Showing 6001 words to 9000 words out of 176055 words
Tunda ta ɗaura ido akansa ta rikice, dan Baseer cikakken namijine abun so ga kowacce mace, yazama handsome na gaske, ga ƙyau ga tsafta da ilimi, gashi ALLAH yayisa irin mutanennan masu shegen alfahari da taƙama, idan kaga yanda yake yarfa ƴanmata dawani ɗaukar kai saika ɗauka wani ɗan mashahurin attajirine ko mai mulki a Nigeria, bazaka taɓa yarda ya fito daga ƙungurmin ƙauyen Ɗilau baneba.
Ita kanta Suhaila kallon irinta ƴaƴan masu kuɗi tamasa da farko, musamman yanda taga ƴaƴan manya da ƴanmata masu aji na makarantar dake naniƙe masa yana yarfasu, sannan abokansa duk ƴaƴan manyane, kwata-kwata baya harka da talaka irinsa, nunawama yake yafi ƙarfin saninsu.
Abinda yake ƙarama Baseer girma da kima a idanun jama'a shine basirar karatu, ba ƙaramin ƙwaro baneba wajen brain, wannan shine sanadin dayasa ƴaƴan manya ke nane dashi.
Dukda son Baseer ya mamaye zuciyar Suhaila sai bata tunkareshiba kai tsaye tamkar yanda sauran ƴan matan ke masa, saima suka ƙulla ƴar tsama, data gansa saita shiga tofar da yawu da yatsine-yatsine tamkar taga kashi, kokuma ta bula masa ƙurar motarta.
Tun abun baya damunsa harya fara sakashi takaici, yanda ake girmamashi a makarantar da jan mata dayake a ƙasa saboda kyawunsa ace wannan yarinyar tazo tana masa wannan cin kashin?.
Sai Baseer yafara biyema Suhaila kulum suna cikin faɗa da juna da jifan junansu da baƙaƙen magana. Ahankali sai faɗan nasu yafara komawa shaƙuwa, daganan sai soyayya.
Jama'ar makaranta sai dai suka wayi gari sukaga Baseer da Suhaima abokan faɗan juna sun ɗinke sun koma masoya............✍🏻
3
...........Yau akaima su Ummukulsoom busting amma ko alamar Baseer ɗinta bata ganiba, sai baba ne yazo mata shi da Inna Laraba, tayi farin ciki da ganinsu tamkar yanda ta saba.
Baba kasa haƙuri yayi ya tambayeta ina basiru?, dan yasaba duk zuwan da zasuyi anan suke iskeshi ya rigasu zuwa.
Kan Ummu a ƙasa tace, “Baba bai zoba”.
Baba yay Murmushi idonsa a kanta, “Karki damu Ummukulsoom, zata iya yuwuwa wani uzurine ya hanashi zuwan, yaron yanada himma, tunda aka kawoki makarantar nan yake ɗawainiya da zuwa dubaki duk bizitin, dukda kuwa shima cikin hidimar nasa karatun yake”.
Kafin Ummu tace komai Inna laraba ta karɓe da faɗin, “Ai basiru yaron kirkine, ga hankali, banyi zaton zai riƙe alƙawari irin hakaba, musamman yanda naga ya canja yanzu yazama ɗan birni na sosai, ga tsoron zantukan jama'ar ɗilau akan alaƙarsa da Ummu, kowa faɗi yake yafi ƙarfinta yanzu”.
Dariya Ummu da Baba suka sanya saboda furucin Inna Laraba da tace yazama ɗan birni, furucinta na ƙarshe kuma yasaka zuciyarsu harbuwa, ita kanta Ummu maganar na damunta, tana dannewane kawai dataga babu wani canji daga Baseer ɗin har yanzu..
Bayan tafiyarsu duk sai Ummukulsoom tashiga damuwa, dan dama a irin wannan lokacin idan sun tafi akan barta da Baseer ɗintane, sukuku tazama gaba ɗaya, daga ƙarshema saitai komawarta hostel, zuciyarta dai namata fatan ALLAH yasa lafiya ta hanashi zuwa, dan ita tafi zargin koma bayajin daɗine.
⚡⚡⚡⚡⚡
Soyayyar Suhaila tai bala'in ɗauke hankalin Baseer ya fara mantawa da wata Ummukulsoom, gidama yaƙi zuwa, ko waya sukayi da iyayensa sai yace karatune ya riƙeshi.
Soyayya ce mai ƙarfin gaske a tsakaninsu yanzu, abinma saiya baka matuƙar mamaki, zuwa yanzu kam tagama fahimtar shiba ɗan kowa bane, amma hakan baisa taji ta daina sonshiba, dan ƙyawunsa na ɗibarta matuƙa, aganinta shine miji na nunama sa'a, dan kuɗi ba matsalarta bane, zatabi hanyar da zata ginashi ya jiƙe kafin aurensu, yanda ƙawayenta zasuyi respecting nashi 100%.
Saima ta samu ƙwarin gwiwar buɗe bakin aljihu tashiga kashe masa kuɗi da masa bajinta tamkar hauka, kai kace itace saurayin shine budurwar, babu ɓata lokaci ta koya masa mota, kaya na ƴan ƙwalisa kam kullum cikin saya masa take, a kwana kaɗan yakuma zama handsome na gaske, ƙyawunsa da taƙamar girman kai takuma bayyana, dan Suhaila har barmasa motarta take wajensa ta kwana, ko an tambayeta a gidan tasan ƙaryar da zata shirma.
A karatunta sosai yake taimakonta, dukda 100L take, shikuma yana shekarar ƙarshe.
Daɗin da Baseer ke samu ga Suhailat yasashi kuma mantawa da Ummukulsoom gaba ɗaya balle alƙawarinsu ko soyayyarta, idanunsa sun rufe Suhailat kawai yake gani, ko yaushe suna nane da juna, sai dai idan ta tafi gida, shima zaka samesu suna charting ko waya.
Wannan ne yasa har akayi Busting ɗin su Ummukulsoom bai jeba, toshi gaba ɗayama ya manta da lamarinta.
Sai bayan busting ɗinne innarsa da yake zaune a wajenta ta matsa masa yaje ganin gida, dan ita lamarin Basiru tsoro yafara bata, gaba ɗaya ya canja, baƙin abubuwa idan ta ganshi dasu ta tambayesa saiyace saya yayi, maƙwafta harsun fara dangantashi da Homo saboda anga ya zama babban yaro dare ɗaya.
Hankalinta sai ya kuma tashi itada mijinta, dan sun rasa sana'ar ubanmi yake da yakema kansa hidimar kuɗi, sai daga bayane ta fuskanci mike faruwa shida Suhaila, hakanne yasata shiryawa taje ta zayyanema iyayensa komai gameda halin da yake ciki.
Hankalinsu yatashi akan Suhaila zata lalata musu yaro, hakkanne yasasu cewa ta turoshi gida.
Humm Baseer, shegiya naira inji ibro⛹♀😂.
⚡⚡⚡⚡⚡⚡⚡⚡
Ummukulsoom kam batasan mike faruwaba, tananan maƙale da son Baseer ɗinta, burinta tagama jarawarnan dake gabanta ta ssce ta koma gida suyi aurensu, ko wani takaicin ya isheta data tunoshi saitaji zuciyarta tayi sanyi, farin ciki ya ziyarceta. Babbar damuwarta da tasan bazasu sake zuwa hutu gidaba sai sun kammala gaba ɗaya, fatanta ALLAH yasa ya ziyarceta ta tabbatar da lafiyarsa ƙalau dai itakam.
Wannan damuwar datanemi sakama kanta sai taso taɓa karatunta, sai da ƙawarta Hafiza isa ta zaunar da ita taimata nasiha, da nuna mata muhimmancin wannan lokacin da suke ciki, bai kamata suyi wasa da damarsuba akan abinda zaune yake yana jiransu, itako jarabawar ta taƙaitaccen lokacice.
Wannan bayani yasaka zuciyar Ummu saisaita, ta nutsu waje ɗaya domin fuskantar jarabawar dake gabansu tareda fatan nasara, dan tasan maganar Hafiza gaskiyace, auren Basheer nacan na jiranta, wannan kuwa lokaci kaɗan za'ayi a gama, kuma ya wuce kenan.
⚡⚡⚡⚡⚡⚡⚡
Lokacin da Baseer yaje gida jama'a da yawa sunsha mamakin canjawar daya kumayi, gashi yanzu yawani ɗaurama kansa girman kai ba kowa yake kulawaba, gashi yazo a dalleliyar motar Suhailat kuma data bashi aro, hakanne yasa magana keta yawo agari Baseer yayi kuɗi yana ƙyamar ƴan garin.
Ran iyayensa a ɓace suka shiga masa faɗa akan rayuwar daya ɗaura kansa a yanzu bamai ɓullewa baceba, inashi ina ɗiyan birni ƴar masu kuɗi, ai *WUTSIYAR RAƘUMI TAI NESA DA ƘASA!*, shidama ga matarsa nan na jiransa.
A razane ya ɗago idanu yana kallon mahaifan nasa, “Baba matata kuma? Yaushe akaimin aure ban saniba?”.
Harara mahaifiyarsa ta danƙara masa, tareda masa daƙƙuwa, “Basiru kaci gidanku dan ƙaniyarka, koba a ɗaura maka aure da Ummukulsoom ba ai kasan akwai maganarka da ita a ƙasa ko”.
Taɓɗijan, shifa saima yanzu da suka ambaci sunan Ummu yatuna da itama, yagaji da jan maganar da faɗan da iyayensa suke masa, dan haka yaɗan murmusa yana miƙewa, “To ai indai maganar Ummukulsoom ce kumabar wahal da kanku inna, tananan ko, badai kun ajiye magana da iyayentaba?”.
“To ina kuma zaka?”.
“Baba zan zagaya bayine mana”.
Tunda Basiru yabar wajen sai inna ta riƙe baki da sallalami, baban Talatu anya kuwa yarinyarnan tabar yaronnan hakannan?”.
“To mizatai masa? Shashancine kawai irin nasa da ƙuruciya, kana ɗan ƙauye irin ɗilau, talaka fitik inakai ina ƴar masu kuɗi ƴar birni? wannan yana ɗaya daga cikin abinda ke tsoratar da irinmu ƴan ƙauye barin yara suyi karatu, dasunje can idonsu ya buɗe saisu kwashi duniya da faɗi, dukda dai bakowa ke koyo banzan halinnan ba na mutanen birni, amma nasan maganinsa ai, ƙwanannan zanje mu tsaida magana da malam Buhari, bazan yarda ya maidani ƙaramin mutunba”.
“A wlhy ina bayanka baban talatu, gara dai kam a tsaida magana tunda dai dagashi har ita sunkusa kammala karatunma, ai halaccin da waɗannan mutane sukai mana baici ai musu wannan sakayyarba”.
“To ALLAH dai ya kyauta, ni bara naje nan gonar bakin tafki na ida kai takinnan, garinnan gab yake da saukar ruwan damuna, yanayi nata ƙara canjawa”.
“To saika dawo, garikam ai yanata harama”.
Baseer duk yana jinsu, babu abinda yake ayyanawa a ransa sai tayaya zai yakice wannan banzan auren ya huta, ina mai zankaɗeɗiyar yarinya irin Suhaila, ga kuɗi ga ƙyawu zai yarda a ƙaƙaba masa wata baƙauya wadda iyakarta secondary, shima da ƙyar ta harhaɗa, shifa saima yanzu ya fahimci bason Ummukulsoom yakeba, tausayinta kawai yakeyi dama can, rashin wayewar kaine da sanin menene soyayya ya hanashi fahimta. Amma yanzu kar yake kallon komai, degree fa zai haɗa, abinda kaf ƙauyen ɗilau wani bai taɓa yiba saishi, ai dolene ya kuma jama kansa girma a ƙauyennan, jama'r ciki su ƙara fahimtar *WUTSIYAR RAƘUMI TAI NESA DA ƘASA!* tsakaninshi dasu fa yanzu.
Hummm.🚶🏻♀☹
⚡⚡⚡⚡⚡⚡⚡
Su Ummukhoolsum na gab da gama jarabawa aka kai kuɗin aurenta daga gidan su Basiru batareda shi yasan hakanba, sosai Malam Buhari yaji matukar daɗi da farin ciki, yayinda zuciyar matansa kamar tayi bindiga dan baƙin ciki, koda wasa basa fatan Basiru ya auri Ummukulsoom, babban burinsuma tadawo da ciki.
Koda malam Buhari ya fahimci hassada ƙarara a fuskokinsu baice komaiba sai girgiza kai da nema musu shirya, baisan mi Ummukulsoom ta tare musuba a gidan da a kullum basa ƙaunar cigabanta, saikace wata sa'arsu ko kishiyarsu.
Ba wai ranar aurenta da Baseer aka tsaidaba, sundai kawo kuɗin gaisuwa domin su tabbatar har yanzufa suna nan, sun ajiye magana bayan dawowar Ummu da kammala karatun Baseer nanda wata biyar sai a tsaida ranar aure kai tsaye.
Shidai Baseer da baisan hidimar da akeba kwannasa biyu ya tattara ya koma saboda zasu fara exam shima..
⚡⚡⚡⚡⚡⚡⚡⚡
Rayuwa ta cigaba da turawa cikin aminci, Yayinda su Ummu keta zana jarabawa, zuciyarta kuma na maƙale dason Baseer ɗinta, saboda son faranta masama taketa ƙoƙarin ganin tayi abun arziƙi.
Hakama Baseer sunata exam, soyayyarsa da Suhaila nata ƙara ƙarfi, ahankali har sunansa da hotunansa sun baje gidansu Suhaila, sai dai ta ɓoye musu shiba ɗan kowa baneba.
Koda yayartama taga hotonsa saita rikice da koɗashi tana tambayar Suhailat ɗan wanene a ƙasarnan?.
Dariya kawai Suhailat tayi, tana faɗin “madam kedai kiga photo kawai, baruwanki da ko ɗan wanene, idan kuma ƴar bayan katanga kike shirin minfa”.
Dariya Amrah tayi tana dukan kafaɗar, Suhailat da faɗin, “Banza kawai, ɓarauniyar saurayi kika maidanima ashe?”.
Kwashewa sukai da dariya har mom nasu dake gefe tana saurarensu.
Suhailat tace, “To ai duniyarce yanzu saida tsaro”.
⚡⚡⚡⚡⚡⚡⚡⚡
Komai kaga farkomshi to yanada ƙarshe, a yau ne su Ummu suka kammala jarabawarsu, kowannensu kagani yana cikin farin cikin gamawarsu da baƙin cikin rabuwa da juna, sunata musayar lambobi da adireshi.
Itadai Ummu number wayar baba taita badawa, sannan kanta tsaye take bada address ɗin garinsu, aganinta minene abin ɓoyewa, tushenta shine abin alfaharinta koda kuwa gidansune kawai a ƙungurmin daji, shiyyasa take mamakin wasu ɗaliban dakan zauna suyita sharara ƙarya gidansu kaza da kaza, to randa ALLAH ya ƙaddara zuwan wani kuma yaga ba haka bane sai kaji kunya kenan?.
Haka dai sukaita sallama da juna har lokacin zuwan baba da yazo ɗaukarta. Ta ƙarasa bankwana ga waɗanda basu tafiba, suka kamo hanyar gida tanata kuka baba na lallashinta.
Bayan sun iso gida taɗan samu tarbar arziƙi darajar suna tare da baba, ko kaɗan yanzu lamarinsu baya damunta, aganinta ma sun cancanci uzuri.
Tana samu taci abinci tai wanka saita fice gidan zuwa gidan kakanninta, gwaggo Hinde taji daɗin ganin Ummu, sai godiya takema ALLAH tana ƙari, “ALLAH nagode maka da wannan boko na Umma ya ƙare, kema kizo kiyi aurenki mu huta da surutun jama'ar garinnan, gashinan su Azima harda yaransu bibbiyu, Ramatu da Atine ma cikin na ukune dasu”.
Murmushi Ummu dake cin gyaɗar da Gwaggo Hinde ke saidawa tayi, sannan tace, “Ohni Gwaggo, irin wannan murna haka, to ai konayi auren nasan Basiru zai barni naciga da bokon, dannifa insha ALLAH saina zama lauya”.
Galala Gwaggo Hinde tayi da baki har zaninta na neman kwancewa, ta tattaro abinta ta ɗaure tana ajiye kwanon shanruwan hannunta da zata damawa Ummu fura, “Kekuwa Umma anyi lalatacciyar yarinya, yo banda shegantaka miye kuma abin birgewa a bokon? Inama laifin abinda kika samu? Kaf garinan fa dagake sai ƴaƴan maigarine kuka gama wannan bokon, ke da ALLAH can ki maida hankalinki ga gidanan an fara gina miki a faƙon amare”.
“O ni kuji Gwaggo, to waya faɗa miki shi karatu ana gamashi, ilimi ai kogine, sannan damai neman arziƙi da ilimi bakiji ance basa ƙoshiba? Kuma dan nayi aure sai akace bazan nema ilimin addini dana zamaniba? Haka zamuyita zama babu wani cigaba a garinmu? Nasan Baseeru zaiyi farin ciki da burina shima?”.
Baki Gwaggo Hinde ta taɓe tareda faɗin, “Ke kikaga zaki iya keda Basirun, shima gashinan anata surutu agari yayi kuɗi yana wulaƙanta mutane, wannanfa karon dayazo amotafa yazo garinan dalleliyama kuwa”.
“Mota kuma Gwaggo? To shi dake karatu ina kuma ya samu mota?”.
“Ina zan sani nikuwa, wasu mutanenma marasa tawakkali harsun fara cewa yankan kai ya fara”.
Babu shiri Ummu ta kwashe da dariya, haka tashiga dariya ba ƙaƙƙautawa, saida Gwaggo ta ɗauki abu ta bugeta dashi sannan ta tsagaita daƙyar, “Kai Gwaggo wlhy dolene aringa cemana gidadawa mu ƴan ƙauye, shikenan wai da mutum yayi arziƙi sai ace yankan kai yakeyi? Toku wama yace muku wai ana yankan kai ɗin da gaskene?”.
“To Umma ai karkiga laifinmu, mi muka sani da duniya ke ciki?, duk wani abu da zamani yazo dashi mutumin ƙauye sai yaje birni yake ganinsa, idan antashi zaɓen shugabanni da mutanen ƙauye akeyi, amma dasun ɗare madafun iko saikiga bazasu kuma tunawa akwai wasu masu numfashi a jejina ba, duba kigafa wutar lantarki ta gagari ƙauyennan, masu waya kullum suna hanyar zuwa Kudan kai caji, saima kwanannan ne akace balarabe jikan tasalla yasayo injin wuta (Genretor) yafara cajin dashi, kuma waya ɗaya wai Murtala guda, yo inba sana'a kakeba kullum ina zaka ɗauki Murtala (20) guda ka miƙa wai dan kawai aimaka caji”.
Cikin sanyin Murya da takaici Ummu tace, “Gwaggo ai duk irin waɗannan abubuwan muke dubawa mu dage sai munyi karatun, girman ƙauyennan bai dace ace irin waɗannan cigaban bamu dashiba, ba wuta, babu hanya mai ƙyau, idan ka hawo mashin zaka shigo garinnan ko zaka fita hanjin cikinka tamkar zasu zazzago dan gwazazzabai, ga talauci ya addabemu, ƴar makarantarnan ta gaba da primary ankasa mana, kullum saimunje cikin Kudan, wlhy da ace za'ayi secondary a garinnan iyaye dayawa zasu samu kwanciyar hankalin saka ƴaƴansu karatu, mufa yandama kikasan ba'a ƙasarnan mukeba, kuma mafi yawan ƙauyukan Nageria suna fuskantar waɗannan matsalolin, shiyyasa wani lokacin bancika ganin laifin shugabanni ba, saboda wasu sun fito daga ƙauyukane, suntashi babu mai taimaka musu abaya, shiyyasa dasun sami madafin iko suma saisu fara tsula tsiya da riƙo da kalmarnan ta malam bahaushe *Wutsiyar raƙumi tai nesa da ƙasa*, gwaggo mu kanmu talakawan mun kasa gyara jiyanmu, tayaya muke tunanun shugabanni zasu gyara mana yau ɗinmu, ƙananan yara irinmu masu tasowa mu amfanu da gobenmu jibi tazama ta ƙanenmu, kowa yazo burinsa yayi ɓarnar datafi ta ɗan uwansa”.
”Wlhy hakane Umma, shiyyasa wataran kike birgeni akwai zancen hankali idan kinso”.
Dariya Ummu tayi tana kwanciya a gadon Gwaggo Hinde, “to nidai bara na miƙe a gadon ƴan gayunki Gwaggo karki tadani sai dare, dan ni yauma anan zan kwana”.
“To kihuta lafiya”. ‘Gwaggo hinde ta faɗa danta kula Ummu na fashin salla ne’.
Bayan Ummu tasha barcinta ta tashine Gwaggo kemata bayani gameda kawo kuɗin gaisuwar aurenta da akayi daga gidansu Basiru, ance saisun kammala karatu za'a tsaida magana, to yanzu gashi ALLAH yakawo lokacin, tasan kuwa za'a tada maganar kenan.
Sosai Ummukulsoom taji daɗi, amma saita danne bata nuna a gaban Gwaggo ba, saima rufe fuska da taita famanyi najin kunya.
Saida taga Gwaggo tafita tsakar gidan taita jin daɗinta da godiya ga ALLAH itama takusa mallakar masoyinta cikar burinta a matsayin miji.
⚡⚡⚡⚡⚡⚡⚡⚡.