Showing 102001 words to 105000 words out of 153675 words
didn't mean anything, Du'a please" ahankali Du'a ta rungume ta, dan ta bala'in bata tausayi, yanzu Asad muguntan shi yakai yaci uban sister shi, cousin dinshi, his blood haka? harda karyata, to ita waye dabazai iya mata sama da hakaba, tadade suna kuka sanan tadago hannunta takai tasharema Aneesah hawaye ahankali tace "Aneesah I am sorry kiyakuri please, dukni najamiki, I am sorry" sharemata hawaye itama Aneesah tayi tace "Anty Du'a stop telling me Sorry, ni yanzu kanwar kice, kece big brother wife dinmu" wani iri Du'a takeji ahankali tace "dan Allah kidena cemin Anty" makemata kafada Aneesah tayi tana tashi tsaye tace "bari natafi gida karki fito fa saisun tafi, zan fadama security kina nan" bata jira amsanta ba tafice, security dataga yana kokarin shigowa dakinshi tagayana Du'a na ciki sanan tafito daga gidan daidai Asad na fitowa a motanshi daga gidansu, chak ta kame awajen a tsaye tama kasa koda motsin kirki saida yazo daidai wajen sanan taga ya saukar da tinted glass dinshi kasa, wanan karan kananun kayane ajikinshi idanunshi sanye da bakin glasses ahankali yasa hannu yazare bakin glasses din yazuba mata mugayen idanunshi dayasa tafara shaking, bakinta narawa sosai tace "Ya Asad is not what u think wlh kallo naje nayi nakai akwatin, dan Allah kayakuri" wani irin kallo yamata wani mugun kalan wulakantaccen kallo dayasa saida taji hanjin cikinta yakara sanan yadauki glass dinshi yamaida a ido yamaida glass din motar sama sanan yaja motar, dasauri tajuya tashiga gidansu tanajin wani kalan bakin cikin dabata tabaji ba arayuwanta barinma na komarda ita Kanon dazaiyi_babu randa zatai salla dabazata roki Allah yasa ya hakura ba.
5️⃣9️⃣
DUK WACCE TAKARANTA LITTAFIN NAN BATARE DATA BIYABA BAN YAFEBA.
THIS BOOK IS 500 PAY INTO 3107021073 AISHA MUHAMMAD FIRST BANK SAIKI TUROMIN EVIDENCE OF PAYMENT TA WATSAPP NUMBER NA 07012181461.
YOU CAN CHAT ME UP DIRECTLY BY CLICKING ON THIS LINK
wa.me/+2347012181461
Sai wajajen 6 aka waste daga gidan Grandma har kawayen ta duk suka tafi yan aiki ne kawai suka rage, kaga Grandma ko ubar Amarya albarka, kawo akwati kawai amman tayi gayu kaman adauketa, karan kiran sallan magrib yatada Du'a daga bacci datayi anan kasan dakin security, jin gidan yay shiru yasa ta tashi ahankali tabude kofa tafito tashiga ciki, taga aike aketayi gidan ya kacahme ga akwatuna ko'ina afalon su Razika nata aiki da matan dake mata gyaran jiki itama tana tayasu, ganinta yasa Grandma tajuyo tai wani murmushi tace "oyoyo taho nan yanaganki wani irin, zonan zazzabi kike ne" Grandma tajata jikinta cikeda so tana taba fuskanta da wuyanta jin na zafi yasa taji dadi tace "bacci kikayi ne" gyadamata kai tayi tace "eh adakin security a kasan falonshi nadawo gida yacika kuma banso a ganni" baki Grandma takama tace "shine bakisa ankirani na nema miki waje ki boye ba, oya wuce kitafi sama kiyi wanka kizo kisha magungunan ki amiki turare, gobe su Maman ki zasuzo, jibi za'a fara shagalin biki" gyadamatakai kawai tayi ahankali sanan tawuce sama, dakinta tabude tashiga ganin yawancin kayanta an kwashe barinma na amfanin ta yasa tafito ganin Grandma natahowa yasa tace "menene"? Ahankali tace "Grandma kayana ina suke"? Murmushi Grandma tayi tace "daga gobe a side dina zaki dinga kwana saisa nai clearing abubuwan dakike amfani dasu nakaisu chance, wanan da yan gidanku zasuzo I don't wanna take any chances wata ta takuraki ko aci zalunki, so u are staying with me all through, tafi kije kiyi wanka kizo" juyawa tayi tashiga dakin nata Grandma tabita da kallo sanan tawuce tana duba sauran dakunan sama datasa agyara sabida bakin dazasu fara zuwa ganin ko'ina fess fess har dakinda Asad ke zama yasa tafito takoma kasa wajen abincin Du'a.
Bayi tashiga zata fara wanka saikuma ta tsaya tai shiru tanason tai wani tunani amman tunanin nabata kunyan yi, wankan tsarki nadaga cikin abubuwan data iya lokacin kafin ma a dena hanata fita, kuma lokacin data fara MP Mami takoya mata wanan, banda haka kwanan nan duk idan lesson Ustaz malamin ta yazo suna fiqihu yana fadamata dalilan dakesa ayi wankan tsarki ciki harda abinda Asad yamata dazu, runtse idanunta tayi taji wani kalan shock tuna abin kafin ahankali tai wankan, wanan uban gashin nata saida tajika, fitowa tayi daga wanka tadaura towel akirji tadaura karami akanta daidai Grandma na shigowa dakin dawani kopi da kula a hannunta, baki tasaki tace "keda za'ama gyaran gashi jibi maisa kika jika kanki" juyawa tayi tai wardrobe dinta tace "kaina ke ciwo" ijiye abincin Grandma tayi tace " bari naje nakawo miki panadol" kaya tasa sanan tai salla karfi tazo tazauna karfi dayaji Grandma ta sata agaba ta shanye abubuwan data kawo mata tass, tana zaune adaki an hanata komi daga anata magunguna sai azo amata wani abu wankan turare daga baya bacci yay awon gaba da ita.
Tunda sassafe aka tashi agidan sai aikace aikace ake itako ko tsinke Grandma tahanata dagawa saima wani special gyaran jiki da akemata nasu dilka da turare, bayan angama wata waxing din dayasa tasha kuka dan saida Grandma ma ta tsaya akanta sanan tahakura, sai wajajen one aka gama komi aka mata wanka Grandma tadauko mata wata sabuwa English atampa cikin wanda tadinka mata milk mai shegen kyau da tsada tasata tasaka, shiryawa tayi ciki aka mata dauri dudda batai kwalliya ba but kana ganinta kaga Amarya to be, dakinta Grandma tawuce da ita tace "Hamad yakirani sun shigo Abuja wai" gyadama Grandma kai tayi ahankali jikinta duk yay sanyi, murmushi Grandma tayi tace "bari nabada nama akawo miki ko kyayi fara'a" murmushi tayi kuwa Grandma tai dariya tafice, tana kitchen tana kokarin debanma Du'a nama aka taji anbude gate, Razika dake kusada ita cikeda murna tace "Hajiya sune" murmushi Grandma tayi tabata naman tace "kaiwa Du'a kiga" sanan tawuce tafita da fara'anta, motoci uku ne, Sienna Abba ce agaba, sai wata karaman mota Honda, saikuma bus din Abba wacce Ya Hamad dake sanye da kayan sojoji keja, sosai Grandma ke murmushi tace "oyoyo oyoyo" yaran ne suka fara fitowa daga mota su Amra, Aneela, Mudasir, da Muhammad suna tahowa wajen Grandma da gudu suna kallon gidan, kafin Mum ta sauko taci wani hadadden atampa fuskar nan ba yabo ba fallasa, saiga Hawwa da Nana dasuka saka kaya iri daya sunyi kyau ba laifi sai kalle kalle suke, saiga Mami itama tadan rake but she is looking okay, sai Hamad daya sauko duk suka taho wajen Grandma, motar tsakiyan kuma wata matace tafito babba ce ba yarinya ba baka tana mika hannunta cikin mota saiga wata tsohuwa tukin tafito rikeda goro a hannunta tana tafiya adudduke ranta abace kana ganinta kasan wanan tsohuwa fitinanniyar tsohuwa ce, ga uban lalitan data daura, saikuma motan Abba wanda yake shine aciki sai kannenshi maza dasuke uwa daya uba daya guda biyu.
Cikeda fara'a Grandma tai gaida dasu Mom da ba laifi basu nuna wani face ba itama ta amsa su, tana rungume su Nana da Hawwa, kana ganinta kaga classic woman sanan takalli Mami dake kallonta asanyaye tace "kaisu ciki daughter" sanan takarasa wajen Kaka cikeda barkwanci tace "kishiyata agidana Allah yakawomin gasasshiyar tsuntsuwa baki barin gidan nan sainasa mai gida ya danna miki saki" tai maganan tana kallon Hamad, hararanta Kaka tayi tace "inkin isa kisashi, kin rabani da jikata wanan ma zaki kwace min shine, nidai ki kaini daki inba sokike kafafuwata su tsinke ba nashayo wanan uban tafiyan" dariya Grandma tayi takalli diyarta data rike mata hannu dake kallon Grandma ganin hadaddiyar mata tace "barni nakaita ciki" takama hannun Kaka sanan takalli su Abba tace "Alhaji kushigo agaisa afalo wanan tsohuwan tagaji" hararanta Kaka tayi tace "dadin abin ban girmeki ba" kwashewa da dariya Hamad yayi tace "zakaci ubanka ne bakin soja kawai" falo suka shiga da already su Mom suna ciki, sun kasa boye kalle kallen dasuke, sunsha jin labari cewa Mami yar masu kudi ne but basusan kudin yakai haka ba, yanzu dama a irin wanan gidan Du'a take, lallai.
Zama duk sukayi dayake falon da girma yaci kowa yaran sai wasa suke, Kaka na zama tace "ina Du'an take" murmushi Grandma tayi tace "zatazo ta gaida ku ku huta kusha ruwa tukkuna ansha tafiya" tai maganan daidai su Razika da Shema'u dasauran yaran suka shiga gabatar da ruwan gora da drinks dabama susan irinshi ba, saida suka gama sanan Grandma takalli Razika tace "Razika kira Du'a" gyadamata kai tayi tajuya tatafi sama.
Duk suna zaune falo harda su Abba duk anyi shiru kaman kowa yakosa yaga Du'a ne, Du'a tafito ahankali kanta akasa tana gyara lullubin babban gyalen da Grandma tabata tasaka, ahankali take tafiya gabanta na faduwa takasa dagokai ta kallesu, daga Mom, Kaka, su Nana da Hawwa sun kasa yarda Du'a suke gani, har shi Ya Hamad ma, kasa rufe baki Kaka tayi tace "jama'a yarinyar nan ce dai wanan koba ita bace"? Hamad dake gefenta yace "Du'a ce Kakus" cikeda masifa tace "yoni wai wagga Y'a kara komawa aljanna take kome" batare da Grandma takalleta ba tace "yarinya tai kyau dai Masha Allah maihadinta da aljanna" daidai Du'a takarasa saukowa, ahankali ta shigo falon takasa kallonsu tsugunnawa tayi atsakiyan falon tana wasa da yatsunta murya chan kasa tace "Abba ina yini, Baffa sannu da zuwa, Kaka ina yini, Inna ina yini, Mom sannu dazuwa, Mami ina yini, Ya Hamad, Ya Nana, Ya Hawwa ina yini, Aneela, Amra, Mudasir and Muhammad welcome" duk maganan nan tayishi ahankali cikin xakin muryanta dayasa jikake dakin yay tsit.
Ahankali Abba dake kallonta yace "Du'a" sai alokacin tadago kanta takalleshi, hannu yamika mata, ahankali ta taso hannunta tasaka kan nashi zaunarda ita gefen kafanshi yayi yana kallon fuskanta yace "how are you Du'a? Ya shirye shirye"? Dan murmushi tayi tana kallon Abban nata ganin yau yamata magana faram faram ahankali tace "Alhamdulillah Abba" hannunshi yakai ahankali yadaura asaman kanta yace "Allah yamiki albarka, Allah yakaimu jibi lpy akaiki dakinki, Allah ya sanyama aurenki albarka" ahankali tace "Ameen Abba" wani irin murmushi Grandma tayi sometimrs rashin wayon Du'a pays her alot, kannin Abba dake kusada ita addu'a suka mata sanan babban cikinsu maibin Abba yace "saiki sanar da mijin naki iyayenki sunzo yazo yagaidamu anjima da daddare, yaga yan uwanki muna muganshi musan wanda muka bama yarmu, ayi zumunci" gyadamai kai tayi, sanan Abba yatashi yace "kutashi mutafi masallaci" tashi mazan Saukayi harda Hamad suka fice dan zuwa mosque.
6️⃣0️⃣
MASU FITAR DA NOVEL DINAN WAJE KUNMA KANKU MARASA AMANA.
PAY 500 INTO 3107021073 AISHA MUHAMMAD FIRST BANK SAIKI TUROMIN EVIDENCE OF PAYMENT TA WATSAPP NUMBER NA 07012181461 SAINAI ADDING NAKI A GROUP DIN DANAKE POSTING.
CHAT ME UP DIRECTLY BY CLICKING ON THIS LINK
wa.me/+2347012181461
Kaka data kasa daina kallon Du'a ne tace "taho nan naganki yarinyar nan" ahankali Du'a tadago kanta Grandma takalla danko kadan jininta bai hadu dana kakarta ba, gyadamata kai Grandma tayi alamun taje hakan yasa ahankali tamike tsaye taje wajenta ahankali tazauna akasa, hanci Kaka taja agaban kowa jin wani hadadden kamshi da Du'a keyi tace "banda kyau har kamshin fata Allah yabaki ne, lallai nidai Allah ma yasani haryau nakasa yarda ke diyar Muhammadu ce billahillazi" Kaka tai maganan tana kama hannun nata tarike sanan tace "Ya sunan mijin naki" ahankali murya chan kasa tace "Asad" gyadakai Kaka tayi tace "tabbas haka Muhammad Muhammadu ko yafadi mini, dana aiko adaukoki akawomin ke chan Ikara ki zauna dani shine kikace ke aure kikeso, shikuma dayake uban naku wani zubin bakai gareshi ba sai ko ya aurar dake, ai shikenan tunda auren kika zaba, nidai addu'ata Allah yasa karya gano kinada jinin ifiritu ajikinki yasakoki tunda mun samu kin sami miji kin aure" daidai nan Grandma tace "kinga Kaka jikata batada jinin ifiritu jinin danki gareta, kumama bakisan wani abuba, Kakan Babana usulin shi balaraben Egypt ne, yazo naijeriya yay aure, to daganan ne abin yatafi muka duk aka haifomu bakake sabida matayen dasuka aura, Du'a tadauko jinin dangin ne na kakanni" baki Kaka tabude ganin Grandma na taran mata numfashi idan tana magana hakan yasa tahadiye sauran maganan tace "asheee" murmushi Grandma tayi tace "eh wlh, yanzu dai kugamacin abinci ayi salla saimu tafi sama kuga akwati" takalli Mom daketa kallon Du'a dake wasa da yatsunta tace "akwai wani abu dakike bukata akawo miki Maman Hamad" murmushin yake Mom tayi tace "a'a wlh" lafiyayyen abinci aka kawo musu daban daban ga namomi zuku zuku, bawai basacin abinci agidansu bane amman kaga wani abincin sai agidan wane da wane ga gasasshiyar rago, dayan flat din da Grandma tasa aka gyarama su Abba suna dawowa wajen aka kaisu dan su saki sanan aka kaimusu nasu abincin, zuzzuba abincin akayi sanan Grandma takalli Du'a tace "oya tashi kici abinci tareda yan uwanki" tanuna mata su Hawwa dasuka zubo abincin su a plate tare, gyadamata kai tayi tai wajen atsakiyansu tazauna ahankali sanan takalli Nana dake kallonta ahankali tace "Ya Nana" dan murmushi tamata tace "Du'a ya kike"? murmushi tayi tace "lpy lau" sanan takalli Hawwa dake kallonta tace "Ya Hawwa" murmushi taga Hawwa tamata tace "Amarya Du'a" dan murmushi tayi sanan tadau spoon dinta sukahau cin abincin bini bini Mami na satan kallon Du'a da tuni Grandma ta lurada ita kuma tasan bakomi take kallo ba illa girma dakuma kyau da Du'a takara, saida sukaci suka koshi sanan Du'a takallesu tace "kutashi muje dakina kuyi wanka ku shirya" basuyi musu ba suka bita sukai sama duk aka bisu da kallo, akwatinan dasuka gani afalon sama sukabi da kallo kusan set 15, sanan suka shiga dakinta shima kallon dakin suka shiga yi, skirt Hawwa tacire tai bayi dagudu tace "zanyi fitsari wayyo karya zubo" murmushi Du'a tayi sanan takoma kan gadonta tazauna, ahankali taga Nana tazo tazauna kusada ita hakan yasa tadan dago kanta ta kalleta hada idanu sukayi, murmushi Du'a takarayi tasaukar da kanta kasa, ahankali Nana takira sunanta."Du'a" dasauri tadago kanta takalleta, hannun Du'a Nana takama tace "nadade ina neman hanyan dazan kiraki nabaki hakuri, I am very sorry Du'a akan duk abubuwan danamiki akan Muhsin, Muhsin is nothing but a jerk nima daga baya nagane haka, bake kadai yabi ba, infact namaji dadi abinda yafaru badadan keba da yanzu na aureshi ina cikin bakin ciki, kece sanadin dayasa Nagano wayeshi, ashe duka friends dina na school daya sani duk yana dating nasu, mayen mata ne na karshe kuma dan iska, I was so blind by his love bangane hakan ba, kiyakuri kinji Du'a" Gyadamata kai Du'a tayi ahankali tana murmushi, Nana tace "bayan Ya Hamad yadawo daga kawoki Abuja yafadima Abba komi, saiya yakulle Uwani, Mai gadi dashi Muhsin din a police station, akayi case sosai sanan aka bashi hakuri yasakesu da sharadin ko akofar gidanshi yasake ganin any one of them hukuma zasu raba shi dasu ahaka case din yakare" gyadamata kai Du'a tayi daidai Hawwa tafito, tashi Nana tayi tashiga bathroom din, Hawwa takalli Du'a tace "kin kara kyau yarinyar nan, yaushe rabon damuyi fada" dan murmushi Du'a tayi tana mamakin yanda duk suka chanza toko sun kara hankali ne oho, salla sukayi sukahau bama Du'a labarin kano daga tai murmushi saita gyadamusu kai, kwala musu kira da Mom tayi yasa suka fita banda Du'a datai zamanta, duk afalon saman suka taru ana bude kayan Du'a dababu na Nigeria ko daya, daga akwatin har atampopin dakomi ma, Mom duk yanda taso kasa boye bakin cikinta tayi, harsaida Kaka yar bala'i tace "kekuma kowa na tofa addu'a bazaki tofa ba" murmushin yake Mom tayi dan daga ganin akwatin wani mai kudin Abuja Du'a zata aura, itada ta dauka wani mai gadi ne kokuma lebura haka zata aura, amman wanan akwatuna haka set 15, kowani saiti nada 3 dan designers akwati ne ba irin na Nigeria ba, ahankali tace "Kaka yarinya tai goshi Allah sanya alheri" da karfi Grandma tace "Ameen" sanan tanuna ma kowa dakinshi asaman dan suje suyi wanka su huta, kowa yatafi, su Hawwa suka koma dakin Du'a duk suna mamakin akwatin Du'a dan basu saba ganin irinshi a kano ba.
Dakin Grandma Mami ta shiga, waje tasamu kusada Grandma tace "Mama Yaya Muhammad yace jibi zasu shigo ko ranan jumma'a" murmushi Grandma tamata tace "ashe kunyi waya haka yagayamin" shiru Mami tayi tana kallon mahaifiyar nata tasan har yanzu fushi takeda ita, ahankali tace "Mama dan Allah kiyakuri kiyafemin komi dan Allah" juyowa Grandma tayi takalleta kaman tai shiru saikuma tace "naso namiki yanda kikama Du'a yarki ne, nima na nuna miki baki da amfani kaman yanda kika nunama yarki, but I guess bazan iyaba Zainab" sauka Mami tayi daga kan gadon, guiwanta tasauke akasa tana kallon mahaifiyar tata, ahankali tace "dan Allah kiyakuri kiyafeni" hannu Grandma tasa tadagata dan tanason yarta bakadan ba, zaubarda ita kusada ita tayi tace "Na yafemiki komi ya riga yawuce Du'a tariga tai aurenta, ranan lahadi war haka ai tanama gidan mijinta so bakomi, yanzu dai akwai magungunan ta wajen Jummai, kinsan zan shiga hayaniya ba lallai nasa idoba kisamata ido makesure tashanye komi sanan taci abinci dan bata iyacin abinci har yanzu, akwai turaruka ma anan zaku dinga mata" gyadama Grandma kai tayi tace "to Mama" ahankali Grandma tace "kinga yaron daya wahala shi Allah yake kyautatamawa akarshen sabida ya wahala yay hakuri, Allah yabama Du'a miji, idan kinga yanda yaron kesonta dudda yana kokarin boyewa sai kinyi mamaki, ko bani duniya ayau Zainab na yarda da Asad zai kulada Du'a kaman kanwarshi wanan shaidar nimishi ita" murmushi Mami tayi hankalinta nakara kwanciya tace "Alhamdulillah".
Wuraren 4 Dad yakira Asad dabayanan awaya, bai daukaba akaro na biyune yadauka, Dad yace "kana office ne" cikin muryan nan nashi na baison magana yace "ganinan zan shigo gida" katse wayan yayi yashigo yay parking sanan yafito yana kara kallon yanda ake aikace aikace ana decorating gidan for event sanan yay falonsu, Dad yagani zaune da kowa afalon ga wasu kwalaye sweet, goro tabarma da sauransu akasa duk ana magana, ganinshi yasa akai shiru yaran duk suka gaidashi, karasawa yayi yazauna kusada Sharif ahankali yana yatsine fuska danyagaji, harara Anty Turai ta watsamai, murya chan kasa yace "Dad gani" murmushi Dad yayi yace "My Son the latest ango, anyway family din wife dinka gabaki dayansu sunzo suna around, mahaifinta da kannen mahaifinta maza biyu, da macen,