Showing 156001 words to 159000 words out of 176055 words

Chapter 53 - Wutsiyar Rakumi Book 1 Hausa Novel Complete

07 Jan 2025

882

Sai kuma abinda tai tunanin zai farun bai faruba, dan kuwa wasanni kawai yaɗan mata suka shilla duniyar barci, shikam dai dama bada niyyar wani abu ya tsaya iya nanba, ya ɗau alƙawarin barinta ta warkene sosai, danshi dai a saninsa soyayya ta gaskiya itace tarayya akan samu ko rashi, tausayi da ƙyautatama juna, amana da gaskiya, adalci da tsantsar farin ciki koda bata hanyar kwanciya ba.
Da asuba yana dawowa salla yay shirin motsa jiki ya fita kamar yanda ya saba, Ummu tana ganin ya fice ta nufi kicin inda takejin motsin desmond.
Risinawa yay yana gaisheta bakinsa a washe, ta amsa fuskarta babu yabo babu fallasa, tareda ce masa yaje ya huta zatai komai.
Cike da tsoro yace, “Please ma'am kar boss yay faɗan na barki da aiki".
Karan farko da tai masa gutun murmushi, “No desmond karka damu bazaiyi faɗaba, jeka kawai”.
Shidai a ɗar-ɗar ya fice badan hankalinsa ya kwanta ba, dan a halin Amaan sai dai ya bama wani labari badai shi a basa ba.
Zagewa Ummukulsoom tayi ta shirya breakfast mai rai da lafiya, tareda tada kunnen duk wanda ya cisa, _a ganinta lokaci yayi da zatabi hudubar ƴan team dinta na wutsiyar rakumi, dan kullum cikin koya mata dabarun riƙe Amaan suke kodan ƴan team Amaan susan yanzu fa ba UMMUKULSOOM TA ƊILAU bace ba_😉.
Dan danan gidan ya gauraye da ƙamshi, desmond kansa da yaje ya karanci wannan fanni duk yawunsa yabi ya tsinke da wannan ƙamshi.
Lokacin da Amaan ya shigo gidan tunda ya shigo falon ƙamshin ya daki hancinsa, mamaki ya kamashi, yau kuma desmond da sabon salo ya zone? Da wannan tunanin ya karasa bedroom ɗinsa, tsaf ya gansa an gyara an saka turaren ƙamshi mai dadi, yaɗan murmusa kawai yana zame kayan jikinsa, shi duk zatonsa ko Ummu tana ɗakinta ne, sam bai kawo itace a kicin dinba.
Koda ya shiga bayi sai ya iske ruwan wankansa a haɗe, jiyay wani girma da kimar Ummukulsoom sun daɗu a ransa, fara wankansa babu jimawa Ummu ta kammala da kicin, desmond ta barma ya gyara, ita kuma ta fiddo komai zuwa dani, falon baya bukatar wani gyara, amma duk da haka sai da taɗan karkaɗe kura abinka da lokacin damina, ta saka turaren wuta sannan ta nufi ɗankinta. Duk sai tajita a gajiye, ruwa mai ɗan ɗumi ta haɗa itama ta shiga wanka.
Tana shiga Amaan na shigowa ɗakin ya biyo sawunta. Yasha mamakin jin motsinta tana wanka, shi duk zatonsa barci take ko kuma tayi wankan tuni bata dai ra'ayin fitowarne.
Sanye yake cikin kakin soji ruwan ganye, sunyi masifar masa ƙyau, gaba ɗaya siffofinsa na jarumta da cikar haiba sun sake bayyana a garesa, ga wani kwarjinin angwanci da hasken musulunci na haska saman kamilalliyar fuskarsa.
Wayarta dake saman drowar gefen gadon ya ɗauka yana dubawa, sam babu wani password a jiki, sai ƙyaƙykyawan hotonta itada bily sunyi ƙyau tamkar tagwaye, hatta da murmushinsu iri ɗaya ne, kowacce fararen haƙoranta sun fito masha ALLAH, haka kawai yaji sha'awar shiga ma'ajiyar hotunanta, da hotonsu na ranar Mothers event ya fara cin karo, sunyi masifar ƙyau, dan suna tsaye a filin rawane time ɗin dasu zaid ke raira musu wakar shakiyanci, duk da shi baiyi murmushi ba fuskarsa a sake take, itako taɗan sunkuy da kanta tana murmushi, yayinda shi ya kafeta da idanu..
Ummukulsoom data fito daga wanka tai yunkurin komawa da sauri saboda ganinsa.
“Garama ki dawo” ya faɗa cikin matukar sanyin murya.
Kallonsa tayi, sai taga sam ba ita yake kalloba, har yanzu idonsa nakan waya da batai zaton tata baceba.
Tamkar zata nutse dan kunya ta dawo, tasan dai tunda ya ambata ta dawo ɗin inhar ta koma ɗin akwai matsala, dan sai ya mata abinda saita gwammaci bin umarninsa tayi. A takure taja stool din mirror ɗinta ta zauna.
Idanunsa masu haske da cikar gashi ya ɗago yana zubasu a bayanta daketa wani raɓar ruwan daya hade da gogaggiyar fatarta mai ɗauke da gashi kwantattu masha ALLAH. take tsigar jikin Amaan ta fara tashi, babu shiri ya janye idonsa ya maida kan wayar yana fisgo numfashi da kyar, bai sake gigin kallonta ba harta kammala abinda take a wajen ta mike zuwa Wadrobe.
Kayanta ta ɗauka zata je bayi ta saka ya mike ya cafkota.
Cikin marairaice face take rokonsa da ido alamar ya saketa. Yi yay tamkar baima fahimci komaiba, yasa hannunsa ya karɓe kayan tareda kwance towel din jikinta ya faɗi ƙasa. Babu shiri Ummukulsoom ta faɗa jikinsa tana rumtse ido, baice komaiba ya fara yunƙurin saka mata kayan a haka, ita dai bata hanashi ba, sannan bata buɗe idonta ba, duk yanda yaso haka yay da ita har aka gama, ya kama hannunta zuwa gaban mirror yana ru gumota ta baya da ɗora habarsa saman kafaɗarta yana magana cikin kunnenta a hankali. “Beauty na tafi kowacce mace ƙyau da iya ɗaukar gayu, wanda duk bai auri lukutar mace ba to lallai ya dage ya ƙosar da tashi a gida ta zama ƴar lukuta😝, dan lokacin ne zai fahimci wani ɓoyayyen sirriiii ko yaya ta wajenaaaa”. Yanda yaƙare maganar da wani salo sai ya nema hautsina tunanin Ummu, dama tunda ya fara magana tsigar jikinta ke tashi, sai ma ta rasa amsar daya dace ta bashi akan wannan magana, tai ƙasa da muryarta cike da nata salon tace, “Nidai babu ruwana, muje kaci abinci”.
Murmushi ya ɗanyi yana gyara tsayuwa tare da ciro wayarsa a aljihu yay musu hoto a haka, ya saka hannu ya juyota suna kallon juna, nanma hoton ya kuma haskasu sannan ya maida wayar cikin aljihu yana kalonta “Faɗi gaskiya Noorulain, kodai kina tsoron siraran mata da mazansu suyi saƙwara dake?”.
Babu shiri Ummukulsoom ta tuntsure da yar siririyar dariya tana fadawa ƙirjinsa, shima murmushi yayi har hakoransa na bayyana ya dora dukan hannayensa a bayanta ya zagayeta yana mai jin tarin kaunarta na kuma ratsashi.
Daga karshe dai sai itace ta janye jikinta tare da kama hannunsa suka fita falo. Shiko babu musu yake binta. A dani ta diresa, ta ja masa kujera tana masa nuni da ya zauna, bai musa ba ya zauna tare da zuba mata ido, komai nata a nutse babu hayaniya ko rawar kai irinta wayayyun mata😝, duk abinda ya dace sai da ta haɗa masa sannan ta dago tana kallonsa cikin salon ɗaukar hankali da tasirantar da soyayyar da ba'a mantawa tace, “Yau bawan ALLAH zaici girkin matarsa”.
Sosai Ummukulsoom ta narkar da Amaan, harma ya nema rasa a wace nahiya yake, idanunta suna cikin abu masu daraja dake matuƙar tasiri wajen narkar dashi a zahiri da baɗini, sai dai ita sam ya gama lura bata saniba, shiyyasa take masa salo iri-iri dasu, sassanyar ajiyar zuciya ya saki yana lumshe ido da budewa a kanta, ya ɗan muskuta yana shafar girarsa da ɗan yatsa..
“Kulsoommmm, yanda kike daban haka komanki yake daban”. Iya abinda ya iya faɗa kenan yay mata nuni da ido akan ta bashi da kanta.
Karan farko da tajita a sama matsayin kowacce matar aure da miji ke martabata da tsaftatacciyar soyayya bisa bigiren addinin islama ta gaskiya, umarninsa tabi ta fara ciyar dashi.
Laumar farko Amaan ya kasa jurewa, ya lumshe manyan idanunsa tsawon wasu sakwanni har saida ya haɗiye sannan ya buɗe, hannun Ummu kawai ya damƙo ya bude tsakkiyar tafin ya sakar mata wata sumbata a ciki ta musamman, wadda sam babu wata ballagazar mace dake samun irinta, sai wadda ta rike kima da darajarta har gidan miji ba tare da ta rabama gayun titi ba ko mata shaiɗanu ƴan uwanta.
Ummu ta ƙankame jikinta saboda harga ALLAH taji wannan saƙon har cikin kwakwalwar kanta babu algus.
Sambatu dai ta shashi na santi iri-iri, duk da bada baki ya faɗaba a aikace yake nunawa, dan aɗan zaman nan da sukai ta gama lura dashi yafi bukatar yin komai a aikace fiye da yi da baki, sai da yay nak har yana ɗan nishi kafin itama ya bata da kansa, yanayi yana cakar da ita da salonsa, da ƙyar kowannen su yasha a hannun ɗan uwansa, badan jiransa ake a office ba da babu inda zaije saiya sha tagomashin amarci.
Ummukulsoom tai masa rakkiya har harabar gidan, sai dai suna gama fitowa yaga su Osin ya dakatar da ita tare da kareta yay mata nuni da ta koma ciki, batai musuba taja baya tana fadin, *_“ALLAH ya tsare zuciyar da bata mance ambaton sa, ka bama gangar jikin da bata gajiyawa da bautarka dukkan kariya, ka bama ruhin dake ƙwaɗayin kusantarka da rahamar ƙarfin imanin kauda idonsa daga haramun da dukkan gangar jikinsa, kayi ƙyau irin wanda babu wani namiji da ya isa kamoka a zuciyar Ummukulsoom, ALLAH ka dawo min da mijina gida lafiya da tarin aminci”._*
Gaba ɗaya Amaan ya kasa motsawa daga tsayuwar da yayi cak, banda kaikawo babu abinda zuciyarsa takeyi tamkar zata faɗo ƙasa, da kyar ya iya waigowa gareta, sai dai kuma ɓat, ta bar wajen ta shige, sai ƙasaitaccen ƙamshinta data bar ma hancinsa yana shaƙa a hankali yana lumshe ido, hancinsa na kaima ƙwakwalwarsa zuwa kowace magudana da jijiyoyinsa saƙo.
Ya kai tsawon minti uku tsaye kafin ya cira ƙafarsa da ƙyar ya nufi motocin saboda ring da wayarsa keyi, yasan dai ogansu ne.
Sai kuma zuciyarsa ta kasa zama waje ɗaya akan basirinta itada da desmond a gidan, ba wai dan yana zarginsu bane, sam wannan baizo kansa ba ma, kishine kawai irin na ma'abota imani da riƙo da sunnar MANZON tsira, waya ya zaro a aljihu yay kiran desmond, bugu biyu ya ɗaga.
Bansan miya ce da shiba, naga dai desmond ya fito da wurwuri yazo inda motocin suke, Amaan ya sauke glass din sashensa yana kallon desmond cikin lumshe idanu, “Shiga mota mu saukeka duk inda kake buƙatar zuwa, idan na dawo kaima ka dawo zamuyi magana”.
“Ok sir” desmond ya faɗa cike da girmamawa, lokacin har Amaan ya maida glass din sama.
Ummukulsoom dake kallonsu ta Window falo tai murmushi, kenan shima zuciyarsa ta fara ƙyara masa zaman desmond a gidan a yanzu baida amfani kenan.
Bedroom ɗinsa ta koma tai kwanciyarta tare da buɗe data danta gaisa da ƴan uwa da abokan arziki, musamman ƴan makarantarsu da sukai mata halaccin zuwa bikinsu, wasuma tun daga nan lagos ɗin suka tafi, wasu daga kano, bauci, adamawa, sokoto, aiko sun cancanci ta kara musu ALLAH ya huta gajiya ashe.

★★★★
Kalaman Ummukulsoom sun zauna daram a zuciyar Amaan, koda ya isa office wajen ogansu yaje, amma sam sai yazam baya fahimtar jawaban ogan, harya dawo Office itace ke masa kaikawo, ya kwanta cikin kujerar data kasance mazauninsa ya lumshe idanunsa yana juyawa a hankaki, duk yanda zai faɗama duniya matsayin Ummukulsoom a zuciyarsa bai zama lallai a fahimcesa ba, shiyyasa yabar wannan sirrin a zuciyarsa da gangar jikinsa kawai, dan sune kaɗai suka cancanci ajiye wannan sirrin. Kusan minti talatin yana a haka yakasa tsinana komai dukda tarin ayyukan saka hannu a takardu dake gabansa, ya sauke nannauyar ajiyar zuciya tareda buɗe lumsassun idanunsa ya ɗauki wayarsa ya fara tafa saƙo.

Ummukulsoom ta shagala da chart a group ɗin da suka haɗa su hɗu, ita, maman Ahmad, Bily, Aziza, sai murmushi take saboda daɗin charting ɗin, dan gaba ɗayansu suna online shiyyasa firar ke tafiya dai-dai cikin birgewa.
Saƙon daya shigo yanzu yaɗan ɗauki hankalinta, danta lura Number Amaan ce, fita tai a group ɗin koma free inda zata iya ganin inbox na kowa.
Tabbas shine, dan haka ta buɗe saƙon, amma sai da ta kashe data yanda bazai fahimci da wuri ta buɗe ba.
*_“Faffaɗar duniya mai cike da abubuwan ƙawa da birgewa, hakan kejan ra'ayin zukata da ƙwaɗaituwar kasantuwa a cikinta, Da ace zan rufe idanuna, na buɗesu a wata sabuwar duniya da ke da kamanceceniya da Aljannah, yazam dagani sai Ummukulsoom a cikinta, sai ƙyawawan furanni masu kamshi da ƙawa, sai tsuntsaye masu raira kukan dake saka nutsuwa, ga ni'imtacciyar iska mai busawa da ƙamshin ruwa, da nace nafi kowa sa'a a duniya, koda ban samu hakanba matata itace ajannata ta duniya, furannina, tsuntsuwata, sannan zuciyata gabaki ɗaya, ALLAH ya ni'imtar dake gareni har cikin aljanna, ya ni'imtar da rahamarsa gareki har ƙarshen numfashinki, ki zama sanadin zuwan iyayenki aljanna saboda nagartacciyar tarbiya da suka baki da kowanne iyaye ke fata ga ɗiyansu, ALLAH ya kara mallaka miki ni a zuciyata, karnaga hasken kowacce mace a idanuna da ruhina da sunan soyayya sai Ummukulsoom kaɗai”_*.
Babu shiri Ummukulsoom taja filo ta ƙankame tana sauke numfashi gudu-gudu kamar wadda tayi gudu a cikin sahara. Amaan na dabanne kamar yanda komansa yake na dabban a gareta.😚

⚡⚡⚡⚡⚡⚡⚡⚡⚡⚡⚡

Haka suka karasa wannan yini a daddafe cike da begen juna, kowanne tunanin ɗan uwansa ne ya zame masa abokin rayuwa, da yamma Ummukulsoom ta kuma dagewa ta haɗa lafiyyen abinci, har sannan Desmond bai dawoba, dan haka tai komanta cike da nutsuwa, gaba ɗaya gidan ya ɗauki haramar ƙamshin abinci dana turaren wuta zuwa na jiki da Ummukulsoom ta mulke kanta a ciki.
A haka Amaan ya dawo gidan ya isketa, gaba ɗaya gaɓɓan jikinsa a kasalance suke, tun a ƙofar falon ya amshi kayansa dake hannun Abbas, dan baya buƙatar su sake shigar masa cikin gida, da da yanzu akwai banbanci.
Motsin buɗe ƙofar ya saka Ummukulsoom dake jere abinci a dani ɗagowa ta kalli wajen, Amaan ya shigo yana baza idon inda zai hangota.
Tai guntun murmushi tare da tsiyaya ruwa a kofi ta nufoshi cikin takunta na nutsuwa da birgewa, sanye take da rigar Material ruwan ganye mai haske, an masa ɗinkin bubu dayay masifar mata ƙyau, ta ɗaura ɗan kwali irin ɗaurin zara buhari da yay masifar fita da dogon hancinta zuwa idanunta. Ko motsi bai iya yiba, yana tsaye a inda yake ya zuba mata manyan idanunsa farare tas harta ƙaraso gareshi.
Daf dashi ta tsaya, ta karɓa kayan hannunsa da hannunta ɗaya ta nufi falo ta ajiye tare da ruwan, shima ta dawo taja nasa hannun dariya na cinta, ganin yanda ya narke mata kamar wani ƙaramin yaro.
Sai da ya zauna cikin kujera sannan itama ta zauna gefensa tana ɗora masa kofin ruwan a kan bakinsa. Dama ƙishi yakeji, hakan yasa ruwan ya kuma masa zaƙi da garɗi a baki, ga sanyi kaɗan da ruwan keda shi yanda bazai cutar da mai sha ba.
“ALLAH shine abin godiya daya dawo min da kai lafiya cikin aminci da ƙarfin jiki dana zuciya, ALLAH ya albarkaci dukkan aikin daka gudanar yau, ya yafe maka kura-kuran da suka shiga cikinsa”.
Lumshe idanunsa yayi ya buɗe akan fuskarta, akan laɓɓansa ya furta, “I love you so much Ummukulsoom”.
Yanda yay maganar cikin wani irin ƙaramin sauti saika ɗauka raɗa yakeyi, gashi ya kafeta da mayun idanunsa dake wani ƙyalli na musamman.
Ƙasa Ummu tayi da kanta, itama ƙasa-ƙasa tace, “I love you too my Zunnurain”.
Babu abinda ya iya banda jawota jikinsa ya rungume yana sauke wani irin numfashi, tsawon lokaci suna a haka kafin su miƙe zuwa ɗakinsa, kaya taɗan rage masa, sai dai bata bari ankai ga cikiba ta gudu, ya bita da kallo kawai yana jinjina kunyarta dake ƙara mata kima a idanunsa.
Ruwa ta haɗa masa ta fito, dan karma ya haɗa sabgar wankansa da ita sai ta gudu da sauri waje ta barsa.
Yasan mi takema gudun, baice komaiba ya shige.

★★★★★★

A daren yau kam sam kasa daurewa Amaan yayi, duk yanda yaso yima Ummukulsoom kawaici saiya gaza.
Sai dai ya bita a salon da bazata cutuba sosai, hakan kuma bai hana Ummu tai masa raki ba, dan ita dai a nata ganin banbancin kaɗanne dana farko, dukda kuwa yau sai da yay amfani da man zaitun.
Tun a daren ya kimtsa kayarsa suka koma barci yana lallashinta da sanya mata albarka.
Ita dai Ummu tana mamakin wannan lamari. wai duk azabarnan da ake sha ahaka wasu ke iskanci, to kosu basajin irin wannan azabarne shin?.
Duk da murzar da tasha a hannun Amaan haka ta daure da safe ta haɗa musu breakfast, lokacin yana wajen motsa jiki, saboda mai sauƙi tayi sai ta kammala da wuri.

Yau kam hatta da wanka shine yay mata da kansa, tunma tana zizzilewa harta barsa yay yanda yakeso, dan ta kula rashin tsayawar tata ɓata masa rai takeyi.

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login