Showing 141001 words to 144000 words out of 176055 words
ɗanyi taga shima ita yake kallo, tai azamar janye idanunta zuwa wani wajen.
Kaɗan ya sauke numfashi yana tasowa shima, hannunta ya kama ya kaita saman gadon ya zaunar, kafin ya kama kafaɗunta gaba ɗaya ya kwantar da ita.
Ita dai kallonsa take kawai ta kasan ido duk sai kuma jikinta yaɗanyi sanyi, bai sake cewa komaiba ya fara mata addu'ar barci, sai da ya kammala tsaf ya tofa mata tare da jan bargo yaɗan lulluɓa mata zuwa ƙirji, ya zame mata hijjabin jikinta. Duk yanda taso hanashi sai ta kasa hakan, dan wani kwarjini taga ya mata fiye da zatonta, shi kansa wani girma ta ƙara a idonsa da mutunci, baiyi zaton tanada sauƙin kai irin haka ba, dan harga ALLAH ya ɗauka yau bazama ta barsu su rintsa ba saboda tanadin rashin mutuncin datai masa. ya kuma yarda duk ɗan gaske baya yarda tarbiyyar gidansu da mutuntakar musulinci. Kansa ya duƙo ya bata sunba akan laɓɓanta daketa motsi alamar sonyin magana amma ta kasa, ya sumbaci goshinta sannan yayo ƙasa inda bata taɓa zatoba nanma ya sumbata.
Sosai ta waro idanu waje saboda matuƙar mamakinsa, ya sakar mata lallausan murmushin daya kusa sumar da ita a wajen. Ai babu shiri taja bargon ta rufe har fuskarta tana juya masa baya.
Miƙewa yay yana cigaba da murmushinsa, ya zagaya ta can ɗayan gefen ya kwanta yana tunanin yanda zai iya kwanciya bashi kaɗaiba a ɗakin, ya riga da ya saba da kwanciyarsa shi kaɗai babu motsin kowa, harga ALLAH jinsa yake duk a takure, to amma ya zaiyi, yana buƙatar matarsa kusa dashi fiye da komai a halin yanzun.
Harya kammala addu'arsa ya gyara kwanciya Ummu bata sake motsawa ba, addu'a dai take a ranta ALLAH yasa ba a ɗakin zai kwana ba, sai dai jin ya kwanta bayanta tasan addu'arta bata karɓu ba kenan.
Abinda ya sata samun nutsuwa dashi sam bashi da wani rawar kai irinna angunan wannan zamanin da suke nuna kamar jikin macen ne mafi kwaɗaituwa a garesu, banda wannan sunbatar tata da yay a ƙirji yanzu bai taɓa kai hannunsa wani sashe na jikinta ba koda wasa, tasan kuma bawai dan baya buƙatar baneba, kawai dai shi komai nasa na nutsuwa ne da dattako.
Tun tana fargabar ko zai far mata har taji ya fara sauke numfashi a hankali alamun barci yama fara tafiya da shi kenan.
Itama dama barcin takeji, tsabar tsorone ya hanata yi, gashi dare yaja kusan 2:15am na dare, cikin ɗar-ɗar dai itama barcin yay gaba da ita.
⚡⚡⚡⚡⚡⚡⚡⚡⚡⚡⚡
Da asuba shine ya fara farkawa, ya buɗe idanunsa a hankali ya sauke akan fuskar Ummukulsoom data juyo tana fuskantarsa yanzu ba tare data saniba, sai dai tana a inda take alamun batada mirgine-mirgine wajen barci.
Fuskarta tayi fayau tamkar tana murmushi, ƙyaƙykyawace mai yawan kwarjini da cikar haiba, komai nata yana da ɗaukar hankali musamman murjajjen jikinta da sam babu rama a tare da ita, luuu yay da idanu ya kuma buɗewa a kanta tare da kai hannunsa ya shafi laɓɓanta da babban ɗan yatsansa.
Yanda ya keyinne ya saka Ummukulsoom kawo hannu cikin barci ta riƙe nasa tare da rungume hannun a ƙirjinta tana gyara kwanciya.
Idanu ya tsura mata yanajin fitar murmushi a ƙasan zuciyarsa, sai dai sam babu akan fuskarsa, bai janye hannun nasa ba kamar yanda bai iya janye idanunsa da suka ƙara girma saboda barci daga kanta ba.
Kuma motsawa tayi sai taji ƙamshin turarensa ya yawaita a hancinta, hakan ya tilasta ta buɗe idanunta dake cike da barci dan ta manta a inda take gaba ɗaya.
Idanun Ummukulsoom kan bada wani yanayi na musamman a lokacin data tashi a barci, cikinsu yaɗanyi jaa su kumburo daga waje, ta buɗesu da ƙyar a kansa saita jasu suka koma tamkar zata lumshe ta sake buɗewa da azama ganin namiji a kusa da ita sabanin Bily da tasaba gani.
Tuni Amaan yayi doguwar shiɗewa akan wannan salo na Ummu da sam ba yanga bace ko ɗaukar hankali.
Saurin ture hannunsa tayi ta juya bayanta tana dafe ƙirjinta ta sauke numfashi.
Shima ajiyar zuciya ya sauke ya yunƙura ya tashi da ƙyar dan jikinsa ya masa nauyi sosai alamun barcin bai ishesa ba. Bai ce da ita komaiba ya nufi bayi ɗaura alwala.
Koda ya fito baiyi mata magana ba, dan yasan idonta biyu, ya ɗau jallabiya ya saka bayan ya zare kayan barcinsa sannan ya fice.
Ummu tai ajiyar zuciya tana mamakin kanta, sai kace Amaan yazo mata da wani asiri, koda yake duk fa sonta da bashi laifi inhar zata tuna a zamansu na baya bai taɓa cutar da itaba, harkarta ce kawai baya shiga, sakin da yay mata da kausasan kalamansa ne kawai suka kasa barin ranta, *_ƙwaila mara zurfin ilimi...,_* wannan kalaman sune mafi ciwo da take ganin da wahala ta iya mantasu harta bama Amaan kanta da rayuwarta yanda kowacce mace kanyi a gidan mijinta......
Jin an ƙwala kiran sallar shiga massalaci yasata tashi itama tai alwala domin gabatar da salla.
Tana zaune bayan idar da salla ya shigo, sallama kawai yay ta amsa, daga haka babu wanda ya kuma tankama ɗan uwansa, ya ɗauki kayansa na trianing ya shiga bayi, mintuna kaɗan ya fito, a bakin gado ya zauna yana ƙoƙarin ɗaura igiyar takalmansa.
“Ina kwana” Ummu ta faɗa cikin kauda kai gefe.
Bai amsa ba ya cigaba da ɗaura takalman, tasan kuma sarai ya jita, juyowa tai ta kallesa cike da takaici, hakan yay dai-dai da miƙewarsa suka haɗa ido, fuskar dai tana a yanda ta santa a tamke, zuwa yanzu hakan baya damunta dan shi da Dad ta gama sallama muskilancinsu.......
Wani ɗan tsigunnon da yay a gabanta na gayune ya dawo da ita hayyacinta, kuncinta ya sumbata cikin lumshe ido da buɗewa yana faɗin, “Amincin ALLAH ya tabbata ga zuciyar da bata fushi Matar Ajiwa”. Ya ƙare da busa mata iska a kan fuska wadda ta tilasta mata kallonsa.
Ido ɗaya ya kashe mata yana mikewa ya fice abinsa ba tare daya damu da rashin amsawarta ba.
Ta daɗe tana kallon ƙofar tamkar zata sake ganinsa a wajen, “Amaan” ta faɗa akan laɓɓanta ba tareda tasan dalilin ambaton sunan nasa ba. Har yanzu akwai barci a idonta, dan haka ta miƙe ta koma kan gadon ta kwanta zuciyarta na tunano mata Bilyn ta, ko yaya ta tashi itama? Oho.
Babu jimawa barci ya kwasheta.
Sai da gari yay haske sosai Amaan ya dawo gidan, a tsakar gida ya iske Dad zaune akan farar kujera yana duba wani littafi na addini, ga Coffee da aka haɗa masa ajiye a copy table ɗin da ke gabansa.
Ƙarasowa Amaan yayi inda Dad yake, ya zauna kan ɗan dakalin da aka zagaye flowers ɗin gidan dashi yana faɗin “Barka da safiya Dad”.
Kallonsa Dad yayi fuskarsa kadaran kada han yace, “Barka dai Fodio, yaya ɗiyata?”.
Moso yaɗanyi kaɗan yana ƙara jinjina irin son da Dad kema Ummukulsoom, ya amsa da cewa, “Lafiya lau Dad”.
“To Alhmdllh” Dad ya faɗa yana ɗaukar mug ɗin Coffee ɗinsa yakai baki.
Buhayyah data ƙaraso ɗauke da gorar ruwa a kan karamin tire da kofi ta ajiye a table din tana gaida Amaan.
Sau ɗaya ya amsa ya ɗauke kai, sai da yaga zata bar wajen yace, “K kawo min cup”.
“To yaya” ta amsa da girmamawa.
Babu bata lokaci ta dawo wajen, sanin Coffee zaisha ya sata ba tare da tama tambayesa ba ta duƙa ta haɗa masa.
Amsa yay ita kuma ta bar wajen, yana sha suna ƴar maganar data shafesu shi da Dad, ya daɗe bai samu irin wannan damarba ga Dad tun bayan rabuwarsu da Ummukulsoom, shiyyasa sai yaji sam bayason tashi ya barsa. Shi kansa Dad zaman nasu yana sakashi shauƙi da nishaɗi, yanason Fodio, sai dai shi yana dannewa ne saɓanin Momcy data gaza.
Anan Momcy ta fito ta samesu, gaisawa sukai da Amaan itama tana tambayar Ummukulsoom da gajiyar biki.
Ya amsa yana maijin nauyin iyayen nasa.
“Fodio tashi kaje ciki baka ganin lokaci yaja kabar min yarinya ita kaɗai”.
Miƙewa yay tare da sakin guntun murmushi jin furucin Dad ɗin nasa.
Momcy ma murmushi tayi.
Falon tsaf alamun an gyarashi, duk zatonsa Ummukulsoom ce ma shi, bedroom ɗin ya nufa, ya murɗa ƙofar ahankali ya shiga, tana kwance abinta tana shan barci, ya taka zuwa gaban gadon, kallon kusan mintuna biyu yay mata ya bar wajen zuwa bayi, baya gajiya da kallon ko kaɗan.
Harya fito daga wankan Ummukulsoom bata tashiba, shiryawa yay cikin ƙananun kaya marasa nauyi ya fito falo ba tare da ya tasheta ba, dan ya lura tanajin daɗin barcin sosai..........✍?
NO. 48
..........Ummukulsoom ta daɗe tana barci kafin ALLAH ya bata ikon tashi, ta sauke ajiyar zuciya ganin babu Amaan a ɗakin. Gadon ta fara gyarawa bayan ta sakko, kafin ta gyara ko ina na ɗakin ta fesa turaren ɗaki, batai gigin koda leƙa faloba, duk da zuciyarta na bata bayama sashen, dan batajin motsin komi.
Bayi ta faɗa tayo wanka, hankalinta kwance ta ɗauro towel ɗinsa, bashi da wani tsawo, dan haka iyakar cinyarta ya tsaya.
Ƙara sowa tai cikin ɗakin da ɗan hanzari saboda wayarta dake ring, ta share ruwan fuskarta tana murmushi da ɗaukar wayar, gudun karta saka a kunne ta jiƙe da ruwan dake bin fuskarta sai ta saka hans free. Cike da tsokana take faɗin, “Kaga ta gidan Muhseen amaryar ƙamshi”.
Cikin sanyin murya daga can Bily tace, “Bestie ykk? I miss you so much wlhy”.
“Nima haka Bily na, an mana wayo ko sallama bamuyiba jiya, amma yanaji muryarki haka ko baki da lafiyane?”.
“Ummu bazaki ganeba, wlhy Muhseen mugune”.
“Na shiga uku ni kulsoom, mugu kuma bily? Ya zaki danganta mijinki da wannan sunan miyay miki haka?”.
Kuka Bily ta kuma sanya mata, da ƙyar ta lallasheta tai shiru. Bily tace “Ummu kofa tafiya bana iyayi wlhy saboda tsabar rashin tausayin da ya gwadamin”.
Sai yanzune Ummu ta ranfo inda Bily ta dosa, ta sauke ajiyar zuciya, dan duk zatonta da wani mugun abu yayma Bilyn, yanda Bily ta kare maganar tana kuka saiya saka Ummukulsoom kwashewa da dariya, harga ALLAH bily ta bata matuƙar dariya da tausayi......
“Yanzu nan bestie dariya ma zakimin ba zakiji tausayina ba? Wlhy serious nake miki maganar nan, yanzu hakama muna asibiti fa”.
Tsayawa Ummu tai da dariyar babu shiri, “Wai dan ALLAH Bestie da gaske kike?”.
“Hummm da kin ɗauka wasa nake ko? Shiyyasa naketa cewa ki faɗamin yaya abun yake? Tunda ke kinsan sirrin, amma kika kifeni Ummu, gaki nan hankalinki kwance k tunda kin wuce wannan siradin tun shekaru shida da suka shige.....”
Murmushi kawai Ummu tayi tsoro na sake tsargata, Bily batasan itace ma wadda batasan komanba, ita a wancan zaman auren banda kiss da Amaan yay mata gaban Bukky batasan komai ba daya shafi rayuwar aure.....
“Kinyi shiru bestie ”.
Ajiyar zuciya Ummu ta sauke idonta yay kwale-ƙwale da tsoro, “Toni bestie mi zance, kiyi haƙuri kawai kowa da haka ya fara, amma shima dai Muhsin yayi wauta wlhy, koda yake bamaga laifinsa ba tunda farin shigane, yanzu ya jikin?”.
“Da sauƙi, gashi nan zamu koma gida, dama babu wanda yasan mun fito sai ke yanzu dana sanarmawa”.
“Sorry bestie kinji, zan aiko a amsarmin sauran kazar amarcin”. Ummu ta kare maganar da tsokana.
Ƙitt Bily ta kashe wayar tana mata ƙunkuni.
Hakan sai ya saka Ummukulsoom ci gaba da dariyarta, ta yaye towel ɗin hankali kwance zata shafa mai.
Ganin kamar inuwar mutum ta cikin mirror ɗinne ya firgitata, tai saurin maida towel ɗin ta ɗaure tare da juyowa cikin zafin nama. Ba ƙaramar faɗuwa gabanta yayi ba ganin Amaan a tsaye jikin ƙofa ya harɗe hannayensa duka a ƙirji, hakama kafafunsa harɗe suke, ya jingina rabin jikinsa a bango. Harga ALLAH batasan adadin lokacin daya ɗauka a wajen tsayeba, babar damuwarta ma ace yaji wayar da sukayi da bily da kuma yaye towel ɗin da tayi yanzun, dan ta tabbata dolene ace ya ganta.
Ƙasa tai da kanta tana haɗe fuska da matse ƙafafu alamar jin kunyar ganinta da yay da mazuran naɗe tabarmar kunya. Ya lumshe idanunsa daya janye daga kanta ya kuma buɗewa a kantan...
“Amma haka bashi da ƙyau gaskiya, yakamata kafin ashigoma mutum a dinga neman izininsa mana” ta ƙare maganar cike da tsantsar takaicinsa da haushi.
Murmushin gefen baki yayi yana warware hannunsa dake a ƙirji, hakama kafafunsa ya tsaya kyam a kansu tare da tura hannayen duka aljihun wandon jeans ɗinsa, Yanda yake kallonta ƙasa-ƙasa ne yasata jin ta sake takura, ya fara takowa a hankali cikin nutsuwa zuwa gareta.
Bata iya motsawa ba, dan tanajin kunyar ta juya baya saboda towel ɗin jikinta, kasantuwarta mai ɗan jiki ya ɗaga daga baya sosai fiye da gaba. Rumtse idanunta tayi da ƙarfi saboda jin tsayuwarsa gabanta gab da ita sosai har tana iya jiyo saukar numfashinsa.
Sunkai minti biyu a haka kowa ya kasa yin abinda ya dace, ita dai kunyace da takaici, shiko tsabar miskilancine da kasalar dake saukar masa a hankali.
Ya turo numfashi kaɗan tare da zare hannayensa daga aljihu ya ɗora bisa kafaɗar Ummukulsoom.
Ko motsi bataiba balle ta ɗago ta kallesa, sai dai salon bugun zuciyarta ya sake canjawa.
Ganin haka sai ya nufi takalar magana, yakai hannu zai kwance towel ɗin.
Babu shiri Ummukulsoom ta ɗago a harziƙe tare da riƙe hannunsa.
Jaa yay kamar zai sunce saboda hannunsa na riƙe da tawul ɗin. Ganin bata da mafita sai kawai ta faɗa jikinsa ta ƙanƙamesa iyakar ƙarfinta.
Ya sauke nannauyar ajiyar zuciya yana wani munafikin moso tare da saka hannayensa biyu duka a bayanta ya zagayeta yana ƙara mannata sosai da jikinsa tare da lumshe idanunsa, duk illahirin tsigar jikinsa na tashi.
Saida sukaja wasu mintuna a haka kafin ya iya buɗe baki da ƙyar yana faɗin, “Ke da baki fara ɗaukar karatunba, amma kike yima wanda yashiga makarantar dariya ko?”.
Sosai gabanta ya faɗi, tai ƙoƙarin janye jikinta ya kuma matseta.
“Ni sakeni, banason haka”.
Babu musu ya saketa, tai saurin barin wajen tana harhaɗe hanya saboda kunya, shiko ya bita da kallo da mayun idanunsa harta ɗauki hijjab ta saka. Numfashi ya sauke a hankali ya zauna akan stool ɗin mirror ɗin.
Bata kulashi ba, ta buɗe akwatinta guda ɗaya da aka kawo ta ɗauki kaya, bayi ta shiga.
Baice komaiba sai kansa da ya dafe, yanason Ummukulsoom, amma yasan ita bata sonshi, amincewarma da tayi ta dawo garesa saboda mahaifin sane. Duk sanda ya tuna shifa kaɗai yake shirmensa a sonta jikinsa yakanyi sanyi ƙalau, haka zuciyarsa take, idan har ta tashi son abu bata ɗaukarsa da wasa, hakama idan ta tsanesa bata ma abun ƙin sauƙi. Iska yaɗan huro a bakinsa ya miƙe ya fice a ɗakin, dama ya shigone dan ya tadata tayi breakfast ganin rana tayi, saiya isketa tana waya da bily.
Lokacin da Ummu ta fito Amaan ya fice, taja siririn tsoki tana zama tai ƴar kwalliya mara yawa, tare da ɗaura ɗankwalin daya zauna ɗas a kanta, ta birkiɗe jikinta da ƙamshi na musamman, daka ganta kaga amarya ta gaske, mayafi ta ɗauka a hannu da wayarta ta fito falon.
Amaan na kwance cikin kujera idonsa a lumshe tamkar mai barci, sai dai idonsa biyu, ya tafi duniyar tunanine kawai a sashen aiki.
Kallo ɗaya Ummukulsoom tai masa ta zauna cikin kujera ta ɗora ƙafa ɗaya kan ɗaya ta fara latsa waya.
Ƙamshin mayen turarenta dake rikita lissafinsa ya mamye dukkan hancinsa da zuciyarsa, duk yanajin motsinta, sai dai yaƙi nuna hakan, kaɗan ya buɗe idanunsa a kanta yana ƙarema ƙwalliyar tata kallo, ta masa ƙyau sosai dan a asalin bahaushiyar tata take.
Sai da ya gama ƙare mata kallo son ransa sannan ya buɗe idonsa sosai a kanta yana mata kallon kai tsaye.
A jikinta taji ana kallonta, dan haka taɗago fararen idanunta tana kallon sa ba tare data ajiye wayarba.
Gira ɗaya ya ɗaga mata. Ita kuma