Showing 42001 words to 45000 words out of 143458 words
ta siyamata su, hawaye ta share tana tuna rayuwansu da Hawwa duk yanda mutum zaiyi tunanin friendship, kawancenta dana Hawwa yawuce haka, sabida kawance ne mai asalin amana, Hawwa harda Maman Ni’ima take fada akanta just like yanda take fada da Baba akan Hawwa tanajin haushinsa kan Hawwa haka sukema junansu wajen iyayensu, they supported each other like better half, kawance su babu ha’inci, babu kyashi ko rowa, babu bakinciki, they’re always happy for each other, dudda tayi aure Hawwa bata taba mata bakincikin wani abuba, datana da ciki wlh wlh ko Baban Yaseer mai cikin baikai Hawwa kula da ita ba, idan tana craving wani abu Hawwa zata iya barin aiki taje ta nemo takawo mata, yanzu haka yaranta su Yaseer sun fison Hawwa kan mahaifiyarta grandmother su sabida aminci da kaunan dake tsakaninsu, she’s just crying bitterly bamatasan ina zata saka kanta ba, kawai taji ta bama kanta tausayi bamatasan inda zatasa kanta ba wannan wani irin intertwine situation ne haka? Wani irin kaddara ne wannan? Ita da Hawwa started friendship ana maganan tun suna around 6yrs old cus primary one suka hadu, yanzu suna 30yrs, 20yrs plus friendship kifa kanta tayi akafanta tana shesheka tajiyoshi an budemai gate yafita tasan mosque zashi yau juma’a.
**
Har yamma na rannan Friday din nan shiru ba kiran Ni’ima which is so unlike her, dudda su Ramla dake damunta da labarai but still binibini Hawwa na duba wayanta ko Ni’ima tamata watsapp message ko kira ko wani abun amman shiru, tasake kira but still ba amsa dan damunta abin yafarayi sosai.
Bayan sallan magrib suna zaune sunacin abinci duka tare harda Hamza wayan Ammi yahau ringing wayan ta kalla taga Baba ne hakan yasa tadauki wayan tafito daga dakin dan bataso yaran especially su Ramla susan maisa Hawwa tazo tawuce ta shiga side nasu Hamza zama tayi kan katifarsu tayi dialing number Baban ringing daya yadaga ya buga mata sallama yace “ya wajen naku Rukayya” Ammi tace “Alhamdulillah” ijiyan zuciya Baba yasauke yace “Baban Yaseer ya sanar dani Hawwa na wajenki kice mata ni ban koreta ba ta tattaro tadawo gidan nan” anatse Ammi tace “sabida kacigaba da tallatata a masallaci kana neman kai da ita” dan shiru Baba yayi saikuma chan yace “kinga Rukayya ni ba kira nayi fada dake nayi ba, tun fadanmu na farko bayan rasuwan mahaifiyan yarinyar nan kikaso tafiya da ita nace a’a kika dinga bala’i dani nasan ba kaunata kikeba da akwai yanda zakiyi ma da rabani zakiyi da yarinyar, ni duk wannan ba itace matsalata ba kawaidai kice mata tadawo gida kar fushina yabita” dan sauke ijiyan zuciya Ammi tayi tace “yarinyar nan kawai sabida kaine mahaifinta saisa muka barmaka, wlh na sanar da Baffan ta saidai duk abinda zai faru yafaru, aure na Allah ne ba nakaba, da iyaye ke aurar da yara da tuni kowa yayi, Allah shine komi ke hannunsa, kaida yakamata ka godema Allah dayabaka irin wannan yarinya a’a sai tsalle tsalle kake” katse wayan Baba yayi danshi dama da Ammi basa jituwa kona sakan daya.
Around 8 nadare Hawwa taga Ni’ima na online ta karanta duka messeges nata amman bata kulata ba, watsapp call ta danna mata but harya katse bata dauka ba abin ya bala’in damunta voice note ta danna tace “Ni’imyyyyy sorry please kidena fushi, wlh I know kema na sanar dake abinda yafaru ni da Baba you will not be happy with abinda yayi, banson na tadamiki da hankali koki hanani zuwa wajen Ammi saisa ban sanar dake ba sorry, ina Yass dina da Meen” ta aika mata voice note din tarike wayan tana kallo ganin yaje but still ba asaurara ba kuma tana online abin yafara damun Hawwa sosai bahaka Ni’ima ke fushi da ita ba saidai tai masifa dukansu basu iya gababa saidai suyi fada ayi zage zage da baki a shirya, dukji tayi ba dadi haka ta tasa wayan agaba tana kallo kusan 20min kuma tana online chan saita sauka ijiye wayan Hawwa tayi ta kwanta kan gadon Ammi tana sauke ijiyan zuciya.
Yau Saturday Baffa (mijin Ammi) na gidan tun goma dayazo baibarta tahuta ba da labarai da surutai dan yana mutuwan son Hawwa, tana yawan turamai kudi akai akai kaman yanda takema Ammi ta, surutunsa yasa tadan manta da damuwanta sai dare kuma tashiga kiran Ni’ima harsaida Ammi talura tace “banji kinyi waya da Ni’ima tunda kikazo ba da tuni tace abani waya tai magana dani, Ni’ima dana sani da saita kawo karinki kin shiga hanya da daddare” dan murmushi Hawwa tayi tace “tana hospital ne Ammi shift take covering, chatting mukafiyi this days Ammi” dan murmushi kawai Ammi tayi bata sake magana ba tace “bari nakaima Baffan ku shayi” tafice.
Washegari Sunday around 11 tafito su Hamza na samata komi a booth, Baffa yace “Hawwa ayi tuki ahankali kinjini” murmushi tayi tace “toh Baffa na” Ammi tace “Allah kiyaye hanya, dan Allah banda gudu” Gyadamata kai Hawwa tayi su Ramla suka rungumeta tamusu sallama tafito, text tama Ni’ima tace “gani nashiga hanya zan dawo office gobe”.
Karfe biyu dawani abu anadai neman karfe uku Hawwa ta shigo Abuja hanyan hospital din su Ni’ima tawuce direct ta shiga tai parking ta kashe motan, wayanta tadauka tafito abayane ajikinta baki tawuce ciki office din Ni’ima tawuce tareda knocking tana budewa wata nurse ce aciki tana ganin Hawwa tai murmushi tace “wajen Ni’ima kikezo? Bakuyi wayaba ai batanan yau is her off” amutunce Hawwa tace “okay okay nagode” tajuyo tafito motanta tashiga tafita daga hospital din wlh she’s so worried rabon datai magana da Ni’ima tun Friday wani irin fushi Ni’ima keyi da ita haka, hanyar gidansu Ni’ima tayi har zuwa layinsu mai kyau, gaban gidansu ta tsaya tai horn maidaidaicin gidane mai kyau ga babban bakin gate nasu, lekowa mai gadin yayi Hawwa tadanmai murmushi tana jiran taga yabude gate saitaga yabude karamin gate da fara’a kan fuskanshi yace “Hajiya barka da yamma” gyadamai kai tayi tace “ya kuke” yace “Alhamdulillah” saikuma ya tsaya sakaka yana kallonta Hawwa tace “budemin gate ko basanan ne”? Bazai taba iya maimaita abinda Ni’ima tacemai ma hakan yasa dasauri yace “eh basanan tun safe suka fita” danjimm Hawwa tayi kaman daga sama sukaji muryan Yasmeen ta tsandala ihu tana kuka wayyo kafanta dasauri maigadin yakalli gate saikuma yajuyo yasauke kanshi kasa, Hawwa dake juyo muryan yaran tace “kace basanan ba muryan Mims naji na kuka ba” dan sosa kai yayi da hannu kanshi na kasa yakasa kallonta yace “ahhhmm Madam tacemini duk randa nakara barinki kika shiga gidan abakin aikina kiyakuri Hajiya” dasauri da kunya yajuya ya shiga gidan tareda maida gate din yarufe Hawwa tai shiru tana wajen she don’t even know wat to think, her mind just went blank wlh takai minti ashirin awajen kafin tadan fuzar da iska taja motan tabar wajen.
[9/18, 5:03 PM] M Shakur: 💫GARGADAN SO💫
✍🏻M SHAKUR
EPISODE 2️⃣4️⃣
LUKUKU GENERAL ENTERPRISE gidan spices kenan da abubuwa daban daban, babu kalan spices din da basuda shi, tundagakan su ginger, garlic, tea different kind da sauransu, this is tasted and trusted brand, chat them up kisai spices now!!!!!
wa.me/+2348095660030
EPISODE 2️⃣4️⃣
Kawai tausayi taji tabama kanta saisa takasa rike hawayen dan tana cikin jarabawan rayuwa, she’s 30 batai aure ba babu miji, kowa is pressuring her, her biggest support, her biggest fan is her best friend Ni’ima da tun suna yara suke tare, kawancen amana da iyayensu sun zama daya ma, she’s not a small girl when she sees love she knows love, wani irin kaddarane wannan? Baban Yaseer can never be her amsa nooo please Ya Allah not my best friend’s husband, ganin hawaye yakasa tsayawa daga idanunta asanyaye Aliyu yace “I’m here for you, I will forever be right here! Ina taredake Hawwa in good times and bad times, dare da rana, I’m right here” ahankali yadaura hanky kan fuskanta wani sanyi taji dayasa ta lumshe idanunta da sauri takai hannunta i ta karbi handky tana goge fuskanta, tadanja majina dadan ragowan karfin zuciya tace “maisa kabiyoni Baban Yaseer? Nace kabiyoni ne must u follow me everywhere? Must you get involved in my issues? An gayamaka I can’t take care of myself ne ko I need your protection”? Ataushashe yana kallonta ganin ranta abace, cikida zazzafan kauna yace “sabida bazan taba iya bacci ba bayan nasan kina irin wannan hanyan, I care for you” ahankali Hawwa tace “wat if something happens to you”? Asanyaye yace “I don’t care koma menene yasameni I just wanna keep u safe” abu tahadiye a wuyanta sai kawai ta juyo ta yunkuro tace “I need to change my tire, spare tire na booth” matsamata yayi tafito tai booth yabi bayanta tana bude booth din takai hannunta zata dauki tayan yarigata dauka yace “let’s go muje motana ki zauna” tsayawa tayi tana kallonshi, “muje dan Allah Hawwa dare ne mu kadai a titi” batai musu ba yayi wajen motanshi da ita yabude mata gaba ta shiga ta zauna ya maida yarufe sannan yadawo booth nata yaciro supanu yaje gaban motan yana kwance tayan dayay less, sosai Hawwa take kallonshi kaman yauta fara ganinshi abubuwa da dama suna yawo aranta, tana zaune awajen saiga yan sanda sunzo wajen fitowa tayi ta nuna musu ID card dinta tayasu gyara tayan sukayi, suna gamawa Baban Yaseer yabar musu motanshi yabasu kudi su tsaremai sannan yashiga na Hawwa, hakan yasa ta zagayo ta zauna ya kunna motan yaja waje tajuyar da kanta tana kallo ahankali yace “do you think is right kije kidan Anty ki middle of the night? Kodai idan mukaje zaria namiki booking hotel, idan gari yawaye saikije”? Tana kallon waje batare data juyoba tace “zan iya zuwa wajen Ammi na anytime anyday” gyadamata kai yayi bai sake magana kusan 30min sai chan yace “Hawwa it’s okay not to be okay” lumshe idanu tayi tabude anatse yace “you got this! Karki bari kalaman Baba natabaki, karki karaya, I hate seeing you like this” yadan kalleta yanda take kallon waje yace “kinji” gyadamai kai tayi daganan basu sake magana ba harsukakai zaria, nunamai hanya tadingayi har zuwa wani gida a wani anguwa mai dan kyau da mutunci, saukowa tayi ta zagayo tadan kalli Baban Yaseer dake kallonta tace “dan bani car key” zare key motan yayi yabata yana kallonta, a gate tasaka wani key dake jikin motan tabude kofan tashiga ciki tana sallama tsakar gida ne mai fadin gaske, tourchlight taga an haskewa taji muryan yan dattijuwa na “waye awajen gate din nan” ana bude kofa da gudu Hawwa tai wajen kofa matan na bude kofa dadan charbi a hannu Hawwa ta rungumeta da karfi tace “Ammiiii na” ririketa matan tayi tace “Hasbunallahu wa ni’imal wakeelu Hawwa kece da daddaren nan, ke tashi kiga na ganki lafiya Hawwa” tadago Hawwa daga jikinta murmushi Hawwa tayi tace “Ammi baban Naseer na waje bani key gate na bude ya shigo da mota saiya dan zauna zuwa safiya yakoma Abuja” wani dan kallo Ammi tamata tace “Baban Yaseer kuma? Aliyun Ni’ima”? Gyadamata kai Hawwa tayi Ammi tabata key fita tayi Ammi itama tafito tana haskawa bude gate din Hawwa tayi yashigo da motan ta maida gate din tarufe Ammi tace “maraba da Baban Yaseer, sannunku sauko sauko” Saukowa yayi kanshi akasa cikeda kunya yace “Ammi mun sameku lpy” cikeda fara’a tace “Alhamdulillah ina jikokina? Da y’ata Ni’ima hope duk suna lpy”? Akunyace ya gyadamata kai yace “Alhamdulillah” murmushi tayi tace “muje nakaika side din su Baffa ka kwanta bazakabi hanya da tsakar daren nan ba sai idan Allah ya kaimu da safe akawo maka abinci ne”? Dasauri yace “a’a Ammi dare nayi bana iya kara cin abinci” satan kallon Hawwa yayi dake gefen Ammi tana wasa da hannunta yamika mata car key ta yace “take” dan dagokai tayi kafin tasa hannu ta karba Ammi tace “muje” suka wuce suna hira itakuma tawuce wajen motar ta booth taciro akwatinta ta gu huri ta shiga dashi ciki, bayin Ammi tafada tana cikin wanka Ammi tashigo tasami waje ta zauna yanda ta ganta haka tasan dawani abu.
Towel din Ammi ta dauro tafito Ammi ta kalleta tace “zonan Jidda” kayan shafanta tadauka tazo kusada Ammi ta zauna tana bata cream dinta a hannu Ammi ta karba tana sauke ijiyan zuciya tace “meya faru?” Dan shiru tayi sabida kawai taji komi yadawo mata sabo, hannunta Ammi takama tana shafa mata mai kafin takalleta strictly tace “ya akayi kike tare da mijin kawarki at this type of time and day Hauwa’u”? Baki tabude zatai magana saikuma tadan sauke ijiyan zuciya Ammi tace “speak” anatse tace “Ammi wlh I don’t know cus ni ko kiran Ni’ima ma banyi da abun yafaru ba, probably Baba ne yakirasu to check ko ina gidansu, saita kirani daga gayamata ina hanya zanzo wajenki hala to shine ta turoshi” Ammi na kallonta ta sauke ijiyan zuciya tace “Hawwa babu wani naki dabaisan relationship dinki da Ni’ima ba, yarinyar nan kawar amana ce, yanda kika daukeni haka tadaukeni, don’t ruin friendship naku under no circumstances, you know maganan danake” gyadamata kai Hawwa tayi tace “nasani Ammi” saikuma ya tashi daga gadon ahankali zuwa akwatin nata tadauki dogon riga na bacci tasaka ta zare zanin wankan ta shanya ta dawo gadon tahau ta daura kanta kan cinyan Ammi tareda sauke ijiyan zuciya tabude watsapp tama Ni’ima chat “Just got to Ammi’s place, Ni’ima why did you send Baban Yaseer? Why” tura chat din tayi taga yayi layi biyu alamun datan ta a kunne amman ba’a budeba jira tayi ta amsata but shiru ijiye wayan tayi ahankali tana lumshe ido kafin kaceme bacci yayi awon gaba da ita dan tagaji yau.
Yanda bacci ya shigeta yasa Ammi bata tadataba ta shiga dakin yammatan ta su biyu Amina da Ramla ta tadasu don salla itama tayi sannan tasa suka shiga kitchen cus taji Baban Yaseer yafice salla.
Wuraren 7 yashigo gidan a tsakar gida yaga Ammi tareda Ramla datake gwadama yanda ake buga kosai sun hada gawayi dan basu soya kosai a gas, ganinshi yasa Ramla tace “ina kwana Baban Yaseer” murmushi yamata yace “lpy lau” yace “ina kwana Ammi” murmushi tamai tace “an tashi lpy sannu da kokari fa Aliyu, Allah ya maka albarka, bari yanzun nan zan kawoma kosai nariga an dama kamu saina kawoma kayi karo kafin kashiga hanya” girgixakai yayi yace “no Ammi bazanyi kari ba bana kari da wuri yan sanda na barma motana chan hanyan kaduna dole nafita yanzu Ammi” yayi maganan yana ciro kudi daga aljihunsa daya samo a ATM fitan nan nasa a kujeran tsakar gida dake gefen Ammi ya ijiye kudin yace “aba Hawwa idan ta tashi, wannan kuma aba su mai girki” cus baisan sunan Ramla ba, hade fuska Ammi tayi tace “kaga dauki kudaden nan karna saba maka Baban Yaseer” dasauri yajuya yayi gate yace “Ammi nagode” yafice dasauri dudda har ranshi yaso yaga Hawwa kuma sarai ta tashi tun dazu har salla ma tayi kawai bataso ta ganshi ne kawai yasa bata fitoba, tanajin fitanshi tafito falo Amina dake gyaran falo na ganinta tai ihu sosai “Ramla Ya Hawwa ta tashi” tawani zo dagudu tai tsalle tafada jikinta Hawwa tai dariya sosai Ramla tasaki kosan datake ta rugo dakin aguje itama tai tsalle kawai Hawwa tai kasa suna kanta, Ammi ta shigo dakin ta kwadamusu duka abaya tace “Oya ku dagamin ita bance ku karyamin diya ba” kankamesu Hawwa tayi tace “Ammi I missed my babies” hararansu Ammi tayi tawucewarta tafito tashiga soya kosan da kanta tunda taga shirme suke Hawwa tafito tareda su tana Ammi wai ina su Hamza da Ahmadu? “Hamza na school, Ahmadu yace anjima zaizo da matarsa su gaidake, Baffan ku na dayan gidan sai gobe zai dawo nan amman hala anjima ki gansa” murmushi tayi ta karbi kosan tana soyawa su Ramla nabata labari she looks so happy Ammi tayi murmushi ganin ayanda idanunta sukadan kumbura jiya sabida kuka sun sauka sosai yanzu kaman batayiba.
Wuraren 12 Ni’ima taji ana bude gate, tunda tasan Hawwa bata taba taga miss call na Hawwa taki kiranta back ba sai yau, nor tai replying message nata, jiya tamata message shiru, da safen nan takirata sau biyu ba amsa sai tamata magana tace “call me idan kin dawo daga hospital Best, su Ramla nata tambayanki”.
Jin ana bude gate yasa ta tashi dagakan kujeran tawuce da sauri tashiga kitchen, ita kadaine agidan su Yaseer na school sai though 1 suke tashi on Friday, sallama taji yayo yashigo abu kawai taji yatokare mata zuciya tama kasa amsa sallaman, kofan bedroom nasu taji yabude ya shiga sannan tasauke ijiyan zuciya tashiga fito da flasks da plates tana ijiyewa a dinning tazauna a dinning din saikuma chan tamike tawuce bedroom din nasu ta zauna bakin gado tanajin karan zubam ruwa ba’a wani jimaba yafito daure da towel a waist yadan kalleta hada idanu sukayi tana kallonshi kaman yau tafara ganinshi dauke kai yayi da sauri yawuce wajen wardrobe nasu yace “wife ya gida? Su Yaseer basu dawo daga school ba”? Tana kallonshi kaman gunki tace “basu dawo ba tukunna” gyadamata kai yayi ya tsaya gaban mirror yadau mai yana shafawa yakasa wani maganan, kalulu ta hadiye a wuya tadan bude bakinta kadan saikuma tarufe sai chan kuma tace “ka kuwa sanar da Hawwa kana sonta?!” Dum! Haka maganan yadaki kunnenshi man daya diba zaikai jikinshi yashafa kasa shafawa yayi yajuyo yakalleta suka hada ido yace “wace irin magana haka kikeyi Ni’ima”? Mikewa tayi a fusace ta nunashi da hannu tace “don’t you dare lie to me, nasan son Hawwa kawata