Showing 63001 words to 66000 words out of 104589 words
abubuwan yanayinsu ne cikin rashin k’arfin jiki, da kuma tsananin dauriya saboda duk jikinsa babu karfi.
Fitowarsa daga wankan kenan ya saka wani, farin dogon wando da kuma farin riga, kasancewar bashi jin karfi ajikinsa sosai ne kuma yasa, ko gama mak’ala bottom din rigar baiyi ba, haka ya juya ya fita.
Adaddafe yake tafiya har ya iso waje, motarsa ya shiga tare da kunnata, kaitsaye ya nufi masallaci.
Yana zuwa kuwa ana shiga Sallah.
Hakkan yasa da d’an hanzari yazo yabi jam’i.
Bayan an idar da sallan magriban ne kuma, ya d’an matsar da jikinsa gefe tare da jingina bayansa ajikin bango.
Idanunsa ya lumshe tare da soma ambaton sunan Allah acikin zuciyarsa.
Sannu ahankali yakejin ciwon na taso masa, tamkar wanda ake yakutsa marar nasa haka yake ji.
Yana nan azaune kuma har aka kira sallan isha, Ganin anan kokarin tsaida sahu ne kuma, ya sashi mik’ewa shima ya gyara tsayuwarsa.
Komai nasa acikin k’arfin Hali yakeyi, saboda ciwon na k’ara taso masa akowanni second, hakan yasa Sallan kawai yakeyi amma ba tare da wani ishashshen nutsuwa ba, dai-dai sunkai Sujjadar raka’a ta uku ne kuma, yaji gaba d’aya duniyar na soma juya masa, Yayinda gaba d’aya jikinsa ya d’auki karkarwa, saboda wani irin matsanancin ciwo da yakeji, sosai yakejin ciwon wanda har hakan ya sashi kasa d’agowa daga sujjadan da yayi, har tsawon minti d’aya kafun ya iya d’agowa.
Adaddafe dai haka ya jure har aka idar da sallan, a sujjadarsa ta k’arshe ne kuma ya lumshe idanunsa, tare da mik’a neman taimakonsa wajen Allah.
Ana idar da sallan ya fice daga cikin jam’in, Cikin yanayin dauriya da cije baki, ya fice daga cikin masallacin, tare da nufan wajen da ya ajiye motarsa.
Acikin zuciyarsa kuwa addu’a yakeyi, ahaka ya shiga cikin motar tasa, ya nufo gida.
Kwata kwata ba acikin nutsuwarsa yake ba, wannan dalilin yasa shi yin wrong driving, ahaka har ya dawo gida.
Da k’yar ya iya shigar da motarsa cikin gidan, ko gama dai-dai-ta parking din motar baiyi ba ya fito, yana sako k’afarsa waje kuwa yaji ciwon cikin nasa na ci gaba da k’aruwa.
Ahankali yake taka k’afansa da yakejin kamar ba zasu iya jurewa d’aukan nauyinsa ba, Saboda ayanzu ciwon ya tashi masa gadan gadan, har takai ga ko bud’e idanunsa ya kasa yi, jikinsa yayinda gaba d‘aya jikinsa ke rawa sosai tamkar wanda aka jonawa shocking wani irin masifeffen zogi da raɗaɗin ciwon yakeji, ahaka ya nufi cikin gidan ido a rumtse dan in ya buɗesu ma jiri ke dibarsa duhu na rufe ganinsa.
*Jannart*
Ahankali ta zare hijab din dake jikinta, tare da mik’ewa tsaye.
Yauma sanye take cikin riga da wando na bacci, the same irin shigar daren jiya tayi, saidai kalan kayan na yau ya banbanta dana jiyan, saboda yau kayan nata pink colour ne, suna da matukar laushi kuma sosai, Yayinda suka bi jikinta suka kwanta.
Ahankali tasa hannunta ta d’an shafa cikinta dake kukan yunwa, saboda yau tun safe bata sake saka wani abu acikinta ba.
Sanin da tayi cewar zuwa yanzu baikai ga dawowa, amasallaci bane yasa kaitsaye ahaka ba tare da tasa wani mayafi ba ta nufi falon.
Dai-dai lokacin shi kuma Rayyern ya shigo, cikin juyawan kai da tsananin azabar ciwo, ya fad’a saman doguwar kujera, batare dako takalman dake k’afansa ya cire ba.
Hannayensa duka biyu ya d’aura akan cikinsa, tare da rumtse idanunsa da k’arfi yayinda gaba daya jikinsa ya debi karkarwa wani irin taune lips ɗinshi duka tamkar zai tsinkesu wata iriyar fitinenneyar zufa ce mai tattare da tsananin azaba da yanke rai da rayuwa yake tsastsafo mishi tako wanne hudan gashin jikinsa.
Cikin azaba yake fitar da numfashin wahala.
Ahankali ta bud’e k’ofar d’akin ta fito, hannunta rik’e da wayarta, sako kanta cikin falon da tayi, yayi dai-dai da sakin wani irin nishi da yayi.
“Hayhhhhhhhhh”.
Wanda hakan yasa cikin sauri ta d’ago Kanta ta kalli inda yake kwance.
Wani irin mummunan harbawa taji zuciyarta tayi, wanda hakan yasa ta tsura masa idanunta, cike da tsoro take Kallon yanda gaba d’aya jikinsa ke rawa.
ad’an tsorace ta shiga takowa cikin falon, har ta k’araso inda yake kwancen, idanunsa dake arumtse ta kalla, kana ta dawo da kallonta ga jajayene labb’an bakinsa, wa y’anda sukayi ja sosai, sai b’ari kuma sukeyi tamkar wanda yake fama da zazzafan zazzab’i.
Ahankali ta d’an sunkuyo da kanta garesa, cikin tsananin fargaba da kuma tsoron abunda zai faru ta k’ira shi da wani sunan da taji bakinta ya ambata kawai.
“Naan! Naan!!”
Sam baya cikin hayyacin da zai iya amsa mata, duk da yaji sautin muryarta acikin kunnuwansa kuma ya fahimci shi din take kira da da sunan Naan din, amma azaba da kuma zafin ciwon da yakeji ya wuce tunaninsa ayau din.
Jannart kuwa ganin bai amsa ta ba, ga kuma yanda jikinsa ke ta karkarwa yasa, ta sunkuyowa tare da matsowa kusa dashi sosai, Ahankali ta d’aura hannunta akan forehead d’insa, wanda jijiyoyin kansa suka bayyana rad’o rad’o.
Jin da tayi jikinsa babu zafi ko kad’an ne, yasa ta Kallon hannayensa daya daura akan cikinsa ya damƙe mararshi.
Duk jijiyoyin jikinsa sun mimmik’e, Yayinda fuskarsa tayi ja sosai.
Ahankali ta sake matsowa kusa dashi, lokaci d’aya kuma Idanunta suka ciko da hawaye.
Saboda ta fahimci cewar acikin biyu d’aya ne ya faru, ko ciwon cikinsa ne ya tashi, ko kuma ciwon kansa wani irin masifeffen raunine ya rufeta lokaci ɗaya ta tuno yadda hankalin ahlinsa ke mamummunan tashi in sun ganshi cikin makamancin wannan yanayin.
“Hamma Naan ka amsa mana meke damunka?.”
Ta fad’i hakan araunace tare dasa, hannayenta ta zare masa takalman dake k’afarsa.
Tana mai jin hawaye na silalo mata cikin rawan murya mai cike da rauni tace.
“Innalillahi
Naan me yake damunka? Kanka ne yake ciwo? ko cikinka? Dan Allah Hamma Naanu ka fad’amin kaji, please kaga duk jikinka rawa yakeyi.”
Jannart din ta fadi haka cikin yanayin tashin hankali, da kuma tsoro hadi da fargaban kada ciwon cikin nasa ne ya tashi.
Saboda taga yana dafe da cikinsa dayin murkususu, ga kuma wani irin numfarfashin da nishin yake sakewa akai-akai.
Ganin yanda yake ta had’a zufa ne kuma, yasa ta matsowa gab dashi, har hucin numfashinsa na dukan fuskarta.
Zip din dan Jacket din dake jikinsa ta zuge k’asa, tare dasa hannayenta duka biyu akan kirjinsa, wani irin rauni da tsananin tausayinsa takeji, d’aura hannunta da tayi akan kirjinsa ne kuma, ya sata jiyo yanda zuciyarsa ke bugawa da k’arfi-k’arfi.
Wannan dalilin yasa araunace ta fashe da kuka, cikin kukan nata ne kuma ta soma kokarin zare masa jacket din dake jikinsa.
D’an matsowa tayi garesa sosai.
Hannunta tasa ta tallaboshi da iya ƙarfinga ta d’an d’agosa daga kwancen tayi, tare da zama abakin kujeran, Ahankali ta d’aura kansa akan cinyarta, cikin sakin sheshshek’an kuka tace.
“Dan Allah Naan ka bud’e idanunka, ka kalleni kada wani abu ya sameka, ka bud’e idanunka dan Allah...”
Ta k’are maganan tana kuka sosai, tare da d’an jijjigasa saboda, zuwa yanzu ta tsorata sosai da yanda taji numfashinsa, na kokarin d’aukewa, ga kuma yanda jikinsa ke ci gaba da rawa, zufa kuwa ya keto masa takota Ina.
Ganin kukan bazai kaita bane kuma, yasa ta tashi kaitsaye ta nufi d’akinsa, Dan nema masa magani.
Saidai Koda ta shiga cikin d’akin, neman duniya tayi amma bata ga Koda kwayan magani ba, hakan yasa ta d’auko wayarsa ta fito.
Ganin abunda yakeyi dinne kuma yasa ta, sake rudewa atsorace ta taho kansa.
Saidai kafun ma ta k’araso har ya tafi k’asa zai fad’o daga kan kujeran, yanata jujjuya jikinsa hannayensa ko na dafe da cikinsa.
Wani sabon kuka ne ya sake kwance mata, cikin matsanancin tausayinsa da takeji, ta k’araso wajen, tare da durk’usawa ta zauna.
Hannayenta duka biyu tasa ta d’ago kansa zuwa kan cinyarta.
Arud’e take fad’in kalmar innalillahi wa’inna Ilaihirraju’un Hasbunallahiwani'imanwakil Naan! Naan!! Hamma Naanu!!!.
Shikuwa Rayyern da ya gama fita ahayyacinsa, jinsa acikin jikinta ne yasa shi sake matse jikinsa waje d’aya, tare da tura kansa acikinta, hannunsa na dama kuwa d’aurasa yayi akan cikin nata, duk ya zauce ya fita a hayyacinsa.
Wani irin numfarfashin azaba kawai yake fitarwa, duk da cewar yanajin duk abubuwan da take fad’a, amma bazai taba iya mayar mata da martani ba, saboda baya ko tantama yana bude bakinsa, gaba d’aya numfashinsa zai d’auke.
Jannart dake kuka kuwa Ganin yanda yake ta shigewa cikin jikinta ne, yasa ahankali ta d’aura hannunta akan cikinsa, rashin sanin abunda zatayi masa dinne kuma, yasa asanyaye ta soma shafa cikin nasa, tare da d’an dannawa kad’an kad’an.
Hakan da tayi d’inne kuma yasa shi jin, tamkar tana danne masa ciwon ne, amatuk’ar wahalce ya d’aura hannunsa akan nata, tare da sake tura hannun nata akan cikinsa, har yakai ga tana tab’o kan mararsa.
Kasancewar baya cikin hayyacinsa, shiyasa duk baisan me yakeyi ba, Haka ita Jannart dinma bata da wani nutsuwa, kuka kawai takeyi tare da sake ci gaba da danna masa cikin.
Almost 10mn suka d’auka ahaka, saidai har yanzu babu wani abu daya sanja, saima jikinsa dake k’ara sak’ewa, domin hatta numfashi yanzun da k’yar yake furgosa.
Ganin hakanne kuma yasa Jannart din k’ara rud’ewa, wayarsa dake hannunta ta kunna, cikin rashin sanin abunyi ta dannawa numbern Ramadan kira.
Adai-dai lokacin kuwa Ramadan din zaune, yake acikin falon sama yana aiki a laptop d’insa, Yana nan zaune kuma kiran wayan ya shigo, Ganin sunan Hamma Rayyern d’insa ne kuma ya sashi d’aga wayar da sauri, tare da cewa.
“Hello Hamma Rayyern.”
Idanu Jannart din ta rumtse, kana cikin tsananin rauni murya na rawa tace.
“Ramadan, Hamma Hamma ciwon cikinsa ya tashi, ya zanyi Ramadan tsoro nakeji.
Dan Allah
Ramadan ya zanyi.....”
Ta fad’i maganar cikin matsanancin kukan da ya riga yaci k’arfin ta.
Ramadan dake zaune kuwa jin abunda Jannart din ta fad’a ne, ya sashi tashi da sauri cikin tsananin tashin hankali yace.
“Innalillahi wa’inna Ilaihirraju’un, Jikin Hamm Rayyern ya tashi? Subahanallah Aunty Jannart yanzu kuna ina? ina Hamma Rayyern di yake? ciwon ya tashi sosai ko? kin basa magani?”
Ramadan din ya had’e mata duka tambayoyin, cikin tashin hankalin daya samu kansa aciki.
“Muna gida Ramadan, kuma na duba ko ina babu maganinsa ya shanye, bansan yanda zanyi ba Ramadan, numfashinsa d’aukewa yake.”
Jannart ta basa amsa murya adisashe.
Saboda kukan da tayi.
Ramadan kuwa jin yanda Jannart din ke kuka ne, yasa shi d’an dai-dai-ta nutsuwarsa a matsayin sa namiji, cikin tausasa murya yace.
“Calm down Aunty Jannart, Insha Allah Hamma Rayyern he’s will be fine, bari na k’ira Dr. Sulaiman nasan zaizo ya basa taimako, ki daina kuka Insha Allah zai samu lafiya.”
Ya kare maganan cikin lallashi.
Wanda hakan yasa Jannart din jinjina kai, tare da zare wayan akan kunnenta ta ajiye agefe.
Ramadan kuwa yana kashe wayan, Dr. Sulaiman ya kira, arude yake fad’a masa halin da Rayyern din ke ciki.
Jin hakanne kuma yasa Dr. Sulaiman tare taxi, Kai tsaye ya nufi gidan Rayyern din.
After 20mn.
Gaba d’aya Idanunta alumshe suke, saidai babu abunda suke fitarwa sai hawaye.
Har yanzu kuma Rayyern din kwance yake akan cinyarta, Yayinda ya mak’alk’aleta k’am, kansa da fuskarsa kuwa duk suna kan cikinta, wannan yasa duk wani numfashin azaba, da yake fitarwa akan cikinta yake sauk’a.
Har yanzu kuma jikinsa bai daina karkarwa ba, ga zufa dake feso masa tako ta ina.
Wani irin rik’o yayiwa Jannart d’in, tare da sake matse hannunta dake saman cikinsa, ahankali take yawo da hannun nata, tare da d’an mammatsa cikin nasa.
Wanda zuwa yanzu ya fara jin dadin hakan da takeyi masa, musamman yanda tausassan d’umin tafin hannunta, ke sauk’a akan mararsa.
Ahankali batare da ta sani ba kuma, hawayenta ke sauk’a acikin gashin kansa.
Duk da cewar baya cikin nutsuwarsa, amma hakan bai hanashi jin dumin hawayen nata acikin kansa ba da shessheƙan kukanta.
Wani irin fitinannen numfashi yaja, alokacin da yaji ta d’aura hannunta akan, faffad’an k’irjinsa wanda yake bud’e, kasancewar ta cire masa aninayen rigar tasa.
Ahankali ta tallabe habarsa cikin tafin hannunta.
Tare da d’an bubbugawa a hankali murya a sanyaye take kiranshi.
“Naan! Nasn!! Naan!!! Ka bude ido ka kada ka rufesu, gaya min dame zan taimaka maka, Naan ka bude idonka”. Take mgnar a raunace tana ci gaba da dan marin kumatunsa a hankali hankali, kana ta zuba idanunta kan kyakkyawar fuskarsa asanyaye takeyi masa komai, saboda har yanzu hawayen idanunta sun kasa tsayuwa.
So yake ya buɗe ido ya kalleta amman ya kasa.
Suna zaune ahakan ne kuma, yaji wani irin fitinanne kuma gigitaccen ciwo na taso masa, ciwon daya fi wanda ya taso masa abaya, ciwon daya sa shi jin duniyar na kifewa dashi.
Haka kuma ciwon da azabarsa yasa shi kasa tantance duniyar da yake, cikin wani irin azaban dake sukan naman jikinsa, ya soma fitar da wani irin numfashi mai kama da nishi, lokaci daya kuma duk jikinsa ya soma sakewa.
Sautin gurnanin numfashinsa da taji acikin kunnuwanta ne, kuma ya sata bud’e Idanunta amatuk’ar tsorace ta zuba masa idanu.
Baza ta tab’a iya jurewa ganinsa ahaka ba, wannan dalilin ya sakata sakin sabon kuka mai tsuma zuciya.
“A’a, A’a Naan Dan Allah karka rufe idanunka, karka tafi ka barni awannan duniyar da Bani da kowa sai kai, bansan kowa ba acikinta, Yah Allah ka taimakeni ka rufamin asiri Yah Allah ka taimaki bawanka ka sauk’a k’a masa wannan ciwon.”
Ta k’are maganan cikin matsanancin kuka tare da silalo da hawaye, kana ta sunkuyowa garesa, dai-dai lokacin kuwa idanunsa suka rufe rub.
Hannayenta duka biyu ta bud’e tare da rungumesa akan kirjinta, ta sake sakin wani sabon kuka, kuka kuma irin wanda bata tab’ayi ba arayuwarta.
Dai-dai lokacinne kuma Dr. Sulaiman ya turo kofar falon ya shigo.
Ita kuwa Jannart dake tsananin kuka kuwa, ko d’ago Kanta batayi ba, acikin kukan nata ne kuma ta sake rungume Rayyern din ak’irjinta.
Azauce take fad’in.
“Please Naan!! Please open your eyes please Naan don’t leave me please.....”
Ta kai k’arshen maganan tana me jijjigasa, Ahankali kuma takai yatsunta daidai saitin hancinsa.
Abunda taji ne kuma yasa ta waro Idanunta, amatuk’ar tsorace, cikin gigita da kuma tashin hankali, irin wanda bata tab’a samun kanta aciki ba, agaba d’aya rayuwarta.
Idanunta dake zubar da hawaye ta zubawa Rayyern din, tare da soma girgiza kanta da sauri, cikin firgici da kuma mugun bugun zuciyar dake dukan k’irjinta, muryar na rawa tace.
“Innalillahi Wa’inna Ilaihirraju’un...!
*Albishirinku! Ma'aurata, GA GARKUWAR KU nan tafe muku da tsarabobi na musamman gareku ma'aurata daga cibiyar mgnin mata mai taken GARKUWAR MA'AURATA*
NI DAI AYSHA ALIYU GARKUWA.
Ina matukar mamakin wani irin lokaci da ya riske mu mai wahalallan fassara. Kullum dai magana daya ce, akan ma’aurata, fada, rashin jituwa, mutuwar aure, akan kuskure kalilan, rashin kula, rashin yi wa juna uziri. Toh wai duk me ya janyo hakan? Na zurfafa a tsananin tunani hakan ya tilasta min bincike mai tarin yawa wanda ya kai ni ga gano inda matsalar take? Shin yar’uwa ke macece amma kin san wacece mace ku? Kin san me ake kira mace kuwa? Mace ita ce matar da take zama iyali a wajan namiji ta zame masa bango, sanyin idaniyarsa, ta zame masa gata da farin cikin rayuwarsa ta zame masa ruwa abar kore ƙishinsa ta zame masa mayafi mai karesa daga gigitar kadaice, ta kuma dorar da mijinta kan turbar gaskiya, ta kashe masa jiki da salonta ta rikita shi da baiwa da ni’imar da Allah ya bata idan har ta san hanyar mayar da kanta sabuwa dal awajanta, wato kullun takasance masa tamkar amarya har ya kasa tantance daren amarcinsu da sauran dararen rakun rayuwar su.
Wannan ita ce mace. Ina da wata saukakkar hanyar da zaki zama abar so da kulawa da soyayya a wajan mijinki ta hanya mafi sauki, 09097853276 hanyar ita ce ki gwada amfani da kayana na gyara ki gani, ina mai tabbatar miki da in sha Allahu sai kin dara da murna sai kuma kin gode min. Kayana kaya ne da aka yi shi da zallan itacanmu na gado marasa illa a cikin jikin dan adam musamman mace, kaya ne da suke taimakawa (sex hormones 😍) dinki.
Misali kina kallon India😘, hollywood, Asian film🥰 kina ganin yanda mazansu ke nunawa matansu tsananin soyayya kamar su ba su kyautar ransu!?
Saboda me hakan? Saboda suna sadaukar da lokacinsu wajan gyara jikinsu da kayan da ke tsattsafo da ni’ima cike da tsukewa, kayan nan kuma ana yinsu ne zallar magungunan gargajiya wanda ba su da illa domin haɗine na ingantattun itatuwa da yayansu.
Ina baiwar Allahn da miji ke daure mata fuska babu hirar arziki?
Zo ki ji yar’uwa zan baki gumbata da zallar gari wanda aka yi su da nagartattun itacen da ke da matukar amfani a jikin mace. Gubar ciko, gumbar tsalle dole, gubar da ba'a baiwa mai kishiya, garin maɗi, garin mallaka, tsumin goron tula, tsumin tsartai, tsumin maratsi, pala-pala butar sirri, kwanon k’asaitacciyar mace, furar mata madararta gareki Hajia takenta sha yanzu mgni yanzu,
Ina mata masu fama da sanyi? Sanyin mara ki zo na hadaki da magani na na sanyi wanda yake wanke mara ya fitar da duk wata cuta da ke samun mazauni a wajan.
Ina da ciccibi mai kyau. Ina da hadin amare mai kyau wanda zai gyara yarinya ya kankaro mata kimarta akwai hadin mai jego wanda muke yinsa na asali inada kekkyawan Hadi maida tsohuwa yarinya.
Akwai daya bangaren wato *KAMSHI*
Kimarki gyaranki da kamshinki. Matan da suka gane suka san yanda za su kankaro da mutunci su ne masu amfani da kayan gyara da kuma sanyaya jikinsu da kamshi, ina da turaren wanka da na bandaki na daki na jiki da na kaya dana tsuguno kamshin turarena na dabam ne mai sanyaya zuciyar wanda ya shaka ina da kayan kamshi na amarya da na maijego da na uwargida da dukkan macen da take kokarin mayar da kanta mai daraja a idon kowa ta zamo sarauni a idon mijinta, akwai shu'umar humra, sayan na gari maida kuɗi gida, banda karanta yayin gyara Hajia.
Zaku iya samun kayyakina a duk garin da kike, zakiyi min mgn ta whatsApp number na 09097853276 domin yin zaɓinki, ko karin bayani, zaki tura kuɗin ta account na 0005388578 Jaiz bank AISHA GARKUWA ALIYU in mun gama mgna zan sa miki kaya a mota yazo duk