Showing 138001 words to 141000 words out of 176055 words

Chapter 47 - Wutsiyar Rakumi Book 1 Hausa Novel Complete

07 Jan 2025

870

kuwa station.
Cikin awa ɗaya ta dawo normal saboda taimakon gaggawa da aka bata, sambatun da take na zagin Basiru ya sakasu fahimtar bata cikin hayyacinta, allurar barci mai karfi sukai mata saboda fisge-fisge da takeyi tana riƙe wuya.
Hakanne ya sake hasala mahaifinta, sam shi dama yaronnan bai masaba, dan kawai baya son ɓatama Meenal rai ne ya yarda ta auresa, ashe matsiyacine, to aiko zai gane kurensa, dan saiya gwammaci inama bai taɓa sanin meenal ɗinba har alaƙar aure ta shiga tsakaninsu.

Sai dare Meenal ta farka, sai dai dukda ta farka a cikin hayyacinta hakan baisa zuciyar mahaifinta da ƴan uwanta ta sauka ba, kowa ji yake inama abashi basiru ya kawo ƙarshen numfashinsa.

★★★★★

A station kam duka sukaima Basiru na fitar hankali, kafin su watsashi bayan kanta shi kaɗai su garƙame ɗan banza.
Duk yanda ya jigata yake nishi da ƙyar babu wanda yaji tausayinsa, dama ya ishesu wani ɗan sanda cayay idan bai musu shiruba wlhy zaizo ya ƙara masa.

Tsitt basiru yayi, ya koma nishin a hankali, dan yasan inhar sukace zasu sake dukansa wlhy mutuwa zaiyi, ƙyaƙykyawar fuskarnan tashi dukta fita hayyacinta da duka, tayi suɓu-suɓu wane ƙwaɓin filawar fanke🥴, ga ƙafarsa ta dama kamarma sun ji masa ciwo a cikin ƙashi, dan nishi yake da ƙyar.

Kwana biyu da faruwar haka Meenal ta dawo dai-dai, basiru kuma dake station yana fama da ciwuka na jiki dana zuciya mahaifinta yay duk yanda zaiyi aka kwashi basiru zuwa prison, acewarsa bashi da lokacinsa yanzu sai randa ya shirya.
Wannan shine dalilin ɓatan Basiru ɓat a duniyar mutane.

Yayinda a gefe ɗaya su Suhailat ke cikin farin ciki, sun san dai sun kaishi ƙasa, aikinsu na gaba kuma yanzu suyita tunzura Meenal akan a kaishi court, ta wannan hanyarne haƙƙin iyayensu da yaci kuma zai fito da na ƴarsa ta wajen Lubna.

😳masoyan Basiru muna ruwa, xoxo a kawo ɗauki yayanki ya shiga jail🙊☹️😝😂⛹🏻‍♀️⛹🏻‍♀️⛹🏻‍♀️


⚡⚡⚡⚡⚡⚡⚡⚡⚡⚡⚡

Hankalin Ummukulsoom ya tashi ganin mota ɗaya zasu koma da Amaan yanzu, bama mota ɗayarne matsalarta ba, fatanta ALLAH yasa gidan Abba za'a koma.
Amma fa sam taƙi nuna tana cikin ruɗanu akan fuskarta, a zuciyarta ne duk take a wannan yanayin.

Motocin su Bily ne suka fara fita tare da waɗanda zasu ɗan mata rakkiya da kuma dangin mijinta da sukazo wajen Mothers event ɗin.
Sai nasu Aziza itada nata angon Zaid da gayyar ƴan ɗilau da wasu a cikin dangin Ummi.
Motar su Ummukulsoom ce ƙarshen tashi, wadda saida Amaan yagama bankwana da abokansu sannan ya shigo aka maida aka rufe.
Rumtse idanu Ummukulsoom tayi tana ɗauke kanta gefe tamkar batasan da zamansa ba. Sai da motar ta fito daga hotel ɗinne ya kalli tsakkiyarsu inda yabar lap-top ɗinsa. Idanu yaɗan fiddo a can ƙasan maƙoshi yana faɗin, “Ƴar lukutar Ummi system ɗitafa”.
Kamar zata shareshi sai kuma taɗan juyo ta kalli sashensa, tabbas tana ɗan jin rabin jikinta akan abu mai tauri, amma sam bata lura mita hauba. Da gaske lap-top ce kuwa, yasa hannu yaja abarsa yana shafawa cikin narke fuska tamkar wani ƙaramin yaro.
Baki ta taɓe tana kauda kai da faɗin “Taɓara”.
Duk da yajita sai yay shiru, danshi sam baya abunda zai zubar da mutuncinsa gaban yaransa ko ƙannensa, saboda Abbas ne kuma bazata samu amsaba.
Har suka iso gidan Dad babu wanda ya sake tankama ɗan uwansa a tsakaninsu, shi ya cigaba da aikinsa a lap-top ɗin ita kuma ta ɗauke kanta gaba ɗaya dagama sashensa.
Iya waɗanda zasu kwana a gidan kawai motocinsu suka shiga, duk wanda zasu juya gidan Abba kuwa a waje suka tsayar da motocinsu, kowa ya fito ya shigo cikin gidan da ƙafa.
Ƙanwar Ummi gwaggo Maryam da kanta ta fiddo Ummukulsoom a mota, Amaan kam saima ya sake gyara zama alamar bazai fitoba, yasan koya fito hayaniyace zata isheshi, wadda ya shawo a wajen fati din ma ta wadatar, dan yanzu haka kansa ciwo yake sai yasha magani.
Ganin bai fita ba Abbas ya kalleshi kaɗan, cike da ladabi yace, “Sir mun ƙaraso?”.
Kansa ya ɗago ya ɗan kalli Abbas ya ɗauke, cigaba yay da aikinsa a yana sauke ajiyar zuciya, da ƙyar yace, “Rufeni kaje a binka”.
“Ok Sir, a bar AC n?”. Kansa kawai ya ɗaga masa alamar eh, batare da ya buɗe baki ba.
Abbas yay masa duk yanda ya buƙata, sannan ya fice ya barsa shi kaɗai a motar, dama Attahir tun acan suka rabu, dan Ahmad yay barci, mamansa kuma bata da lokacinsu, shine kuma ya maida su Hajiya Yaya gida.

★★★★★

Sashen Yaa Amaan aka kai Ummukulsoom, komai an canjashi, dan kayan ɗakin da Abba yay musu kala bibbiyu itada Bily sai aka sakama Ummukulsoom ɗaya anan sashen Amaan na gidansu, ɗaya kuma aka wuce dasu legos tare da wanda Dad yay mata matsayin tasa gudunmawar.
Kayane ƴan gaske da suka ƙawata falon, dan har fenti an canja, sai ƙamshin sabon fenti da sabon katako sashen keyi, har cikin bedroom ɗinsa da komai yay ɗas aka kaita aka zaunar, hawaye take a cikin gyalen na takaicin zartowa da akai da ita gidansa yau, itafa dukma zatonta gidan Abba za'a maidata itama, sai zasu koma legos a ɗakkota, ashe ƙullalliyar da akai musu kenan, gashi ko sallama batai da Bily ba. Hawayene masu zafi suka kuma silalo mata a kumatu saboda jin harta fara kewar ƴar uwarta.
Ƴan rakkiya basufi mintuna goma sha biyarba kowa yay mata sallama ya fita akan sai sun dawo buɗar kai gobe idan ALLAH ya kaimu.
Maman Ahmad taɗan duko ta gwargwaɗa mata wani abu a kunne tare da dora mata Handbag ɗinta a cinya ta fita.

Cikin mintuna kalilan gidan yay tsit, waɗanda zasu kwana anan duk sun shige sashen Momcy, dama duk ƴan Ajiwa ne ma, sai ƙannen Momcy da ƴan uwanta ƙalilan.

Aneesa ce kawai a sashen Ummukulsoom, itama tana ɗanyin Morping ɗin inda aka tattaka ya ɓaci ne, dan tasan mai sashen ya tsani ƙazanta, inma basu gyara ba kafin ya shigo to ko sunyi barcine saiya saka an tadosu sun gyara, kokuma ya kare akan Buhayyah. Sai da ta gyara komai fes ta saka turaren wuta saboda akwai wutar Gen.. Da aka kunna sannan ta fito tanama Ummukulsoom dake zaune har yanzu tana ƙwalla sai da safe.
Tashi Ummukulsoom tai taje ta sakama ƙofar key tana hararta, dan bataso yace zai wani shigo mata, sai kace ƙofarce Amaan.
Har aranta tasan bai daceba, amma fa ita bazata yarda yama ce zai zo su kwana ɗaki ɗaya ba, sai dai yaje sashen su Bassam ya kwana, dan bazata kwana ɗaki ɗaya da ƙaton gardi ba............✍🏻


Babu ruwana Ummukulsoom ce tace *ƙaton gardi*, karna sha suburbuɗa wajen ƴan Team ɗin Amaan 😝😂.


NO. 47

.............Aunty Ummy ce tai Knocking glass ɗin motar da Yaa Amaan ke ciki har yanzu yanata aikinsa hankali kwance, gefe ɗaya raɓar AC na ratsa sa.
Saida yaja wasu seconds kafin ya ɗago manyan idanunsa yana kuma ɗan ɓata fuska ya sauke glass ɗin a hankali.
Aunty Ummy dake tsaye ta ranƙwafo tana faɗin, “Angon nan kodai ɗaukarka zamuyi mu kaika?”.
Guntun murmushi yayi kaɗan yana buɗe murfin da faɗin, “Uhm-Uhm Aunty, zanma kai kaina ne, dan nafiku zumuɗi, nabaku dama ku gama nakune”..
Dariya sosai tayi ita da aunty Nurse dake bayanta, a ransu suna mamakin irin wannan dogon sharhi haka tamkar ba shiba.
Shikam tuni ya basar kamar bashine yay maganarba, aunty Nurse ta karɓi kayan hannunsa daya tattaro a motar, bata yayi babu musu. Gaba yay suna binsa a baya, Aunty Nurse da aunty Ummy na tsokanarsa suna ƴar dariya.
Uffan baicema kowannensu ba har suka isa ƙofar sashensa, juyowa yay ya amshi kayansa a hannun aunty Nurse yana musu alamar sai da safe da hannu.
Basu ja zancenba suka juya shi kuma ya murɗa ƙofar ya shiga da sallama a ƙasan maƙoshi.
Sosai ƙamshin turaren da aka saka ya tasiri a ransa, ya shaƙa ya lumshe idanunsa tare da takawa cikin falon sosai ya ajiye kayan hannunsa a kujerar farko.
Babbar rigarsa ya zare, ya bar ƴar ciki kawai da wandon, dama hular a hannu ya shigo da kayansa, hannayensa duka yasa a ƙugu yana bin ko ina na falon da kallo, komai ya masa ƙyau tamkar shiya zaɓa, ya sauke idanunsa akan ƙofar bedroom ɗinsa yana ƙiyasta yanda zasu kwashe da ƙwailarsa (Ummu team bani na faɗaba Yaa Amaan ne kuma😂😝⛹🏻‍♀️).
A hankali ya taka zuwa ga ƙofar, ya kama handle ɗin ya murɗa sai yaji gam a lamar a kulle take. Wani lallausan murmushi ya suɓuce masa yana girgiza kansa da kai hannu ya shafi girarsa. Hannunsa ya janye daga handle ɗin ya zubasu a aljihu gaba ɗaya, tsaye yay ya zubama ƙofar ido yana nazari. tsawon mintuna uku kafin ya sauke numfashi ya tako zuwa cikin falon.
Zamansa yay cikin kujera kawai ya maida kansa ya jingina tare da lumshe idanusa ya faɗa duniyar tunani. Shi kansa bai san iya adadin lokacin daya ɗauka a haka ba, har aka kashe Gen... Saboda wuta da aka maido.

Ummukulsoom kam tunda ta kulle ɗakin saita cire kayanta ta canja dana barci, dan a ganinta hankalinta kwance zatai barcinta ita kaɗai a ɗakin.
Bayi ta shiga taɗanyi uzurinta, komai an kuma canjasa saɓanin sanda aka kawota da farko, bayan ta kammala ta fito.
Gadon ta haye kewar bily na dawo mata sabuwa fil a zuciya, tsawon shekara shida basu taɓa rabuwa ba, duk inda ɗaya tasaka ƙafa ɗaya na tare da ita, sai gashi yau zasu kwana mabanbanta gidaje, bayan suna a cikin gari ɗaya. Ta share hawayen fuskarta tana gyara kwanciya, sama-sama tai addu'ar barci ta ɗora tunaninta daga inda ta tsaya.

Amaan ya buɗe lumsassun idanunsa jin agogon dake falon ya buga ƙarfe ɗaya, iskar daya zuƙa ya turo ta bakinsa da hanci, kafin ya miƙe cike da takun dake nuna gajiya da kasala tattare dashi, harma da ƴar yunwa.
Dani ya fara zuwa ya buɗe kwanikan dake wajen duka, gasashshen namane mai romo a kula, sai abinci da akaima dahuwa ta musamman, duk haɗuwar abincinnan bazai yuwu yacisa ba, dan dare yaja, ko yaci takura masa zaiyi. Maidawa yay ya rufe ya sakko daga ɗan tudun dani ɗin ya nufi ƴar durowar dake gaban tv, keys ya ɗakko aciki, da alama dai Ummukulsoom tayi bonono rufe ɗaki da ɓarawo🤣😝.
Sai da ya ɗauki lap-top ɗinsa da babbar riga da hula a hannu sannan ya nufi ƙofar ɗakin ya zura key ɗin, cikin sa'a kuwa ya shiga alamun ta zare wanda ta kulle da shi. Ƙaramar ajiyar zuciya ya sauke tare da murɗewa....

Da sauri Ummukulsoom da barci ya fara figarta ta buɗe ido jin ana taɓa ƙofa, tashinta zaune jiki na rawa yay dai-dai da shigowar Amaan cikin ɗakin, maida ƙofar yay ya kulle kafin ya cigaba da takowa idonsa a kanta yana haɗiye murmushin dake neman kufce masa da ƙyar ganin yanda ta tsaya tamkar wata status tana kallonsa.
Basarwa yay ya ajiye kayan hannunsa gaba ɗaya kan gadon ya zauna a bakin gadon shima. Takalminsa ya hau ƙoƙarin cirewa ba tareda ya ma nuna yasan da ita a ɗakinba, sai da ya gama tsaf sannan ya juyo ya kalleta gira a ɗage, sam fuskar babu walwala tamkar kullum, amma ƙasan ransa cike yake da farin cikin wannan ranar mai cike da tarihin da bazai mantaba.
“Na miki ƙyau ne ƴammata?”
Harara ta zuba masa tana ɗauke kai. Shima ya ɗauke nasan kan yana faɗin, “Bandama ƙarfin hali mai fada da masarautarsa har a nuna masa ƙofar da zai shiga?”.
Sharesa tai ta fara yunƙurin sauka a gadon, baice mata uffanba, sai ma ya miƙe hankali kwance ya hau cire botirran gaban rigarsa ƴar ciki, tsaye Ummukulsoom tayi tana jiran ya matsa ta ɗauki key dake bedside drawer ɗin dake gefensa bayan ta ɗauki hijjab ta saka akan kayan barcin jikinta duk dama masu kaurine , kuma basu kama mata jikiba balle fidda mata tsiraici.
Fahimtar hakan da yayne yasashi shareta ya cire rigarsa, ya zam daga shi sai dogon wandon da bes ɗinsa faɗa ƙal.
Ƙin kallonsa tai, saima ƙunƙuni take a ranta wai wannan ai iskancine.
Baisan tanayiba, ya kwashi key ɗin data ajiye da wanda shi ya shigo dasu ya nufi bathroom ɗin batare daya tanka mata dinba balle kallon inda take.
“Nikam bazan kwana da ƙato ɗaki ɗaya ba, ka bani key na fita sashensu Momcy”.
Saida ya kama Handle ɗin ƙofar toilet ɗin sannan ya juyo fuska a matuƙar ɗaure, da hannu ya nuna mata hanya alamar taje mana, yay shigewarsa.
Takaici ya kume Ummukulsoom, ko motsawa a wajen kasa yi tayi, yaufa za'ayita kenan, dan koma mi zaiyi yayi ya gama bazata kwana a ɗaki ɗaya da shi ba.....
Tana wajen tsaye tajiyo motsin ruwa alamar wankama yakeyi, ta harari bayin ta koma gaban mirror ɗinsa dake cike da turare da mayuka da kayan dai tsaftar jiki kala-kala, stool ɗin ta janyo ta zauna zaman jiran fitowarsa.
Baifi mintuna ashirin ba ya fito.
Ɗago kai Ummukulsoom tayi da hanzari ta kallesa, cikin azama ta janye idanunta saboda daga shi sai towel yellow ya fito, sai ƙarami a hannunsa yana goge kansa da bawani gashin kirki, dan askewa da yakeyi saboda yanayin aikinsa.
Murmushin mugunta yayi, ya tako zuwa wajen mirror ɗin, gabanta ya tsaya yana kallonsu shi da ita ta cikin madubin tsawon seconds goma sha biyar kafin ya janye idanunsa ya matsa sosai gaban madubin ya ɗauki abinda zai ɗauka ya bar wajen.
Sam batai zaton zai iya yunƙurin shiryawa a ɗakinba a gabanta, sai taga ya nufi drawer ɗinsa hankali kwance ya ciro kayan barci masu taushi farare tas.
A saman gado ya ɗorasu, ya rufe durowar ya koma bakin gadon ya zauna ya ɗauki mai yana shafawa.
Sosai kunya ta lulluɓe Ummu da mamakinsa, ga barci na fisgarta saboda hayaniyar biki ta kwana uku.
Kanta ta ɗora saman madubin yanda bazata gansaba. ya kalleta kawai yana ɗaukar kayansa ya hau sakawa hankali kwance. Harya gama ya dawo gaban mirror ɗin ya ɗau turare ya fesa bata motsaba, gaba ɗaya ji take ta gama takura, yau kam taga ƙarshen rashin kunyar gayen nan.
Wata kujera dake gefe ya jawo ya zauna kusa da ita, ya ɗora hannunsa a kan bayanta.
Gabanta ne ya faɗi, dan haka ta ɗago ta kallesa da sauri, ganin yanda ya shige mata sosai ta ɓata fuska tare da yunƙurin miƙewa. Cikin sa'a ya jawota gaba ɗayanta ta zauna bisa cinyarsa, ram yay mata yanda bazata taɓa iya motsin kirki ba ma balle yunƙurin tashi.
“Fushin da jan ajin ya isa hakanan mana matata”.
Hararar da ta ruɗa dukkan kuzarinsa ta zuba masa, harga ALLAH inta hararesa yana tasiri a jikinsa fiye da zatonta. Lumshe idanunsa yayi ya buɗe a kanta yana jan numfashi da ƙyar da haɗiye busashshen yawun daya daskare masa a maƙoshi, dama tun jin jikinta da yay a jikinsa sosai jijiyoyin jikinsa suka saki......
“Kariga da kayi saken da bazaka taɓa daina ganin wannan fushin a fuskar Ummukulsoom ba, Abubuwa uku idan sun tafi ba su dawowa: Magana da lokaci da mutunci. Mutane iri uku ne: Wasu kamar guba suke, gudunsu akeyi. Wasu kamar magani suke, akai akai ake nemansu. Wasu kamar abinci suke, a kullum dole ne a nemesu. Yi ƙoƙari ka zama wanda a kullum ake neman sa saboda amfaninsa”.
A hankali ya kuma lumshe idanunsa tare da manneta da ƙirjinsa sosai, kalamanta na shiga kowanne kafa ta jinin jikinsa, yasan maganace ta faɗa masa cikin hikima, a hankali yakai bakinsa kan kunnenta yace, “Ba ka sanin daɗin lafiya sai idan ciwo ya sameka. Ba za ka san daɗin zaman lafiya ba sai ka gamu da tashin hankali. Ana sanin daɗin haɗuwa ne idan rabuwa ta zo Ummukulsoommm”.
Yanda yaja sunan natane a cikin kunnenta ya tilastata sake cusa kanta ƙirjinsa, dan gaba ɗaya tsigar jikinta ta tashi, a tare suka sauke ajiyar zuciya, ya sassauta mata riƙon dayay mata alamar ya bata damar tashi.
Da sauri ta yunƙura ta sauka, sosai maganganunsa suka bata mamaki, kenan yana nufin tun bayan rabuwarsu ya damu da ita komi?. Kallonsa ta

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login