Showing 135001 words to 138000 words out of 176055 words
shima ya hau jibgarta.
Iyaka iyawa meenal ke zabga ihu itama tana kai masa duka, baba mai gadi daya iso da gudu saboda jin hayaniyarsu duk saiya ruɗe ya rasa ina zai nufa, fita yay da gudu neman mutane, hakan yay dai-dai da shigowar motar Su'ada yayar Meenal. a ƙofar gida ta faka motar ta fito hankali tashe saboda ganin yanda mai gadi ke tsaidata.
“Kai lafiya kuwa?”.
“Hajiya kiyi taimako Alhaji zai kashe hajiya wlhy.....”
Bangajesa tai ta afka cikin gidan, saboda jiyo ihun meenal da takeyi sama-sama.
Ɗane-ɗane ta iske Basiru saman Meenal yanata duka tamkar ya samu jakarsa.
Sai da ta fara yin gajeren bidiyo sannan tasa iya ƙarfinta ta hankaɗashi gefe, lokacin meenal ta gama fita hayyacinta gaba ɗaya saboda shaƙar da Basiru yay mata a wuya.
Waya Su'ada tasa ta kira mahaifinsu kafin police, cikin mintuna da basu fi 20 ba saiga police tare da yayan meenal da yay aure kwanan nan.
Duk yanda Basiru yaso musu bayani sunƙi fahimtarsa, tunma anan suka fara dukansa saboda gaddama da yaso musu, aka cukuykuyesa aka jefa a mota, ita kuma Meenal akai asibiti da ita....
⛹🏻♀️⛹🏻♀️⛹🏻♀️😞
⚡⚡⚡⚡⚡⚡⚡⚡⚡⚡⚡
Tun isowarsu suka tabbatar da bikifa ya kankama, dan gida ya fara cika da dangi makusanta na nesa, inna laraba ma ta iso ta ɗilau da sauran dangin maman Ummukulsoom, hakama wasu daga dangin Ummi.
Abokan wasa suka fara tasasu da tsokanar amare-amare, duk sai sukaji abun banbara kwai wai namiji da suna hajara.
Isowarsu baifi da mintuna 40 ba saiga ƴan kawo lefe daga gidansu Amaan, ita Ummu ma abin ɗaure kanta yay sosai, lefe sai kace wani auren farko? Dan danan gida ya kacame da guɗe-guɗe, kasancewar zuwan ƴan kawo lefen Ummukulsoom babu jimawa sai ga lefen Bily itama, gidafa ya kuma kacamewa, komai sunyi abinsu akan tsari.
Dole su Ummukulsoom suka fice gidan badan sun soba.
*_WASHE GARI_*.
Da hantsi aka kai lefen yaya Zaid gidansu Aziza, wannan kam da Ummukulsoom akaje, taji daɗi sosai ganin ƴan uwansu na ɗilau ɓan garen babanta suma sun fara isowa.
Sai surutu suke mata wai taji ƙyau da jiki, harda masu mata habaici a kaikaice wai shiyyasa ta guji ɗilau dan tafi ƙarfin mazajen can, (adai taƙaice suna mata shaguɓen sun san aurenta ya mutu), sarai ta fahimcesu kasan cewarta lauya, amma saita basar kamar bata fahimta ɗinba.
Sai kuma akai sa'a Amaan ya kira wayarta dake hannun Bily a dai-dai wannan lokacin.
Cike da tsokanar magana Bily da sam bata fahimci gugar zanarba tace, “Bestie ga mijinki na kira”.
Duk kallon bily sukai su masu shaguɓen, Ummu kuma taɗan yatsine fuska kamar bazata amsaba sai kuma ta amsa saboda maida murtani.
Sakin ranta tai cike da yanga tai sallama bayan ta saka wayar a hans free kowa naji.
A hankali ya amsa tare da cewa “Inason ganin matata”.
Murmushin ƙarfin hali Ummukulsoom tayi tana faɗin, “ba yau ba”.
“Why?" ya faɗa a marairaice.
Mikewa tai tabar wajen dan tasan wannan amsar kawai ta ishesu. Aiko duk sai jikinsu yay sanyi suka faɗa wasi wasin to kodai ƙarya akeyi dama aurenta bai mutuba?.
Ita dai tuni ta koma gefe tana cigaba da wayarta da Amaan dake tambayarta kalar kayan da takeso suyi amfani dashi wajen mothers day ɗin da Momcy ta haɗa musu.
Ita kuma ta dage akan bazata jeba gaskiya.
Shiru yay mata bai sake tankawa ba, bai kuma yanke wayarba.
Itama sai tai shirun tunda kuɗinsa akeci. Ƙitt ya yanke kiran ba tare da ya kuma cewa komaiba.
Itama saita harari wayar ta koma cikin ƴan uwanta.
*WASHE GARI ALHAMIS* akai kamun amare har Ummukulsoom, da safe sukaje wankin kai da ƙunshi su duka ukun har Aziza, sai yamma lis suka dawo aka shiga taron kamu da akai a gidan Hajiya yaya.
Babu wata hayaniya dan iya dangine na kusa suka zo kasan cewar auren duk tuwona maina ne.
Abin ya kayatar sosai dan matane kawai a wajen, akaɗan sha kiɗan ƙwarya kowa ya kama gabansa zuwa magriba.
JUMA'A bayan tasowa massalaci aka ɗaura auren Aziza da Zaid, sai Bilkisu da angonta Muhseen, a masallaci ɗaya aka haɗa dan kar a wahal da mutane, shiyyasa abun ya kayatar matuƙa,anguna sunsha ƙyau abin har ba'a magana.
Hakama amare su Ummukulsoom dake a cikin gida. Zuwa yamma aka cigaba da shan karasun biki da Ummi ta shirya.
Gaba ɗaya sai Ummukulsoom ta samu kanta da zubar hawaye, dan taji ana cewa yau ɗin za'a miƙa kowacce ɗakinta.
Can bayan ɗakunan maman Ahmad sukaje ita da Bily suka haɗa kai sunata kuka ita da Bily, Peace da sukazo bikin da ƴan uwanta da Mom nasu tana zaune tana musu dariya, sai da ta fuskanci da gaske fa sukeyi saita koma lallashinsu, rayuwar hausawa na birgeta, inda sune amarya tata ɓarar da rashin kunya kenan da taɓara ita a dole ana bikinta, amma jiba su Ummukulsoom yanda suka shiga damuwa, sam babu wani rawar kai a tattare dasu kuma.
Ana fitowa daga sallar magriba akace su shirya, duk sai suka rikice, sai da maman Ahmad taita lallashinsu sannan suka kimtsa, an miƙasu falon Abba inda baban Ummukulsoom da Dad da Hajiya yaya, gwaggo hinde, Inna laraba da yayyen Ummi ke zaune, daga Ummukulsoom har Bily fuskarsu a rufe take suna sharar ƙwalla.
Bayan an fara saka musu albarka aka ɗora da faɗan bin miji da kiyaye dokonin ALLAH, aka koma kuma nasiha, kowa saida yay musu tashi a taƙaice kafin Abba ya dankama kowaccensu ƙyautar key ɗin mota yana haɗiye ƙwallarsa da ƙyar, bai taɓa aurar da mace ba sai yau, shiyyasa duk sai ya damu, ƙarfin hali kawai yakeyi. Ummi kam kasa dairewa tayi saida ta share hawaye.
Ana idar da Sallar isha'i aka kwashi amare bayan an caɓa musu kwalliya, za'a fara zuwa wajen Mothers day ɗinne, daga nan kowanne ango ya ɗau amaryarsa.
Sai dai fa su Ummukulsoom basu san da wannan shirin ba, ganin anmusu kwalliyar zuwa wajen taron sai suka ɗauka ko an fasa kaisu yau, dan haka daɗi ya kamasu sosai.........✍🏻
NO. 46
............Sun isa wajen Mothers event ɗin daya gama ƙawatuwa, duk wanda ya kamata ya hallara ya iso, dama amare kawai ake jira, hatta da anguna sun iso, Muhsin da Zaid ma na tsaye a jikin mota, suna baza idon isowar amare.
Amaan kam yana cikin mota bai fitoba, lap-top akan cinyarsa da alama aiki yakeyi, dan Attahir ne a gefensa da takardu a hannu shima. Sai Abbas daya tuƙosa yana daga waje ya rufe musu ƙofar tare da kunna musu AC.
Bayan an fito dasu Ummukulsoom daga mota kowacce na walwali da ƙyalƙyalin amarci Aunty Nurse ta ƙarasa ga motar su Amaan tai knocking glass ɗin motar.
Attahir ne kawai ya kalli wajen, yasa hannu ya sauke glass ɗin.
Aunty Nurse tai murmushi tana faɗin Yaya Attahir amarefa sun iso, Yaa Amaan ake jira”.
Dukda yajisu bai ɗagoba, sai da Attahir ya zunguresa yana faɗin, “Wai Ajiwa bakaji bane? Amaryafa sun iso”.
Numfashi ya sauke tare da ɗago manyan idanunsa farare tas ya kalli Attahir ɗin, baice komaiba ya ɗauke kansa kuma, lap-top ɗin ya ajiye gefe bayan ya kashe.
Aunty Nurse ce dake riƙe da hannun Ummukulsoom ta zagaya gefensa ta buɗe masa.
Fita Attahir yayi, shikuma ya ɗauki hularsa ya saka yana gyara zamanta da kallon kansa ta mirror ɗin gaban motar, sosai ta ƙara masa wani kwarjini na musamman da fitowarsa asalin bahaushe haihuwar arewa. ƙafarsa dake sanye da takalmi cyan color sau ciki ya fara zirowa a hankali, sai kuma ya fito gaba ɗayansa yana shaƙar iska mai haɗe da ƙamshin khumrar da aka zazzagama Ummukulsoom ajiki itada bily mai saka nutsuwa ga mai shaƙa, ya lumshe ido ya buɗe a kanta.
“Oh god” ya faɗa akan laɓɓansa yana binta da wani kallo ƙasan ido. Itama ɗin a kaikaice take kallonsa, Shaddace gizna da taji ɗinkin babbar riga ta zamani, dan iyakarta gwuywarsa, komai na jikinsa cyan color ne, agogonsa ne kawai ya kasance na azurfa. Fuskar dai babu walwala sam, amma kuma bai ɗaureta tamau ɗinnan ba........
Tattausan hannunsa daya zura cikin nata ne ya katse tunaninta, ya kuma damƙe hannun nata cikin nasa saboda wani santsi da laushi da yaji yanayi, gaba ɗaya ƙamshin turarenta ya saukar masa da wata irin kasala mai tsaida gudun jinin jiki, sai faman haɗiyar yawunsa daya tsinke yake da sauri-sauri.
Saida Attahir yay musu maganar suje saboda sauran angunan sun shige da amarensu, kasantuwarsa babba garesu yasa sukai gaba, dan bai dace ya jera dasu ba.
Ɗan juyowa yay ya kalli Ummukhoolsum da itama jikinta yay sanyi ƙalau, kanta a ƙasa bata kallon kowa, janyewa yay yana sauke ɓoyayyar ajiyar zuciya, da ƙyar ya iya cira ƙafarsa sukai gaba, taku suke a hankali tamkar masu tsoron taka ƙasar, masu wayoyi a hannu sai ɗaukarsu hoto suke har suka shiga cikin hall ɗin da mutane ke cike harda ƴan ɗilau.
Sun burge kowa, kamar yanda sauran anguna da amarenma suka burge mutane, kujerar su guda ɗaya dake a tsakiyyarsu bily sukaje suka zauna. Ƙiri da muzu Amaan yaki sakin hannun Ummukulsoom, sai faman murzashi yakeyi a nasa a hankali, wanda hakan ba karamin kasala da tashin tsigar jiki yake sakama Ummukulsoom ba, ta gwada ƙwace hannunta yafi sau uku amma yaƙi saki, saima kuma damƙewa da yakeyi sosai.
Yanzunma da zasu zauna taso janyewa ya kuma damƙe kayansa sosai.
Babu yanda ta iya, dole ta ƙyalesa suka zauna akujerar, basu matsuba, amma spece ɗin dake a tsakaninsu bashida wani yawa, dan da waninsu zaiyi zaman da zai buɗe sosai dolene su gogi jikin juna. Yanzu kam kasa jurar salon da yake murza hannun tayi, ta ɗago manyan idanunta tana kallonsa da ƙunƙuni. Sarai ya jita, amma saiya basar kamar baisan tanayiba. sosai Ummu ta ƙulu da haushi, cikin salon muguntar da shi kansa baisan ta ƙwareba tasa ɗayan hannunta ta danƙara masa mintsini a gefen hannun.
Juyowa yay ya kalleta tare da sakar mata hannu yana wani yamutse fuska alamar tabbacin yaji zafi sosai.
“Ƙaramin gwalo Ummukulsoom tai masa tana ɗauke kanta”.
Murmushine yaso suɓuce masa, amma kuma saiya haɗiye kayansa ya fuske yana ɗauke kansa. Tasan tabbas saiya rama, dan haka duk motsinsa sai yazaman a kan idontane.
An fara buɗe taro da addu'a, kafin afara abinda ya tara mutane, Momcy tazo da kanta ta amshi Micrephone taima kowa godiya da halartar wannan taro, tareda fatan alkairin komawa gida lafiya, taja doguwar Addu'a ga amare da angwaye ta fatan kasancewa cikin aminci da zaman lafiya nahar abadan.
Kowa ya amsa da amin, Ummi ma tayi bayani mai birgewa, amma mafi yawansa akan Amaan da Ummukulsoom ne saboda kara da dattako irin nata. Daga nan Attahir ma yazo yay nasa.
Taro yaci gaba da gudana cikin aminci da kayatarwa.
Gaba ɗaya Amaan a takure yake da hayaniyar, hakama Ummukulsoom dauriya kawai takeyi, ga haushin Amaan ya isheta da jan tsaki. Cike da takaici ta kallesa tana faɗin, “Kai jama'a, nikam gaskiya an isheni da tsaki”.
Yasan dashi take, amma saiya share tamkarma baijita ba, saida yaja wasu mintuna ita harma ta manta ta takali faɗan, sannan ya juyo ya kalleta, baiyi magana ba, sai hannunsa daya saƙala ta bayan ƙugunta.....
A matuƙar firgice Ummukulsoom ta kallesa, dukta rikice tana waige-waigen ko mutane na kallonsu, wannan rashin kunya har ina?.
“Sake faɗa naji?” yay maganar a hankali cikin kunnenta.
Hannu takai zata turo kansa ya riƙe ɗayan hannun, “Wlhy zakija na baki kunya gabansu Ummi babu ruwana ni”.
Janye hannun tayi tana son muskutawa sai dai iyakar maƙurar kujerar kenan.
“Kin ceci kanki” ya sake faɗa a hankali yana sakinta ya koma yanda yake ya sake zama.
Numfashi Ummu ta sauke a hankali tana hamdala ga Ubangiji da girmama rashin ta ido irinna Amaan, ta tabbata komai yazo masa kai zai iya mata, shikuma ya basar abinsa............
Kururuwan da mc yakeyi ta kiran Buhayyah da Zaid ce ta maidota hayyacinta. Buhayya da Zaid suka mike suna kallon juna da murmushi, dan sunsan misuka shirya.
Suna fitowa cikin fili MC ya miƙama Zaid Micrephone yana faɗin, “Ango Zaid ya fito filine ba'a matsayin angoba yanzu, shida Buhayyah sun fitone zasu bamu nishaɗi domin farin cikin babban yaya *Lieutenant Colonel Usman Ajiwa da Amaryarsa Barrister Ummukulsoom*, dan haka muna buƙatar ganin babban yaya a filin nan tareda Amarya Brr.. Ummukulsoom”.
Tafi gaba ɗaya Hall ɗin ya ɗauka.
Amaan da duk yakeji kamar ya gudu ya kalli Ummukulsoom saboda alamar ya tashi da Momcy tai masa daga inda take zaune, hannunsa ya sake saƙalawa a nata suka miƙe tare. A hankali suka taku suka fito tskkiyar filin, Ummu ta zare hannunta a hankali dan bataso yacema zasu tsaya a haka, shima sai bai hanata ba ya saki hannun yana kallonta ƙasa-ƙasa, sosai Miss Green ɗin riga da zanin sukai mata ƙyau, ga mayen ƙamshinta da yay tasiri a kowanne fitar numfashinsa.
Da hannu Zaid yayma DJ magana alamar ya saki sauti.
Dj yay masa jinjina yana sakin waƙar Umar m shariff ta *Burin so*
A hankali Zaid ya fara taku yayinda sauti. yafara kaɗawa, kafin ya nuna Buhayyah yana bin Umar cikin ƙwarewa na fitar kowanne lafazi.
*“Kin haɗu ƴammata, kinji manufata, soyayya nazo kibani ki maidani ɗan gata! Kin haɗu ƴammata, kinji manufata, soyayya nazo kibani ki maidani ɗan gata”*
🎷🎷🎷🎸🎸🎸🎼🎼🎼
Buhayyah dake wani yamutse fuska ta hau takawa a hankali tana zagayawa saitin Ummukulsoom Zaid na binta a baya da cigaba da rairo waƙarsa.
_Baniyin ƙarya lokaci ɗayya sanki yaymini mamaya._
_kirani na shirya gani kan hanya gunki zanzo da soyayya._
_Saƙo na zuciya baniyin ɓuya zani nunawa duniya._
_Nasako kaya naci kwalliya na tahone mu gauraya_.
_Kenake kallo, hasken ki ya ɓillo, ya saka naita zillo ke zakimini gata._
*Kin haɗu ƴammata, kinji manufata, soyayya nazo kibani ki maidani ɗan gata! Kin haɗu ƴammata, kinji manufata, soyayya nazo kibani ki maidani ɗan gata*
🎷🎸🎼🎼🎼🎼
Ya ƙare baitin da komawa bayan yaya Amaan ya maƙale a zuwan dai shine shi😂, ya ɗan tako zuwa gaban Ummukulsoom da Buhayyah yana zagayesu da cigaba da faɗin,
_Dana nufo gunki kin kauce, zuciya tawa kin sace, inda zaki soni kin dace, ruwan zuma ungo zaƙice, kina cikin raina, safiya dare rana, kona mace babu raina, da sonki zani ƙwanta._
🎷🎷🎸🎷🎷🎼🎼
Lumshe idanu Amaan yayi a hankali yanajin wani irin yanayi a ransa, shi idanma su Zaid da wasa sukai toshifa har cikin ƙasan ransa yakejin waƙar, baitin da Buhayyah ta karɓa cike da salon yanga tana bayan Ummukulsoom kamar yanda Zaid yake bayansa makale ne ya dawo dashi hayyacinsa yana kafe Ummukulsoom dake murmushi da ido.
_Ɗan matsa baya, kaji ɗan ƙarya na wucema a tarayya, bakajin kunya ka taho gaya ni kake cema soyayya, ka farama ɓuya ko a kan hanya baniso daina bibiya, na shige ƙurya kai kana baya karkasa nai ash......(Buhayyah ta dafe baki bata ƙarsa ba), ƙwarya tabi ƙwarya, gaye cire ƙarya, dai-dai da kai jeku shirya ni nayimaka rata._
🎷🎷🎸🎼🎼🎷🎷🎷
Atare suka ɗago ido wajen satar kallon juna sai caraf suka shige cijin na juna, gira ɗaya ya ɗaga mata alamar wai “Niɗin?” itama cikin salonta ta maida masa murtani wai “Eh”. Lallausan murmushin da bai shiryaba ya saki yana maida hankalinsa gasu Zaid dake zagayesu suna cigaba da rairo Baiti.
_Ohhh kin haɗu, ni nace kin haɗu, kin haɗu! Kin haɗu! Kin haɗu ƴammata._
_Kin haɗu ƴammata, ni dai kinji manufata, soyayya nazo ki bani ki maidani ɗan gatahhh._
🎷🎷🎷🎸🎷🎷🎸🎼🎼
Nuna Ummu da Amaan yayi yay dai-dai da faɗin *_Ki mai dani ɗan gatahhhh_*.
Gaba ɗaya hall ɗin ya ɗauki ihu, Momcy ta fara tasowa tana zuba musu liƙi suda su yaya zaid, su Aziza da Muhsen da Bily ma suka taso aka saki sabuwar waƙar da Aunty Ummy yayar Amaan tasa akai musu.
Cikin raɗa Momcy data matso kusa da yaya Amaan tace, “My dear Fodio adinga murmushi, yaufa ɗin ta musamman ce”.
Murmushin ya sakar mata ba tare daya shiryaba, itama sai tayi tana rungumo Ummukulsoom jikinta.
Haka taro ya gudana cikin farin ciki da birgewa, zuwa 11pm aka tashi.
⚡⚡⚡⚡⚡⚡⚡⚡⚡⚡⚡
Asibitin gidan gwamnati aka wuce da Meenal dake a sume, Basiru