Showing 69001 words to 72000 words out of 153675 words

Chapter 24 - Kyawuna Jarabta Ta Hausa Novel Complete

M SHAKUR   

15 Dec 2024

626

bazan bada yarinyar nan ba bazan bayarba" dasauri Ammi ta tashi ganin Hajiya tadauki zafi sosai tace "Hajiya calm down" cikin fushi sosai tace "don't tell me to calm down, sunason yarinyarne suka azabtar da ita, yarinyar dabaya lissafata cikin yaranshi, sun kulle yarinya, Du'a became so depress, sunyi depriving yarinya of her right, na education, bata iya komi an yaa mace ba, bata iya girki ba, yarinya sun maidata doluwa mara wayau, yarinya yar 15yrs yanzu zata iya saida Du'a, sun cutar da Du'a shine yanzu sukeso su dauketa su maidata gida sabida wacce tace akoreta da farko tace yanzu adawo da ita to wlh wlh kura yay kadan afadan giwa" Ammi karan kanta saita taji tsoro tunda take da Hajiya bata taba ganin bacin ranta da bala'intaba sai yau......


Sosai Du'a kejin hayaniya wanda tunda tazo gidan bata tabajin irinshi ba, tashi tayi dagakan gado gabanta nafaduwa hakanan ahankali tabude kofanta muryan Grandma taji dasauri tafito, jin maganganun da Grandma take duk akanta ne yasa tai hanyar stairs din tana tafiya ahankali, hango Mamin ta da Abban ta, da Ammi da Dad, saiga Grandma a tsaye tana masifa sosai yasa taji jikinta yafara rawa, su Mami sunzo su komarda ita, wani irin kuka ne yazo mata dasauri tasa hannu ta toshe bakinta tahana kukan fitowa, saikuma tajuya da gudu tai dakinta kaman mahaukaciya tana wani irin kuka kaman wacce ke hauka, memory gidansu yahau flashing akanta, rawa jikinta yafara sosai tace "no....no oooo" wani irin bude kofan sip tayi jakan goyonta na makaranta sabo da sum sayo ta fizgo kome tagani turawa take ajakan, gyalen abayan dake jikinta tadaura ta yana akanta sanan ta goya jakan tana kuka sosai, fitowa daga dakin tayi tana kalle kalle saikuma tasake komawa dakinta tai wajen window dakin, bude window tayi tana kallon kasa dan abene take, wani irin fashewa tayi da kuka tana goge idanunta da bayan hannu tace "bazan koma gidan nan ba, bazan koma ba, nooo" kawai tahau kan window kaman wanda aljanu suka shiga, runtse ido tayi kawai tai jumping tundaga saman nan har kasa aiko tafado timmm kan grass carpet din dake wajen wani irin bugewa tayi ahannu da kafa amman bata damuba ta tashi tana kuka sosai tana wani irin dingishi tana tafiya da gudu gudu sauri sauri ko kallon maigadinsu batayiba tabude gate tafice, tana fita tawani irin kwasa dagudu rikewa kafanta yayi hakan yasa tai kara, da kyar ta tashi bamatabi takan kakkabe jikinta ba ta kwasa da mugun gudu tana dingishi, Asad da fitowanshi daga Gate kenan da motanshi zashi office lokacin itama tafito ganin tafadi tasake mikewa tana gudu still tana kuka yasa yatabe baki, saka sit belt dinshi yayi ya danna waka yaja motan yana gudu ahankali.



💫 KYAWUNA JARABTA TA 💫


✍️ M SHAKUR

EPISODE 4️⃣3️⃣
kafin yakai gate din estate dinsu harta wuce tayi titi tana gudu sosai, fita yayi daga estate din yana jiran traffic light abashi go ahead yawuce, kaman ance yakalli side din left dinshi, ganin yanda take gudu tana dingishi tana kuka sosai yasa yadanyi jim kaman mai tunani, maganan Ammi ne yafadomai rai datamai ranan nan what if kanwar kace su Rahima da Aneesa, yatsine fuska yayi ya karya kwana yaja motan dawani irin mugun gudu, saura kiris yabugeta akan titin hakan yasa ta tsaya chak ganin mota yasha gabanta tana goge hawayen fuskanta tana kallon motan dayake tinted dan bata iya ganin naciki, saukar da glass din motar yayi yana kallonta fuskanshi babu ko alamun strictly yace "get in" girgixa mai kai tayi jikinta ko'ina narawa saikuma tafashe da mugun kuka sosai akan titi tace "dan Allah dan Allah kabarni natafi, Dan Allah Dan Allah Dan Allah narokeka Ya Asad" tunda take bata taba kiran sunanshi ba sai yau, jin yanda ake bugamai horn akan titi yasa azuciye yabude marfin motan dawani irin gudu tajuya zata tafi sabida dingishin datakeyi yasa taku daya yayi ya dauketa tana ihu ko kallon mutanen dake titi baiyiba yabude baya ya jefata ciki yay locking car, sanan yashiga gaba yaja motan dawani irin mugun gudu.


Wani irin mahaukacin kuka take a motan shi kaman yana yankata, takasa shiru, saida yay tafiya mai nisa sosai sanan yakai wani filin kwalo dake kan titi yay kwana ya shiga dan babu kowa ciki, parking motar yayi awani irin zuciye yabude motan yafito yabude bayan motan hannunshi yasa yawani irin fizgota waje sanan yabugata dajikin motan yasaka mata mugun tsawa. "shut up!" ko tari bata karaba gabaki dayan kukan datake daya kusan taushemai kunne hadiyeshi tayi jikinta na bala'in rawa, rasa yanda zatayi yasa kawai saita zube agabanshi tai kneeling looking so helpless and pitiful da zakaji kaman ma kamata kuka, kaman karaman yarinya harwani jiniyan kuka take cikin muryan bala'in tsoron shi tace "Ya Asad dan Allah kayakuri kataimakeni allow me to run, dan Allah Ya Asad karka bari su komar dani kano, dan Allah karka bari su komardani kano, dan Allah dan Allah dan Allah ya Asad dan Allah karka bari su komarda ni kano, dan Allah kataimakeni" yanda take rokonshi jikinta narawa kanta akasa dan tsoron shi ma yahanata ta kalleshi yasa yabitada kallo saikuma yay shiru still kallonta yake, yakai kusan 1min ahaka bazaka taba iya tantance yanayin shi ba yace "stand up" tashi tayi tana sauke ijiyan zuciyan kuka tana kuka, gaba yabude mata yace "shiga ki zauna" shiga tayi batare datai musu ba ta zauna, maida kofan yayi yarufe sanan yazagaya ta side dinshi yabude yashiga yazauna yadade yana kallon filin kwallon yanajin yanda take rera kuka ahankali tana sauke ijiyan zuciya sanan yajuyo ya kalleta yanda riganta yay budu budu duk kasa sabida faduwan datayi, dauke kanshi yayi yamaida gefe yana kallon filin kwallon yace "maisa bakison komawa gida" kaman jira take tafashe da kuka tace "Abban mu baya sona, Mum bata sona, su Ya Hawwa da Ya Nana duk basa sona, Kakan mu bata sona,Ya Hamad kadai kesona agidan" murya chan kasa batare daya kalleta ba yace "waye Ya Muhsin waye Ya Hamad, maisa kowa baya sonki" gabaki daya tabashi labarin gidansu dudda in a childish way ne but he understood everything, sosai take kuka tace "Ya Asad dan Allah kataimakeni kaji, dan Allah karka bari su Abba su koma dani kano dan Allah kataimakeni" tafashe dawani irin kuka mai tsuma rai tana daura kanta akan cinyoyinta, yakai kusan 2min kallon football field din dasuke ciki yake sanan yajuyoda kanshi wani makirin murmushi yasaki for the first time sanan yace "kinason in taimaka miki"? Dawani irin sauri tadago kanta da jajayen idanunta takalleshi dasuke cikemda hawaye, gyadamaikai tayi ahankali tana goge hawayen da bayan idanunta, yana kallonta still yace "are you sure kinaso na taimaka miki"? gyadamai kai tasakeyi cikin muryan kuka tace "eh" tabe baki yayi sanan yadauke kanshi daga kallonta yace "idan kinaso na taimaka miki dole ki koma gida and face ur father and ur Mum" girgixamai kai tayi wani sabon kuka yana zuwanmata tace "wlh zaku komar dani gidan nan dan Allah Ya Asad kayakuri kataimakeni karsu tafi dani" dan juyoda kanshi yayi yakalleta, zubamata mayun idanunshi yayi dayasa taji tahadiye kukan datakeyi tana kallonshi cikin wani irin murya yace "do you trust me"? hakanan taji idanunshi na compelling nata dan batasan lokacin data gyadamai kai ba tace "eh" ahankali yana kallonta yace "I will help you, I have a plan but dole ki koma" gyadamai kai tayi badan tasoba, juyawa yayi yasa hannunshi abayan yazaro wani rag, jefa mata ajiki yayi yace "first thing first clean ur body" dasauri tadauki tsumman ta goge jikinta tass dashi, wani kalan earpod taga yadauko dabatasan na mene ba, gani tayi yayi connecting nashi to wayanshi sanan yajuyo ya kalleta yace "saukar da this thing kasa" yanuna mata gyalen kanta baki, kallonshi tayi ganin yamaida hankalinshi kan wayanshi da abin daya rike a hannu yasa gently takai hannunta taja gyalen abayan kasa, yan kananun kalabanta suka wani bayyana, ga kwantaccen suman gaban goshinta, juyowa yayi ahankali yakalleta, murya chan kasa yace "come closer" matsowa tayi kusadashi ahankali hartanajin saukan numfashin shi kan fuskanta, dauke idanunshi yayi dagakan fuskanta yadaura kan fararen kunnuwanta, ahankali yadauko abin guda daya yakai kunnenta yasamata aciki yana kallon yanda takeda gashi har akunne a kwance, murya chan kasa yace "the other ear" juyoda kanta tayi fuskanta yataba kafadanshi ajiyan zuciya tasauke, gently yasaka mata sanan yakoma sit dinshi yazauna hakan yasa itama yakoma tazauna, ahankali yace "I will help you, namiki alkawari baza'a tafi dake ko'ina ba inhar u do what I will tell u, idan kuma bakiyiba u are on the own, I have one condition koda wasa karki sake kafadama wani ko wata cewa nine na taimakeki understood" yay maganan yana kallonta dasauri ta gyadamai alamun eh, yace "duk ranan da kika fadima wani what happen ranan nida nataimakeki ni din still zansa amaidaki Kanon" dasauri ta girgizamai kai, kunna mota yayi yaja yace "zanuje yanzu, I will drop u outside zaki shiga direct wajensu zaki ki gaidasu, daganan I will be telling you kome zaki fada musu sanan kome sukace zan baki amsan abinda zaki fada musu, remember say exactly what I said kingane" dasauri tasake gyadamai gabanta na mugun faduwa dan gani take kaman wayau yake mata, har gaban gidan sanan yakashe motan yajuya yakalleta yace "gyara gyalen karsu hango abun nan, and don't show them any sign cewa magana ake miki a kunne" sake gyadamai kai yayi, ahankali yace "sauka kitafi" kallon fuskanshi tayi hawaye taji zasu zubomata murya chan kasa tace "Ya Asad dan Allah karka bari su tafidani kano dan Allah kataimaka min" yadade yana kallonta kafin ahankali yace "I will help u Du'a, now go, remember kome nafada miki repeat my words exactly" gyadamai kai tayi tabude kofan tasauka ahankali tabude gate tashiga gida bayan tabar jakanta a motan shi, saida yaga tashiga gida sanan yaja motar shi zuwa gidansu horn yayi aka budemai yay parking awajen parking lot dinsu sanan yay locking motar yana gyara zama ya kara wayanshi saitin bakinshi yanajin sautin karan bude kofan datayi dakuma hayaniya dake tashi afalon.



Binta kowa na falon yayi da kallo, ahankali Grandma da ranta ke abace tace "me kikayi anan" hawayen daya zubomata ta share tana gyara tsayuwanta tanajin maganan da Asad yayi sanan takalli Grandma tace "nazo wajen Abba da Mami ne inason magana dasu" kowa kallonta yake, barinma Dad dako kyafta ido ba yayi yana kara kallon halitta irin na ubangiji Baba baki Mama baka, y'a balarabiya, zama tayi ahankali agabansu ahankali tace "Abba ina kwana, Good morning Mami" anatse Babanta yace "Du'a ya kike? Maganan me zakimin bazaki iya bari anjima ba idan mugama magana da kakanki" girgizamai kai tayi ahankali sanan takalleshi tace "Abba Grandma batada lpy sosai, banson sabida ni wani abu yasameta" tsareta da ido Abba yayi sanan ahankali yace "okay to ina jinki menene" shiru tayi kusan 2min takasa magana hakan yasa Abba yace "speak up Du'a, yauzan koma kano" bakinta duk suka gani yafara rawa sosai kaman tana kokarin fighting abinda zata fadi, saikuma ta runtse idanu gam kaman daga sama duk sukaji maganan kaman saukan aradu. "Abba ni aure nakeso!" ba Abba kadaiba da Mami har ita Grandma saida tadan jinkirto daga kujera tana kallon Du'a jin maganan daya futo daga bakinta, tadauki kusan 1min idanunta a runtse sanan tabude idanunta ahankali tadago kanta takalli Abba dake kallonta asanyaye murya chan kasa hawaye na taruwa a fuskanta tace "Abba wlh ni aure nakeso, da inkoma Kano gwara nai aure" tai maganan ahankali dayasa Abba kasa koda motsin kirki hakama Mami dasu Ammi daduk ke falon, ahankali Mami tace "Du'a! Aure kikeso?" Tamata tambayan da mugun mamaki, gyadama Maman nata kai tayi ahankali tace "aure nakeso Mami" Abba da yaji ranshi yasosu sosai da kalamanta yace "Du'a kinsan mekike fadi kuwa? Aure kikeso, wazai aureki? wakikeso to ki aura eh"? Wanan karan shirun datayi yamafi nada sosai lips dinta kerawa takasa fadin maganan dake bakinta hakan yasa Abba da ranshi ke abace yadaka mata tsawa yace "I told you I don't have all day I still have to go back to kano yau, wakike so Du'a!" Yasaka mata tsawa dabatasan lokacin da maganan tafito ba. "Ya Asad!" Tai shiru tana wani irin sauke ijiyan zuciya kaman kirjinta zai fito sanan tace "Ya Asad nakeso Abba!" Wani irin kwalalo idanu Dad yayi, Ammi batasan lokacin dawani irin kayataccen murmushi ya kufce mata a labba ba, surprise look Grandma kemata danyau Du'a takasheta da mamaki, Abba dake kallonta yace "waye Ya Asad" ahankali tanuna Ammi tace "ga Babanshi da Maman shi anan" wanan karan saida Grandma itama tai murmushi bama tagama kai karshen murmushin ba tace "Abba dan Allah ka auramin Ya Asad ina sonshi sosai" wanan karan Abba jiyayi duka karfinshi yakare Du'a humiliated him to the core dabaisan lokacin daya dago kanshi ahankali yakalli Dad ba ahankali Akuma natse yace "waye Asad"? hada idanu Grandma da Ammi sukayi kafin Abba yamayi magana Ammi ta mike zumbur dasauri tace "I think har yanzu baitafi office ba, bari naje gida nakirashi kaganshi Baban Du'a" tafita daga falon dasauri batare data jira amsansu ba Abba da kowa na falon yazubama Du'a idanu.



Gida Ammi ta shiga, ganin Ammi yasa Asad yayi kaman irin zai tada motarnan yafita ne dawani irin sauri ta bubbuga kofan motan tace "Asad wait wait" saukar da glass din motar yayi yace "Ammi what is it am late fa office zani" dasauri tace "Asad wait kashe motan kaji I have something very important to tell you, kashe kashe kafito" yanda yaga jikinta narawa yasa ya kashe yafito yana kallonta yace "is everything okay maiya faru Ammi"? Hannunshi takama tarike duka biyun tace "look at me Asad we don't have much time but we will go into deep details later,Asad kasan nina haifeka ko, nai rainon cikinka na haifoka na tarbiyantan dakai zuwa what u are today nataba tambayanka kabiyani ko kasakamin"? dasauri yace "no Ammi" ahankali tace "tom I need u to do something for me, taimako zakayi kuma duk wanda yataimaka ma wani Allah zai taimaka mishi, at this point wata yarinya her life depend on u wlh Asad, please Asad dina, and just know this bazan taba saka kai abu mara kyau ba so u should trust me" kallonta yake kaman wanda bai gane komiba yace "Ammi maizanyi" danshiru tayi kaman wacce ke shakkan fadamai tace "inaso ka auri Du'a jikan Hajiya" dawani irin sauri ya fizge hannunshi yay baya dasauri sauri yace "no way! Ammi, kinsan mekike fadamin kuwa" cikeda damuwa Ammi tabiyoshi hannunshi tasake rikewa tace "Asad bamu da time ana jirana naso dakaine dan girman Allah that's just the only thing I need u kamin right now, any other thing we will discuss it later, at this point kawai u need to save her ne please Asad dan girman Allah idan kana kaunata ni mahaifiyarka, Asad dan darajan Allah karka zubamana kasa a idanu, As......" Ammi! yawani irin kirata da mamaki, cikeda damuwa tace "Asad lemme kneel for u toh halan sainai hakan zakayi" takai gwuiwanta zatasa akasa, dasauri yarike mata hannu yace "Ammi don't kneel for me" kaman zatai kuka tace "Asad I have to kneel for u inhar hakan zaisa kayarda ka taimaken ka auri yarinyar nan nagayama we will discuss d matter later yanzu kawai ina bukatan ka ceci rayuwanta ne inba hakaba tafiya da ita za'ayi, gwara na duka maka Asad na rokeka" tai kaman zatakai gwuiwanta kasa dawani irin sauri yariketa yace "ohhh ohkay Ammi naji basaikin kneeling ba" dasauri ta tashi takalleshi tace "zaka aureta"? Yatsine fuska yayi yace "yes Ammi for now just to save her kuma sabida ke" wani irin ihu Ammi tayi ta rungume shi tana kissing fuskanshi tanamai addu'a kafin taja hannunshi sutafi.


Sallama Ammi tayi tabude kofa tashiga Asad biyeda ita kanshi akasa yana cikin suit din aiki, kallo daya Abba yamai yagane yaron dan yaga program din dayayi na youth a channels television news, zama Asad yayi kanshi akasa anatse yace "ina yini Abba" ahankali Abba yace "Alhamdulillah kaine Asad"? Gyadamai kai yayi ahankali yace "tell me about ur self Asad" danshiru Asad yayi sanan ahankali yace "sunana Asad Abdullahi Kitse, I am 33yrs old, nai karatu a UK inada 2 degree my first degree is medicine I am a Doctor, sai na biyun business Administration, currently yanzu bana aiki as a Doctor, business nakeyi inada company kaina" yay shiru daidai nan, gyadamai kai Abba yayi sanan yadaga kai yakalli Grandma dake kallonshi yace "kin yarda da tarbiyan Asad Mama" gyadamai kai tayi tace "a hannuna Asad ya girma nasan waye Asad, na aminta da tarbiyan yaron nan dari bisa dari" gyadakai Abba yayi babu ko alamun wasa tattare dashi yakalli Asad yace "zaka auri y'ata Du'a Asad"? shiru Asad yayi, ahankali Mami tataba Abba, kabarda hannunta yayi batare daya kalleta ba still yana kallon Asad yace "zaka auri y'ata Asad"? kaman Asad bazaice komiba har lokacin kanshi akasa ahankali yace "eh zan aureta Abba" gyadakai Abba yayi yakalli agogon dake daure a hannunshi yaja daya saura, dagakai yayi yakalli Dad dakenan azaune kaman ruwa yacishi yace "bismillah mutashi mutafi masallaci, Asad bismillah" tashi Dad yayi, Asad ma yatashi duksu Grandma na kallonsu suka fita daga gidan, suna zaune nan shiru afalo aka tada sallan azahar akayi sai sukaji sanarwa ana adakata jama'a akwai daurin auren da makocinmu Sanata Abdullahi Kitse yakeson ku shaida, kafin kaceme kawai su Grandma sukaji ana an daura aure tsakanin Asad Abdullahi Kitse da Du'a Muhammad akan sadaki dubu dari.



💫 KYAWUNA JARABTA TA 💫


✍️ M SHAKUR

EPISODE 4️⃣4️⃣

Ko minti biyu basu karaba sai gasu sun shigo gidan da Sallama, Amsasu Grandma tayi suka shigo, kan Asad akasa kowa yanemi waje yazauna, Abba yadade ahaka sanan yay gyaran murya yace "Du'a" dago kanta tayi ahankali takalleshi, anatse yace "zonan gabana" gyadamai kai tayi ahankali jikinta duk yay sanyi sanan ta rarrafa zuwa gabanshi ta lankwashe kafa, hannunta yakama ahankali yarike yana kallonta yace "Du'a you always feel

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login