Showing 69001 words to 72000 words out of 176055 words

Chapter 24 - Wutsiyar Rakumi Book 1 Hausa Novel Complete

07 Jan 2025

876

Ummu tayi ta ɗauke kanta, yayinda maman Ahmad take binsu da kallo baki buɗe, dan itakama tafara fahimtar akwai wata a ƙasa. Bily kam data saba gani dariya kawai tayi tana zama ɗauke da Ahmad.
“Wai Aunty Hafsat kallon mi kike mana hakane?” cewar yaya Zaid.
“Babu ko ɗaya Uncle, sai daifa ina bada shawarar abi a sannu kar ai karo da muruci, dan ramin damisa ba wajen wasan yara baneba”.
“An samu matsala Aunty Hafsat, kinsanfa ni bawani gane wannan hausa cikin hausar nakeba”.
Bily tace, “To balleni kuma yaya Zaid”.
Ummukulsoom dai kam tsaf ta fahimci maman Ahmad, shiyyasa ta miƙe tama bar falon, a ganinta bada wannan amsarma ɓata lokacine, tarasa yanda zata hana mamana Ahmad dangantata da Yaya Amaan, mafi yawancin lokacima itace ke tuna mata sunansa, dan itakam tama manta da har sunan nasa, kamar yanda takeda tabbacin ita dama baima san natanba.


⚡⚡⚡⚡⚡⚡⚡⚡⚡⚡⚡

*_Gidan Alhaji Mahmud_*

“Mun shiga uku Momcy, mike damun Dad ne, ina zamu samo mazan aure a wata biyu kacal? Wlhy Momcy kaf samarina babu maimin zancen aure”.
“Toke kinama da Samarin Aneesa, ni nace mi, banda Huzaifa wanene ke zuwa wajena, Huzaifa kam iyayensa wlhy bazasu masa aure yanzuba”.
Momcy na zaune ta zuba tagumi tareda zubama ƴaƴan nata idanu, abin duniya duk ya isheta, tarasa gane kan Abban Fodio a kwanakinnan, sai fito mata da salon abubuwa yake waɗanda ita kaɗaice ke fahimtarsu, yanzu daga Aunty Nurse ta samu miji shine yace Ummayya da Aneesa ma su fidda gaba ɗaya zai haɗasu ya aurar.......
“Momcy magana mukefa”. ‘Aneesa tafaɗa cikin girgizata’.
Cikin sauke ajiyar zuciya ta dawo hayyacinta, “To ni Ummayya mikukeson nace muku? Kunsan dai wanene mahaifinku da abinda duk ma zai iyayi, amma kubari zan gwada, ina zuwa”.
Fatan samun nasara sukai mata, ta miƙe ta fita zuwa falon Dad.

Zaune yake a falo yana danna Lap-top, yana waya kuma, hajiya jamila taji daɗin samunsa cikin walwala, gefensa ta zauna harya kammala wayar yana faɗin Alhmdllh, ALLAH kabani tsawon ran sauke wannan nauyin”.
Da “Amin” hajiya jamila ta amsa, duk da bata fahimci komaiba a zancen nasa.
Juyowa yay ya kalleta yana gyara zamansa, “Lafiya dai ko?”.
“Lafiya lau Abban Fodio, dama dai akan maganar yaran nanne”.
Ɗaure fuska ya kumayi sosai, “Waɗanne yara kenan?”.
Tuni zuciyarta ta fara hautsinawa ganin yanda ya koma mata, cikin in ina tace, “Su su Ummayya, kayi haƙuri ka kara musu lokaci”.
“To, to, saboda ga mijin hajiya Jamila ko? Jamila wlhy ki kiyayeni, ina tarakine kawai, idan kika bari nakai bangon da zan amayoki bazakiji da daɗiba, wlhy kinji na rantse duk wadda bata kawo mijiba a watanni biyunnan danace saina aura mata duk wanda yaymin, har shima Ameer ɗin, niba shashasha bane dazan zauna naita tara ƴaƴa a gida manya-manya babu aure, ko Buhayyah ta samu miji bayan kammala secondary ɗinta aure zan mata, dan haka wannan shine gargaɗi na farko, kuma na ƙarshe tsakanina dake, karki sake zuwamin da wannan batun, ina buƙatar ɗakunan da suke ciki dan mai zama cikinsu tana gab da shigowa”.
Wani irin duka ƙirjinta yayi, ta waro idanu waje cikin tsantsar firgici, “Abban Fodio ban gane maganarka ta ƙarsheba wlhy”.
Miƙewa yay tsaye tareda kwasar tarkacensa yana faɗin, “Ai bazaki taɓa ganewaba tunda kinacin kan kifi”.
Tamkar sha katafi haka tabisa da kallo, manyan idanun nan da Amaan yay gado tamkar zasu zubo ƙasan carpet ne, jinta yay wani diimm, hakama ƙwaƙwalwarta tai jingim bata aiki gaba ɗaya, sam saita daina fahimtar komai, dukda wani gefe na zuciyarta na faɗa mata bafa abinda take tunani baneba.

Sam a kwana biyunnan gidan ya sauya, saika ɗauka ko Amaan ne yazo, amma ba hakan baneba, dafin umarnin Dad ne kecin kowa a zuciya, idan ka ɗauke Aunty Nurse dake cikin farin ciki da shirin Dad ɗin, dan itace tabasa wata shawarar a cikin shirin nasa, bama tai zaton zai ɗaukaba ashe ya amsa.

Ana cikin wannan yanayin a gidan saiga admission ɗin su Ummukulsoom ya samu, sai dai kuma a Rivers state ne, University of port harcourt suka samu, hakan bai damu Alhaji Mahmud ba kam, dan a ganinsama canne Ummukulsoom zatafi samun wayewar kai kasancewarta cikin ƙabilu daban-daban, zata samu ilimin zamantakewa da jama'arda koda ba kabilartaba.
A ranar yakira Abban Attahir ya sanar masa, shima yayi matuƙar murna da hakan.
Babu ɓata lokaci aka hau yima Ummukulsoom da Bily shirin tafiya port, duk da ita a ranta tana tunanin yaya zasu rayu a inda basusan kowaba, gashi ita koɗan turancinma bawani iyawa tayiba, danma Bily na nuna mata wasu abubuwan a zamanta gidan, sai karatunta na islamiyya, tana bukatarsa matuka, dan babu wani ilimi dazai tasiri ga rayuwar ɗan musulmi idan babu na addini a cikinsa.
Kasa daurewa tai taima Bily tsokacin maganar, Bily kuwa ta samu Ummi da zancen ba tareda Ummukulsoom ta saniba.
Murmushi Ummi tayi tanajin ƙarin ƙaunar Ummukulsoom a ranta, haka takeson mutum ya kasance mai sananin ciwon kansa da martabar addininsa.
“Karku damu Bilkisu, zanyi magana da Abbanku saimuga yanda za'ai gameda islamiyyar taku, idanma wani malami za'a samu sai a sama muku acan, dan namaji kamar bacikin makaranta zamu zaunaba”.
“Tofa, ba cikin makarantaba Ummi, to wajenwa muda ba dangi garemuba acan ɗin?”.
“In banda shirmenki Bilkisu ko babu dangi ai akwai abokan arziki ko, mudai jira muji yanda za'ayi ɗin, kudai yanzu ku kammala shirin tafiyar taku ɗilau ɗin”.
“Aini Ummi kinma tunamin, kinsan kuwa yanda na ƙagu muje garin nan nasu Ummukulsoom? A rayuwata inason naganni a inda ban saniba, musamman ma ƙauye wlhy”.
Dariya Ummi tayi tana girgiza kai, “Hajiyar zumuɗi kenan, koda yake Ummu mafa na lura tana cikin tsantsar farin ciki, tana dai dannewane kawai, yarinyar tanada nutsuwa sosai wlhy, shiyyasa a kullum take sake shigemin rai, narasa miyasa Abbanku yace karna kaita wajen Hajiya yaya?”.
“Wlhy nima Ummi abinnan na bani mamaki, nasan kuma Hajiya yaya batada matsala, tanada son jama'a zakuma taso Ummukulsoom sosai”.
“Karmu damu, na tabbata akwai nashi dalilin shima ai”.
“Hakane kuma Ummi, yanzu dai bamu kuɗin mutafi wankin kan kar rana tayi, nadsan Ummukulsoom ma tagama wankan yanzu”.
“Duba a bag ɗincan da nadawo aiki ɗazun ki ɗaukar muku dubu biyar, sai ai muku har ƙunshi ko, dan sonake taje tsaf”.
“Hakane Ummin mu, shiyyasa nake ji dake barci da ido biyu”.
“ALLAH shirya minke Bilkisu, kindai maidani kakarki wlhy”.
Dariya Bily ta fita tanayi da faɗin “Ni na isa Ummina.

Ummukulsoom na zaune gaban Mirror tana rolling gyalen doguwar rigarta Bily ta shigo.
“Hummm kaga ƴammatan yaya Zaid, irin wannan ƙyau haka”.
Harara Ummu ta ɗago ta zabga mata, amma batace komaiba, Bily ta kwashe da dariya tana jingina da mirror ɗin, “Miye na hararata to? Kin zata ban harbo jirginku baneba shin?”.
“Bakida man kai wlhy Bily, a'a garinmu kika harbo ba jirginmuba, idan kin shirya muje, idan kuma bazaki jeba nai gaba”.
“Oh ga maganata ta fito, bama kwaso na biku dama ai, to duk tsiyarku sai naje”.
Dariya Ummukulsoom tayi, ta ɗauki bag ɗinta tana faɗin “Ki sameni wajen Ummi parrot”.
“Nice parrot ɗin?”.
“Kinmafi Parrot ai Bily”.
Bayan Bily ta gama shiryawa ta samu Ummukulsoom a wajen Ummi suna hoto, shiga tai itama akayi da ita sannan suka fita zuwa sashen maman Ahmad da itama taketa shirin komawa legas, amma anan zatabar Ahmad wajen Ummi, tare suka tafi wankin kan.
Sai yamma lis suka dawo gidan, ammafa sunyi ƙyau sosai, barema Ummu datai kitso, sai fuskar ta ƙara fitowa fes da ita, dukda baza'ace takuma zama wata cikakkiyar maceba amma jikinta ya murje sosai, fatarta tayi wani irin ƙyau da kwanciya saboda bawani yawo takeba, kallo ɗaya zakai mata ka gamsu hankalinta a kwance yake, batada wata damuwa sai wadda ba'a rasaba.
Hankalin Ummi saiya sake kwanciya dataga yanda Ummukulsoom ɗin tai ɗas, koba komai ƴan garin nasu bazasu taɓa samun hanyar yin ƙananun maganaba, dan babu wanda zai kalleta bai sake kalloba.

*_Washe gari_*

Washe gari saiga Aziza itama, dan tare zasuyi tafiyar zuwa Ɗilau.
Tsaf suka fito kamar ka sacesu ka gudu, haka kawai Ummukulsoom saita tsinci zuciyarta da fargaba, amma saita danne dan a yanzu bata buƙatar halin tsoro a rayuwarta, burinta akomanta ta zama jaruma, su ukune kaɗai zasuyi tafiyar, sai yaya Zaid dazai kaisu ya dawo, dan 1week zasuyi su dawo.
Sunyi sallama da maman Ahmad, itama insha ALLAH gobe zata wuce Lagos ɗin.

tunda suka tafi a motar Aziza da Bily ne kawai ke fira, sai Yaya Zaid dakan ɗan saka musu baki idan yaso, amma sam Ummukulsoom kamar bata ma a motar, sai kallon hanya take abinta, shirun natane dai kan ɗan saka yaya Zaid janta da hira lokaci-lokaci shima, a haka har suka isa Zaria, tsaraba ya ƙara musu ta kayan marmari sannan suka hau hanyar ɗilau bisa jagorancin Ummukulsoom.........✍🏻


NO. 24


..........Babu abinda ya sauya mata a garin a kusan shekara ɗaya da bata ciki, sai dai gine-gine da aka ƙara na jar ƙasa alamun dai matasan garin sunsha aurarraki, sanin babanta na gida yasata nunama Zaid hanyar da zata kaisu babban gida, yara saibin motar suke da gudu dukda basusan wanene a cikiba.
Sai suka bama Ummu tausayi, duk wanda ya rayu a ƙauye yasamu wani cigaba dolene ya tausayama waɗanda suke a ciki, bawai dan suna cikin ƙunciba ko koma baya na rayuwa, a'a sai dan kawai suna rayuwane tamkar shugabanni sun manta dasune, ka shekara goma bakaje ƙauyenkuba idan kaje saika tarar babu wani canji da aka samu, idan kayi wasama saikaga ankuma samun taɓarɓarewane.
Tunda Ummukulsoom suka fito yaran dake binsu sukai cirko-cirko suna kallonsu, hakama manya dake cikin inuwoyi zaune ana zaman gulmar mata sai duk suka zubo musu ido.
Mariya ce data dawo daga ɗibar ruwa rafi tai tozali da Ummukulsoom, cikin ƙaraji tace, “La'ila, yaya Umma”.
Hakan da tayine ya fargar da waɗanda basu gane Ummu ba, Ummu na kiranta amma tuni tayi cikin gida kai rahoto.
Kafin kace mi an zagaye su Ummukulsoom har mata na leƙe ta katanga kowa burinsa yaga Ummukulsoom yata komane.
Itako sai zuba musu murmushi takeyi, fuskarta a washe take tarbar kowa.
Duk sun ɗauka Zaid ne mijinta, dan danan aka bashi masauki, Ummu tashiga matuƙar mamakin tarbar da suka samu gasu baba yalwa, kafin kacemi ƙauyen ya ɗauki zuwan Ummukulsoom. Ƴan gidan kam sai kawo musu abinci ake da fura, sunci iya abinda zasu iya ci, Bily sai daɗi takeji, harga ALLAH garin yamata sosai.
Da yawan ƴan gidansu Ummu jikinsu yayi sanyi da ganin yanda Ummukulsoom ɗin takuma canjawa, ta murje tayi ras da ita, saidai fa dukda hakan sunata ƙananun gulma wai babu komai (Ciki🤣).

Lokacin da Ummu ta fito zasuma yaya Zaid rakkiya gidan Gwaggo hinde ya gaisheta sai mata ke leƙensu ta katanga, oho sudai basusan anaiba, gashi abindama zai ƙara ɗaukar hankalinka, da Ummu suka tafi jere da Zaid ɗin, Bily kuwa da Aziza suna gabansu, duk Aziza ce da shirinnan, dan fatanta karsu bada wata ɓaraka da wani zai fahimci Ummukulsoom batada aure yanzu.
Shiko Zaid da hakan yay masa daɗi sai jan Ummukulsoom yake da hira akan mizai shirya musu kafin su dawo na tafiya makaranta, wannan ne yasata biye masa harda murmushin dake narkar da mazan garin.

Gwaggo hinde na tsakar gida a garken dabbobi tana basu ruwan tsari su Ummu sukai sallama, dukda an sanar mata da zuwansu saida taji wani irin daɗi, sai dai kuma a lokacin da take ma su Ummukulsoom lalale marhabun sai idonta ya sauka akan Zaid dake shigowa a ƙarshe, gabantane yay tsananin faɗuwa, tai kasaƙe tana kallonsa baki a hangame.
Daga Bily har Ummu har Aziza duk juyawa sukai suma suna kallon abinda Gwaggo hinden ke kallo, ganin Zaid sai duk suka juyo gareta.
Ummukulsoom ta karasa inda take taɗan girgiza hannunta, ”Gwaggo! Kin ko baƙya murna da zuwan nawa na koma?”.
Ajiyar zuciya Gwaggo hinde ta sauke, kafin tai murmushi tana canja zancen da faɗin, “Sannunku da zuwa amarya, kumuje ciki mana, angona lalale marhabun (tazata Zaid ne mijin Ummu itama).
Zaid da duk yasha jinin jikinsa da kallon Gwaggo hinde yay murmushin yaƙe yana amsata.
Koda suka zauna a tabarmar da Gwaggo hinde ta samusu gindin bishshiyar mangwaro dake gidan sai bin Bily da Zaid take da yawan kallo a sace, Ummu da Zaid ne kawai suka lura da hakan, amma dai basuce komaiba duk da shima Zaid mamakin kamannin Gwaggo yake da Abbansu, sai dai ita tsufa daya kamata.
Bayan an gaggaisa sukasha ruwan da Gwaggo ta ajiye musu sai aka hau ƴar hira, musamman tsokanar Ummu da gwaggon keyi akan ina zatakai jiki?, watanni kaɗan hartayi irin wannan canjawar, Mi Zaid ke batane? Itama a kawo mata nata kar kishiya tafita a wajensa.
Dariya kawai Zaid kema Gwaggo dajin wani nishaɗi a ransa, inama ace zancen Gwaggo zai tabbata daya zama cikin masu sa'a, saidai gefen zuciyarsa na mamakin shin Ummu ta taɓa aurene? Dansu babu wanda yama taɓa sanar musu komai akan dalilin zaman Ummukulsoom gidansu shi da Bily, dukda ita bily takanji maman Ahmad na ambatar sunan Amaan ɗin bata taɓa sanin matsayinsaba a wajen Ummu, bama ta zata yaya Amaan na gidansu Buhayyah ba.
Sunsha har zuwa biyar na yamma Zaid yayma gwaggo alkairi suka rakoshi har mota tanata saka masa albarka da fatan saukarsa lafiya, anan aka sauke kayan su Ummu tareda tsarabar gwaggo yatafi cikeda kewar Ummu da Bily, tareda alwashin dawowa ya kwana garin dan yamasa daɗi sosai.
Su Ummu kuwa nan suka dawo suka cigaba dashan hirarsu, sai dare taje babban gida itada Aziza, dan Bily maƙalewa tai wai ita tana gidan Gwaggo suje su dawo.
Acan su Ummu sukasha hirarsu da baba saida suka farajin barcine suka dawo gidan Gwaggo, dan baba cayay su kwana acan safi samun sakewa.
Gwaggo kuwa tanata jan Bily da hira cikin hikima, dan ganin Zaid ya tada mata wani tsohon tabonta, hakama kamannin Ummu da Bily wanda saika daɗe tare dasu zaka fahimci hakan.
Bily batasan dawan garinba, duk tambayar da Gwaggo tai mata itadai kai tsaye take amsa mata harsu Ummukulsoom suka dawo gidan.


⚡⚡⚡⚡⚡⚡⚡⚡⚡⚡⚡

“Wow ga wata kaya fa alhaji tana tunkaromu”.
Baseer dake zaune a mota yana latsa waya ya ɗago ido a sace yana kallon zankaɗeɗiyar yarinyar fara tas, motar da aka buɗe mata ta fitoma kawai abar kalloce.
Karon farko a rayuwar Baseer dayaji son mace na gaskiya a ransa bayan Ummukulsoom, ya cije leɓe da ƙarfi yana binta da kallo harta shige wajen hutawar.
Hafez sabon abokinsa da shima yake binta da kallo sake da baki ya sauke sassanyar ajiyar zuciya yana maido kallonsa ga baseer daketa kokawa da busashshen yawu a maƙoshi.
“Bas abari ya hucefa”.
Da ƙyar Baseer ya iya faɗin “Abokina shike kawo rabon wani, amma muja aji”.
“Aji kuma? Yo kai mace ne? Ai irin waɗannan ina faɗa maka idan bakai ka tayaba saika ƙaraci haɗiyar yawunka ko kallo baka ishesuba, kaidai tashi muje kawai”.
Fitowa Baseer yayi bayan yakuma fesa turare tun a mota ya goge fuskarsa sosai, nufar wajen sukai shida Hafiz suna tafiya ɗai-ɗai tareda basarwa dan shima Hafiz ɗin masha ALLAH ƙyaƙyƙyawane.
Tunda suka shigo wajen suke baje ido amma ko alamarta basu ganiba, nanfa suka shiga zagaye-zagaye amma babu ita, fitowa sukayi waje

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login