Showing 159001 words to 162000 words out of 176055 words

Chapter 54 - Wutsiyar Rakumi Book 1 Hausa Novel Complete

07 Jan 2025

865

A wajen cin abinci ma shine ya ciyar da ita suna zubama juna salon kallon soyayya mai kwantar da hankali.
Da zai wuce wajen aikima haka ta zuba masa doguwar addu'a makamanciyar ta jiya, ya tafi maƙale da ita a ransa, duk motsinsa saita faɗo masa a rai, daga bisani ma saiya kasa jurewa ya kirata a waya, lokacin maman Ahmad na gidan taje mata.
Duk da bawata maganar kirki yayiba taji daɗi sosai, koba komai taji muryarsa taji sanyi.

⚡⚡⚡⚡⚡⚡⚡⚡

Haka rayuwar gidan taci gaba da tafiya cike da farin ciki, randa bai soba ya miskile mata, da yake tasan halin kayanta sam bata damuwa, rashin yawan maganarsa kuwa bai dameta ba, idan tanason suyi doguwar hira saita masa magana ta chart koda gata gashine, anan ne zai saki jiki suyi doguwar hira mai ban mamaki da birgewa.
A haka suka kwashe sati huɗu da dawowa lagos, a kuma time ɗinne jarabawar su Ummu result ya fito.
Sun tsinci kansu cikin tsantsar farin ciki ganin komanta ta sameshi yanda tai fata, aranar kam har ƙyauta ta musamman ta samu ga Amaan da Attahir, hakama Ummi da Abba suka kirata suna jera mata Addu'a, Dad ma saida ya kira, saiga Bily da yaya Zaid, duk sai Ummu ta rasa inda zata saka kanta dan daɗi, gani take tafi kowa zama ƴar gata a duniya, Baba kuwa ai dogon lokaci suka ɗauka suna shan hira, hardasu baba yalwa sai da ta gaisa...........✍🏻

NO. 53 & 54


............Rayuwa kenan, mai tafiya da farin ciki daddd ƙalubale, wataran a tashi haƙora washe da murmushi, wataran kuma saɓanin hakance ke faruwa. To suma su Ummukulsoom hakance take faruwa daga garesu, a kwana a tashi babu wahala wajen ubangiji, yau gasu da shekara ɗaya da watanni biyu da aure, zuwa lokacin cikin bily da Aziza duk sun tsufa sosai, dan suma ba daga zuwa suka samuba, sai dai Ummukulsoom shiru kakeji babu wani motsi.
Abun naɗan cin ranta, sai dai bawai ya dameta sosai-sosai ba, dan Amaan ma ko a fuska bai taɓa nuna mata damuwa da rashin samun cikinta ba, lobewarsa yake hankali kwance.
Zuwa yanzu dai Ummukulsoom ta zama lauya cikakkiya, sai dai muce ALLAH yayi jagora a dukkan lamura kuma.

⚡⚡⚡⚡⚡⚡⚡

Tunda ta tashi yau da ciwon kai ta tashi, gashi Amaan baya gida, dan tunda ya samu ƙarin girma ya zama *Colonel* ɗinan busy ɗinsa ya sake yawa, a daddafe ta gyara gidan ta haɗa tea tasha sannan tai wanka ta sake kwanciya.
A wannan yanayin maman Ahmad tazo ta sameta, cikin riƙe haɓa tace, “wai kuwa Barrister anya bakiyi gamo ba kuwa? Wannan ciwo-ciwon naki fa yana bani mamaki, halan yauma bakije aikinba?”.
Zaune Ummu ta tashi tana danne ciwon, cikin murmushi tace, “Kai aunty nikam ke da yaa Amaan bansan wayafi samin idoba, nifa banda komai, yau kuma bana gaya miki ina hutu ba”.
“Oh aina manta, dama daga kd ne akace anata kiran wayarki kinƙi ɗagawa, shine nace bara naga ko lafiya? Dan Ummi ta damu matuƙa”.
Da sauri Ummukulsoom ta dafe kanta tana laluben wayarta, ita sam tama manta da wayar na'a silent ne, tasan har Amaan kansa ya kira yama gaji kenan....
Maman Ahmad ta katseta da faɗin “Al'bishirinki?”.
“Goro” Ummu ta amsa tana cigaba da laluben wayar.
“Bily ta haihu namiji, Aziza ma na asibiti”.
Babu shiri Ummu ta saki wayarta data ɗakko ta daka tsalen murna ta rungume Maman Ahmad, ta rikice da farinci ainun maman Ahmad na mata dariya, kafin kace mi ta shiga bige-bigen waya.
Maman Ahmad dai na zaune tana kallon ikon ALLAH.
Amaan kansa da ta kira ta sanarma ya tayasu murna, shima a ransa yana addu'ar ALLAH ya basu idan suna da rabo.
Tuni ciwon kan Ummu taji ya watsakke, ga hotunan baby sun cika mata waya, sai mamaki take wai bily ce ta haifi ƙaton yaronnan?, zuwa ƙarfe huɗu na yamma itama Aziza ta sunkuto nata babyn namiji, saiko murna ta daɗu.
Yau farin cikin da Ummu take ciki ko itace ta haihu iyaka kenan, ko da Amaan ya dawo bai samu kulawarta yanda ya kamata ba, rabin hirarta duk tana kan babys ɗinta, duk sai yaji ta bashi tausayi.

Suna kwance da daddare ta sake ƙadandanesa saboda sanyin da takeji, jikinta ma da ɗumin zazzaɓi, murya can ƙasa tace, “Zunnur! Amma dan ALLAH gobe ne zamu tafi kd ko?”.
Kansa ya girgiza mata ba tare da yace komaiba, ta narke masa da sakin kukan taɓara tana murje-murje a jikinsa, “Ni dai dan ALLAH ka barni na tafi, kagafa maman Ahmad ma gobe zata wuce”.
Ƙafarta da take tutturzawa ya danne da tasa yana kuma lumshe idanu, ganin zata kuma haɗa masa zafi ya matseta a jikinsa, murya ƙasa-ƙasa cikin kunne yace, “Haba Beauty ki bari mana kinfa hanani barci, banda abunki ke da baki da lafiya inake ina tafiya wani waje.....”
“Ni dai dan ALLAH na warke fa” tai maganar hawaye na tsiyayowa a idonta suka gangara ƙirjinsa.
Numfashi ya sauke kaɗan ya miƙa hannu ya kunna fitilar ɗakin, haskene ya gauraye ko ina, ya ɗago fuskarta da ƙyar yana sauke manyan idanunsa kan hawayenta, shagwaɓarta tayi yawa kwanakinnan, abu kaɗan saita farama mutane kuka, haka shekaranjiya akan wata shari'a da takeyi, bamafa an kadata bane, daga dai taso a yanke hukunci sai alƙalin ya ɗaga shari'ar sai kawai Ummu tazo masa tana kuka, jiya ma da zaiyi tafiya harda kuka, shi yarasa wannan kuka kukan na miyene?
Numfashi ya sauke a hankali yana maidata ƙirjinsa, murya a cinkushe yace, “Shikenan naji zakije, amma ba gobe ba, ki bari nanda kwana uku saimu tafi, nima aikin kusan sati uku zai kaini Abuja saimu dawo”.
Dukda bataso hakaba taji daɗi, dan koba komai zata halarci bikin wasu ƙannensu a ɗilau su uku da za'ayi, dama tanata tunani ta ina zata lallaɓasa ya barta taje, to ga hanya mai sauƙi ta samu.
Yanda ta ƙanƙamesan ya basa tabbacin ta amince, saiya dan murmusa tare da ɗago fuskarta ya haɗe bakinsu yana bata wata sumba mai kwantar da hankali da nuna tsantsar kulawa da soyayya a gareta.
Sakin jiki tayi itama tana bashi haɗinkai da ƙyaƙykyawan saƙo mai zurma masoyan da zuciyoyinsu suka gama aminta da juna hundred percent.

(Da baya-baya nima na fito dan sunfi ƙarfina walle😬😑🤭).


★★★★★

Kamar yanda Amaan ya alkawarta kwana uku suka shirya tafiya kd, Ummukulsoom na cike da tarin zumuɗi, bawai wannan ne farkon zuwanta ba bayan aurensu, a'a tajajje harma ɗilau kusan sau uku, biyu tare da Amaan ɗaya kuma biki sukaje har dasu bily ma da maman Ahmad.
Gidan Dad suka sauka kamar yanda suka saba a sashensu, sun sami tarba ta ƴan gata tamkar yanda Momcy ta shagwaɓasu yanzu, duk yanda Amaan yaso Ummu ta bari sai washe gari ya kaita gidan Abba idan zai wuce Abuja sam taƙi, tabi ta addaba masa da shagwaɓa, daga karshe dai dole ya hakura ya kaita a ranar taje taga babys dayake duk suna wajen Ummi hatta da Bily ɗin. Farin cikin da Ummukulsoom ke a ciki ɓata lokacine, Ummi dai itama sai kallonta take da murmushi, dan ta hango itama dai Ummu ɗin ta kamu, musamman yanda ta ƙara buɗewa da cikar ƙirji, ga fatarta tayi wani luff tamkar bata ganin rana, sai yawan Complain kanta na ciwo, bata son ƙamshin turaren wane, batason na wane.
Ummi taji daɗi sosai, fatanta ALLAH dai ya raba lafiya.
A ranar dai bai barta ta kwana a gidanba, dole ta bisa suka koma gidan Dad badan ranta yasoba, washe gari kuma ya kafa ya tsare sai da yamma da zai wuce Abuja ya sauketa anan gidan Abba ya wuce nasa uzuri shima.

Ranar kusan raba dare sukai hira ita da Aziza da Bily, maman Ahmad ma sai da Attahir ya kasa haƙuri ya biyota ya tasa ƙeyar kayarsa suka wuce, ita kanta Ummu da Amaan ya kirata yaji basuyi barciba faɗa ya kama mata, tayaya wai zata zauna surutun banza har tsawon wannan lokacin ita da bata da lafiya, ta inda yake shiga ba tanan yake fitaba, ita dai shiru tayi, daga ƙarshe ya maida kiran nasu bidiyo kol, saida yaga ta kwanta ta fara barci sannan ya yanke kiran.
Zuwa ranar suna ai Ummukulsoom ta gama yin tiɓis da ciwo. amma tsabar kar Amaan ya hanata zuwa ɗilau taita daurewa da jurewa, koda yazo kd ranar juma'a da yamma bayan suna da kwana ɗaya kenan daurewa tai taƙi bari ya fahimta, aranar kuma ya tarkatota daga gidan Abba suka dawo gidan Dad.

★★★★★

Haka taita dauriya har washe gari suka wuce ɗilau ita da shi. Osin ne ke jansu suna bayan mota, sai motoci biyu na yaransa, tun Ummukulsoom na dauriya harta gaza ta matso jikinsa ta lafe. Takardun hannunsa ya ajiye yana maida hankalinsa gareta, yanda ya tsira mata idanune ya tilasta ta lumshe nata tana kauda kai gefe.
Hannunsa ya ɗora a goshinta, tai saurin riƙewa tana narke masa fuska, shima yanda zafin ya ratsa masa hannu saiya ɗan lumshe ido ya buɗe a kanta, da ƙyar ya iya buɗe baki yana faɗin, “Kinata wani danne ciwo saboda kar a hanaki zuwa yawo ko?”.
“Nifa a'a” Ummu ta faɗa tana ɓata fuska.
Bai sake cewa komaiba ya maida idonsa ya lumshe hannunsa bisa goshinta, a haka suka isa Ɗilau har barci ya fara kwasarta.
Tunda motocin uku suka shigo yara ke binsu, duk majalisar da suka gitta zakiji ana ga Umma nan tazo, daga nan saikiga an dasa hirarta ita da mijinta.
A ƙofar gidansu motocin suka tsaya, Amaan ya tsirama fuskar Ummukulsoom idanu yana tunanin yanda zai tasheta, dan da alama barcin na mata daɗi, gashi matasan gidansu sun fito tarbarsa tamkar yanda suka saba, dan duk lokacin da yazo garin haka suke masa tamkar wani shugaban ƙasa.
Abbas da yasan dokar bai buɗe ƙofarba, shidai ya fito ya tsaya daga waje, hakama sauran sojojin dake a sauran motocin.
Amaan ya ɗan kalli agogon dake ɗaure a tsintsiyar hannunsa yana turo numfashi kaɗan ta hancinsa, dolene ya tasheta badan ya soba, bakinsa ya kai dai-dai kunnenta ya hura a hankali.
Buɗe ido tayi da ƙyar ta kallesa, harsun ƙara fitowa da canja launi,
“Sorry Beauty mun iso” Amaan ya faɗa akan laɓɓa. Badan tana kallon bakinsa ba bazata taɓa fahimtar miyake faɗaba, yunƙurawa tayi a hankali ta tashi zaune, ta gyara mayafinta da fuskarta sannan ta kai hannu zata buɗe sashen da take, saurin riƙota yayi yana zuba mata mayun idanunsa masu haske da cikar gashi, “5pm zamu wuce”.
Narke masa fuska tayi dayin rau-rau da idanu tamkar zatai kuka, “Wai yanzu da gaske bazaka barni na kwana ba Zunnur?”.
Kamar bazai tanka ba sai kuma ya nisa yana murza hannunta da sake haɗe fuska, “Kinsan dai banason gardama, ke baƙya tausayin kankine, yau zamu wuce kiga Doctor”.
“Ni dai lafiyata ƙalau, sai aita ɗoramin ciwo” ta ƙare maganar da cuno baki.
Yatsansa yasa ya ɗalli bakin yanda zataji zafi, sauri saka hannu tayi tako dafe bakin idonta na cika da kwalla.
Ɗauke kansa yayi daga gareta ya fara ƙokarin fita, cikin yaransa wani yay azamar buɗe ƙofar ya fice abinsa ba tare da yabi takan Ummukulsoom ba data cika tayi fam da haushinsa.
Ganin ya fita itama sai aka buɗe mata ƙofar, kunya sosai ta kamata ganin wajen cike da jama'a, sam batai tunanin hakaba, da tuni ta fito a motarnan, yanzu fa wani sai yamayi tunanin wani abun sukeyi....
Ta ɗan kalli sashen da Amaan ke gaisuwa da mutane ta janye ido, shaddar jikinsa tai masa ƙyau sosai, a koda yaushe ya saka manyan kaya saisu kara masa cikar haiba da kamala tare da wani girma na musamman, tuni itama su murja sun fito tarbarta, kowa sai farin cikin ganinta yake, dan sun san koba komai zata jiƙasu da abinda ALLAH ya hore mata.
A cikin gida mutane sai kallonta ake, kowa burinsa yay mata koda maganane ta kulasa, Ummukulsoom tariga da ta zama *Wutsiyar raƙumi* a cikin ƙauyen ɗilau da kewaye, yanzu haka shirye-shiryen kafa wata ƙungiya take a ƙauyen domin taimakon karatun ƙananan yara da matan aure. Abinda ke kara burge mutane da Ummu, sam bata da girman kai, gata da sakin fuska wa jama'a, bata nuna ƙyankyaminsu balle gudun abincin ƙauyen, idan tazo komai ci takeyi babu ruwanta.
Yanzu haka tana ajiye gyale da handbag catai a bata tuwon dawa.
Murja dake mata wani kallon sama da kasa suka kwashe da dariya ita da Hadiza da sa'ade.
Hararsu tayi cikin wasa, “malamai lafiya?”.
“A'a lafiya ƙalau, cika aikin soja muke kallo” cewar Azima da itama ke kwasar tata dariyar.
Sam Ummu bata fahimcesu ba, ta ƙwalama mariya kira da taga ta gitta da tire an ɗora ruwa da kwanon shan ruwa sabo fil (itama yanzu yaranta biyu).
Shigowa mariya tayi tana faɗin “Na'am aunty Umma, yi hakuri zanzo mu gaisa baba ne ya sani aiki”.
“Keni ba wannan ba, tuwon dawa nakeso miyar kuka ko kuɓewa ɗanya, asamo yajin daddawa da manshanu”.
“Naga ta kaina, Aunty Umma wannan lissafin fa? To bara nakaima yaya Amaan fura na dawo”.
“To maza, idanma babu manshanun a aika gidan Inna laraba nasan baza'a rasaba”.
Fita mariya tayi tana amsawa, yayinda su Hadiza suka dasa sabuwar dariya.
“Wai ɗan tuwon dawa muka samo kenan? Lallai soja baka da dama”.
Sai yanzu Ummukulsoom ta fahimci iskancin da suke mata, cikinta ta shafa tana yatsine fuska, “Oh kufa baku da man kai, wai dama iskancin da kukemin kenan? To kuma saita kanku ni banida komai”.
Nusaiba taimata gwalo tana faɗin, “Hakane kam baki da komai”.
Ganin basu yardaba ta sharesu, aka koma tsokanar Hassatu dake fama da tsohon ciki, Ummu na faɗin ya kamata ta huta hakanan haihuwa bakwai, ai sai jininta ya gama ƙarewa.
A haka Baba yalwa ta shigo ma Ummu da tuwon dawa sai tururi yake, “Umma ga tuwon, ga Ramatu can zata soya miki man shanun”.
“Lah baba na sakaku aiki, maimakon kubar mariya ko bilki suyi”.
Dariya Baba yalwa tayi tana faɗin, “Inani ina zama, nasani ko mijine, dan banason kishiya nima soja nakeso”.
Murmushi kawai Ummu tayi kunya na kamata, shin kodai wai cikinne da ita, kowa sai jifanta da wannan kalma yake, hakama a wajen sunan su Bily. Koda aka kawo manshanu saita miƙe ƙafafu taci tai nak abinta, sunata hira da ƴan uwanta da suka cika ɗakin, cakakin suruntunsu yasa har aka shafa fatihar ɗaurin auren basuji bama, zafi ya ishi Ummu ta mike tana faɗin waje zata tasha iska, dama zamanta yasa duk suka taru, dan haka kowa ya fito, saida ta wanke hannu sannan suka sake kafa dandakin sabuwar hira, kowa sai kallon Ummukulsoom yake, komai nata birgesu yakeyi, kallonta suke tamkar wata sabuwar halitta daban a cikinsu.

Shikam Amaan tunda aka ɗaura aure baba yasa aka kaisa can shagon dake soron wani maƙwafcinsu saboda sanin shi ba mutum bane mai son yawan hayaniya, wajen akwai sanyi kasancewar rufin kasane, kuma sabon gini sosai Amaan yaji daɗin hakan, yana ciki abinsa su Abbas na daga waje zagaye dashi, yara sai kallonsu suke daga nesa, hatta da manyan ma kwarjininsu ya cika idonsu, kowa dai yasan mu ƴan ƙauye da tsoron soja da ɗan-sanda😃🙊.
Sai da za'ai salla ne ya fito yay alwala a ƙofar gida, mafi yawan mutane gani suke Ummukulsoom tariga da tayi nisan da sai dai a hangeta daga nesa, mijinta abin sha'a da birgewar kowa, itama haka komai nata a cike da birgewar.

A cikin kananun maganganu na mata Ummukulsoom taji abinda ke faruwa na ɓatan Basiru daya janyowa iyayensa ciwo su duka saboda damuwar da suka tsinci kansu a ciki, da farko taso ta share zancen, amma kuma saita gaza hakan, saboda har gobe tana ƙaunar iyayen basiru, dan sam basuda laifi na komai a gareta, basu suka hana ɗansu ya aureta ba, hasalima suma sun shiga damuwa da rashin auren.
Murja taja gefe tana tambayarta mike faruwa ne?.
Murja ta sauke numfashi tana gyara tsaiwa, “Ai wlhy Umma abun babu daɗi, kinsan dai halin garinnan, idan abu yazo tun kanajin gaskiyar zance har kaji an canja labarin, kusan shekara biyu kenan babu basiru

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login