Showing 90001 words to 93000 words out of 176055 words
ƙuruciya na ɗawainiya da ita, dan bata taɓa kawo komai gameda zamanta gidanba, hakama sometimes mutane kance tana kama da Bily, amma bata taɓa gasgata zancenba saboda ita bata ganin kamannin.
“ALLAH yay maka albarka Abubakar, ba abun kunya yasani ɓoye maka komaiba, bin Umarnin mahaifinane, inason garinmu, inason zuwa cikinsa, inason ahalina dake cikinsa, sai dai wani furuci yay min hijjabi da tsintar kaina a cikinsa”.
“Sunana Ummukulsoom na yanka”.
Gaba ɗayansu suka kalli hajaiya yaya da mamaki.
Murmushi tai musu tareda jinjina kanta, “Ƙwarai da gaske sunana kenan Ummukulsoom, Mu uku mahaifinmu ya haifa a duniya wato malam Ado ba rinji”.
Da sauri Ummukulsoom ta kalli hajiya yaya jin sunan wanda ta ambata.
Nanma murmushi Hajiya yaya taima Ummukulsoom ɗin, sannan ta cigaba da faɗin, “Ni ce babba a gidanmu, sai ƙanwata Hindatu, sai autanmu Lirwanu. Muna samun gata a wajen mahaifinmu dan mahaifiyarmu tun a wajen haihuwar Lurwanu ALLAH yay mata rasuwa, kulawar da mahaifinmu ke manace ya saka iyami tsanarmu, wato matar babanmu, a haka muka rayuwa cikin wata bahaguwar rayuwa a hannun Iyami, a wajen baba kawai muke samun sauƙi. Shekarata 12 baba yay shirin aurar dani, dan haka ya bada sadaka ta ga Ɗan-asabe, anyi baikonmu da ɗan-asabe duk da ba sonsa nakeba, amma biyayya ta saka ban musaba. Bayan baikon mu da sati guda na tafi kiwon dabbobi daji ni da Hindatu kamar yanda muka saba a kowacce damuna, dan anayin ɗaurene, zalincin iyami yasa da ta sai ciyawa gwamma ta sanu kwance dabbobin mu tafi kiwonsu daga safiya har yammaci, randa mukayi gigin dawowa da wuri ta lakaɗa mana duka tace cikin dabbobinta bai ƙoshiba, idan kuma lokacin rani ne bata sakinsu, saidai muje daji muyo musu abinci, hakan ba komai bane face salon ƙuntata mana. A wannan ranar da muma fitane muna tsaka da kiwo sai maciji ya sareni, take a wajen na zube, dan haka hankalin hindatu ya tashi ainun, tashiga kuka da kururuwar neman taimakon wani. Ana haka ALLAH ya kawoshi cikin mota”.
“Hajiya yaya wake nan?”. Cewar Attahir.
Murmushi hajiya yaya tayi tana gyara zama, “Attahiru mi kakeci na baka na zuba, ai yanzu zaka sanshi. Ba kowa bane face kakan ku, shine ya taimakeni bai saurari komaiba ya ɗaukeni yasa a mota tare da Hindatu ya nufi Zaria da mu. Ni bamma taɓa zuwa zaria ba sai ranar, ALLAH ya taimaka dafin macijin mai sauƙine, sai aka samu kaina cikin amincin ALLAH, amma dai an kwantar dani a asibitin. Shine ya koma da Hindatu Ɗilau suka sanar da halin da nake a ciki, hankalin baba ya tashi matuƙa, yay ta sakama kakan ku albarka tare da godiya. Amma Iyami gareta ba hakan baneba, ita masifa ma take ina dabbobinta? Sai a sannan kakanku ma yasan abinda yakaimu jeji har wannan lamari ya faru. Gidan maigari baba yakai cigiyar dabbobinta, kaifin yabiyo kakanku su dawo Zaria wajena. Indai taƙaice muku zance shine yayta ɗawainiya da hidimar asibitinmu harna warke, sai dai kuma Ubangiji mai hikimane, dan kuwa shiyya saƙa soyayya mai ƙarfi tsakanina dashi a wannan jiyya, bayan warkewata muka dawo ɗilau, sai ya zamana duk sati saiyazo ɗilau. Hakanne ya tashi hankalin Iyami, dan kuwa ta ɗau alwashin waninmu bazai taɓa samun cigaba ba, yanda bata haihuba a gidan mu da aka haifa sai dai muƙare rayuwarmu a wahala. Ita ta fara fargar da baba wai soyayya nake da Ibrahim. Hankalin baba saiya tashi saboda yana ganin yarigada ya badani, janye waccan maganar kuma tamkar zubar da kimarsa ne, sannan hana Ibrahim ni tamkar butulcine, sai yay yunƙurin datse alaƙar da hanzari, amma kuma sai hakan bata faruba, dan kuwa yana tunkarata danson jin gaskiyar zance na sanya kuka akan nifa lallai Ibrahim nake so, dama kuma banason Ɗan-asabe kowa ma yasan hakan. Da farko Baba kam lallaɓani ya farayi, ganin naƙi saurarensa saiya canja salo saboda zugashin da Iyami keyi. tun anayin abu iya gidanmu harya fito ya fara yawo a garin ɗilau, kowa ya samu abin faɗa. Hakan ya kuma birkita baba ya gaza fahimtar ba laifina bane, zuciyata ce, yagaza fahimtar sheɗancin Iyami. Ibrahim shima yana matuƙar sona sosai, dan kullum cikin zuwa roƙon baba yake amma baba ya baɗe idonsa da toka yaƙi saurarensa. A wani dare sai hindatu ta tadani na rakata banɗaki amma sam naƙi, nace in bazatajeba sai dai tayisa a wando. Ƙyaleni tayi ta fice dukda tanajin tsoro, batafi mintuna uku ba sai gata tadawo, “Yaya, yaya tashi kiga mi Iyami keyi”.
“Tashi nai zaune da sauri, nace, “Mi Iyamin keyi?”.
“Ke dai taso ki gani Yaya, dan bayanina bazai gamsar da keba”.
“Ban musaba na tashi na bita, ta can bayan ban ɗakinmu inda Rumbu yake muka iske iyami tana haƙa rami, laɓewa mukayi ta gama tsaf ta saka wasu layu a ramin, sai da tagama harda yayyafa ruwa ta maida ƙasa ta rufe kafin ta miƙe tana ƴar dariya, “Umma ɗan-asaben ma basamun damar aura zakiyiba balle wani Ibrahim ɗan birni, kamar yanda malam ya sanarmin layunnan na cika kwana goma a ƙasa Ibrahim zaiyi iskanci dake, na tabbata hakan ne zaisa kowa ya tsaneki a ƙauyennan idan kikayi cikin shege, mahaifinki ya tsine miki ya koreki, na gama da babinki, saura Hindatu itama”.
Gaba ɗayanmu mun tsorata da kalamanta, danni harma na fara hawaye, da ƙyar muka ɗauke numfashi yayinda zata wucemu, a ranar bamuyi barcin sauran darenba daya rage. Washe gari tunda safe muka nufi gidan ƙanwar mahaifiyarmu muka sanar mata abinda mukaji, itama hankalinta ya tashi, dan haka tace mu turo mata Ibrahim idan yazo. Dato muka amsa, cikin amincin ALLAH kuwa washe gari saiga Ibrahim, dayake a lokacin a ɓoye muke haɗuwa, shine na sanar masa da zancen Innarmu. Bai musaba mukaje wajenta. Bayan sunyi gaisuwar mutunci tace, “Bawan ALLAH da gaske kake son ƴata kuwa?”.
Cike da ladabi Ibrahim yace, “Wlhy Ina sonta Inna, kuma a shirye nake na aureta ko a yanzunnan ne”.
“To Alhmdllhi, yanzu inaso ka ɗauki Umma kuje garin ɗan-gamau a katsina, idan kunje garin kuyi tambayar gidan Malam Baushi, kuyi masa bayanin komai daya faru, kuce masa nace ya ɗaura muku aure, Ibrahim ga amanar Umma nan, idan kaci ALLAH ya ci taka, karku zo Ɗilau saita haihu”.
Godiya mukai mata muduka muna kukan jin daɗi, a ranar muka tafi babu wanda yasani har Hindatu, duk yanda Inna tace muyi haka kuwa mukayi, Malam Baushi ya ɗaura mana aure, satinmu ɗaya a can Ibrahim ya ɗaukeni muka wuce legas wajen aikinsa, ban fuskanci matsala a wajen danginsa ba danshi marayane. Ban sake waiwayen garin ɗilau ba, dukda kuwa ina matuƙar kewarsu, sai da na shekara biyar, dan har lokacin ban haihu ba, saida na shekara biyar da wasu watanni nasamu cikin Abubakar, bayan haihuwarsa naso zuwa Ɗilau domin cika alƙawarin inna amma sai wani aiki ya riƙe Ibrahim, dan haka ya bani haƙuri, dan shi burinsa muje tare mu nemi gafarar baba, zamu-zamu tafiya bata yuwuba har na yaye Abubakar, kwatsam kuma saiga wani cikin, ganin haka sai Ibrahim ya lallabani akan nai haƙuri na haihu saimu tafi, ƙilama Baba yafi karɓarmu. Hakance ta faru kuwa, dan saida na haihu tagwaye duk mata sannan muka shirya zuwa ɗilau. Komai ya canja mini daga yanda na sanshi, abubuwa da yawa kuma sun faru, dan ansha tashin hankali bayan nemana da akai aka rasa, a maimakona sai aka ɗaurama Hindatu Aure da ɗan-asabe, baba kuma yace ya barma duniyani, har abada ya cureni cikin ƴaƴansa. Har zuwanmu ɗilau baba na akan bakansa na ƙin karɓata, dankuwa muna fita a mota bai bari nataka koda zauren gidanmu ba yace mu juya, tareda furucin inhar na sake dawowa garin ɗilau ALLAH ya isa bai yafemin ba.
Hajiya Yaya ta fashe da kuka mai tsuma rai, wanda yasaka su Ummukulsoom da Attahir harma da Abba kuka suma, da ƙyar Hajiya yaya ta tsagaita taci gaba da faɗin, “Bansan yanda zan fassara muku halin dana shigaba dagani har ibrahim, da ƙyar nasamu wani ya faɗamin inda Hindatu take aure, Lurwanu kuwa na iske ya rasu sanadin zazzaɓi da yayi. Naje gidan Hindatu, muka rungume juna muna kuka, na isketa har tayi haihuwa Uku ita, ƴar da take goyo ma tsakanin haihuwarta da ƴan biyuna kwana ukune, na amshi ƴar saina ganta a langaɓe, hankali tashe na kalli Hindatu da itama take kallona tana kuka.
“Hindatu miya sametane?”..
“Yaya ta rasune yanzunnan, ina kukan mutuwartane ma kika shigo”.
Sosai hankalina ya tashi nima, na rungume yarinyar a jikina ina hawaye, muna cikin haka saiga ɗan aike daga baba, yace inhar ban zo nabar garinnanba yazo gidan hindatu ya iskeni saiya min abinda ban taɓa tunaniba, kuka na kuma fashewa dashi, na kalli hindatu da itama kukan takeyi.
“Hindatu dan ALLAH kimin wani taimako kafin nabar garinnan”.
“Inajinki yaya ki faɗi komiye zan miki”.
“Hindatu ba kowa yasan ƴarki ta rasuba, dan ALLAH ki bani gawarta, nikuma na baki guda ɗaya cikin ƴan biyu, inason ɗaya a cikinsu ta tashi a garin haihuwata, tunda ni an haramtamin koda zuwa cikinsa, dan ALLAH hindatu ki taimakeni, nasan har abada ba sake haɗuwa zamuyiba”.
Fashewa tayi da sabon kuka tareda ƙankameni, tace, “Yaya mizai hanani aminta da shawararki, wlhy na yarda, ke kaɗai gareni kaf duniya, gashi kuma ƙaddara ta daɗe da shiga tsakaninmu, mizai sa bazan ji daɗiba idan har kika bar jininki a wajena amatsayin ƴar dana haifa”.
Nace Na gode hindatu, sauri sauri muka cire kayan jikin Hassana muka maida jikin gawar Ɗahara, na ɗahara muka sakama Hassana, inaji ina gani nataho na baro ƴata hannun ƴar uwata, ko mahaifinta bai saniba, dan baba tozarci bana wasaba ya shigo har gidan Hindatu yanamin dagani har Ibrahim dake mota yana jirana shida Abubakar dake ya yayye. Saida mukazo gida nace masa Hassana ta rasu a madadin gawar Ɗahara ɗiyar Hindatu, damuwar da muke cikice ta kauda damuwar rasuwar Hassana a zuciyarsa, niko inata kewar ɗiyata tunda nasan bata rasuba. Tun daga wannan ranar ban kuma waiwayar ɗilauba, tunma ina kuka harna haƙura, naci gaba da rainon Husaina, bayan shekara biyu Husaina ta rasu saboda ƙyanda da tayi, daga nana Abubakar kaɗai ya rage mana a gabanmu, a legas muka cigaba da rayuwa har Abubakar yakai minzalin aure sannan muka dawo kd, koda muka dawo ban taɓa waiwayen ɗilauba, saboda katangar da Baba yaymin da ita, Har ALLAH yayma Ibrahim rasuwa bayan haihuwar Attahir kuma yanata burin hakan, amma ALLAH yay alƙawarin bazai sake taka ƙasar canba shiyyasa harya rasu bai cika alƙawarinsa na dai-daitani da Baba ba. Wannan shine labarina, inaji a jikina kuma lallai Ummukulsoom tanada alaƙa da ahalina, amma tambayoyin dazan matane kawai zasu bani wannan tabbacin.
Jikin Hajiya Ummukulsoom ta faɗa ta fashe da kuka, “Hajiya wlhy basai kin tambayeni komaiba, ni ɗin jininki ce, dan kaf sunayen waɗanda kika ambata sun tabbatar min da hakan, Gwaggo hinde kakata ce, itace ta haifi mahaifita Ɗahara......”
Ɗagota da sauri Hajiya yaya tayi, jikinta har rawa yake tace, “Da gaske kike ƴarnan?”.
“Wlhy hajiya na tabbatar da hakane kuwa”.
Fashewa da kuka Hajiya yaya tayi yanzu kam mai ban mamaki da yafi na ko yaushe, tabbas inhar maganar Ummukulsoom gaskiyane to itaɗin jinin ƴartace Hassana data bama Hindatu.
Zaid da Bily dake maƙale a ƙofa suna kuka suma suka kalli juna, cikin kasa-ƙasa da murya maman Ahmad tace, “Ba kallon juna zamu zaunaba, hanyar ɗilau yakamata mu dosa ɗakko Gwaggo hinde”.
“Maganarki gaskiyane Aunty Hafsat, kumuje kawai, insha ALLAHU daga nan zuwa bayan isha'i na tabbata zamu dawo”.
A tare suka ɗaga kai tareda juyawa suka fita da hanzari.
A ɗaki kuwa numfashin Hajiya yaya ne yafara gagarar ƙirjinta, hakane yasaka Abba da Attahir rikicewa, dan tabbas ciwontane ke barazanar tashi.
Ummukulsoom da batasan komaiba akai tai masifar kuma rikicewa, sai girgiza hajiya yaya take tana kiran sunanta.
“Attahir maza kira Ummin ku tazo da gaggawa”.
A rikice Attahir ya amsa da to, tare da zaro wayarsa daga aljihu............✍🏻
GASKIYA HASKE CE. AKASINTA DUHU NE
NO. 32
*PARIS*
.........Yanda yake kwara rar da uwar zufa ga mutsu-mutsu da ya keta zubawa cikin barci ya bama Meenal mamaki, ta girgiza ƙafarsa yafi sau goma amma bai farkaba, ruwan dake a ajiye a durowar gefen gadon ta ɗauka ta ɗansa a hannu ta yarfa masa akan fuska.
A matuƙar firgice ya farka yana faɗin, “Suhailat! Suhailat!!”. Tare da rarumo Meenal zai riƙe.
Duk da ta lura ba a hayyacinsa yakeba saita fusge hannunta.
Baseer da bai gama dawowa hayyacinsa ba yacigaba da sambatu, “Suhailat dama kece kika saka Meenal ta aureni? Suhai.........”
Ƙara Meenal ta ƙwala da ƙarfi a saitin kunnensa, hakan yasashi dawowa hayyacinsa sosai, ya waiga yana kallon ɗakin tareda Meenal dake zabga masa harara, ta kumbura tayi fam da kishi, a hasale tace, “Munafuki, ALLAH ya toni asirinka, wacece kuma Suhailat?!”.
Innalillahi wa'inna ilairirraji'un ya shiga mai maitawa a zuciyarsa, domin dai ya fahimci mafarki yayi ashe, jin Meenal ta fashe da kuka yay azamar dirowa daga gadon yay kanta jikinsa na ɓari, “Please Meenal wlhy mafarki nayi, dan ALLAH ki tsaya ki fahimceni....”
“Anki a fahimcekan, Baseer ni zaka yaudara? Dama akwai wata mace a ranka amma kacemin baka taɓa son wata mace ba saini?.....”
“Wlhy gaskiyane Meenal, dan ALLAH ki saurareni na miki bayani, a tsawon shekara biyar da mukayi da ke kin taɓa jin na ambaci sunan wata mace idan ba yauba? Kin taɓa kamani da wata mace koda a cikin waya ne? Haba Meenal”.
Shiru tai tana kallonsa, dan kuwa maganarsa gaskiyace, tunda sukai aure suke zaune a Paris bata taɓa kamashi da hakanba, dukkan soyayyarsa da kulawarsa akanta yake nunata, ta sauke numfashi tana mai zuwa da ɗan gudu ta shige jikinsa.
Nannauyar ajiyar zuciya ya sauke yana ambaton Alhmdllh. Sai dai dukkan jikinsa a sanyaye yake, wannan mafarkin yay masifar tada hankalinsa gaskiya.......
Meenal ta katse masa tunani da ɗagowa daga jikinsa tana faɗin, “Ammafa wannan ko wacce shegiyar Suhailat ce da tazo maka a mafarki na tsaneta, nifa koda macen ƙuda bana fatan ta raɓeka balle har asamu shegiyar da zata ziyarceka a mafarki”.
Murmushi kawai yayi yana haɗiye tashin hankalinsa, “Ai wannanma ba da arziki tazo minba a mafarkin Dear, dan haka karma wannan ya dameki”.
“Shikenan My boo..., dama fa mun kusa makara, kai maza ka shirya, kasan dai jirginmu 4:30pm zai tashi zuwa 9ja”.
Kai kawai ya iya ɗaga mata tareda nufar bayi.
Ko a cikin ban ɗakinma ruwa kawai ya sakarma kansa, ya tsaya yana zuba a jikinsa, yayinda zuciyarsa ta kuma lulawa tunano mafarkinsa.
Miyasa tunda yabaro Nigeria bai taɓa irin wannan mafarkinba sai yau? Mafarkin fa ya nuna masa Meenal haɗa baki sukai da Suhailat ta auresa, ya rumtse ido da sauri zuciyarsa na tsitstsinkewa, sai kuma maimaita sunan Suhailat yake, shikam dai da ya na da dama da komawa Nigeria ɗinnan da ba'ayi dashiba, duk da yana kewar Innarsa da baba da yayarsa Talatuwa, tsawon shekara biyar kenan tunda sukai aure da Meenal sukazo bai taɓa waiwayar gidaba, koda sha'awa ma baya son zuwansa, yanzun ma zaɓen da akaine mahaifin Meenal yasamu kujerar gwamna shine za'a rantsar dasu zasuje, amma shida Meenal ko wajen zaɓen basujeba, Abban Meenal ya hanasu, a cewarsa yana gudun rikici, bama su kaɗaiba dukkan sauran ƴan Uwan Meenal din dake anan basu jeba.
Knocking ɗin da tai masane yasashi katse tunaninsa yay sauri yay wanka ya fito, sauri-sauri ta taimaka masa ya shirya, dan Maman Meenal nata musu waya akan sufa ake jira.
Sai da suka kashe komai na kayan wutar gidan kafin su fice zuciyar Meenal fari ƙal, saɓanin ta Baseer dake a dagule da mafarkin da yay, kai tsaye airport suka nufa, inda dukkan ahalin Meenal suke jiransu suma.
Bayan ƴan gaishe-gaishe aka fara shirin tafiyarsu, sune sunayen farko da aka fara kira, dan haka sune suka fara shiga waje na musamman.
Gaba ɗaya zuciyar baseer ta kasa sukuni, duk hirar da akeyi ya kasa saka baki, harma yayan meenal ɗin ya fahimta yafara tambayarsa ko bai da lafiya ne?.
Murmushin yaƙe yayi, yana gyara zamansa, “Lafiya ta ƙalau Bro.. Haneef, kawai dai barcine bai isheniba”.
ƴar dariya Haneef yayi yana masa jin jina......
A filin jirgin lagos suka sauka, daga can suka hau jirgi mai zuwa Katsina kai tsaye.
Wannan shine karon farko da Baseer zaije gidansu Meenal na Nigeria, motoci na alfarma ne sukazo kwasarsu, Baseer sai wani faɗi ake ana buɗawa shi mijin ƴar gwamna🤣.
Ƙayataccen gidane wanda ya amsa sunansa