Showing 66001 words to 69000 words out of 176055 words
zuciya dayaji ainahin sunan garin da Ummukulsoom ta fito, ya daɗe yana maimaita sunan garin *ɗilau* a ransa, sai dai kuma ya haɗiye komai batareda yabar kowa ya fahimtaba.
Abinda yakuma saka Ummu sakin jikinta da gidan shine zuwan Maman Ahmad, dan Attahir ya kawosu gida har sai an koma yajin aiki, sai kuma ga Aziza da Inna harira sunzo gidan ganin Ummu, daɗi ya kama Ummu matuƙa, harda kukanta kuwa, yini sukai a gidan ranar, Ummi tace a bar Aziza ta kwana biyu.
Hakan yakuma sakama Ummu ƙaunar Ummi da ahalin gidan su Attahir gaba ɗaya.
Haka suke haɗuwa ɓangaren maman Ahmad susha hirarsu idan Ummi ta wuce wajen aiki, Abba dama bai cika zamaba saboda yanayin business ɗimsa, hakama Zaid aiki kan hanashi sukuni, Attahir kuma tunda sukazo yanata cuku-cukun amso takardun Ummukulsoom a Zaria, dan so suke itada Bily su wuce makaranta, itama shekararta ɗaya da kammala secondary, saidai result ɗinta baiyi ƙyauba saida ta gyara a wannan shekarar.
Yaa Amaan har gidan yazo ya gaida Ummi kamar yanda ya saba, dan shima yazo yin sallama gida akan tafiyarsu.
Har yazo yatafi ma Ummu na barci a ranar, saida ta tashine Maman Ahmad ke sanar mata da Bily, baki ta taɓe tai tamkarma bata jisuba, dan ita a halin yanzu baya gabanta.
⚡⚡⚡⚡⚡⚡⚡⚡⚡⚡⚡
Tunda Amaan yazo kd yake samun gata ga Momcy kamar yanda ta saba a duk lokacin da yazo garin, inda sukuma su Bassam suka shiga tsantsar takura hatta da Ameer, ko kaɗan babu mai ƙwaƙwƙwaran motsi na jin daɗi, sai rayuwar gidanma ta canja, ƴan aiki suka sami ƴancin kansu dan babu mai musu kallon banza hatta da Momcy.
Ko a fuska Dad bai nunama Yaa Amaan abinda yayba na sakin Ummukulsoom, baima bashi fuskar tado masa zancenba, abinka ga ɗan gado, shima saiya basar tamkar bai aikata komaiba, saima Momcy dake zungurarsa da zance, amma sam yaƙi biye mata, ko sau ɗaya yaƙi cewa komai game da zaman Ummu gidansa balle sakin nata.
Momcy tasan zaimayi abinda yafi haka, dan hallayar Fodio sai dai du'ai kawai.
Kwanansa goma a kd shida Attahir suka koma legos cikeda addu'ar ƴan uwansu da iyayensu.
Ranar saboda jin daɗin tafiyarsa su Aneesa har ƙaramin perty suka haɗa, dama ga Dad baya nan yana Ajiwa shida Ameer, shi kansa Fodio saida yaje, dan yana matuƙar ƙaunar garin sosai.
Momcy ce kawai taji kewar tafiyar ɗan nata mafi soyuwa a gareta, dan ranar yini tayi a gidan tamkar mai zazzaɓi.
⚡⚡⚡⚡⚡⚡⚡⚡⚡⚡⚡
Komai da ake buƙata na takardun Ummukulsoom Attahir bai tafiba saida ya kammalasu, yabarma Dad neman makarantar dasu Ummu ɗin zasu tafi.
*_BAYAN GAMA IDDAR UMMU_*
Rayuwa mai juyi da sauyi, akwana a tashi kuma baida wahala a wajen ubangiji, musamman a wannan zamanin da babu abinda yakai lokaci gudu da sauri, zuwa yanzu tabon dake cin zuciyar Ummukulsoom yafara dasashewa, a da kam kullum dare sai tayi kuka, ahankali tafara sabawa da sabuwar rayuwa tareda janye duk wani ƙududun mazaje biyu dake ranta tamkar rubutu bisa dutse.
Rayuwar Ummu agidansu Attahir abin birgewa, hankalinta saiya kuma zama waje ɗaya bayan ta gama idda taje gidan Inna Harira ta kwana biyu sun gana da babanta, nasiha yay mata mai ratsa jiki tareda ƙarfafa mata gwiwa akan burin Alhaji Mahmud na tayi karatu, dan shima da farko bai yardaba, saida Dad yay masa bayani na gamsuwa sannan ya fahimci lallai a yanzu karatu shine gatanta, dan haka ya amince hundred percent.
Ummukulsoom ta murmure sosai, jikinta ya fara dawowa, zuwa yanzu batada zumuɗin daya wuce su fara karatunsu, dan Islamiyyar data shiga inda Bily keyi saita kuma zaburar da ita amfanin ilimi, tareda jin ƙarfin gwiwar cikar burinta tunna farko tana ɗilau.
gaba ɗaya ta shafe babin Amaan balle wani Baseer a ranta, takuma dunƙule maza tamusu kuɗin goro a yanzu, Dad da mahaifinta da Abba sai ko Attahir ne kawai sukaciri tuta mai girma a ranta.
★★★★★★
Yau ta kasance asabar, shiyyasa kowa yana gida, maman Ahmad ma bata koma legas ba saboda makarantarsu basu koma yajin aiki ba har yanzun, su kansu su Ummu can ake jira su koma a samar musu, kasancewar Ummi batada ƴan aiki sai wata dattijuwa mai wanke-wanke kawai sai suka zage suka gyara ko ina tamkar yanda suka saba.
Bily dake Morping ta riƙe ƙugu tana faɗin wash ALLAH na, ALLAH bayana kamar zai cire”.
Baki Buɗe Ummukulsoom take kallonta, kafin tace, “Oni Ummu, wai Bily ke wace iriyar raguwace? Morping kawai kikema raki irin haka?”.
Hararan wasa Bily ta mata tana zama a hannun kujera, “ALLAH bazaki ganeba Kulsoom, kefa shaidace akan wahalar da muka shawo jiya a kasuwa”.
“Kai babie nan kina bani pepe wlhy, yanzu nan har ɗan yawon jiya yakai a kirashi wahala? ALLAH ya bama Yaya Zaid haƙuri dayayta yawo da kayan nauyi a hannu, kinga muyi sauri wlhy time ɗin islamiyya zai ƙure”.
“Kai nifa yauma kamar karmuje islamiyyar nan wlhy, dama Ummi ta yarda muje gidan su Aziza musha weekend ma........”
“Mu kuma kubarmu shiru a gidan dagani sai Hafsat ko? Anƙi wayon”.
Da sauri suka juyo jin maganar Ummi dake fitowa daga ɗakinta.
Dariya sukayi suna durƙusawa suka gaisheta, ta amsa cike da fara'a tana kallon yaran nata tamkar tagwaye, ita badan karta zula ƙaryaba da tace har kama tame gani Ummukulsoom nayi da Bily da maigidan.....
Bily ce ta katse tunanin Ummi da faɗin “Please Ummin mu, kingafa ga yaya Zaid ma yana gidafa, muma muɗan miƙe ƙafa muga gari dan ALLAH”.
“Bily duk daɗin bakinki ƙyayi ki barni, indama yinine sainace kuje, muma sai muyi tafiyarmu gidan Hajiya yaya”.
Da sauri Bily tace, “Mun yarda koma yini ɗinne ko Ummukulsoom ”.
Murmushi Ummu tayi tana gyaɗa kai alamar amsawa.
Ummi tayi dariya tana faɗin “Ok, saiku shirya Zaid ya kaiku, amma islamiyya fa? Bilkisu banason baƙin yawonki yasaki faramin wasa da karatun yarinya”.
“Kai Ummi ALLAH a'a, itamafa tanason zuwa”.
Cike da tsokana Ummu tace, “Nidai a'a banaso Ummi, muje islamiyyar mu kawa......”
Cikin wani tsalle Bily ta isa gaban Ummu tareda rufe mata baki da hannu alamar karta ƙarasa.
Dariya Ummi da Yaya Zaid dake shigowa suka sanya musu.
Yaya Zaid ya ƙarasa wajen cin abinci yana faɗin “ALLAH Ummi karki bari Bily ta koyama Ummukhoolsum baƙin yawonta da tamkar anmata ƙauri da ƙafafun kare”.
Baki bily ta turo gaba tana kallon Ummu, “Yanzu kin yarda ashiga tsakaninmu kenan?”.
Dariya Ummu da Ummi sukayi, Ummu tace, “Inafa zan yarda, ai ko saɓani haka ya ganmu ya barmu tawajena”.
“To aiko saidai kufita anguwar a Napep” cewar yaya zaid yana musu harar wasa.
Ummi dake ƙarawa inda yake tace, “A'a ba ayi hakaba Yaya Zaid, gwiwar autocina bisa ƙasa, sun tuba”.
“Ummi karki nemar musu alfarma, gara kibarsu su ɗana suji, dama ni inada gun zuwa”.
Ummukulsoom tai saurin cewa, “Yi haƙuri Yaya Zaid, karmuje a sake irin ta wancan karon muka ɓata”.
“Ai hakan shine dai-dai daku ma”.
Haka suka cigaba da hirarsu suna shirin yin breakfast har maman Ahmad ta shigo itama, da gudu Ahmad ya nufi Ummi kasan cewar kakar tasa na matuƙar sonsa.
Itama zama tai suka cigaba da breakfast ɗin har suka kammala Ummu da Bily suka gyara wajen, kafin kowa yanufi ɗaki ya shirya.
Ummi da maman Ahmad ne suka fara tafiya gidan hajiya yaya suka bar su Bily na jiran fitowar yaya zaid a harabar gidan.
Tunda ya fito idonsa nakan Ummukulsoom da tai ƙyau cikin sket da riga na shadda pink, sai dai kuma ta saka hijjab mai hannu, dukda babu kwalliya a fuskarta sai tayi ƙyau sosai.
Ɗauke kanta tayi dan batason yana mata wannan kalon, shima sai yay murmushi kawai yana musu nuni dasu shiga mota.
Da sauri Bily ta shige baya ta kulle, hararta Ummu tayi ta buɗe gaban ta shiga badan tasoba.
Ta mirror bily tai mata gwalo, dan tasan ta tsani zaman gaban mota dama.
Yaya Zaid na tafiya yana jan Ummu da hira, itako iyakarta murmushi, dama bata sakin jiki dashi inba taga Ummi a wajenba, har ƙofar gidan su Aziza ya kaisu, daɗi ya kama Aziza sosai da inna harira. Bayan Zaid ya shiga sun gaisa komawa yay ya barsu nan.........✍🏻
NO. 23
...........Yau kam sunsha shargallensu agidan inna harira, dama Aziza yaya lafiyar giwace itama, har dare suna gidan, baba yazo suka gaisa bayan sallar magrib.
Da zai tafi saita bisa soro dansu ɗan tattauna.
“Baba dan ALLAH ku amince naje Ɗilau, wlhy ina kewarsu sosai”.
Baba dake zaune a tabarma yay ƴar dariyarsu ta manya, “Ummukulsoom kenan, indai ɗilau ce zakije, kibari su Alhaji sugama shirin karatun naku, dan dama munyi dashi sai kin kammala iddarki, tunda dai yanzu kin kammala nasan da kansa zaimace kije ɗin”.
“Hakane baba, amma ya jikin Gwaggo hinde ɗin?”.
“A jikin Gwaggo kam Alhmdllhi wlhy, ta murmure dan talatar satin can data wuce mun haɗu da ita wai zataje tsinkar gyaɗa gonar babanki Ayuba, harma naita faɗa akan bai kamataba, amma sai tacemin itace tace zataje saboda likita yace take ɗan motsa jikinta”.
“ALLAH sarki gwaggo, to ALLAH ya ƙara musu lafiya, amma baba ai batasan aurena ya mutuba ko?”.
“Haba Ummukulsoom, ya za'ai a sanar mata da wannan maganar banda dai wautarki ta ƙuruciya, ai ba abune na daɗiba kinga, balle ita dake fama da jikin tsufa”.
“Hakane kuma baba, ALLAH yasa mudace”. ‘Ummu tai maganar cikin share hawaye’.
“A'a Ummukulsoom, nifa wannan kukan bana sonshi, idan akai haƙuri komai mai wucewane, saikiga yazama labari tamkar baima faruba, a rayuwa kowanne bawa da tasa ƙaddarar, ki ɗauka keɗin taki kenan, idanma kikaji ta wani saikiga ai ke takin ba komai baceba”.
“Hakane baba, insha ALLAHU zan kiyaye”.
“Yauwa ko kefa ƴar albarka, ni bara natashi naje, dan gobe idan munkai da rai asubanci zanyi”.
“To baba ALLAH ya tsare hanya, a gaishe mana da kowa”.
“Amin dai Ummukulsoom, duk zasuji ”.
Har baba yay musu sallama ya tafi Yaya Zaid bai ƙarasoba, sai wajen tara saura yazo, ko shiga gidan baiyiba, waya yayma Bily akan su fito waje.
Aziza ta rakosu har ƙofar gida, bayan su. gaisa da yaya Zaid suka ɗau hanya, itakuma ta koma gida abinta.
⚡⚡⚡⚡⚡⚡⚡⚡⚡⚡⚡
Lubna shiru zaune a falo ita kaɗai sai masu aikinta, ta zuba tagumi tana tunanin wai ina Baseer yake zuwane ne, a ƴan kwanakinnan takan rasa ina yake zuwa duk bayan kwana biyu, na farkoma saida yay kwana tara, ita dai a saninta sai kanada kishiyane kowa gidansa daban miji ke wannan asha ruwan tsuntsayen, itako ba kishiyace da itaba balle tace.....
Motsin da taɗanjine ya sata waigowa da sauri, shine sanye cikin ƙananun kaya tamkar yanda ya saba, cike da zumuɗi tai masa sannu da zuwa.
Amsawa yay tare da tambayarta jikinta da gida, tai murmushin yaƙe da amsa masa, hakan da yake mata yake sakata samun nutsuwa koda zuciyarta ta fara mata rawa a kansa.
Da kanta ta taimaka masa yay wanka dukda ƙaton cikin dake gabanta kuwa, bayan sun dawo falo suka baje suna ƴar hirarsu.
Kiran da ya shigo wayarsane ya saka Baseer saurin ɗaukar wayar ya danne ƙarar, Lubna ta ɗan tsura masa idanun tuhuma, “Babie ka ɗaga mana”.
Murmushin yake yay mata, “Lah karki damu Hafiz nefa”.
Murmushi tai tareda ɗauke kanta, shima haka, kusan minti biyu sai aka sake kira, nanma yay azamar danne ƙarar. miƙewa Lubna tai ta bar masa falon, dan ta lura bayason ɗaga wayar a gabanta.
Da yake baseer ɗan barikine na gasken gaske sai yama kashe wayar gaba ɗaya, Lubna dake laɓe taga kozaiyi wayar harta gaji da tsaiwa ta dawo falon suka cigaba da zamansu, da zaije masallacima a gida yabar wayar yanda zata kuma yarda dashi ɗari bisa ɗari.
Sosai kam hakan yay tasiri a zuciyar Lubna.
Shikam yana fita ya ciro ƙaramar wayarsa ya kira fannah, “Oh babie sorry kinata kirana wlhy barci yaɗan kwashenine, kinsan matafiyi”.
“ALLAH sarki babie na ya gajiyarka ya aikin?”.
“Alhmdllh babie na, sai daifa kewarki tareda kewar lallausan jikinki da ƙamshinki”.
“Karka damu, indai wan nanne nakane ai dear, bara na barka ka huta anjima mayi waya mijina abin alfaharina”.
“Ok amaryar ƙamshi ki huta lafiya kinji”.
“Insha ALLAH” Ta faɗa tana kissing wayar.
Murmushi yayi ransa fes, duniya sabuwa yake jinsa, yasan da Lubna ta fahimci yayi auren nan da sai anyi uwarwatsi, dan ya gama lura tafi Suhailat kishin masifa, shiko baya buƙatar rabuwa da Lubna a yanzu, dan yana amfanuwa da mahaifinta fiye dana Suhailat, zaitabin hanya mai ɓullewa da wani bazai taɓa fahimtar yayi aureba balle har wani a family ɗin Lubna ya sani.
★★★★★
Kwansa biyu a gidan Lubna ya ballaƙa mata karyar zuwa gaida iyayensa a kaduna, bata damuba, dan dama yana irin hakan, kuma tasan iyayensa acan suke, tunda itama kanta acan ɗin suka fara haɗuwa.
Yana barin nan sai gidan daya kamawa amaryarsa Fannah haya, wadda duka-duka auren nasu bai wuci sati ukuba kacal.
Yanda su Suhailat suka mutu akan son Baseer haka Fannah ma ta mutu, sosai take bashi kulawa da tattali, banbancinta dasu Lubna ita mahaifinta ba mai kuɗi bane sosai, amma gwargwado sunada rufin asiri, ƙarfin soyayyarta a zuciyar Baseer kam sha'awa ce, dan Fannah mace ce har mace, akwai diri ɗan gaske dako wanne irin namiji zaiso samun matarsa haka, ga uwa uba ƙyaƙyƙyawace jinin shuwa ɗan asali.
Tarba tai masa ta musamman, kasancewar tunda sukai aure wannan ne karo na biyu dayay tafiyar kwana huɗu, iyakacinsa kwana dayane a matsayin aikin Office, nanko gidan Lubna yake zagayawa itama yaɗan kare yawa.
Haka rayuwar tasu taci gaba da tafiya batareda sun fahimci wa suka auraba, garama Fannah idan taga abinda bai mataba takan tanka, wataranma har suyi faɗa da baseer ɗin, daga baya kuma yadawo su shirya.
A haka har ALLAH ya sauki Lubna lafiya ta haifi ƴarta mace ƙyaƙyƙyawa mai tsananin kama da baseer, sosai yay farin ciki da wannan babie, sai dai abinda zai baka takaici babu ko mutum ɗaya daga dangimsa na jini, sai iyayensa na bogi dayay amfani dasu wajen aurensa, sukansu su Inna sai a hoto sukaga ƴar, amma hakan bai hanasu saka mata albarkaba da addu'a, dansu har yanzu bama susan ba Suhailat bace uwar ƴar, a tunaninsu har yanzu itace matar tasa, lamarin baseer yabar ɓata musu rai, sun zubamasa idone kawai.
⚡⚡⚡⚡⚡⚡⚡⚡⚡⚡⚡
Ummukulsoom ce farkon fita a motar, tai gaba tabarsu, shi Zaid ma dariya ta bashi, yasan duk dan karsu kasance su biyune take wannan abun.
A falo ta iske su Ummi da suma basu wani jima da dawowar ba, Ahmad yazo yana mata oyoyo ta ɗaukesa tana shillawa.
“Ku yanzu dama haka ake yini?”. Cewar maman Ahmad.
Dariya Ummu tayi itama tana zama gefenta, “Kai aunty, kuma da alama fa yanzune kuka dawo, muma dan yaya Zaid baije da wuri baneba, Ummi fa?”.
“Ummi tanada baƙo, suna falon Abba”.
Kafin Ummu tayi magana su Bily ma suka shigo. Yaya Zaid dake kallon Ummukulsoom yace, “Hajiya bamu ɓataba, muma man gane hanya”.
Murmushi kawai