Showing 102001 words to 105000 words out of 176055 words

Chapter 35 - Wutsiyar Rakumi Book 1 Hausa Novel Complete

07 Jan 2025

867

sau 100”.
Dariya Ummukulsoom tayi tana faɗin “Amin Ahmadi na”.
Maman Ahmad dake bayansu tace, “Wai dama kin shigo?”.
“Wlhy na shigo aunty, tiɓis nake, banason shigowa kicin ɗinnna naga abinci yunwata ta ƙaru shiyyasa”.
“Hhhh anya wannan azumin zai kai labari kuwa?”.
“ALLAH aunty zai kai insha ALLAHU saina gamashi, saura biyu fa ya rage yau idan nakai uku”.
“To ALLAH ya taimaka, shiyyasa nayi nawa da wuri na huta”.
Miƙewa Ummu tai ta nufi kicin ɗin itama, “Ai kinyi dabara wlhy Aunty, nima a time ɗin muna tsaka da exams ne wlhy, shiyyasa bana ko sittar shawwal banyiba fa, ALLAH dai ya bamu ladan niyya”.
“Amin” Bily ta karbe tare da ma Ummu sannu da dawowa.

Suna a kicin ɗin har aka kira sallar magriba, Ummu sai tambayarsu take wai wannan uban abincin da akayi duk wa zai cisa? Ko suma duk shi zasuci matsayin abincin dare?”.
maman Ahmad tace, “Kusan hakan za'ai, dan bazamu bari kici dadi ki fimu kibaba”.
Murmushi Ummukulsoom dakecin Dabino tayi, ta ɗauki kofin ruwa tasha sannan ta fice zuwa ɗaki yin sallah.

★★★★

Ana idar da sallar magrib suka nufo gida shi da Attahir, Bily kawai suka iske a falon dan tana fashin salla, tai musu sannu da zuwa a zuciyarta tanama Ummukulsoom dariya, ashe Yaa Amaan ne baƙon da Maman Ahmad tace zaizo shan ruwan, lallai yau akwai kallo.
Shidai Amaan kai tsayema dani ya nufa, dan ba yaune ya fara zuwa shan ruwa gidanba idan yay azumin litinin da alhamis, ba komai ke kawosa ba kuma sai abinci irin namu na hausa, dan desmond ba iyawa yayiba, koya kamanta yi bayayi masa daɗi, shiyyasa inhar yana bukata baya cutar kansa saiya ce maman Ahmad tai masa, itako bata taɓa gajiyawa ba da yimasan.
Matsowa Attahir yay kusa dashi yana faɗin, “Ajiwa nikam dai bara na watsa ruwa”.
Kansa kawai ya ɗaga masa ba tare da yayi magana ba, sai ƙoƙarin buɗe kwanikan saman dani din yakeyi hankalinsa kwance tamkar a gidansa.
Yana ƙokarin zuba kunu a kofi Ummukulsoom ta fito daga dakin tana waya da Umar dake mata barka da shan ruwa, sam bata lura da shiba, sai dai tabbas taji ƙamshin turarensa, hakan kuma baisa ta kawo a ranta yana kusa ba, kujera ta ja ta zauna sunayin sallama da Umar.
Tunda ta fito shikam idonsa ya sauka a kanta, harta ƙaraso yana mata kallon ƙasa-ƙasa, amma sam babu wanda zai fahimci hakan sai shi da yakeyi, kusan gagararsa zuba kunun yaso yi, sai dai ya dake harta karaso wajen, yanda take magana ƙasa-ƙasa a wayarne yasa baiji mi take faɗaba, amma hakan ya soki zuciyarsa sosai.
Ajiye wayar Ummu tayi tana murmushi mai sauti, sai dai tana ɗagowa da nufin ɗaukar kunu ta zuba idonta ya sauka a kansa, ya wani basar yana motsa kunun da ya zubama sukari tamkar bai gantaba.
Tuni fara'ar fuskarta ta ɗauke, a ranta tana mamaki shikuma miyazo yi? Harda yima mutane ɗare-ɗare a dani, aiko ta ɗau alwashin bazata tashiba, dan haka itama ta basar tamkar bata gansaba, ta ɗauki kunun dake gabansa ta zuba tana kuma wani ciccije fuska ita a dole kar a kawo mata raini.
Duk motsinta yana kallonsa ta ƙasan ido, jira yake yaga zata gaisheshi.
Kununta ta gama zubawa ta ɗiba ƙosai tare da farfesun kifi ta fuske abinta tanaci hankali kwance, harda ma yanga ta neman magana, babu wanda ya kula ɗan uwansa a cikinsu, sai dai kowanne yana satar kallon ɗan uwan nasa ta gefen ido.
Saƙo ya shigo wayar Ummukulsoom, hakanne ya sata ɗaukar wayar dan tana ƙyautata zaton A-Waheed ne. Ilai kuwa shine, ta buɗe saƙon kamar haka,

_Safiya ta shuɗe, rana ta gushe, yammaci ya wanzu, alkairin ALLAH yakai gareki ma'abociyar kamewa, barka da shan ruwa._
*Naki UMA*

Lallausan murmushi Ummukulsoom ta saki, wanda yakusa sumar da Amaan dake satar kallonta, ya lumshe idanu ya buɗe akanta a hankali.
Ummu kam da batasan yana yiba reply take ƙokarin maidawa A-Waheed, dan yau taji a ranta zata fara kulashi, jan ajin ya isa haka.

*Kaima Abincin ALLAH ya tabbata a gareka, tare da alkairin da baya yankewa har ƙarshen numfashi.*
_Kulsoom_

Tana gama turawa takuma sakin wani murmushin, jitai kawai an take mata ƙafa da ƙarfi, ta matse fuska saboda zafin daya ratsa har cikin ƙashinta tare da kallonsa, dan tasan sarai shine, kuma yaki ɗaga ƙafar, saima kara murzawa yake tsabar mugunta, ya kuma basar tamkar baya aikata komai.
Filas ɗin kunu ta ɗauka ta diba kaɗan mai azabar zafi, ba tare da ya kula da abinda ta keba dan waya yake dannawa da hannu ɗaya, ɗaya kuma yana rike da cokalin da yake shan farfesu, ta zuba masa kunun a kan hannun dake riƙe da cokalin.
Da sauri ya saki cokalin tare da wayar yana janye ƙafarsa akan tata tare da yarfe hannu saboda azabar zafin kunun data shigesa.
Tuni Ummukulsoom ta mike tabar wajen, ko waiwayensa batayiba ta koma falo dariya nacinta.
Da kallo kawai ya iya binta yana cigaba da yarfa hannun, wajen har yayi jajur abinka da fari......
“Ajiwa lafiya?”. ‘Attahir daya karaso wajen ya faɗa yana kallonsa’.
Sam fuskarsa babu walwala matuƙa, alamar yaji zafin abinda tai masa har cikin ransa, murya a dakile yace ma Attahir ƙonewa yay.
Hannun Attahir ya kama yana kallo da mamaki, “Ƙonewa kuma Ajiwa? Garin yaya haka? ga wajen haryay ja kamar zai tashi”.
Baice ma Attahir komaiba, sai zuciyarsa dake ƙara wani kumbura saboda takaici.
Kira Attahir ya kwalama Ummukulsoom dake zaune a falo, ta amsa tana tasowa tamkar ba ita ta aikata tsiyar ba.
“Samo ƙankara a kicin”.
“To” ta faɗa tana harar Amaan da shi bama ita yake kalloba.
Saida tasha dariyarta a kicin sannan ta kawo ƙanƙarar, ta iske maman Ahmad da Bily ma sun fito, Handkherchief ɗin da Bily ta kawo wanda na Ummukulsoom ɗinne Attahir yace ta amsa ta zuba ƙanƙarar a ciki.
Saida ta harari Bily sannan ta amsa tayi yanda Attahir yace, Amaan dai duk yana jinsu, amma baiko tankaba, ko sannu dasu maman Ahmad suketa jera masa kai kawai ya ɗaga musu.
Attahir na shirin amsar ƙanƙarar yay masa sai kawai sukaga ya mikama Ummukulsoom hannun.
Da wani uban haushi Ummu ta kalli hannun sannan ta kalli Attahir, amma sai yace mata “zauna ki saka masa to”.
Fuska ta ƙwaɓe tamkar zatayi kuka dan takaici amma sai Attahir ya ɗauke kansa, danshi yaji a ransa akwai abinda ya faru, ba hakanan Ajiwa ya ƙoneba, kuma tunda ya nuna Ummu zata saka masa ƙankarar ya tabbatar akwai dalili, dan yasan halinsa sarai.
Ganin babu wanda ya goyi bayantane yasata zama idonta cike da ƙwallar takaici, da mugunta ta danna handkherchief ɗin dake ɗigar da raɓar ƙankarar akan hannunsa, amma ko motsi baiyiba dukda yaji zafi kuwa, haka taita danna masa cike da mugunta har ƙanƙarar ta kusan gama narkewa, hannunsa ya janye, batareda kowa ya lura ba ya ɓara mata kunun gaban Ahmad da aka zuba mawa yanzu a hannu itama.
Tana ƙwalla ƙara yana mikewa cike da basarwa, babu wanda zaice shiɗinne ya aikata.
Duk kanta sukai suna tambayar lafiya, hawayenta ta goge ta ɗago ta kalli Amaan dake shirin wucewa, kallon ido cikin ido sukaima juna wanda babu wanda bai jisaba har cikin jininsa ita da shi.
“Maman Ahmad na gode sosai, ALLAH ya raya Ahmad ya kawo ƙannensa masu albarka, Attahir na wuce”.
Kallonsa sukai, yayinda hankalinsu ke kan Ummukulsoom, bai jira amsar kowa ba ya fice abinsa, hakanne ya saka Ummukulsoom saurin faɗin, “ALLAH ya saka min kuma”.
Wani murmushin da bai shiryama zuwansa bane ya subuce masa, ba tareda ya juyoba ya karasa ficewarsa.
Ita da yake ma kunun ya huce nata bai tashi ba, sai dai zafi da yake mata.
“Ummukulsoom wannan ya tabbatar min da kece kika ƙona Ajiwa ko?”. Attahir ya faɗa yana tsareta da idanu.
Baki ta ɗan tura gaba tana share ƙwalla, “Yaya shinefa ya fara takani”.
“Ke kuma sai kika ƙonashi ko? maganinki ai, na kula sam baki gama sanin halin Ajiwa ba, idan har kikace ta wannan hanyar zakibi ki ringa masa abu wlhy wahala zakiyita sha, dan ba raga miki zaiyiba”.
Ita dai batace komaiba, sai maman Ahmad daketa mata sannu, bily kam tanajin tushen zancen saita hau dariya, dama tayi zargin hakan.


⚡⚡⚡⚡⚡⚡⚡⚡⚡⚡⚡

Da ƙyar Baseeru ya samu Meenal ta barsa ya tafi ɗilau gaida su baba, yaso suje tare tace, bazataje ƙauye ba wlhy, shidai daya zamarma tilas yaje, sati ɗaya kuma ta bashi kacal.
Babu tunanin komai ya amince, sai kace itace mijin shine matar.
Tsananin son da yake matane yasa ko kaɗan baya iya ƙetare maganarta, ga kuma daula daya samu kansa a ciki wadda baya fatan ko a mafarki ta yanke masa.
Yauma dai kamar ko yaushe yara bin motar sukeyi tamkar yanda suka saba aduk lokacin da bakuwar mota ta shigo ƙauyen, da murnarsa ya shiga cikin gidansu da yagama lalacewa, katangar gaban gidanma ta faɗi sai danni akayi na itacen geza, sai dai kuma jikinsa yay sanyi ƙalau tunda yay sallama a cikin gidan, dan ya iske tashin hankalin baba kwance babu lafiya sosai, dan haka ya rikice, baiko zauna hutawa ba suka ɗakkoshi zuwa zaria asibiti...........✍🏻

*_CIGIYA!_*

_Ɗaliban makarantar ɗanzabuwa da suka ƙare a shekarar 2010 (Zolo) suna cigiyar dukkanin ƴan uwansu da suka kammala suma a wannan shekarar, amma fa ƴan *DAN ZABUWA* kawai, akwai taro da zai gudana ranar 11/3/2020 a cikin harabar makarantar *DAN ZABUWA*, karku bari abaku labari, shekara goma ba kwana goma baceba, gara dai kowa ya garzayo, muga wanda ya koma ƙato😂😝, da wanda yake siriri😉😝, bayan duk da ƙwailayene⛹🏻‍♀️⛹🏻‍♀️⛹🏻‍♀️⛹🏻‍♀️kar insha suburbuɗa._

+234 810 999 2578
*Duk wadda tasan ƴar 2010 ce ɗan-zabuwa saita ma waccan Number magana, ALLAH yasa a dace😃🤝🏻.*



*_NO 36_*


...........Tun da ga randa Amaan yazo gidan shan ruwa basu sake haɗuwa ba, ALLAH dai ya sota wajen da ya sa mata kunu bai tashiba, tunma a daren yabar zafi.
Yau tana makaranta Baba ya kirata, bayan sun gaisa yake cewa, “Ummukulsoom dama magana nakeson muyi”.
Nutsuwa ta kumayi sosai, murya a sanyaye dake nuna alamun a gajiye take tace, “To baba ina jinka”.
“Ummukulsoom baƙya ganin zuwa yanzu ya kamata ki fidda miji kiyi aure kuwa? Tunfa muna ɓoyema mutane akan zamanki babu aure wataran zata bayyana kowa ya sani, niko bana fatan hakan gaskiya, dan maƙiya zasu mana dariya”.
Idonta ne ya ciko da hawaye, amma ta daure ta haɗiyesu bata bari sun zuboba, ta gyara zamanta tana kuma raunana murya saboda ɗacin da takeji a maƙoshinta har zuciya, “Baba kayi haƙuri, insha ALLAHU zanyi, amma kaga watannine ya ragemin na gama shekara ɗayannan.......”
Katseta baba yayi da faɗin, “Nasani Ummukulsoom, dan Alhaji Mahmud yaymin bayanin komai, jiya mun daɗe tare dashi akan maganarki, shima kuma ya amince da maganar ki fidda mijin auren, idan san samune dakin kammala shekara ɗayannan sai a kaiki ɗakinki, munyi maganar da Hajiya yaya da Gwaggo hinde da babanki Alhaji Abubakar, kowa ya amince da hakan”.
Yanzu kam dai kasa riƙe hawayen tayi, suka ziraro bisa kumatunta masu ɗumi, muryarta na rawa tace, “Shikenan baba, insha ALLAHU zanyi ƙokari kodan na saka farin ciki”.
“Yauwa Ummukulsoom, ALLAH ya albarkaci rayuwarki kinji ko”.
“Amin ya rabbi baba, nagode”.
“To masha ALLAH, kukan ya isa haka kinji share hawayen, ALLAH ya baki miji na gari”.
Murmushi tayi tana share hakawayen, tanason babanta dan shima yana nuna mata ƙauna sosai.
Bayan sunyi sallama class ta koma, lecture ɗaya ta rage mata, dan haka ana kammalawa tai yunƙurin wuce wa gida jiki a matuƙar sanyaye, dan itakam batasan wazata nuna ba amatsayin abokin rayuwarta.
Umar yana sonta, itama kuma harga ALLAH bazata ce bai mataba, dan ya haɗu fiye da zaton mai hasashe, sai dai haka kawai batajinsa a zuciya a matsayin miji.
Zata iya auren yaya Zaid ma, amma sam batajin hakan a ranta, saboda tun fil azal bata ra'ayin yin auren zuminci saboda wani dalili nata.
“Abdul-Waheed” zuciyarta ta ayyana mata, nannauyan numfashi ta sauke, komai ya haɗa a yanda kowacce mace zatai fatan ya zam mijin urenta, sai dai bai bata damar sanin hallayyarsa ba, a yanda yake mu'amulantar ta kuma sam kamar ba son aure yake mataba, a ganinta kuma halayya itace abinda ma'aurata ya kamata su fara fahimta a rayuwar aurensu kafin maganar ƙyawun fuska ko wani ƙyale-ƙyale ya biyo baya, wannan kuskuren shiyya janyo mafi yawan rikicin aure a wannan zamanin, har ake gaza fahimtar ina aka dosane?..........
Wayarta dake ring ce ta dawo da ita hayyacinta, ta sauke numfashi tana ƙoƙarin lalubota a cikin bag. Bily ce, dan haka ta ɗaga tana faɗin, “Babie yaya dai?”.
Daga can Bily tace, “Komai dai-dai, cazan idan baki fito makaranta ba ki jirani nazo sai mu wuce kasuwar muyi gaba ɗaya mu hutu goben kawai”.
Cike da gajiya ta ce, “Kai Bily, wlhy kin cika matsala, ALLAH na gaji sosai”.
“Sorry Bestie, ALLAH ki daure kawai muje”.
“Shikenan, amma ke yanzu kina inane?”.
“Gani a taxi mana”.
Yanke wayar Ummu tayi kawai batare da ta ce komaiba, ta samu waje ta zauna zaman jiranta, yayinda maganar baba keci gaba da mata kaikawo a rai.
Ba tafi zaman minti talatinba saiga Bily ta iso, babu wani ɓata lokaci ta shiga suka tafi.

Suna cikin kasuwa har 5pm, ga garin yay masifar ɗaurewa da hadari, hakan saiya saka Ummukulsoom ruɗewa, gashi duk taxi ɗin da suka tare saisu ganta da mutane, Ummukulsoom tamkar zatayi kuka, batason ruwannan ya taɓata saboda kanta dake ciwo sosai, ita kanta Bily dukta damu.
Tafiya suka cigaba dayi a ƙafa suna kuma bincika abin hawan, ga maman Ahmad sai kiransu take, babu wanda ya samu damar ɗagawa, ita kuma acan Attahir nata mata masifa akan tana ganin hadarin miyasa ta barsu suka fita.
Yayyafin da aka farane ya saka Ummukulsoom ja ta tsaya idonta na cika da ƙwalla, Bily ta kalleta cike da damuwa, ga kaya riƙi-riƙi a hannunsu.
“Bestie ya kika tsaya kuma?”.
“Bily minene amfanin tafiyar tamu, tunda dai harma ruwan ya sakko gara kawai mu tsaya komu samu mafaka”.
“Ok to mu tsallaka ga wata rumfa can”. Cewar Bily tana kama hannun Ummukulsoom.

Zaune yake a bayan motar cikin Uniform, kayan sun masa ƙyau sosai, gaba ɗayan hankalinsa nakan lap-top da alama abu mai amfani ya keyi.
A ɗarare Osin yace, “Sir! Ga wasu da alama suna bukatar taimako”.
Shiru yay tamkar bazai tanka ba, harma sunɗan gota su Ummu dake ƙoƙarin tsallaka titi ya buɗe baki da ƙyar, “Ka tambayesu idan hanyarmu ɗaya”.
“Ok sir, thanks you”.
Bai sake cewa komaiba yaci gaba da abinda yake, Osin ya dawo baya gaban su Bily, kaɗan ya sauke glass ɗin gefensa yay musu nuni da su zo.
Babu wani batun jan aji Bily tace, “Ummu inaga ALLAH ya kawo mai taimakonmu, saura kuma kice bazamu shiga ba”.
Hararta kawai Ummu tayi suka nufi motar, Bily ce ta gane Osin, kamar shima da tana matsowa ya shaidata, yay murmushi yana musu nuni da su zagayo su shiga.
Ummu da batason shiga gaban mota saita tura Bily gaba ita kuma ta buɗe baya ta shiga, Osin na ƙoƙarin nuna mata ta dawo gaba itama amma sam bata luraba.
Sai da ta rufe motar hancinta ya shaƙo mata ƙamshin turarensa, dukda zuciyarta bata gaskata ba sai da gabanta ya faɗi.

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login