Showing 18001 words to 21000 words out of 176055 words
uwar zufa dukda garin bama zafi akeba.
Yana yanke wayar Aneesa ta faɗa jikin momcy tana faɗin “Nashiga Ukuna momcy, wlhy cayay gobe Sani yakaini legos, dan ALLAH Momcy ki hana, wlhy gawata zai maido miki nasani”.
Ita kanta Hajiya Jamila ta shiga damuwa, tace, “Aneesa saboda wannan nake faɗa muki a kullum ku a lura da abinda kukeyi a waje, yayanku yasaka masu sakama duk wani motsinku ido amma bakwa fahimtar yaren da nake muku, kema kinsan tunda ya hau dokin zuciya indai Fodio ne bazai fasa abinda yay niyyar mikiba, inma bakibi Umarninsa kinje legos ba wlhy zai iya ajiye aikinsa na wuni ɗaya yazo garinnan danya gurjeki”.
Kuka sosai Aneesa keyi, dan tasan duk abinda Momcy tafaɗa hakane.
Ana haka Ameer yashigo shima, ganinsu cirko-cirko yasashi faɗin “Kukuma Lafiya kuwa?”.
Bassam ne ya sanar masa Yaa Amaan ne.
Wata yar zabura Ameer yayi yana dafe ƙirji, “Mi akai masa kuma? Kudai yarannan akwai jazama mutane bala'i, munsamu *DAMISA* tai barci, wani cikinku halan ya taso mana ita?”.
Ummayya tace, “Wlhy kuwa yaa Ameer Aneesa ce, nifa har daɗi nakeji dayay kusan shekara baizoba, gashinan ta ɓallo mana ruwa, yace gobe isa yakaita legos”.
A firgice Ameer ya waro idanu waje, yace, “Legos!!?, Aneesa ALLAH ya jiƙanki, wlhy gobe da sassafe zan wuce Abuja, dan inaji a jikina Yaa Amaan yana gab da shigowa kaduna kuwa”.
Ummayya tace, “Wlhy yaya Ameer nima kano zanbi aunty Nurse nayi hutun sati biyu”.
Sum-sum Ummukulsoom tasamu tabar falon kafin wani yaganta, hakanne yasa batasan ya ƙarshen zancen ya ƙareba.
Washe gari dai tunda safe taga Aneesa ta ƙaramin akwai tana kuka Isa driver ya ɗauketa a mota sun tafi.
Wannan lamari ya tsayama Ummukulsoom a zuciya, dan yafi kwana uku yana mata yawo a rai da mamakin wane wannan *Yaa Amaan ɗin da sukema laƙabi da suna Damisa?* dama duk rashin kirkin yaya Ameer dasu Ummayya akwai wanda suke shakka har haka bayan mahaifinsu?.
Satin Aneesa ɗaya a legas saigata tadawo wujiga-wujiga, dukta rame tayi baƙi, dukda Muguntar da takema Ummu saida taji tausayinta da tunanin komi yay mata haka?.
Tadawo babu jimawa saiga likita yazo dubata wai inji Yaa Amaan.
Indai taƙaice muku zance saida Aneesa ta kashe sati biyu tana jiyya a gida, dukta zama wata shiru-shiru a gidan.
Wannan lamari yakuma firgita Ummu, addu a take ALLAH yasa itadai harta bar wannan gida bama zata haɗu da wannan Yaa Amaan ɗinba.
Haka rayuwa tacigaba da matsawa, yayinda bikin Ummu ke ƙaratowa, A kullum Ummu cikin lissafin kwanakin bikinta take da Baseer ɗinta, ga tsananin kewarsa da take, rabonda ta gansa a idonta kusan shekara biyu kenan, har Alla-alla take kwanakin bikin suzo, yanzu hakama an faɗama su hajiya Jamila nanda wata ɗaya Ummukulsoom zata bar aiki za'ai mata aure.
Randa Rahine tazo tana faɗama hajiya maganar auren Ummu Alhaji Mahmud yana gida, kuma yana jiyosu dayake yana ƙaramin falonsa na hutawa.
Dukda bawani kallon tsaf yakema yarinyarba ya lura tanada nutsuwa, sannan batada hayaniya, yana kuma gamsuwa da gyaran sashensa da takeyi, danshi mutumne mai bala'in son tsafta, shiyyasa tunda ya lura matarsa da ƴaƴansa ragwagene sai bayajin ƙyashin biyan a ɗauka ƴan aiki a gidan, ko nawa Hajiya jamila tafaɗa yakan bada indai yana dasu.
Inda ta shine da sunbar Ummukulsoom karsu mata aure, dan tun randa yataɓa jin hirarsu da Aziza akan karatu ya ƙudirci taimakon yarinyar yasata tacigaba da karatu, to ashe kumama akwai zancen aure akanta.
Daga nan yaci gaba da sabgarsa bai sakebi takan zancenba gaba ɗaya. Dan ko kaɗan baya shiga wata sabga da batashiba shikam.
⚡⚡⚡⚡⚡⚡⚡⚡
A ƙauyen ɗilau kuwa tsaf iyayen Baseer suka kammala masa gininsa da akeyi a faƙon amare, ginine na ƙasa irinnna ƙauye, amma sam ko sau ɗaya bai taɓa zuwa ya leƙaba, danshi dariyama su baba ke basa, waye zai zauna a wannan gidan? yoshi bama gidanba ko garin baya fatar zama cikinsa wlhy.
Hakama lefe su inna sun dage suna siyan ɗai-ɗai dama suna tarawa, gakuma gudunmawa da dangi suketa kawowa, dan haka zuwa yanzu Alhmdllh, abinda ba'a rasabane kawai ya rage a ida haɗawa, sunma jinkirtane basu sayaba saboda wajen wata uku da aka ƙara akan wata takwas ɗin farko, yanzuko da biki yazo gab wasu awakin Basiru dana inna aka haɗa aka kai kasuwa aka sayar, talatuwa yayarsa da ƙanwar inna dake zaria suka shiga kasuwa suka haɗo sauran abinda ya dace da akwatunansu guda biyu, sai basket na riyo da ake zuba kayan yara a ciki.
Yanzu kam sudai biki kawai suke jira abinsu.
★★★★★★★★
Ɓan garen baba Ummukulsoom ma Alhmdllh kamar yanda ya ƙoƙarta yayma su Azima kayan ɗaki itama Ummu yamata dai-dai ƙarfinsa, harda ɗan gadon ƙarfenta na mutunci, yasan ba uwa garetaba, dan haka yasai katon ɗin samira biyu blue yakai gidan Gwaggo hinde yace a ajema Ummu, albarka Gwaggo hinde taita saka masa, dukda itama sunata sayen ƴan abubuwanan itada sauran ƴaƴanta ƴan uwan mahaifiyar Ummun.
Acan kaduna ma ƴan kuɗin da Ummu ke tarawa na aiki inna harira ta cire wasu taɗan saya mata su kuloli dadai abubuwan da suka dace na amfani irinnan birni.
Zuwa yanzukam Alhmdllh ranar biki kawai zamu iya cewa muke jira ta kowanne ɓangare, saidai fa banda ango, danshi nasa hangen daban.
⚡⚡⚡⚡⚡⚡⚡⚡
Kwata-kwata Suhailat tagaza lafiya, ta jefa kanta a bala'i bisa ga jagorancin Baseer dake zugata a gefe yana tunzura mata wutar kishi a ranta, saboda ya fahimci tana tsananin sonshi ga kuma kishi da take dashi mai tsanani shima.
Yau har takai Suhailat a asibiti ta kwana.
A jiya da daddare yakirata yake shaida mata saura sati ɗaya ɗaurin aurensa da Ummukulsoom, shine ta yanke jiki tafaɗi a sume. Aka kwasota zuwa asibiti.
Biris daddynta yay da lamarin, danshifa komi zatayi bazai aura mata ɗan talakawa ba. Yau da ace wani ɗan mai kuɗi ta kawo irinsa wlhy saiya aura matashi, yasan konan gaba bazata sha wahalaba, tsakaninta da wanda take ƙulafucin kuwa *Wutsiyar raƙumi tai nesa da ƙasa* tama gaji ta haƙura.
Mahaifiyarta kam tashiga damuwa matuƙa, hakama ƴan uwanta.
Har asibitin Baseer yaje ya duba ta, yay ta zubama su mamin ladabi, harda hawaye yake sharewa wai na tausayin Suhailat.
Hakan da yayi, sai ƴan uwan Suhailat sukaji ƙaunarsa a ransu, danfa sosai ya nuna damuwarsa akan lamarin kamar mi.
Bayan kwana biyu da faruwar haka likita yayma daddyn Suhailat magana akan zuciyar yarinyarsu tana cikin haɗiri, dan daga yanzu inhar wani abu na firgici ya kuma samunta makamancin wannan zuciyarta zata buga su rasata gaba ɗaya.
Wannan magana da mamin Suhailat tajiya yasata zaman dirshan tanama daddy kuka da roƙonsa yabar Suhaila ta auri yaron da takeso, indai batun talauci ne ALLAH bai hanashi abinda zai taimaki yaronba.
Dayake shima hankalinsa a tashe yake baija zancenba ya amince, dan yana tsananin son Suhailat, ga yayuntama maza duk sun matsa masa da roƙo akan yay mata abinda ta keso dan ALLAH.
Shi da kansa yayma Suhaila albishirɗin ya amince ta auri Baseer, gani sukai kawai ta rungume daddy ta fashe da kuka, duk sai tausayinta ya kuma kamasu, ALLAH ya jarabceta da soyayya mai ban tsoro, wanima saiya ɗauka ƙarya take, itako harga ALLAH son Baseer take tsakaninta da wanda ya halicceta.
Itace ta matsa akan ta warke a sallamesu, shima likita fahimtar da yay tasamu maganin ciwonta saiya basu sallama suka dawo gida a daren.
Bata iya haƙuriba, sai da ta kira Baseer a daren ta shaida masa, yanda yanuna mata tsantsar farin cikinsa ne yakuma dasa sabuwar ƙaunarsa a ranta, gani take shima yana tsananin sonta da ƙaunarta fiyema da yanda take masa, dan anbata labarin kukan dayazo yayi tana kwance a asibiti.
Da kansa ya tsara duk matakan da daddynta zaibi wajen shawo kan babansa shima, dan yanzu haka bikinsa da Ummukulsoom kwanaki biyar kacal yarage, shirye-shirye kawai sukeyi.
Hakan yaso birkita zuciyarta, amma yashiga kwantar mata da hsnkali saɓanin da da saidai ya rura zuciyarta da ɓacin rai.
⚡⚡⚡⚡⚡⚡⚡⚡
Kwanaki biyarne kacal suka rage bikin Ummukulsoom da Baseer, zuciyar su baba yalwa tamkar zatayi bindiga, sai daifa babu yanda suka iya da ikon ALLAH, dan haka suka zuba na mujiya kawai.
★★★★★★
Yau Ummu zata baro kaduna, ma'aikatan gidan Alhaji Mahmud Ajiwa su Jud duk sun shiga damuwa, dan Ummukulsoom yarinyace mai shiga rai, batada damuwa, kakan zauna tsawon lokaci da ita bakace gashi tamaka kazaba, sukansu ƴan gidan zukatansu duk babu daɗi, dan Ummu tayi juriya da halayyarsu ba kaɗanba, gashi duk abinda sukace tai musu babu wani ja'inja takeyinsa komai gajiyar da tayi, sai daifa aransu sukejin babu daɗin, amma a fili basu nunaba.
Bayan ta kammala shirinta taje kiranda Alhaji Mahmud yay mata.
Durƙushe take agabansa yana mata nasiha akan rayuwar aure, hawaye kawai take sharewa da hijjabinta, tareda jin ƙaunar dattijon mai adalci da ɗaukar kowa ɗaya, gashi yana mata nasiha tamkar mahaifinta, daga ƙarshe yay mata doguwar addu'ar zaman lafiya, sannan yabata wani abu a ✉ dabatasan ko mineneba, yace, “Gobene zaki tafi can garinku ko?”.
Kai Ummukulsoom ta ɗaga masa tana share ƙwala.
Yace, “Ok, insha ALLAH driver zaizo ya kaiku can ƙauyen yaganomin, dan insha ALLAH zan halarci ɗaurin auren inhar wani uzuri bai dakatar daniba, ALLAH ya sanya albarka yabaku zaman lafiya, ko anan gaba kike buƙatar taimako kizo gidannan kanki tsaye, dan kema kinzama ƴar uwa kodan wahalta mana da kikayi, dan komi mai gida zai biya ma'aikaci bai gama biyansaba, ALLAH yay miki albarka, kodai kaduna kika shigo kidinga daurewa kina zuwa ayi zuminci”.
Ummukulsoom na share hawaye tace, “To baba, nagode ALLAH ya ƙara girma da lafiya mai amfani”.
”Amin ɗiyata nagode nima”.
Sauran ma'aikatan sunsha kuka da Rahine tazo tafiya da Ummu, tareda kawo wata yarinyar da zata maye gurbin Ummukulsoom ɗin.
Koda suka koma gidan Inna harirah ma ba zama sukaiba, dan itama Aziza tataho gida saboda bikin Ummu da zasu tafi.
Duk abinda zasu tafi dashi suka kimtsa saboda jin Alhaji Mahmud yabasu mota ta kaisu.
★.
Yau da biki ya rage saura kawana ukune su Ummu suka nufi ɗilau a motar da Alhaji Mahmud yabada akaisu............✍🏻
NO. 7
Mahaifin Suhailat yay shiri tsaf shida babban ɗansa yayansu Suhailat suka nufi ƙauyen ɗilau, babu abinda kecin zuciyarsa sai takaici, wai ƴar cikinsa, jininsa ce zata auri wanda yafito daga wannan ƙungurmin ƙauyen da ko hanyar kirki basuda shi, Wlhy badan ciwon da akace yanama Suhaila barazana ba babu yanda za'ai ya amince da wannan shirmen nata.
Tunda suka shiga cikin ƙauyen ransa yakuma ɓaci ƙololuwa, hakadai ya danne da ƙyar, da tambaya suka isa gidansu baseeru, banda kallon raini babu abinda dadyn Suhailat kema gidansu Baseer shida Mika'il, yama akai wanda ya fito a wannan banzan gidan yasamu kuɗin karatu? har yaje ya ganarmasa ɗiya?, koda yake ance mutanen ƙauye kuɗine dasu amma shegen maƙo baya barinsu suci.
Koda baban Basiru yafito yaga waɗannan baƙi a jibgegiyar mota duksai ya rikice, yama rasa ina zai ajiyesune.
Dadyn Suhailat dake cika yana batsewa yace, “Kaga malam kaimu daga cikin gida, dan wannan maganar ta sirrice”.
Jikin baban Basiru na rawa yace, “To to Alhaji ayi haƙuri, kushigo, bismillanku”.
A cikin gidama inna tasha mamaki, dardumarta da baffanta yaje makka yakawo mata tsaraba shekaru kusan ashirin ta ɗakko, dan bata fito da ita kwata-kwata, bayan an saka musu tabarma sai aka shimfiɗa dardumar a sama, amma dukda haka sun zaunane kawai bisa ƙyanƙyami cewar daddyn Suhailat.
Baseer daduk yasan da zuwansu saigashi ya shigo, dan dama yana laɓe a bakin gari yana kallon shigowar su Daddyn Suhailat.
Maganin daya amso wajen wani malami na rufe bakin iyayensa da malamin yace saisu daddyn Suhailat sunzo zaizo ya barbaɗa a gidan, da tun jiya ya binne wata laya a tsakkiyar murhun gidan dukdai na rufe bakinne, ya zaro maganin a aljihunsa, cikin hikima yaringa zubda maganin a ƙasa kaɗan-kaɗan, tabbas innarsa ta lura ƙurar wani abu na fita a hannun Basiru, sai dai bata kawo komai arantaba.
Kamar yanda malamin ya faɗa maganin na ƙarewa su inna da baba suka shaƙa sai duk tunaninsu ya juye, suka kuma ganin Dadyn Suhailat yamusu wani mugun kwarjini, hakama Basiru.
A dake Daddyn Suhailat yafara magana, saikace yana gaban ƴaƴansa ne ko ɗaliban makaranta, sai wani faman mazurai yakeyi.
“Bisaga Nacin ɗanku na liƙema ƴata harta kamu da ciwo, munyi-munyi ta rabu dashi hakan ya gagara, dukkan abinda takeso mukuma zamu iya mata domin samun lafiyarta, dan haka mukazo akan maganar aurenta da ɗanku, na farko dai yarinyata bazata iya zaman ƙauyennan ba gaskiya, balle rayuwar talauci dabata taso tagani ba. Zanbama ɗanku gidan da zasu zauna, da motar hawa, nakuma bashi aiki, komai na hidimar bikin na ɗauki nauyi, sannan Suhailat bazata taɓa rayuwa da kishiyaba, sai kusan yanda zakuyi da wadda kuke shirin haɗashi da ita”.
Takaici da baƙin ciki sun cika zuciyar Inna da Baba fam, amma bakinsu da fuskarsu yagaza nunawa, sun rasa dalilin hakan kuma, shi kansa Basir maganar daddyn Suhailat ya ƙona zuciyarsa, amma ayanzu bazai nunaba sai ƙudirinsa ya cika a kansu sannan...........
“Kunyi shiru, ko bakuda abin faɗane bayin ALLAH?”. Cewar mika'il.
Da sauri baba yace, “To Alhaji duk yanda kace ai haka za'ayi ALLAH ya sanya alkairi yabada zaman lafiya, indai maganar auransa da waccan yarinyane an barsa, yanzuma zanje na sanarma mahaifinta”.
“Muna jiranka kaje ka sanar musu kadawo, muma saimu bama ɗanku abinda mukai masa alƙawari, sannan mu tsaida maganar auren”.
Baba ya amsa da “To” yatashi ya fita, dolene yabaka tausayi, jikinsa sai rawa yake tamkar wani almajiri gaban ubangidansa, Inna kam banda suya babu abinda ranta keyi mata, tarasa mike damunsu itada baban talatu, anzo ana wulaƙantasu a gidansu, akan ɗansu amma sun gaza ɗaukar wani mataki.
Baba na fita yasa gefen rigarsa ya share hawayen da suka gangaro a kumatunsa, wanda kwata-kwata yama rasa dalilinsu.
A ƙofar gida baban basiru ya iske baban Ummu yanajin redio shida wasu dattijai biyu, saida suka gaisa cikin mutunci sannan baban Basiru yaja baban Ummu gefe ɗaya dan yay masa bayani, amma saiya kasa sai inda-inda yakeyi.
A dai-dai wannan lokacin motar su Ummukulsoom ta tsaya, hango babanta dataine yasakata ɗokantuwa da fitowa taje gareshi, dukda kuwa kwanansu 6 kacal da rabuwa yataho gida.
Tunda Baban basiru da Babanta suka hangota sai hankalinsu ya koma kanta, kowanne fuskarsa washe da murmushi, a zukatansu suna ambatar kalmar masha ALLAHU, dan ganin Ummu ta kuma cika da buɗewa alamar duk inda take bata cikin wahala, tana gab da isa gaban su baban, Basiru da Daddyn Suhailat da Mika'il yayanta suma suka iso. Dan basiru ne yacema daddyn Suhailat yakamata yaje da kansa, babansa zai iya kasa faɗama baban Ummu sun fasa auren, shikuma ba son Ummu yakeba daman.
Babu wani dogon tunani a maganar, daddyn Suhailat ya amince suka biyo bayan baba.
Tunda Ummukulsoom ta hango Basiru sai takejin zuciyarta na wani tsitstsinkewa, babu abinda takeyi sai ƙara tsarkake sunan ALLAH da yay wannan ƙyakykyawar halitta, lallai ta more da samun miji abinso ga kowa....
Basiru kuwa kallo ɗaya yay mata ya ɗauke kansa, dukda harga ALLAH yaji wani abu ya soki ransa gameda canjawar da Ummu tayi gaba ɗaya, sai dai kuma kuɗi sun rufe idonsa, burinsa kawai yagansa da gida da motar da daddyn Suhailat ya ambata masu, idan yasamu wannan daga baya yazo yabama Ummukulsoom haƙuri ya aureta, yasan zatai masa Uzuri......
Bayanin da Daddyn Suhailat kema baban Ummukulsoom gatse-gatsene yaja hankalin dayawan mutanen wajan, dan cikin hargowa yake faɗin, “Malam munzone mu sanar maka Baseer ya fasa auren ɗiyarka, dan bama su daceba, ina wannan ƙyaƙyƙyawar halittar ina matar data fito daga wannan ƙungurmin ƙauyen, ka nemawa ƴarka mijin aure kawai”.
Babu wanda yasan miya faru, kawai ganin Ummukulsoom akai a ƙasa wanwar ta yanke jiki ta faɗi, Aziza