
By
*GARKUWAR FULANI* âNaan please ka budâe idanunka, Dan Allah kayi numfashi!!â
Ta kare maganan cikin matsanancin kukan, dake bayyana karyewar zuciyarta da rauninta.
Hakan da Dr. Sulaiman ya ganine kuma ya sashi, kâarasowa cikin falon da sauri, hankalinsa amatukar tashe yace.
âInnalillahi Waâinna Ilaihirrajuâun, please Jannart stop crying, kiyi min bayanin abunda yake damunshi.â
Jin muryar Dr. Sulaiman acikin kunnuwanta ne kuma, ya sata dâago Kanta da sauri cikin shasshshekâan kuka, kana murya asarkâe tace.
âKa taimakamin Doctor, Dan Allah ina tsoron ya rasa rayuwarsa, numfashinsa tafiya yakeyi, tun dâazu cikinsa keyi masa ciwo, kuma bansamu maganin da zan basa ba.â
Kâarasowa wajen nasu Dr Sulaiman yayi, cikin kuma tsananin yanayin damuwa yace.
âCalm down Jannart, Insha Allah Rayyern zai samu lafiya, ki daina kuka kinji.â
Ya kâare maganar yana me lalubâo waya daga aljihunsa.
Rayyern dake rungume acikin kâirjinta kuwa, har yanzu da sauran numfashinsa, sannan kuma ahankali zuciyarsa ke bugawa, wanda kuma hakan na tafiya ne, da taimakon bugun zuciyar Jannart din da yake iya jiyowa acikin kirjinsa, kasancewar kâirjinsa da nata suna manne awaje dâaya.
Kâwarai yana so ya budâe idanunsa da suke lumshe, amma kuma bashi da kâwarin guiwar yin hakan, saboda zuwa yanzu komai na jikinsa yayi sanyi.
Jannart kuwa ahankali tasa hannayenta, ta sake matsetshi acikin jikinta, still kuma hawayen dake kwance akan fuskarta na dâiga ajikinsa.
Duk ta rudâe Yayinda Idanunta sukayi ja sosai.
Dr. Sulaiman kuwa Ganin yanda take arudâen ne yasa shi dâan rankâwafowa, kana cikin kulawa yace.
âYa kamata mu kaisa asibiti mafi kusa, domin bashi taimakon gaggawa, amma firstly yanzu sakeshi bari na fara sakashi a mota.â
Ya Æare mgnar yana matsowa kusa dasu,
Sunkuyowa yayi da niyar janye Rayyern dake jikinta.
Dai-dai lokacin kuma Rayyern Éin ya fara wani irin numfarfashin masu nauyi.
Saurin girgiza kanta tasoma yi, cikin tsoro da kuma fargaban abunda ka iya zuwa tace.
âAâa Doctor Idan na sakeshi suma zaiyi fa.
Kalli yadda numfashinsa keyifa zai dâauke gaba dâaya, Ina jin tsoro ni dai bazan iya sakeshi awannan yanayin ba, Dan Allah kakira mana Dr yazo ya duba shi.â
Ta kai kâarshen maganan nata tana me, sake rungume Rayyern din acikin jikinta, Yayinda hawayen dake kwance akan fuskarta kuwa ke ci gaba da tsiyaya, tamkar ankunna famfo.
Baki Dr. Sulaiman din ya budâe da niyar cewa wani abu, saidai kiran daya shigo cikin wayar tasa ne, yasa shi yin shiru tare da dâaukan wayan ya kara akan kunnensa.
Daga can bâangaren Ramadan jin Dr Sulaiman din ya dâaga wayan, cikin tsananin tashin hankali yace.
âPlease Dr ya ake ciki, ya jikin Hamma Rayyern din? Kun kaishi asibitin Ina fatan babu abunda ya sameshi?â
Ramadan yayi tambayan duk agigice.
Kai Dr Sulaiman din ya girgiza, kana cikin yanayin damuwa yace.
âRamadan ya zanyi Jannart ta rikâe sa gam, ta yanda babu yanda zan iya dâaukarsa, saboda tace wai Idan ta sakeshi suma zaiyi, na rasa makama Ramadan Domin ciwon nasa ya tashi sosai awannan karon.â
âInnalillahi waâinna Ilaihirrajuâun, Dr Sulaiman kayi wani abu mana, kayi wani abu kada Hamma na ya rasa ransa, Dan Allah ko Doctor ne kaje ka kira a waje.â
Ramadan ya fadi haka cikin tashin hankali.
Kai Dr Sulaiman ya jinjina, tare kuma da kadâa kansa cikin gamsuwa yace.
âOkay Ramadan amma inajin tsoron tafiya nabarsu awannan yanayin, Rayyern yana gab da suma, gashi Jannart kuma sai kuka take kamar zata shidâe, gaba dâaya na kasa iya control dinsu dukansu biyu.â
âYah Allah help us.â
Ramadan ya fadâa cikin muryarsa da tayi rauni sosai, cike kuma da tausayin dâan uwan nasa, ga kuma Jannart dake ta kuka, domin daga cikin wayar yana iya jiyo sautin kukan da takeyi.
Jannart dake rungume da Rayyern din kuwa, kwata kwata bama tasu Dr Sulaiman din takeyi ba, damuwarta shine taga Rayyern din ya budâe idanunsa.
Ahankali ta dawo da kallonta garesa, tare dasa hannunta dâaya ta tallafo habâarsa cikin kuka tace.
âDan Allah Naan ka budâe idanunka, kada ka daina numfashi, kada kuma ka cire rai da rayuwa in sha Allah, ai zaka samu sauki ko, nasan zaka warke zaka samu lafiya mu koma Nigeria lfy en Mamynka da Abbanka su ganka lfy, za kayi rayuwa kamar kowa muna bukatar ka a tsakiyar mu, dan Allah ka budâe idanunka yanzu, ka dawo cikin hayyacinka Dan Allah...â
Ta kâare maganan cikin tsananin kuka da kuma raunin zuciya, ahankali kuma tasa hannunta akan kumatunsa tana dâan bubbugawa, cike dason taga ya budâe idanunsa.
Idanu Dr Sulaiman ya zuba musu, lokaci daya kuma duk jikinsa yayi sanyi, musamman da yaga yanda Jannart din ke kuka sosai da sosai.
Maida wayar tasa cikin aljihu yayi, cikin sauri kuma ya dâauki key din motar Rayyern din, da ya gani akan table, tamkar wanda zai tashi sama saboda sauri, haka ya sa Kai ya fice daga cikin falon.
Kaitsaye wajen da motar Rayyern din yake ya nufa, yana shiga kuwa ya cilla motar kan titi, tare da nufar babban hospital din garin, wanda kuma shine mafi kusa dasu.
Jannart dake zaune kuwa duk da taji fitansa, amma bata dâago Kanta ta kalleshi ba, Idanunta har yanzu suna kan fuskar Rayyern, still kuma ko wani dâigon hawayenta dâaya, da zai fita akan fuskarsa yake saukâa.
Ahankali take yawo da hannunta dake kan habâarsa, har ta kâaraso zuwa kan kirjinsa.
Lallausan tafin hannunta ta kife akan kirjin nasa, dai-dai saitin zuciyarsa, Jin zuciyar tasa na dâan bugawa ahankali ne kuma ya sata, lumshe Idanunta tare da motsa labbâanta cikin sanyi tace.
âYa Allah ka taimaki Naanu na Yah Allah ka bashi lafiya, kasanya juriya acikin rayuwarsa, Allah kagani bamu da kowa anan saikai, Kai ke kulawa damu akoda yaushe, Ya Allah yauma ka kula damu, ka saukaka mana tsanani izuwa sauki ya Allah ka rufa min asiri ka bawa Naanu na lfy.â
Takai karshen maganan hawaye yana me shatata akan fuskar nata.
Rayyern dake kwance ajikinta kuwa, duk wani abu da take fadi yana jinsu acikin kunnuwansa, saidai kuma yakanji kalaman nata da sautin amon muryar nata tamkar acikin mafarki, saboda gangar jikinsa ne kawai take wannan duniyar, hankalinsa kuwa ya tafi izuwa wata duniyar ta daban.
Suna ahakanne kuma kâiran Ramadan ya shigo cikin wayar Rayyern din dake gefe, Ganin sunan Ramadan ne kuma, yasa ta dâaga wayar da sauri tana kâarawa akan kunnenta, ta sake fashewa da kuka, still cikin muryar sheshshekâa tace.
âRamadan har yanzu baidawo cikin hayyacinsa ba, na shiga uku Ramadan banason wani abu ya sameshi, duk jikinsa rawa yakeyi, gaba daya ya fita ahayyacinsa, Ramadan ya zanyi....â
Sautin kukan nata ne yasa Ramadan dâan rumtse idanunsa, zuciyarsa cike da damuwa, da kuma tashin hankali yace.
âZai dawo Hayyacinsa Aunty Jannart, Insha Allah nan bada jimawa ba Hamma Rayyern zai dawo hayyacinsa, ki daina kuka dan Allah, ki kula dashi kafun Dr. Sulaiman ya dawo.â
Cikin kukan ta jinjina kai, saidai ta kasa cewa komai sai sheshshekanta da yake tashi.
Acan Nigeria din kuwa Mamy dake gefen Ramadan, itama hawaye takeyi gaba daya ta shiga cikin damuwa.
Haka ma Abba wanda ya zauna yayi ta gumi, abubuwa da yawa yake sakâawa acikin zuciyarsa, kallo daya kuma zakayi masa kafahimci cewa yana cikin matsananciyar damuwa.
Kasancewar kuma Ramadan din a hands free ya saka wayar ne, yasa dukansu suke iya jiyo kukan Jannart din, harma da nishin Rayyern dake tashi kâasa kâasa.
Ahankali Abban ya dâago ya kalli Ramadan, da hannu Yayi masa alama akan ya bashi wayar.
Ganin hakanne kuma yasa Ramadan mikâa masa, kara wayar Abban yayi akan kunnensa, cikin son bâoye damuwa da kuma tausasa murya yace.
âJannart.â
Jannart dake zaune kuwa jin muryar Abban acikin wayanne yasa ta dâan zabura, cikin rawar murya tace.
âAbba Hamma! Hamma!! Abba jikinsa yana ta bâari, ga numfashinsa ya kusa dâaukewa, ciwo yakeji sosai, Dan Allah Abba ka taimakeshi.â
Idanu Abban ya dâan lumshe saboda tsananin tausayin yarinyar da yaji, domin ayanzu kukan ta yafi komai dâaga musu hankali sabida yanaga tashin hankali da take ciki zai hanata yin abinda ya dace.
âJannart, Jannart!!â
Abban ya kira sunanta ahankali.
Yanda taji sautin muryar Abban ne kuma yasa ta, dâan tsagaita kukan nata tare da amsawa.
âKiyi shiru kinji ki kwantar da hankalinki, ki daina wannan kukan In sha Allah Rayyern zai samu lafiya, ki daina kuka ki zama mai juriya akan ciwon sa kinji ko Jannart, yanzu adduâa ya kamata ki masa, ki daina kuka domin yawan kuka zai iya jawo miki wata matsalar kema, saboda haka ki share hawayenki Allah nanan kuma zai Iyar muku.â
Abban ya fadâi haka cikin son bata kâarfin guiwa.
Jin hakanne kuma yasa ta sanya hannu ta share hawayenta, cikin nuna biyayyarta agaresa tace.
âTo Abba.â
Kai Abban ya jinjina cike da yabawa halin yarinyar, kana Ahankali ya zare wayar akunnensa ya kashe, saboda shi dâinma dazai samu dama, kukan zaiyi Domin har abada bazai tabâa son ace wani abu ya samu Rayyern din ba, haka kuma bazai so ace Rayyern yabar duniya batare da ya saukâe wani kâaton nauyin dake wuyansa ba, Lallai zaiso ace Rayyern ya rayu, har zuwa lokacin da gaskiya zatayi halinta.
Baya ga haka kuma Rayyern din shine komai nasu, shine AHALIânsu kuma kâashin bayansu.
Ahankali ta zare wayar daga kan kunnenta, tare da lumshe Idanunta tana mejin yanda Rayyern din ke sake shigewa cikin jikinta, Yayinda ya saka duka hannayensa biyu ya rungume cikinta gam.
Wanda hakan da yayi din kuma alamace dake, nuna cewar yanajin ciwo sosai.
Acan bâangaren Dr Sulaiman kuwa.
Koda yaje EUROUPEAN Medical senter mascow (E.M.S) din emergency Doctor ya nema, bayan ya shaidawa Doctorn matsalan Rayyern din ne kuma, suka nufo gidan kaitsaye.
Suna isowa kuwa ko gama dai-dai-ta parking ba suyi ba, direct suka nufi cikin gidan Dan bawa, Rayyern din agajin gaggawa.
Jin motsin shigowar su Dr Rayyern dinne, kuma ya sata dâago da kanta ahankali ta kallesu.
Dr James ne wanda Sulaiman din ya dâauko, ya kâaraso cikin falon tare da matsowa inda suke, Cikin kulawa da kuma harshensa na turanci yace.
âMadam ko zaki iya matsawa na dubashi, saboda akwai bukâatar sai nayi checking nasa sosai.â
Idanunta da sukayi jajur ta zubawa farin baturen likitan dake gabanta, kaman mai nazartar wani abu, Cikin sheshshekâan kuka kuma ta girgiza masa kai, murya araunace tace.
âKa dubashi ahaka saboda bazan iya barinsa ba, inaji ajikina Idan na barshi mutuwa zaiyi, Dr ka kalla fa numfashinsa seizing yakeyi, Dan Allah kayi sauri ka dubashi ahaka kada wani abu ya sameshi.â
Kai Doctorn ya girgiza saboda yasan duba, patient din ahaka ba abu bane da zai yiwu, saboda akwai bukâatar dole sai anyi checking dâinsa, saidai kuma da gaske yaga Jannart ba zata tabâa bari a dubasa, ba tare da yana jikinta ba.
Sanin cewar Idan aka kâara wasu mintuna ahaka komai zai iya faruwa ne, yasa doctor din matsowa, ya dâaura hannunsa akan wuyar Rayyern, tare dasa wani abu mai kaman naâura adai-dai kan cikin Rayyern din.
Bayan ya gama saka abunne kuma, ya dâago ya kalli Jannart dake hawaye, shikam har acikin ransa yana me mamakin kâarfin halinta.
Wani kâwayan magani ya bâallo daga cikin wani sachet, mikâa mata maganin yayi kana Cikin harshen turanci yace.
âKisa masa wannan akâasan harshensa, saboda zaifi saurin yi masa aiki, zai kuma yi tasiri acikin jijiyoyin jikinsa.â
Da sauri ta jinjina kai tare da karbâan kâwayar maganin, kasancewar har yanzu Rayyern din na kwance ajikinta ne kuma, yasa ahankali ta juyo da fuskarsa, ya zamana suna fuskantar juna, fuskar tasa da tayi ja sosai ta dâan kalla, cikin sanyi da kuma tsananin tausayawa, tasa hannunta na dama ta saka mishi cikin bakinsa, dâaya daga cikin yatsunta tasa ta dâan dâaga harshensa, tare da tura kâwayan maganin akâasan harshen nasa, kamar yanda doctor dâin ya bukâata.
Ganin nan take maganin har ya soma narkewa, acikin bakin nasa ne yasa ta, zare yatsarta ahankali tare da zubawa kyakkyawar fuskarsa idanu.
Lokaci dâaya har rama ta bayyana akan fuskar tasa, Yayinda saman fatar idanunsa sukayi wani irin ja, haka ma labbâan bakinsa, da tsabar ja tamkar zaka latsa jini ya fito.
Dogon hancinsa da ya tafi straight ta kalla, hadi da Zara zaran gashin idanunsa wanda sukayi wasar wasar.
Wani irin hawayen tausayinsa ne ya cika Idanunta, wanda yasa ahankali tasa hannu ta shafa fuskar nasa.
Saukâan dâumin hannunta akan fuskarsa ne kuma, ya sashi saukâe wani irin ajiyar zuciya.
Ahankali kuma ya sake shigewa jikinta, batare da sanin abunda yakeyi ba kuwa, ya cusa fuskarsa acikin kâirjinta, domin ananne kadâai Idan ya saka kansa, yakejin nutsuwa na saukar masa, duk da baisan cewa akan kâirjinta yake ba, amma aduk sanda ya dâaura kansa akan kirjin nata, yana iya jiyo sautin bugun zuciyarta, hakan kuwa na taimakawa zuciyarsa, wajen ci gaba da bugawa amaimakon tsayawa da take kokarin yi.
Jin yanda ya saka fuskarsa acikin kâirjinta ne kuma, ya sata lumshe Idanunta, tare da dâaura hannunta akansa, ahankali ta shiga tura yâan yatsun hannunta, acikin tarin sumar kansa.
Dr James kuwa fatar jikin Rayyern din ya tsurawa ido, ganin yanda kowacce gashin jikinsa ke mimmikewa ne, kuma ya sashi zare wannan abu mai kaman naâurar daya likâa masa acikinsa.
Ahankali ya koma kan kujera ya zauna, saboda yasan zuwa yanzu maganin daya bawa Rayyern din ya soma aiki, kasancewar yasan maganin yana da kâarfi sosai.
Ganin Dr James din ya zauna ne, yasa Dr. Sulaiman shima ya zauna.
Kallon Dr. Sulaiman James din yayi, cikin son bashi kâwarin guiwa yace.
âZaiyi sauki domin maganin dana bashi yana da karfi sosai, just 20mn zai samu relief donât worry.â
Ajiyar zuciya Dr Sulaiman ya saukâe, Dan bashi da wani burin da ya wuce haka.
Duk idanu suka tsurawa su Rayyern din, wanda har yanzu jikinsa ya kasa daina bâari.
Jannart kuwa habâarta ta dâan dâaura akan Rayyern din, tare da zubawa hannunsa dake kan marar tasa idanu.
Ganin yanda yake ta danna marartasa ne, yasa ahankali ta dâaura hannunta akan nasa hannun.
Aikuwa kamar jira yake hakan ya kasance, cikin sauri ya kamo hannun nata ya dâaura akâasan nasa.
Akâagauce ya shiga danna hannun nata asaman cikinsa, wanda da dukkan alama anan yafi jin ciwon.
Ahankali hankali kuma ya shiga tura hannun nata zuwa kan mararsa, har dai ya zamana yatsunta na dâan tabo boxer dâinsa, maâana asalin kan mararsa, wanda hakan yasa take iya tabâo, kwantaccen gashin dake saman marar tasa.
Ahankali ta lumshe Idanunta, da suke fitar da wasu irin hawaye masu zafi, duk da tasan cewar agaban su Dr Sulaeman suke, amma ta kasa janye hannunta daga inda ya kai mata, kuma Koda ace zatayi hakan ma, to ba zata samu dama ba, saboda wani irin riko da yayiwa hannun nata.
Sake damkâe hannun nata yayi, cikin kuma zafin ciwon da yakeji ya danna tafin hannunta akan mararsa da kâarfi.
Atake ya saki wani irin nishi da kuma Ajiyar zuciya mai karfi, still cikin gigita ya sake danna hannun nata akan mararsa, wanda ayanzu har tana iya jiyo tudun marar tasa.
Idanunta ta sake lumshewa, fahimtar abunda yake so dinne kuma yasa, Ahankali ta soma yawo da hannunta akan marar tasa, tare da dâan daddanawa tana yi masa massaging jin yanajin sassaucin ciwon yasa cusa hannunta cikin boxer Éinsa kadâan yana mai danna hannunta.
Dai-dai hannunta ya iso saman penis dâinsa ne kuma, ta dâan danna kadâan, batare da ta bari kuma hannunta ya tabâa penis din nasa ba.
âHyyyyhhhhhhhhhimmâ.
Haka da tayi dinne kuma yasa shi, sauke wani irin nannauyan Ajiyar zuciya, tare da jan dogon numfashi, ya sake shigewa cikin jikinta.
Bayan ya dâaura hannunsa akan nata hannun.
Haka ya dinga danna hannunta akan marar nasa, yana me sauke Ajiyar zuciya akai akai, idanunsa dake arufe kuwa, ahankali suka soma matsawa, saidai yanajin yanayinsa tamkar wani dâan maye.
Ahankali ya gyara kwanciyarsa, tare da juyawa ya kifa kansa akan cikinta, saidai kuma still har yanzu hannunta na kan mararsa, tana dâan mammatsa mishi.
Dr James ne ya kuma Kallon Dr Sulaiman da yayi jigum.
duk alamomin damuwa sun bayyana akan fuskarsa.
âCalm down Dr, zai samu sauki na fadâa ma, saidai maganin dana bashi yana sa bacci, amma daya farka komai zai dawo normal, saidai amma kada yayi wasa da maganin, ya zamana yana sha kullum kuma akan lokaci.â
Dr James din ya fadi haka yana me mikâawa, Dr Sulaiman magungunan Rayyern din.
Kâarbâan maganin Dr. Sulaiman yayi cikin kuma nuna godiyarsu yace.
âInsha Allah zamuna kulawa wajen shan maganinsa, mun gode sosai doctor.â
Kai Dr James ya jinjina tare da mikâewa tsaye, hannunsa rike da yâar jakar maganinsa, ya kalli Jannart da take rungume da Rayyern din.
âDonât worry madam mijinki zai warke nan bada jimawa ba, amma kina kulawa dashi sosai akan shan magani.â
Kai Jannart din ta jinjina masa alaman to.
Shikuwa Dr Sulaiman dâan kallonta yayi, cikin tausasawa yace.
âBari nayi dropping dâinsa Iâm back, ko akwai abunda kike bukâata?â
Still kanta ta girgiza alaman babu, saboda duk kukan da tayi ya galabaitar da ita.
Dr Sulaiman kuwa bayan Dr James yabi, suka fice daga falon.
Fitar nasu ne kuma yasa ahankali ta dawo da kallonta ga Rayyern dâin.
Wanda yayi kwance lub ajikinta.
Idanu ta zuba masa saboda zuwa yanzu, duk wani karkarwa da jikinsa keyi ya bari, sannan numfashinsa ya dâan dai-dai-ta, Dan ahankali yake sakin ajiyar zuciya, saidai kuma har yanzu ya kasa sakin hannunta dake kan mararsa.
Kyawawan Idanunta masu dâauke da ruwan hawaye, ta tsayar akan kyakkyawar fuskarsa.
Idanunsa dake marairaicewa ta kalla, wanda sukayi yanayi dana dâan maye ko kuma maijin bacci.
âNaan!!â
Ta kâira sunansa da wata irin cool voice, mai ratsa jiki da jijiya.
Muryar da amon sautinta ya ratsa cikin kunnuwansa, duk da cewar baya cikin yanayi mai dadi amman yajita kuma ya gane muryarta ne.
âNaan!!!â
Ta sake kiran sunan nasa akaro na biyu, saidai kuma ganin bai amsa ta bane, yasa ahankali ta sake tura dâayan hannunta cikin sumar kansa.
Ajiyar zuciya mai nauyi ta ji ya saukâe, ahankali kuma taji ya sake matsewa ajikinta, tare da gyara zaman hannunta dake cikin boxer dâinsa.
Sassanyar Ajiyar zuciya Itama ta saukâe akaron farko, tun bayan tashin ciwon nasa, da taji nutsuwa ya dâan saukâar mata.
Sakâe mikâe kâafafunta tayi, tare da dâan rankâwafowa kansa ahankali.
Idanunsa dake ta narkewa ta kalla.
Hakan kuwa shiya kâarawa zuciyarta wani irin