Showing 123001 words to 126000 words out of 176055 words
tare dashi ne ya fito daga ɗakin da aka kaishi Nurses biyu na biye dashi.
Momcy dake ta kuka tai saurin tasowa tana tambayar Dr ɗin ya jikinsa?, cike da tausayawa ya kalleta, kafin ya ɗauke kansa yana sauke numfashi.
“Hajiya sai dai addu'a kawai, ita yake buƙata”. ‘ya ƙare maganar da barin wajen’.
Zubewa Momcy tai a ƙasa tana kuka, su Aunty Nurse suka riƙeta da bata haƙuri suma suna hawayen, sai dai sam taƙi yin shiru, da alama ma ta fara fita hayyacinta.
Abba ne ya matso yana bata baki da mata nasiha akan tai masa addu'a bawai kuka ba.
Kallo ɗaya Dad yay musu ya ɗauke kansa, saima ya fice yabar wajen gaba ɗaya.
Ganin dare ya fara ja Amaan bai farfaɗoba Abba yace su Momcy su tafi gida haka nan, abarma safiya kuma.
Dagewa Momcy tai akan ita dai abarta ta kwana dashi, Abba ne yayta lallashinta akan tayi haƙuri taje, bazai yuwu mace tayi jiyyar namiji ba.
Badan tasoba suka tafi. aka bar Abba da Dad da Attahir, Zaid, Ameer a sibitin.
Suma duk sai Attahir yace suje gida shi zai kwana.
Kusan 12 suka tafi har Attahir ɗin dan shima zai canjo kaya ya ɗakko abinda zasu iya buƙata.
⚡⚡⚡⚡⚡⚡⚡⚡⚡⚡⚡
Abba da Attahir da Zaid a tare suka dawo gida.
Su Ummukulsoom suna falo zaune kowa da hidimar da yakeyi, sarai ɗazun taji ance Amaan baida lafiya, amma bata maida kai akan zancenba, dan a halin yanzu ko sunansa bata ƙaunar a ambata mata.
Ummi tace, “Alhaji yaya jikin Amaan ɗin?”.
Zama Abba yay yana faɗin, “To da sauƙi za'ace Umminsu, sai dai fa gaskiya yaron yana bani tausayi, dan yanajin jiki matuƙa, ni harma na rasa yanda zan fassara al'amarin”.
“Ya salam, ALLAH ya warware komai cikin sauƙi to, ya farko ko?”.
“A'a har yanzu dai bai farfaɗo ba, amma Doctor yace babu damuwa a rashin farfaɗowar tashi, shiyyasa muka taho, jininsa ne yay mugun hawa sosai”.
“Ya ALLAH, ɗan yaro dashi ko iyalanma ba'a ajiye da nisan zango ba ace hawan jini?”.
Cikin sauke ajiyar zuciya Attahir yace, “Ai Ajiwa ya daɗe da hawan jini Ummi, shi mutum ne da inhar kika iya fahimtar damuwarsa a fuskarsa to lallai abu yakai matuƙar tiƙewa a garesa, duk abinda kuma za'a cutama wani yaga yana da ƙarfin da zai iya karesa to lallai zai shiga koda shi zai cutu, shiyyasa ko a lokacin da yace min ya saki Ummukulsoom nasha mamaki matuƙa, dan ban taɓa kawo hakan a raina ba wlhy, abubuwan da yake sakama ransa sune suka haddasa masa ciwon, gashi dama shi bamai son yawan magana baneba...”
Ummi tace, “Babu abinda yafi ƙarfin ƙaddara ai Attahir, tunda har ALLAH ya ƙaddara sai igiyar auren ta tsinke babu wani mai hana hakan koda su a karan kansune, irin masu halayyar Amaan a wannan zamanin ƙalilanne, su bada farin cikinsu dan wani yayi, ALLAH ya bashi lafiya da dukkan sauran musulmai, amma sam abun baiyi daɗiba dai wlhy”.
Miƙewa Attahir yay zuwa sashensu, duk abinda zasu iya buƙata ya ɗauka ya koma asibitin
★★
Amaan bai farkaba sai Washe gari da hantsi, zuwa lokacin duk su Momcy sun koma asibitin, suma su Ummu da maman Ahmad da Bily da Ummi duk suna can.
Attahir ya fito ya kira doctor suka koma ɗakin tare, dukkan taimakon daya dace shi aka sake bashi.
Ba'abar kowa ya shigaba sai Abba da Dad, suma kuma basu daɗeba suka fito, saiko Momcy data samusu kuka, itama an barta ta leƙasa na ƴan mintuna.
Momcy sai ƙara kallon Ummukulsoom take mamaki fal ranta, ko a mafarki akace mata yarinyar datai aikatau a gidansu ce saita ƙaryata tace shirmen mafarkine, lallai ta cutar da ɗanta, dan ko Amaan yanada laifi ta fisa, itace taita cusa masa ƙin Ummukulsoom a zuciya ta hanyoyi da dama bisa ga shawarar ƴar uwarta mansura, ashe batasan ɗanta takema zagon ƙasa ba, wadda kuma take ganin sunfi ƙarfi yau itace tazamar musu wutsiyar raƙumi. Hawaye masu ɗumi suka biyo kumatunta, tasa bakin gyalenta ta share, gaba ɗaya ta kasa ɗauke idonta a kowanne motsin Ummukulsoom, hakama su Ameer sai kallon Ummu sukeyi kowa yana saƙa abinda yazo masa a rai.
Yayinda kuwa Ummukulsoom ta ɗaukema kowa kai a cikinsu, bayan gaisuwa bata kuma kallon kowa ba sai yaran Aunty Nurse.
Ganinma kallon yamata yawa ta miƙe da nufin ficewa ta jirasu a waje.
Lokacin da su maman Ahmad suka fito domin tafiya gida hararta sukaitayi akan abinda tayi.
Amma sam sai taƙi kallon kowa, sai da akaje gidane kowa ke mata faɗa akan karta sake yin irin haka, babu mai matsa mata akan Amaan, amma gameda lalura da yake ciki ta bar nuna halin ko in kula gaban ƴan uwansa kodan darajar Dad.
Ta gamsu da wannan maganar, dan haka ko a washe gari ma da sukaje dubashi bayan ta gaishe da Dad ta gaida Momcy dasu Aunty Nurse. yau dai an barsu sun shiga, saidai fa shine ba kowa ya fahimta ba saboda bayajin daɗin jikinsa sosai, bakuma yason hayaniya kwata-kwata.
★★★★
A kwana na uku da kwanciyar Amaan asibiti suka koma legos saboda makarantar Ummukulsoom da Ahmad, amma shi Attahir sun barsa anan, dukda haushin Amaan da yakeji bazai iya tsallakewa ya barsa a cikin wannan halinba, ko a jiyyar nan tashi da yake yana bashi dukkan kulawa, sai dai baya masa irin kaffa-kaffa ɗinnan da tsokana sam.
Sai da su Ummukhoolsum suka biya ta asibitin suma, sai dai fa sam ita ba'a son ranta ba, ko zuwan kullum ɗinnan da sukeyi tana ƙyautata zaton baima taɓa ganinta ba.
Yau ma sai dama Ummi tai mata jan ido sannan, amma harda hawayenta na haushi.
Har lokacin da sukaje ma barci yakeyi, tunda yay sallar asuba ya koma barci, hakan yasa ko ma shiga basuyiba.
Har sunyi niyyar tafiya sai Attahir daya fito daga ɗakin da Amaan ke kwance ya dakatar dasu ta hanyar faɗin su shigo Amaan ɗin ya tashi.
Jitai tamkar ta rusa kuka, amma yaya zatayi, dole ta dawo da baya tana kuma ɓata fuska suka shiga.
Zaune yake a saman gadon jinyarsa, an saka masa filo ya jingina, ya ɗan rame ba laifi, amma sai ya kuma haske dayin fayau a fuska, kallo ɗaya zakai masa ka fahimci lallai bayajin daɗi sosai.
Ameer dake haɗa masa tea ya ɗago tare da miƙa ma Attahir, dan inhar bashi ya bashiba baya sha.
Tunda suka shigo kallo ɗaya yay musu ya ɗauke idanunsa, Bily da maman Ahmad suka matso suka gaishesa da masa ya jiki?.
Murya can ƙasan maƙoshi ya amsa, ba tare da ya kalli kowa ba.
Da hannu Bily ta zunguri Ummukulsoom da batace komaiba, Attahir ma ya dalla mata harara.
Tasan minene laifinta, dan haka ta kumburo baki tana faɗin, “Ya jiki?”.
Bai amsa ba, sai idanunsa da suka canja launi ya ɗan ɗago ya kalleta, caraf suka haɗa ido, tai saurin janye nata tana hararsa.
Lumshe nasa yayi a hankali yana kuma haɗe fuska.
Babu wanda ya sake magana a ɗakin, Amaan yanata shan tea ɗinsa a hankali, Attahir dake zaune gefensa yana ɓalla masa magun guna, da alama jira yake ya gama ya basa yasha.
Wayar Ummukulsoom ce tai ring, ta lalubota a handbag tana dubawa.
Wani lallausan Murmushi ta saki ganin Umar rinta.
Amaan dake kallonta ta gefen ido batare da wani zai iya fahimtar hakanba ya cije haƙwaransa ta cikin baki, haka kawai yaji zafin murmushin nata saboda zargin namiji ne ya kirata....
“Hallo Umar!” ta faɗa tana ficewa daga ɗakin gaba ɗaya.
Su duka da kallo suka bita, banda Attahir da Amaan da baka isa fahimtar yana kallon nata ba.
Tea ɗin hannunsa ya miƙama Attahir alamar ya ƙoshi, da mamaki Attahir yace, “Wai kana nufin ka ƙoshi?”.
Fuska ya ɗan yatsine ya ɗaga masa kai batare da yace uffanba, yakai hannu ya ɗiba maganin da Attahir ɗin ya ajiye masa, Ameer yay saurin miƙa masa ruwa da ya kalla.
Sai da ya gama shan maganin sannan su Maman Ahmad sukai masa sallama tare da addu'ar samun sauƙi mai ɗorewa suka fice suma.
Lumshe idanunsa yayi zuciyarsa a matuƙar cinkushe, saɓanin da iyayensa suka samu a kansa shine babbar matsalarsa a yanzu, duk yanda yaso kaucema hakan bai tsallake ba, ya haɗiye abinda ya tokare maƙoshinsa da ƙyar, gaba ɗaya ji yake rayuwar ta daina masa daɗi, babu abinda ke saka sa farin ciki a halin yanzu.
*_BAYAN KWANA UKU_*
Kwana uku da komawar su Ummukulsoom legos aka sallami Amaan ya koma gida, abinda ya kuma sakashi cikin ƙunci barin Momcy gidan, ƙiri da muzu Dad yace bazata zauna masa a gida ba, duk roƙon da ƴaƴan suke masa yaƙi sauraren kowa.
Wannan yasa duk suka kasa komawa gidajen aurensu suma, ga jarumin gidan da kan iya tunkarar Dad ɗin shima yayi laushi, dan Dad ɗin yamafi jin zafinsa fiye da kowa, a haka aka cinye kwanaki biyu.
Dole a ranar lahadin data zagayo kwana takwas da faruwar abun Amaan da Attahir suka shirya suka koma Legos wajen aiki.
Komai ya kuma canjawa a garesa, ƴar magana ɗaya biyu ma da yakeyi ada yanzu ta gagaresa kwata-kwata.
Bayan ya gama kimtsawa ya nufi sashen Dad, a falo ya iskeshi zaune yana shan fura da Aunty Nurse ta dama masa, yay ma Amaan kallo ɗaya ya ɗauke kansa.
Shima kansa a ƙasa yaje gabansa ya zauna, “Dad barka da hantsi”.
“Barka” kawai Dad yace ya ɗauke kansa;
Shirune ya biyo baya, ga magana cike da ran Amaan amma bakinsa ya kasa furtawa, sai da yaga Dad zai miƙene yace, “Dad ka gafarceni, ni mai laifine a gareka tabbas, sai dai wlhy bana aikata bane danna nuna maka baka isa dani bane, inhar haƙura da ita da kace nayi zaisa ka dawo da Momcy gidannan na ɗauki maka alƙawarin haƙura da ita, insha ALLAHU kuma bazan sake bibiyar rayuwarta ba, na yarda cewa ƙaddarace ta haɗa mu, itace kuma ta rabamu, sakejin zan iya zama da ita da barinta a yanzu kuma na amsheshi matsayin jarabawa, dan ALLAH Dad kadawo da Momcy”.
Cifaba da tafiya Dad yayi baice uffanba, sai da yaje gab da shiga ƙofar bedroom ɗinsa ya tsaya, “Inhar ka nisanci Ummukulsoom kamar yanda kai alƙawari to tabbas kaima zaka samu yanda kakeso ga mahaifiyarka, zan saka dukkan idanuna akanka kuma”. Yana gama faɗa ya shige abinsa.
Yaa Amaan ya sauke wani nannauyan numfashi sannan ya miƙe ya fito, koda ƴan uwansa suka rakosa har mota bakinsa bai saɓa da kowa ba, sai hannu daya iya ɗaga musu kawai.
⚡⚡⚡⚡⚡⚡
A ranar suka dawo legos shida Attahir.
Tunda ya dawo kuma bai haɗu da Ummukulsoom ba, duk wata hanyar da zata haɗasu kowanne ya tosheta tsakanin ita da shi, shi yanayin komaine bisa umarnin mahaifinsa, ita kuma tanayine dan batason ganin sa sam.
A yanzu haka ta bama Umar damar tura iyayensa gidansu.
★★★★★
“Ajiwa wai bazaka cire abinnan a ranka ba dan ALLAH, kusan wata biyu kenan sai zabgewa kake a tsaye, kana kallon kanka a madubi kuwa?”.
Numfashi ya sauke kaɗan yana lumshe idanunsa, yakai hannu kaɗan ya shafi girarsa, “Attahir kenan, kaine kakemin kallon mai damuwa, amma fa ni bani tare da kowacce damuwa a raina a halin yanzu, Momcy ta koma lastweek, to mikuma zansa a raina?”.
Murmushi Attahir yay yana faɗin, “Hakane Ajiwa, amma sam kaƙi sakin ranka ai”.
Ɗan murmushi yayi yana maida idanunsa ya lumshe ba tare da ya ƙara cewa uffan ba.
Shima Attahir sai ya sakin zancen kawai ya kamo masa wani.
⚡⚡⚡⚡⚡⚡⚡⚡⚡⚡⚡
A ƙarshen wannan satin Attahir ya shirya zuwa kd na kwana ɗaya.
Kai tsaye gidansu Amaan ya sauka, yayi farin cikin ganin Momcy ta dawo, sai dai fa da alama har yanzu akwai damuwa, dan ayanayin daya ganta kawai ya isa bashi wannan amsar, komai nata sukuku take yinsa, sam babu walwala a tare da ita, hakama su Bassam dake gida.
Bayan sun gaisa da Momcy ne ya tambayeta Dad fa?.
Cikin ɗan yaƙe tace, “Attahir yana baya zaune, kaje can ka samesa”.
Har Attahir ya miƙe Momcy ta dakatar dashi.
“Attahir yaya jikin ɗan uwan naka? Nasan daurewa kawai Fodio keyi, har abada bazan yafema kaina ba inhar wannan damuwar takai fodio ƙasa Attahir....” hawaye masu zafi suka gangaro a kumatun Momcy.
Sosai tsoro ya kama Attahir, ya rikice da bata haƙuri.
“Attahir babu wani abinda zai tsayar da waɗannan hawayen nawa a irin wannan lokacin, dan girman ALLAH Attahir ka roƙi Ummukulsoom tayi haƙuri ta komawa Fodio, wlhy na tabbata yana sonta, amincewarta ce kawai zata saka Abban Fodio janye katangar da yayma Fodio da ita, wlhy Attahir a yanda nakeji yanzu zan iya haƙura da nawa auren inhar Abban Fodio zai amince Ummukulsoom ta dawo”.
Kan Attahir a ƙasa idonsa yay jajur ya ɗago ya kalli Momcy, “Momcy kibar faɗar haka, mu cigaba da addu'a, insha ALLAHU komai zai daidaita”.
“ALLAH ya daidaita Attahir, sannan ka bani Number Ummukulsoom”.
“Ok gata” yafaɗa yana danna wayarsa, sai da ya faɗa mata ta saka sannan ya fice zuwa wajen Dad.
“A'a, Attahiru ne a garin namu?”.
“Eh Dad nine, mun sameku lafiya?”.
“Lafiya lau Attahiru, ya aikin naku da iyali? Ina kuma ɗiyata Ummukulsoom?”.
“Alhmdllh Dad, Ummukulsoom na lafiya, yanzu ma akanta nazo wajenka”.
“To mike faruwa?”.
Kai Attahir ya sosa yana kuma sunkuyarwa, “Dad ka gafarceni, nasan kai mana katanga da wannan maganar, sai dai halin da ɗan uwana yake ciki yasa naji bai kamata nayi shiruba, wlhy Abba Amaan yayi nadamar abinda ya aikata, dan ALLAH kai mana afuwa mun tuba.....”
“To inbanda abinka Attahiru aini dama ban riƙeku a rai ba ko”.
“Hakane Dad, amma...”
“Attahiru! Mubar wannan zancen kaji”.
Duk yanda Attahir kema Dad magiya sam yaƙi saurarensa, hakane ya sakashi tashi jikin a sanyaye ya tafi ba tare da ya samu yanda yake soba.
⚡⚡⚡⚡⚡⚡⚡⚡
Washe garin dawowar Attahir Ummukulsoom zaune a harabar gidan daga can baya iskar la'asar na busata tana karatu, kwanaki kaɗan ya rage musu su gama exams nasu, sallamar Attahir ce ta sakata ɗago idanunta ta kallesa.
“Lah yaya Attahir ashe ka dawo?”.
Zama yay a gefenta yana faɗin “Eh shigowar kenan, naji gidan shirune inasu Bily?”.
“Aunty dai taje kitso, Bily kuma a ɗaki na barta tana barci”.
“Ok to masha ALLAH. Ai dama inason muyi magana tun kusan kwanaki biyu haka”.
“To yaya ina saurarenka, ALLAH ya jishemu alkairi”.
“Amin ƙanwata. Dama akan maganar Umar ne, iyayensa sunce zasuje ƙarshen satin nan sukai kuɗi”.
Kanta a ƙasa tace, “Eh haka yace yaya”.
Idanu yaɗan tsura mata na wasu sakwanni, kafin yaɗan gyara zamansa, “Ummukulsoom na baki shawara mana?”.
“Yaya ko Umarni kabani zanbi balle ma shawara”.
“To na gode, amma ita shawara ra'ayin wanda akaimawace ya ɗauka koya ajiye, musamman idan ta shafi rayuwarsa. Ummukulsoom ina ganin ki sake bama Ajiwa dama a karo na biyu”.
Sosai ta ware manyan idanunta tana kallon Attahir da shima ita yake kallo.
Bai jira tace komaiba ya cigaba da faɗin, “Nasan wanene Ajiwa fiye da zatonki, tun bayan rabuwarku dashi na fahimci yana cikin damuwa, sai dai a koda yaushe cikin ɓoyemin yake, lallai yayi kuskure sosai, sai daifa abinda zamu duba babu wani hannu a duniya daya isa goge abinda ƙaddara tazo dashi a littafinmu, haka ALLAH ya ƙaddara a tsakaninku, da Ajiwa baiso karɓar aurenki ba tun farko zai san yanda ya zamewa Dad, sai dai shi mutumne maison bin umarnin iyayensa koda ace zai cutu, Ajiwa