Showing 129001 words to 132000 words out of 176055 words

Chapter 44 - Wutsiyar Rakumi Book 1 Hausa Novel Complete

07 Jan 2025

874

Basiru ya sayo masa kaza, tun basiru na ɗaukar hakan girmamawa harya fahimci ƙasƙantar dashi kawai akeyi, duk ma'aikatan gidan ace anrasa ɗan aika sai shi, wannan abu yamasa matuƙar ciwo.
A haka aka fara gudanar da events, da yake na gidan mata aka fara sai bai halarci ko ɗaya ba, Meenal ma tamasa wahalar gani, tsakaninsa da ita saidai takira tamasa gargaɗi akan ya kula da kansa, wlhy karta ganshi da wata, inko hakan ta kasance wlhy duk abinda ya biyi baya shine yaja.
Cikin haushi da hasala ya gimtse wayar, dan kiran ma datai masa yanzu kenan, a fili yace, “Wlhy zan koya miki hankaline, bar ganin ina sonki”.
Oho batasan yanaiba ma ita, dan daga can ta ɗaukama itace ta fara gimtse wayar ba shiba.

A ranar juma'a su Suhailat suka iso gidan gwamnatin katsina ita da Daddynta dasu Lubna.
Kasantuwar abotace tunta secondary a tsakanin daddyn Suhailat da Abban Meenal saiyay murna sosai daganin harda iyalansa, da kansa ya kira Meenal a waya ya haɗata da su Suhailat a zuwan ga ƙawaye, dan bazasu wuce sa'anni ba.
Ganimsu suma fa manyan yarane sai meenal ta amshesu hannu bibbiyu, dama ita ALLAH bai yita mai yawan tara ƙawayeba sam.
Duk wani motsin Meenal akan idansu Suhailat yake gudana, sunata baza ido suka Baseer yana fantamawa sai sukaga bulum, koma ƙyallinsa basu ganiba acikin hidimar bikin.
Sai dai cikin sauƙi suka ɗauki Number sa da Meenal ce kawai tasanta, saboda kuma tai saurin kamashi idan har yanacin amanarta yasa ta bashi kayin tare da shinfiɗa masa dokoki tunda suka dawo.
Bai musa mataba a lokacin yace yaji ya kuma gani.
Kowaccensu tai saving Number a wayarta, sauran aiki kuma Abu ne zai ƙarasa musu insha ALLAH.

Basuga Baseeru ba sai ranar dinner, yana nane da Meenal data hanashi rawar gaban hantsi, gashi ƙyawunsa da gayun da yayi yay bala'in tafiya da ƴammatan wajen.
Zaune suke a tabiri ɗaya shi da Abu da meenal ɗin, sai su Suhailat dake can bayansu saboda kowacce kujera mutum huɗu ce, kasantuwar Meenal bata buƙatar kowa tare dasu yasa su suke zaune su uku.
Zulfah dake charting da Abu ta turo masa wani sabon saƙo.
A kaikaice ya ɗaga kai ya kalleta, tai masa signal da ido.
Murtani ya maida mata yana gyara zamansa.
Meenal ce taja hannun Basiru suka miƙe saboda itace takeso ta farama amarya da ango da suka taso liƙi.
Abu yay saurin janye wayar Basiru dake a saman tebir ajiye.
Koda basiru ya laluba baiji wayarba sai kawai yabi meenal gudun karta dizgashi, ga Zulfah da tun ɗazun idonsa ya sauka a kanta, yasha matuƙar mamakin ganinta, dama kawai yakeson samu yaji miya kawota wajen? Tanada alaƙa dasu meenal ne kokuwa danshi tazo?.
Cikin dabara Abu ya miƙama Lubna wayar ta baya, dan itace a kusa dashi.
Sauri-sauri sukayi duk abinda suke buƙata da wayar, sunyi copy ɗin abubuwa da dama na ciki, sannan suka loda masa hotunan ƴammata, harda wanda yayi da wasu ƴammatan da Abu ne yayta jan ra'ayinsa sukeyi, amma sai baya yarda asa a wayarsa sai iya na ƴammatan kawai.
Gaba ɗaya Abu ya rikice ganin Basiru da Meenal sun gama sun doshi hanyar dawowa, ya zunguri Lubna da itama taketa yarfe hannu saboda abunda suke Copy ɗin bai gama shigaba.
Harsun zauna Basiru na laluben wayarsa sai MC ya kuma kiran sunan Meenal, hakan yasa ta kuma miƙewa tareda kama hannunsa suka koma.
Ajiyar zuciya Abu ya sauke, hakama su Suhailat, bawai dan sunajin tsoroba ne, sundai fi son komai su bisa ta siyasa sai yafi shigar basiru, tunda shima hakan yay musu, bayan sun gama wayar suka goge da handkherchief, ahaka Aby ya amsa shima yaje wajen rawar, cikin hikima ya jefama basiru wayarsa aljihu.

⚡⚡⚡⚡⚡⚡⚡⚡⚡⚡⚡

Duk da ba kowa yasan da ɗaurin aurenba saiga mutane sunɗan taru. musamman ma dasu aunty Ummy suka ƙaraso, sai gidan ya sake ƴar cika.
Gaba ɗaya sai Ummu taji ta takura, musamman da Aziza tazo suka sakata gaba itada Bily, dan tsaf Bily ta zayyanema Aziza abinda ta gani, harma da sharri ta ƙara.
Tun Ummu na tanka musu harta tsaresu.
Koda su Aneesa suka zo wai gaidata bata nuna musu komaiba, sai dai kuma bata wani sake musu ba sosai.
Hakan saiya ƙara mata ƙwarjini a idonsu, harma zukatansu suke jin shakkarta, aransu kam ƙiyastawa suke Yayansu ya samu dai-dai shi.
Inda adane wani yace musu Ummukulsoom ƴar aikin gidansu zata koma haka saisun ƙaryata, su dama suka tashi a birnin, cikin gatan da wayewar da sukeji da ita duk sai suka raina kansu a gabanta, dan ita wayewar tata mai aji ce, bawani rawar kai ko shirmen rashin tarbiyya da rashin wayo, komai nata anutse yake, takan girmama Addininta da al'adarta koda a magana ne fiye da wayewar da mutane ke ɗauka ƴan boko keda ita.
Sunata zuba hira dasu Bily amma ta share kowa tanata danne-dannen lap-top ɗin Yaya Zaid data amso tana wani bincike, inhar ba wanine ya ambaci sunanta a ɗakinba da sigar tambaya bata ko kallonsu, shima saita zaɓa wanda taga zata iya amsawa, wani kam sai dai tai murmushi kawai ta ɗauke kanta.
Sun ɗanyi hotuba a waya zuwa gab da magrib kowa ya kama gabansa, sai gidan yay tsit, dan Aziza ma ƙin zama tayi, wai ita kunyar surukai.
(Sai yau Ummukulsoom takejin zancen ashe yaya Zaid Aziza zai aura, kuma da ƙulla maganar bai gaza wata biyu da wasu satittikaba, gab da za'a kai kuɗinnan ne ma hakan ta faru, ko lokacin da Amaan ya bayyana kanshi da fuskar A-waheed ashe kuɗin Zaid gidansu Aziza aka kaisu, Zaid kuma shiya zaɓi a ɓoyema Ummukulsoom wannan zance bisaga wani dalilinsa can, shiyyasa bata taɓa saniba sai yau).
Sosai taji daɗin wannan haɗi, koba komai wani zumincin mai ƙarfi ya kuma ƙulluwa tsakanin dangin mahaifiyarta dana mahaifinta.

*_WASHE GARI_*

A yau sukai niyyar komawa amma sai Abba ya hana akan wani dalili, yace su bari sai gobe lahadi saisu koma tunda dai babu makaranta.
Wannan dalilinne ya saka su Ummukulsoom shan barcinsu suka ƙoshi har tashin hantsi.
Ummukulsoom ce ta fara farkawa, gidan tsitt babu wata hayaniya, dama sunsan Abba da Attahir da Zaid zasuje wajen wani ɗaurin aure, Ummi da maman Ahmad kuwa sun fita karɓo kayan gyaran jiki da Ummi keson su Ummukulsoom su fara idan sun koma legos, hakan yasa daga Bily sai Ummukulsoom kawai a gidan........✍🏻

NO. 44

..........Sai kusan ƙarfe ɗaya su Ummi suka dawo gidan, lokacin itama Bily ta tashi suna kicin suna haɗa abincin rana da ƴar hirarsu.
Ummi data shigo tana faɗin, “Ummm autocina duk kun cika mana gidan da ƙamshi”.
Dariya sukai suna juyowa, duk sukazo suka rungumeta suna mata sannu da zuwa.
Sai da ta buɗe komai taga mi suke girkawa sannan ta fita danta watsa ruwa.
Ummi na fita maman Ahmad ta shigo, dama kunyar Ummi ta sata maƙalewa.
“Habawa yara, inacan inata tattalin yanda za'a shiryaku amma na dawo ko ɗan ruwa baku kawo minba?”.
Dariya duk sukayi, Bily tace, “Aunty wai dan ALLAH ina kukaje?”.
“Gidan wata hajiya ce wlhy, kai-kai angunan nan zasu more fa, yara ina tausaya muku”.
Kafin su bata amsa yaya Zaid ya shigo. Sannu da zuwa sukai masa.
Ya amsa yana buɗe firij ya ɗauki ruwa da faɗin, “Wai dan ALLAH baku gama abinci ba? ALLAH yunwa nakeji.
Cikin tsokana Ummu tace, “Tofa, yaya Zaid kuda kukaje kuka ciwo kajin ɗaurin aure?”.
“Kajin wahala ba, wanifa ƙauyene can Abba ya kaimu, ni bammasan miye dangan takarsu ba, ko ruwa ban shaba harmuka taho, garama Ameer da Yaa Attahir sunsha fura, dan su dama mayun tane”.
“Oh wai harda Yaya Ameer kukaje?” cewar Bily.
“Eh, harma da Dad da yaa Amaan da Bassam fa”.
“To, to ALLAH ya sanya alkairi”.
“Amin dai, ammafa naci dariya, kunga angon kuwa? ALLAH Bassam ya girmesa sosai, bai wuce 20years ba”.
Maman Ahmad tace, “20years fa? Kai Zaid banda sharri”.
“Wlhy babu wani sharri Aunty Hafsat, bara kiga hotonsa”.
Wayarsa ya zaro ya miƙa musu bayan ya lalubo hoton, sai mamaki sukeyi, amma banda Ummukulsoom da tai murmushi kawai, dan ita wannan ai ba sabon abu bane a wajen ta, garinsu har ƴan 18 yima aure ake kuma maza.

Ranar dai yini sukai a gida suna shan hira hankali kwance.
Sai washe gari da yamma suka koma legos tare da tarin kayan gyaran jiki da Ummi ta haɗasu dashi, sai maganin sanyi da aganinta shine mafi muhimmanci a garesu, garama Ummukulsoom ita ance ta fara shan wasu kayan ƙarin ni'ima dana matsewa, dan ita Ummi duk zatonta Ummu tasan komai tunda dai an kaita gidan miji.
Sai dai koda suka dawo sai Maman Ahmad bata bataba, dan tasan ita dai yanda Ummukulsoom ta rayu a gidan Amaan a wancan zaman.

Su Ummukulsoom ba tare suka dawo da Amaan ba, shi sai safiyar litinin ya dawo saboda wani uzuri daya tsaidasa na zuwa Ajiwa.


⚡⚡⚡⚡⚡⚡⚡⚡⚡⚡⚡

Washe garin litinin da wuri Ummukulsoom tai shirin makaranta, tea kawai tasha a tsai-tsaye, shima sai da Maman Ahmad tai mata jan ido, tana gama sha ta miƙe ta tattara kayanta domin tafiya.
Sanye take da doguwar riga ja mai taushi, rigar robace, dan haka ta ɗan kama jikinta, amma ba sosai ba, sai dai saboda kasantuwarta mace mai cikar halittar jiki za'ai saurin fahimtar yanda rigar tabi jikinta, gyale baƙi madaidaici ta naɗa a kanta.
Maman Ahmad nason mata maganar ta canja gyale sai ta shafa'a har Ummukulsoom ta fice.
Abbas ta iske a ƙofar gidan Attahir tsaye jikin mota.
Cike da girmamawa ya gaisheta, ita harma abin yaso bata mamaki, sai dai bata ja zancenba tai shirin wucesa.
“Uhm auntyn mu ai nine zan kaiki”.
Juyowa tai tana kallonsa da mamaki, kamar bazatai magana ba sai kuma tace, “A'a Abbas nagode wlhy kaje abinka, dana fita zan samu taxi”.
Ganin zata cigaba da tafiya yay sauri cewa, “Ai boss ne yace a kaiki”.
Tsaf ta gane wanda yake nufi, kuma tajishi sarai, amma saita share tai gaba abinta tamkar bata jiba.
Abbas ya rasa yanda zaiyi, sai kawai ya zuba mata idanu harta fara nisa.


★★★★

Cikin nutsuwa take tafiya tamkar yanda ta saba, wanda bai mata farin saniba saiya ɗauka yanga ce ko salon iya shege, amma sam ba haka baneba, tunma ba yanzu ba wannan shine asalin takun tafiyar Ummukulsoom tun tana a Ɗilau, tana tafiya tana kallon agogo, fatanta ta fita daga Barrack ɗin akan lokacin kawai.
Cak ta tsaya ganin ansha gabanta, ta ɗago a fusace dan son ganin wane ɗan iskane? Dan ita ba sakarma mazan Barrack ɗinnan fuska takeba.
Tsaye yake a ainahin sojansa, da alama daga motsa jiki yake, dan sanye yake da kayan training na Adidas farare tas, fuskarnan a ɗaure babu walwala kamar ko yaushe, duka hannayensa biyu zube a aljihun wando, sai earpiece daya maƙala a kunne wanda batasan mi yake jiba.
Duk da taji wani iri sai ta janye idanunta itama tana kuma ɗaure fuska ta ratsa ta gefensa zata wuce.
Hannunsa dake cikin wanda ya zaro tare da kamo nata ya maidota gabansa yana kuma haɗe fuska.
Waige-waige Ummukulsoom ta fara, babu yawan mutane sosai, amma akwai ɗaiɗaikun sojoji irinsa masu fitowa motsa jiki da sanyin safiya, yanda baiyi magana ba itama sai bata tankaba, sai hannunta da take kici-kicin ƙwacewa wani haushi na kuma cikata, gashi yanata ɓata mata lokaci.
“Banason abinda kakemin wlhy, ka sakarmin hannu malam”.
Banza yay mata tamkar bai jiba, baikuma sake mata hannunba, sai da ya shaƙi iska ya fesar sannan ya watsa mata manyan idanun nan nasa masu matuƙar tasiri a gareta, itama hararsa tayi ta ɗauke kai.
Murya ƙasa-ƙasa yace, “Ki koma ki canja waɗannan kayan, kokuma ki fasa zuwa makarantar, kuma daga yau Abbas zai kaiki ya ɗakkoki, ya rage naki kiyi yanda nace, kokuma kiyi naki tsarin”. ‘Ya ƙare maganar da sakin hannunta yay gaba abinsa ko wai-wayenta bai sake yiba’.
Harara tabi bayansa dashi, itama ta juya taci gaba da tafiyarta batare da ta koma ɗinba.
Tana tsaye a hanya danta samu taxi, mota tazo ta tsaya a gabanta, ƙin ɗaga kai tai ta kalli motar balle wanda ke a ciki.....
Jitai kawai an fisgeta an tura a motar, tana niyyar yin ihu ya maida murfin ya rufe ya zagaya mazaunin driver ya zauna.
yana shiga ta buɗe zata fita, fisgota yayi ya maida murfin ya rufe tare da saka luck.
Duk yanda taso haɗiye kukanta ta kasa, saida hawaye suka silalo mata a kumatu, hankalin sa dake kan tuƙine ya hanashi ganin kuka take.
Ita kuma taƙi kallonsa, takumaƙi magana dan zuciyarta a maƙoshi take.
Har suka isa makarantar babu wanda ya tankama ɗan uwansa, kowa ya ɗauke kai ya haɗe fuska.
Koda yay fakin sai bai cire luck ɗinba, hijjab ɗin dake bayan motar ya jawo ya ɗora mata akan cinya, cikin kakkausar murya yace, “Wlhy wannan yazama first and last da zan miki magana kiyi ignoring ɗina, dan zakisha wahalane wlhy. Fitarmin a mota”.
Ko kallon inda yake bataiba ta buɗe ta fice abinta.
Shikuma yaja motar tare da bula mata ƙura ya bar wajen.
Tsaki Ummukulsoom taja tana harar hijjab ɗin, ta tsani mulkin mallaka a rayuwarta, wlhy badan furucin baba a kantaba da bazata sakaba sai taga yanda zaiyi.
A fili tace “Sai shegen zuciya da faɗin rai kamar kuturu”.
Hijjab ɗin ta warware ta saka kafin ta karasa class.


Tun daga wannan ranar Abbas ya koma kaita maƙaranta, dan Attahir da kansa ya kirata yay mata faɗa akan hakan, yakuma ja kunnenta akan kayan da zata ringa fita dasu, dan ya kula ran Amaan yakai ƙolluwar ɓaci da abinda Ummukulsoom tai masa aranar, ba komai ya hasala shiba kuwa sai kishi mai tsanani da ya dade da karantar Ajiwa na dashi.
Tabi dukkan shawarar Attahir kuwa, danshi matsayin uba yake a gareta, sai dai kuma bata sake ganin Amaan ba tun ranar, bata damuba, dan ba buƙatar ganinsa takeba, hankalinta ma gaba ɗaya yana kan exams ɗinta da yazo gangara.

Tana saura kwana biyu ta kammala exams Attahir da Amaan sukayi tafiya.


⚡⚡⚡⚡⚡⚡⚡⚡⚡⚡⚡

Biki ya tashi lafiya su Suhailat dai basu kai ga komawa ba sai yau, taget nasu na gaba shine haɗuwar Zulfah da Basiru, dan haka suka sanya Abu duk yanda zaiyi yayi ya saka Basiru fitowa gida a yau.
Kasancewar Suna tare da Meenal sai Abu bai wani sha wahala akan hakanba.
Wajen wani hutawa na ƴaƴan manya sukaje, tunda suka shigo Zulfah na kallonsu, tana zaune a rukunin kujeru nacan gefe tana danna waya da shan Ice-creem.
Kusan mintuna goma da shigowar su taga sun nufota, ɗauke kai tai tamkar bata gansu ba, Abu ne ya fara jan kujera ya zauna a wajrn yana faɗin “Assalamu alaikum, ƴammata ko zamu iya zama dan ALLAH”.
Saida taja lokaci kafin ta amsa masa batare data kallesu ba.
Basiru kam Uffan bai ceba, yama ɗauke kansa gaba ɗaya shima, shi adole mai aji mijin ƴar gwamna😝.
Suna zama Zulfah ta

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login