Showing 63001 words to 66000 words out of 176055 words
Hannun takamo tana kallonsa da faɗin, “Wannan kam ya wuce ƙaramin ciwo, kallifa yanda tafin hannunki ya yayyanke, kinga ga kayan barcinan ki saka bara na dawo”.
Ummu bata iya cewa komaiba, sai binta da kallo datai harta fice, ajiyar zuciya taɗan sauke kafin ta ɗauki kayan barcin wando da riga masu ɗan kauri ta saka, tana ƙoƙarin saka hula taji sallamar yarinyar tareda Attahir. saurin jan ɗan kwalin kayan data cire tayi ta yafa a jikinta, dukda kayan ba matseta sukaiba kuwa.
Kallo ɗaya yay mata shima ya kauda kansa, yayinda budurwar kuma ta ajiye ƙarmin tire mai ɗaukeda kofin shayi da madai-daicin cake a gefe.
“Yaya bara na akarɓo maganin wajen Ummy”.
Kansa ya ɗaga ɗaga mata kawai ya zauna a kujerar data kasance guda ɗaya a ɗakin.
Ummu dai na tsaye tana saurarensu, sai dai kallo ɗaya zakaima fuskarta ka fahimci bata tareda walwala.
Attahir ya furzar da huci yana faɗin, “Bismilla ki zauna mana”.
Bata musa masaba ta zauna a bakin gadon tana haɗiye hawayenta, maganarsa ta sata ɗago ido taɗan kallesa.
“Shine ya jimiki ciwo a hannu ko?”.
Kanta ta girgiza masa tana juya idanunta saboda hana hawayen da suka tara zubowa, amma hakan bai hanasu fitowarba, bakin gyalen tasa ta goge, “Bashi ya jimin ciwoba Abban Ahmad”.
Kansa ya iya girgizawa kawai, yace, “Ok, kiyi haƙuri Ummukulsoom, ki ɗauki hakan a matsayin ƙaddara, dare yayi yanzun, zuwa da safe zamu tattauna insha ALLAH, kisha wannan tea ɗin bilkisu zata kawo miki magani, dan ALLAH ki fidda komai a ranki, ki kuma saki jikinki a gidannan, domin ke ba bare baceba”.
Kanta ta ɗaga masa tana kuma share ƙwallarta, “Nagode sosai Abban Ahmad, amma kayi haƙuri, zuwa yanzu babu inda nake kwaɗayin zama irin ƙauyenmu, kuma yadace mahaifina yasan matsayin aurena a yanzun”.
“Wannan tilas ne ai Ummukulsoom, dolene baba yasan komai, maganar ina zaki zauna kuma duk zamuyi magana daga baya”.
Nanma kanta ta jinjina masa.
Bai bar ɗakinba har Bily takawo maganin, suka saka Ummu tasha tea ɗin dukda taƙii cin cake ɗin, magani tasha yay musu sallama ya fice.
Gajiyar datai a hanya ce tasaka barci saurin ɗauketa, dukda sunsha kokawa tsakaninsa da damuwarta kafin barcin yaci nasara akan damuwar tata.
A washe gari da safe saida Ummu ta makara sallar asuba, bily kuma taƙi tashinta.
A gaggauce tayo alwala tafito, dan ƙarfe takwas saura, bayan ta gabatar da sallar tai addu'a tana kuma tariyo abinda ya faru a jiya, kusan iyanzu duk sun baro cikin Barrack ɗin.
Ganin dukkan kayanta a ɗakin sai mamaki ya kamata, ta kasa fahimtar ma'anar hakan, ita duk tunaninta gari na wayewa zasu ɗauki hanyar ɗilau, kallonta ta maida ga Bily dake ƙudundune a bargo tana barci, Ummu ta sauke nannauyar ajiyar zuciya kawai.
⚡⚡⚡⚡⚡⚡⚡⚡⚡⚡⚡
“Honey wai meke damunkane kwana biyunnan?”.
Baseer dake kwance ɗai-ɗai a gado yana danna waya ya ɗago idanu ya kalli Lubna mai maganar.
“Mikika gani?”.
“Ba komai, kawai dai naga kamar kacika maida kanka busy a kwana biyunnan, bakason zama a gida, idanma ka zauna kata danne-dannen waya kenan”.
Idanunsa ya janye a kanta ya maida kan wayarsa, “Kece dai kikaga hakan, amma ni nasan babu wata canjawa danai”.
Shiru tai kawai tana kallonsa, tama kasa cewa uffan.
Tsawon mintuna suna a haka kafin ta miƙe tabar bedroom ɗin.
Bayanta ya raka da harara yana taɓe bakinsa, a yanzu kam ko kaɗan bata birgesa, bakaramin haushinta da takaici yakeba idan ya kalli ƙaton cikin gabansa, ya tunano zabgegiyar yarinya jinin kanuri Fannah ɗinsa, yarinya mai zamani mai lokaci a zuciyarsa, tuni soyayya tai ƙarfi a tsakaninsu, harma mahaifinta yace ya fito, burinsa ƙarshen watannan ya tura kuɗin aure, dan bayason bikin ya wuce nanda wata biyu, hotonta dake wayarsa ya latso yana kallo, wata nutsuwa da ƙaunarta tareda sha'awa wadda itace ƙarfin son na rinjayar zuciyarta, yarinyar komai yaji kam, dan akwai halitta mai ƙyau.
Tsawon lokaci yana kare mata kallo lungu da saƙo ta hoton, kafin ya rufe yana zamewa ya kwanta.
Lubna kam bata sake shigowa ɗakinba, kwanciyarta taje tayi a ɗayan ɗakinsu kodan ta hutama ranta.
⚡⚡⚡⚡⚡⚡⚡⚡⚡⚡⚡
Sai da su Ummukulsoom sukazo yin breakfast sannan takejin ashe A'i ta wuce gida tun ɗazun, ita kaɗaice a gidan yanzun, suna cin abinci amma banda ita, sai tsakura take kaɗan-kaɗan.
Lura da hakanne yasaka Ummi mahaifiyar su Attahir janta da hira tareda lallashinta akan taci, duk sai kunya ta isheta, dan haka taɗanci abincin.
Kammalawarsu babu jimawa Attahir ya fice akan zaije ya dawo yanzun.
Addu'ar dawowa lafiya sukai masa, itama Ummi ta shirya tafita wajen aiki kasancewar ita likita ce.
Daga Ummu sai Bily aka bari a gidan, Zaid ma yafice wajen nasa aikin.
Kamar yanda Attahir yacema Bily ta ɗaukema Ummu kewa haka ta dake taita janta hira, dukda bata amsawa iyakarta murmushi ko e ko a'a.
⚡⚡⚡⚡⚡⚡⚡
Koda Attahir ya fita gidan su Fodio ya nufa, a falon baƙi akai masa masauki, dan haka hajiya jamila batasan wanene baƙonba, Jud ya kawomasa ruwa da lemo. Babu daɗewa da fitarsa saiga Dad dayasan da zuwansa ya shigo, fuskarnan babu fara'a tamkar kullum.
Zamowa Attahir yay daga kujera ya koma saman Carpet yana gaidashi. Cike da kulawa Dad ya amsa da tambayarsa wajen aiki.
Attahir yace, “Alhmdllh Dad”.
Kujera ya nuna masa alamar ya koma ya zauna, amma sai Attahir ɗin yace, “A'a Dad nanma ya isa”.
Attahir sai juya maganar da zaiyi yake a ransa, amma ya kasa, saikace shine Fodio ɗin, lura da hakanne ya saka Dad gyara zamansa, “Attahir bakinka da magana, sai dai bansan mikake son ɓoye minba? Inhar maganar abokinkace karkaji komai, yama rubutomin text massege a jiyan, ina tsumayen isowar Ummu ɗinne kawai, ɗazun da safe tsohuwar dataje ta tayata zama ta iso gidannan tareda driver, shine yame sanarmin dama tana tare dakai, Saƙo ɗaya zan baka kabama abokinka Attahiru, yayi yanda yakeso, nima saiya jira lokacin dazan masa yanda nakeso, duk duniya ban haifi ɗan dazai jayayya daniba wlhy, ni nafisa tsaurin ido dagashi har uwar tasa data sakashi, idanma shine ya aikoka ka sanar masa bana buƙatar kowa akan wannan maganar”.
jikin Attahir sai tsuma yakeyi jin Dad a matukar fusace yake magana, yakuma kasa da kai yana kwantar da murya, “Wlhy Dad ba Amaan bane ya turoni, hasalima baisan nabaro legas ba a yammacin jiya, amma amin afuwa bisa yin gaban kaina da nayi, nayi hakanne gudun kartace zata wuce garinsu a daren dan bansan shiyama sanar mukuba”.
“Babu komai Attahiru, hakan dakai ba laifi baneba, yanzu ina ita Ummukulsoom ɗin?”.
“Tana gidanmu na barota, dama nafara zuwane akan wata shawara”.
“To to ina saurarenka wace irin shawarace?”.
Shiru Attahir yay yana juya zancen, kafin yace, “Dad dan ALLAH kayi hakuri akan abinda Amaan yayi, karka nunamasa fushinka dan zai taɓa rayuwarsa sosai, mubi ta hanya mai sauƙi wajen nuna masa kuskurensa kawai, sannan mizai hana Ummu ta koma makaranta ita kuma”.
Shiru Dad yay yana kallon Attahir tareda nazarin maganarsa, yaɗan nisa yana kaɗa kansa, “Shawararka mai ƙyauce Attahiru, shikam dama ai bazan taɓa masa maganarba daman, maganar karatunta kuwa zan zauna da mahaifinta muyi magana, dan dama naso takomane tana ɗakinta, a yanzu kam bamuda hurumin hakan tunda bata a ƙarƙashin ikonmu”.
“Eh gaskiyane Dad, sai kuma maganar zamanta a gidan namu”.
“Eh to wannan kam ka bani lokaci, dan nafison tadawo kusa dani kam, amma zuwa anjima zanzo gidan itama na ganta insha ALLAH ”.
“To Dad nagode sosai, ALLAH ya ƙara girma da lafiya mai amfani”.
“Amin ya rabbi Attaru, nine da godiya ai basa zamowarka aboki na ƙwarai, ALLAH yay muku albarka, shima ALLAH ya shiryesa”.
“Amin Dad mun gode, ALLAH ya huci zuciyarka, bara naje ni, shima Amaan ɗin a satinnan zaizo kd ɗin ai”.
“Ok babu damuwa”.
Attahir ya koma gida zuciyarsa na cigaba da takaicin Amaan, sai dai a ransa yanajin cewar yanzune za'a fara wasan, fatansa ALLAH yabasu tsawon rai na dawowa lafiya daga inda zasuje kawai, ALLAH yasa ita kuma Ummukulsoom karta basu kunya.........✍🏻
NO. 22
............A falo Attahir ya iske Ummukulsoom da Bily suna hira, dukda dai bily ce mai firar Ummu tana dai tayata da murmushi da e ko a'a ne, dan tunani gaba ɗaya ya hazuciyarta sukuni.
Sannu sukai masa ya zauna cikin kujera yana amsawa, da ido yayma Bily alamar ta tashi. Murmushi kawai tayi ta miƙe zuwa kicin.
Attahir ya tattara dukkan hankalinsa akan Ummu da kanta ke ƙasa tana wasa da yatsun hannunta, “Ummu ina fatandai komai lafiya? Gidan namu yana miki daɗi?”.
Murmushin da baikai cikiba tai masa, kafin tace, “Komai Alhmdllh, kuma gidannan namin daɗi, musamman dattakon jama'ar gidan da ƙyawawan halinsu abin alfahari da koyi, sai dai kayi haƙuri, ina bukatar tafiya gida kodan iyayena susan halin danake ciki”.
“Hakane, kema kinzo da magana mai ƙyau, amma kiyi haƙuri kiɗan bamu lokaci, dan Dad ma yace zaizo anjima. Dan ALLAH in tambayeki mana”.
Kaɗan ta ɗago kai ta kallesa ta maida, “Ina saurarrenka”.
“Please iya ina karatunki ya tsaya?”.
“Secondary ne kawai”.
Da tsantsar mamaki yake kallonta, “Wai Ummukulsoom dama kinyi karatu har zuwa secondary?”.
“Eh Abban Ahmad ”.
Wani daɗine ya kama Attahir, danshi duk zatonsa Ummukulsoom bata wuce primary ba, a lallai aikin nasu mai sauƙine, cike da zumuɗi yace, “Kin amshi result nakine?”.
“A'a gaskiya bankai ga karɓaba”.
“Wannan mai sauƙine ai amaryarmu”.
Karan farko da wannan sunan ya sosa zuciyarta har fuskarta ta nuna, Attahir dayaga yanda ta ɓata fuska sai yay murmushi yana miƙewa.
Babu zato Ummu taji yace, “Ayi haƙuri bazan sake faɗaba, daga yau Ummukulsoom kawai”.
Kunyace ta kama Ummu, dan batai zaton fuskarta ta tona asirin zuciyarta baneba.
⚡⚡⚡⚡⚡⚡⚡⚡⚡⚡⚡
Cikeda farin ciki ta shigo gidan nasu, dan daga kano take, turus taja ta tsaya a bakin ƙofar tana sauraren labarin da A'i kebama Momcy, wasu hawaye masu zafi suka gangaroma fuskarta batareda ta shiryama hakanba.
“Momcy lallai kinyi kuskure mai girma”.
Daga A'i har Momcy da basusan da shigowar aunty Nurse ba suka juyo da sauri suna kallonta. Da hannu Momcy taima A'i alamar ta tashi taje, miƙewar kuwa tayi ta fito, amma saita maƙale jin gulma.
Aunty Nurse taci gaba da takowa cikin ɗakin tana share hawayenta, “Yanzunan Momcy rayuwar ƴarki bata zama isharar kiyaye ƴaƴan wasuba kenan? Momcy da kanki kika saka Yaa Amaan sakin matarsa, miyasa? Mita tare miki ne? Kin manta raɗaɗi da ɗacin da kikaji a lokacin da Muzaffar ya sakeni bisa tursasawar mahaifiyarsa? Kin mance kukan da mukayi ni da ke da ƴan uwana? Zamana a gida matsayin bazawara baisa zuciyarki raunin tausayama yarinyar da bata tsare miki komaiba Momcy, acikin ƴaƴanki mata kaf ɗinmu Aunty Ummi ce kawai zaune gidan miji, gani ga Ummayya ga Aneesa ga Buhayyah dako yanzu aka mata aure saita zauna amma har kikaba shaiɗan damar ingizaki maida ƙaramar yarinya Bazawara, Momcy nasan kinyi amfani da ƙarfin ikonkine akan Yaa Amaan saboda kinsan bazai taɓa bijire mikiba, amma lallai shima ya tabbata saiyayi dana sani wlhy, kuma yayi asarar mace wadda inada yaƙini a raina bazai taɓa samun koda kwatankwacintaba.......”
A zafafe Momcy ta daka mata tsawa, “Jalilah! Wane irin banzar fatane wannan, wlhy ki kiyayeni”.
Ƙin amsawa Aunty Nurse tayi tama juya ta fice daga ɗakin, ko kallon A'i dake laɓe bataiba dukda kuwa ta ganta, akwatinta taja ta fice takoma motarta tabar gidan, dan yau tamaji gidan nasu gaba ɗaya ya fice mata a rai, duk kayan farin cikin data kwaso sai taji bata sha'awar juyesa anan kwata-kwata, gidan kakanninta ta tafi waɗanda suka haifi Momcy, saidai ƙin faɗa musu abinda ya faru tayi.
Dukda jikin Momcy yayi sanyi da kalaman Aunty Nurse hakan baisa taji zata iya barin Ummukulsoom ta rayu da ɗantaba.
★★★★
Duk abinda ke faruwa tsakanin Aunty Nurse da Momcy Dad na jinsu daga falonsa, murmushi kawai yayi wanda yakan daɗe arayuwarsa bai yisaba, musamman irin wannan dahar hakoransa farare tas suka bayyana, koda ya fito domin tafiya zuwa gidansu Attahir baiko kalli hanyar ɗakin matar tasa ba ya fice abinsa, su kansu yaran wasu a ciki suna falo zaune wasu kuma na ɗakunansu. Hannu kawai ya iya ɗaga musu koda suka gaisheshi.
⚡⚡⚡⚡⚡⚡⚡⚡⚡⚡⚡
Gidansu Attahir Isa direba ya kaisa, dukda kuwa yasan mahaifin su Attahir ɗin baya ƙasarma, amma ya kirasa sun tattauna akan batun Ummu kasancewarsa abokinsa tun barowarsa Ajiwa, kasuwanci ma tare sukeyi abinsu.
A falon Alhaji Abubakar akai masa masauki, kasancewarsa ba baƙo bane a gidan.
Ummi ta fara shiga suka gaisa, tareda tattaunawa itama akan batun Ummu ɗin, kafin atura masa Ummukulsoom.
Tunda ta shigo falon sai kawai taji wasu hawaye na neman ɓalle mata, a gaban Dad ta zube a ƙasan carpet ta fara gaidashi cikin rawar murya.
Shima tunda ta shigo idonsa na kanta, wani tausayinta na ratsasa.
Yay ɗan gyaran murya yana kuma maida hankalinsa a kanta sosai, “Ummukulsoom badai kuka ba?”.
ƙasa tai saurin yi da kanta hawayen na sakkowa.
Nannauyan numfashi Alhaji Mahmud ya sauke, kafin yace, “Yanzu ba lokacin kuka baneba ɗiyata, lokacin sanin ciwon kaine, ni na haifi Fodio amma bazan taɓa hanaki damarkiba domin maida masa murtani, bana buƙatar jin abinda ya rabaku a yanzu, fatana kizama jaruma wajen neman abinda yake tunanin kin rasa kinji”.
kanta ta ɗaga masa alamar amsawa tana share kwallar data zubo mata, “Baba to dan ALLAH inason komawa gida, kodan su baba susan halin da ake ciki suma”.
“Ummukulsoom kenan, bazance miki a'a ba, bakuma zance miki eh ba, sai dai albishir dazan miki shine, Babanki yasan komai, dan ɗazun da rana mun haɗu dashi agidan innarki mun tattauna”.
Cike da mamaki ummu ta kalleshi, cikin suɓucewar harshe tace, “Amma baba shine baice na koma gidaba”.
Sosai ya kalleta shima yanzu, “Ummukulsoom ba komawarki gidane matsalarba, mutuncinki shine abin dubawa, kindai san miya faru kafin aurenki da Fodio, idan kin koma a matsayin bazawara wace kalar dariya kike tunanin za'ai miki da mahaifinki a wannan ƙauyen? Dama akwai masu jiran irin wannan ranar a gareki, waɗanda a kullum suke jifar babanki da kalmar saidaki yay gamasu kuɗi, ke yarinyace, sai nan gaba zaki fahimci abinda muka hango miki, ki kwantar da hankalinki kicigaba da zama anan gidan, yanzu haka an fara bincika miki makaranta”.
Wani ɓangare na zuciyar Ummu a ƙuntace yake, wani gefen kuma yayi farin ciki da komawarta karatu, dan aganinta shine farkon tsanin nasara a alwashinta. Godiya ta shiga yima Alhaji Mahmud, yayinda kaunarsa keta ratsa ranta, samun irin waɗannan a cikin al'umma abune mai matuƙar wahala, irinsu Dad sune jagororin masu kishin ƙasa da al'ummarsu na gaskiya, da ace irinsune suka yawaita a yankinmu da bamuyi kuka da attajiraiba da shugabanni.
Dad yaji matuƙar daɗi ganin Ummu tabasu haɗinkai, ya saka mata albarka sosai kafin yay musu sallama ya tafi bayan yabata kwalin waya sabuwa fil da wasu ƴan kuɗi.
⚡⚡⚡⚡⚡⚡⚡⚡
*_SABUWAR DUNIYA_*
Dole mu kira wannan ƙaddara ta Ummukulsoom da suna sabuwar duniya, dan kuwa tazo mata da sauye-sauye na haƙiƙa, a sati ɗaya kacal datai gidansu Attahir harta fara canjawa, dan kowa a gidan ƙoƙarin canja damuwarta yake da farin ciki, Ummi tajata a jikinta sosai tamkar uwa mahaifiya, Bily kam amsa suna biyu takeyi, ƙawa kuma ƴar uwa, Attahir ya zama yaya hakama Zaid, saiko Uwa Uba Dad da Abba mahaifin su Attahir da tun dawowarsa gidan yaji wata tsantsar ƙaunar Ummukulsoom, tareda girgizar