Showing 45001 words to 48000 words out of 176055 words

Chapter 16 - Wutsiyar Rakumi Book 1 Hausa Novel Complete

07 Jan 2025

862


Ummukulsoom ma koda ta shiga ɗaki saita zube a gado tana mamakin wannan rayuwar, itadai tunda ta taso bata taɓa ganin mai irin wannan halin nasaba, miskiline irin na gaske ɗinnan, gashi abin ya haɗe masa biyu da aikin sojoji, saidai takula bashida wulaƙanci irinnasu Momcy, koda yake lokaci baiyi dazata yanke wannan hukuncinba, tunda dai kwana ɗaya kacal kenan tayi dashi a gidan.
Ta daɗe a wajen tana saƙawa da kwancewa, rabin tunanin dukna Baseer ne da sonsa ya zame mata gyambon zuciya, sai dai tana cigaba da kaima ALLAH kukanta akan ya yaye matashi, tasan badan halaccin Alhaji Mahmud ba da sai dai taƙare rayuwarta a ƙauyen ɗilau babu mijin aure, dan Baseer yariga yay mata fenti mai wahalar goguwa, wannan ƙauyen nasu da inhar aka saki mace take jan tsawon lokaci bata samu mijin aureba, mafi yawama saidai suyi aure a wajen ƙauyen. Ko a mafarkinta bata taɓa kawo Baseer zai mata hakanba akan kuɗi.


⚡⚡⚡⚡⚡⚡⚡⚡

Su Baseer anata kwasar garar amarci kam, danma Suhailat ɗin raguwace, daya cika matsa mata tahau raki dacewa zata sanarma Daddynta, shiko yakoma bata haƙuri da lallashi.
Tunda suka tare agidan ba ai sharaba, abinci ko kullum daga gidansu Suhailat ake kawowa, idan sunci sun ƙoshi bazasuyi wanke-wanke ba, sun tara uban kwanuka a kicin sunƙi su wanke.
Yauma suna zaune a falo suna hutawarsu, shi yana zaune itako tana kwance a jikinsa suna kalon film.
Idanunta ta ɗago taɗan kallesa tana yatsine fuska, “Love yaya dai?”.
Cikin tura baki tace, “Love nifa ice-cream nakeson sha wlhy”.
“To love, ya kikeson ayi yanzu?”.
“Mu fita mana”.
“Amma kina ganin baza'ace kin fara fita da wuriba, kofa sati baki cikaba a gidannan”.
Wata banzar harara ta zuba masa, “Kaifa na lura har yanzu ƙauyanci ba gama sakinka yayba, an gaya maka munan muna wannan saka idon da tsarin banzar, ni tashi muje ka shiryani mu wuce Please”.
Maganar ƙauyencin data jefesa dashi ta sosa masa rai, amma saiya danne ya ɗauketa suka nufi sama inda bedroom ɗinsu yake.
Shiyya shiryata ya shirya kansa, sai dai kuma kayan data zaɓa ya saka matan sunyi ƙanana, ya matso inda take zaune yana taje sumar kansa, “Love in nemi alfarma mana dan ALLAH?”.
“Tami?”. Cewar Suhailat dake naɗa siririn gyale a kanta.
Ya ɗan sosa wuyansa yana murmushin yaƙe, “Kayannan ne sai nake ganin kamar sunmiki ƙanana, da da yanzufa akwai banbanci”.
“Tofa” tafaɗa cikin taɓe baki damasa wani kallon banza, kafin tacigaba da faɗin, ”Sokake na zuba dogon hijjabi uwa wata matar liman? Kaiko in baka ajiye wannan rayuwar ƙauyenba ALLAH zamuyita samun matsala dakai, idan bazaka iya bina a hakaba yi kwanciyarka agida saina dawo”. Taja key ɗin mota da bag tai gaba abinta.
Cije leɓe yay cikin tsantsar takaici, wai dama haka yarinyarnan take bai saniba, yay ƙwafa tareda binta da ɗan gudu yana ƙwala mata kira.
Harta tada motar ya fiton gefenta ya buɗe ya shiga, ta taɓe baki da ɗauke kai.
“Love kawo nai driving ɗin, bai kamata ace kiyiba”.
Horn tayi mai gadi ya buɗe mata gate, saida ta fice a gidan kafin tabashi amsa, “Bana buƙata, zanja kayata”.
Shiru yay baikuma cewa komaiba, sai dai ƙasan ransa mamakinta yakeyi, wato lulluɓin biri taimasa da fatar kura akan hallayarta, aiko dai bazai ɗauki rainiba, dolene ta girmamashi a matsayinsa na mijinta.
Har suka isa wajen shan ice-cream ɗin babu wanda ya sakema ɗan uwansa magana, ita waƙarma data saka taketa bi a hankali, shiko takaicinta yagama kawo masa maƙoshi.
A wajen shan ice-cream ɗinma itace tai komai shi yana tsaye zororo tamkar wani yaronta, sai da aka gama haɗa musune tamiƙa masa ya ɗaukar musu suka sami wasu kujeru acan gefe suka zauna sha.
Sunɗan jima a wajen, yanda taga ƴammata suna kallon Baseer ɗinne ranta ya ɓaci, dan haka tace masa ya tashi su koma gida.
Murmushi yay danya kula dai kishin kallon da matan ke masane yasata faɗin su tafi, sai yakuma ƙara bada faɗi yana taku ɗai-ɗai danya tunzura zukatan ƴanmatan.
Yanzunma ita tajasu zuwa gida, sai kumbura fuska take wai ita fushi, da sukazo gida saida yayta lallashinta sannan ta fara kulashi.
“Wai Love dattin gidannan bai ishekiba ne?”.
Kallonsa tayi a wani yanayi, “Mikake nufi to? Koni zan gyara?”.
“A'a bance kezaki gyaraba, amma kibari ƴan aikin da Mami tace akawo suzo hakanan mana”.
Zaune tatashi daga kwanciyar da tayi tana yatsine fuska, “Kasan mikake faɗa kuwa Baseer? Kana tunanin zanbar wata ƴar aiki mace tarayumin a gida ne? Idanma tunaninka kenan ka canja shawara, sai dai idan maza za'a kawo wlhy”.
Babu shiri ya waro ido waje da matuƙar mamakinta, “Maza kuma love? Nanfa gidan matar aurene ya za'ai maza suzo suna shigar mana ɗakuna? Idanma sabodani ne wlhy ki kwantar da hankalinki, nifa babu wata mace data isa ɗaukar min hankali bayanke, dagake babu ƙari dan kinriga kin tsare ko ina baki barma wata fili ba”.
“Eh nayarda da wannan, amma dukda haka babu wata ƴar aiki da za'a kawo a gidannan”.
“Amma Love idan ba'a kawoba wazai mana wannan aikin, kedai ba iyawa zakiyiba, kibari ko tsohuwa akawo to”.
“Tsohuwa? To lallai kanka ya kwance wlhy, ai waɗanan tsoffin sunfi kowa illa a gida, dan jikokinsu suke kawowa ko ƴar ƴar uwarsu, kainifa nagama magana wlhy, idan baka yarda akawo maza ba saidai karinga aikin da kanka”.
Ba karamin sakin baki yayba yana binta da kallon mamaki harta gama haye benen, wai wannan yarinyar mitake nufi dashine? Tunma kan ayi nisa tafara maidashi tamkar wani yaron gidanta, to lallai zai saitata a hanya bazai ɗau rainiba.
Ya daɗe zaune a falon yana saƙawa da kwancewa kafin yamiƙe yanufi kicin ɗin, dan harga ALLAH bayason ƙazanta a rayuwarsa.
Zagewa yay yafara wanke-wanken, yagama tsaf yagyara kicin ɗin yadawo falo, ina faɗa muku saiga Baseer yagyare gida tsaf yay morping, sai faman riƙe kugu yake na gajiya, Suhailat kam tanacan miƙe a gado tana kwasar barcinta ma batasan bikin dayakeba.

(Mijin Hajiya sai haƙuri🤣zafafa fans na gaisheka da ƙyau😝).


⚡⚡⚡⚡⚡⚡⚡⚡⚡⚡⚡

*_Lagos_*

Da safe Ummukulsoom tunda tai sallar asubahi tai azkar sai bata kwantaba, ɗakinta ta gyara tsaf sannan ta fito falo, A'i ta iske tana shara, tai mata sannu yayinda itama A'i ta rissina ta gaidata, fuskar Ummu ɗauke da fara'a ta amsa mata, babu inda tasani a gidan ko kicin, dan haka ta zauna tana kallon A'i na cigaba da gyaran falon, sai fira da sukeyi jefi-jefi.
A'i ta kammala gyaran falon tsaf, dan haka Ummu taje ɗakinta ta ɗako turaren wuta dana ruwa takawo mata aka saka, tareda waɗanda suka gani, dandanan falon ya ɗauki wani ƙamshi na musamman.
Cikeda bariki A'i tace, “To Uwar ɗakina saura ɗakinki dana oga ko”.
Murmushi Ummukulsoom tayi, “A'a Baba, wannan zan dinga gyarawa insha ALLAH, aikin ai sai yay miki yawa”.
“A wane yawa Uwar ɗakina? Shifa aka turoni nayi, indai bazaki iyaba zan dinga gyarawa”.
Ummukulsoom ta girgiza kanta alamar a'a, dan bata manta maganar baba halima datace ko acan bai yarda ƴan aiki su shigar masa sasheba sai ƙannensa.........
Motsin da taji a bayantane ya katse mata tunani ta juyo da hanzari, shine sanye cikin kayan training ash, zubewa A'i tai tana gaidashi, ya amsa sau ɗaya yay gaba abinsa.
Sanyi ƙalau jikin Ummu ya ƙarayi, gashi ko gaisheshinma ita bata samu damar yiba.
A'i tace, “Uwar ɗakina bara to na gyara nawa ɗakin nima”.
Kai kawai Ummu ta iya ɗaga mata, A'i na barin wajen ta sauke ajiyar zuciya da saƙa wasiƙar jakinta, ta bisa ta gaidashi kota bari saiya sake fitowa? Tarasa matsaya, dan haka tacigaba da zaman falon.
A'i ma dake laɓe gajiyatai da tsaiwa takoma cikin ɗaki ta zauna tana neman Number Momcy a waya ta fesa mata labari harda na jiya.

Ummukulsoom na nan zaune kusan awa ɗaya saigashi ya fito sanye cikin Uniform, yayma Ummukulsoom masifar ƙyau, dan haka ta shagala da kallonsa batareda ta saniba.
Bakinsa yaɗan taɓe yana lumshe idanunsa ya buɗe a kanta, kafin ya zauna kujerar dake kusa dashi.
Anan Ummu ta dawo hayyacinta, ta zamo daga kujerar tana gaidashi.
“Lafiya” kawai yace, takula wannan shine salon amsa gaisuwarsa dai, bata tashi a ƙasanba shikuma bai miƙeba, magana yakeson yi amma yakasa buɗe baki. Kusan mintuna biyar suna a haka kafin ya fisgota da ƙyar, “Maman Ahmad zatazo anjima ta nuna miki tsarin gidan, akwai maiyin abinci dazai dawo anjima”.
Yanda yay maganar a dunƙule sai Ummu ta gaza fahimta, amma dukda haka saita ɗaga masa kai kawai alamar amsawa, yakuma jan wasu seconds ɗin kafin yacigaba da faɗin “Naje Abuja ni”. Yana gama faɗa ya miƙe.
Kan Ummu a ƙasa tace, “ALLAH ya tsare ya saukeka lafya”.
Akan laɓɓansa ya amsa yana ƙoƙarin ficewa, harya kai ƙofa sai kuma ya tsaya yaɗan juyo ya kalleta batareda ya iya cewa uffanba.
Mikewa Ummu tayi ta nufosa, danta lura kiranta yakesonyi amma bakinsa ya gagara hakan, zata risina yay mata nuni data miƙe tsaye, mikewar tai, saidai kanta a ƙasa ta gaza kallonsa.
“Akwai kuɗi a ɗaki, idan Desmond yazo kibasa yayo cefanen duk abinda ake buƙata”.
Bai jira cewarta ba ya fice abinsa.
“Ni Ummukulsoom naga takaini, wanene kuma desmond ɗin?”.
Babu mai bata amsa dan haka takoma ciki bayan taji tashin mota alamar sun tafi.
A'i dai nacan ɗaki zaune batasan mike faruwa ba, dan batayi zaton fitowar Amaan a wannan lokacinba.
Ɗakin nasa Ummukulsoom tayi yunƙurin zuwa ta gyara saiga ƴar aikin maman Ahmad yauma takawo musu abinci, godiya tace tai mata ita kuma tanufi ɗakin nasa danta gyara.
Yanzu ne tasami nutsuwar yima ɗakin kallon tsaf, komi Coffer Color ne, yayinda bedsheets yakasance fari, hakama labulaye, ƙamshine mai daɗi ke tashi tamkar ba ɗakin namiji ba, gashi babu wani tarkace ko kayan hauka irin nasu Yaa Ameer datake shan wahalar gyarawa. Tsaf tazage ta gyara ko ina ta bajeshi da ƙamshi har toilet ma, ta jinjinama tsaftarsa gaskiya.

★★★★

Sun gama karyawa babu jimawa saiga maman Ahmad, sosai Ummu tai murnar ganinta, bayan sun gaisa maman Ahmad ta zagaya da ita lungu da saƙo na gidan, tareda nuna mata komai dalla-dalla, suna cikin zagayen ne Desmond kukun gidan yadawo, dama yaje duba mahaifiyarsane da batada lafiya shiyyasa su Ummu basu iskeshiba a gidan.
Yayi matukar murna daya iske boss ɗinsa yayi aure, dan shi bai faɗa masaba, Ummukulsoom dai aranta tace da matsala kenan, dan desmond bayajin hausa sai turanci da yarensa na ƴan Calaber, sai ƴar haukar hausarsa dayake ƙwaɓowa itama tsinta yake wajen Amaan idan sunayi da Attahir ko waya.
Kuɗi ta ɗakko masa kamar yanda Amaan ɗin yace, ya amsa yanufi kaduwa cefane cikin matuƙar ɗokin wannan mata ta ta boss.
Har yamma maman Ahmad na gidan tana kuma koya mata abubuwan daduk ya dace, tareda bata shawarwari, dan ta lura Ummukulsoom tanada bukatar koyan abubuwa, itakuma harga ALLAH yarinyar tashiga ranta sosai.

Da daddare Desmond yay musu girki kamar yanda yay musu na rana dama, ita kaɗanma ta iya tsakura ta kwanta, dan sosai kewar babanta ke damunta, gashi matsalar ma ko Number sa bata riƙeba, data amshi ko wayar maman Ahmad ce ta kirasa sun gaisa.


⚡⚡⚡⚡⚡⚡⚡⚡⚡⚡⚡
*_KADUNA_*

Koda Suhailat ta tashi taga aikin da Baseer yayi sai abunma yabata dariya, ta kallesa cike da tsokana tana faɗin “Lah ashe Love ɗin nawa ya iya aikin mata, aiko kahutar da kuɗin Daddy wlhy”.
Takaici ya hanashi amsa mata ma, yay hayewarsa sama ya barta tana tuntsurar dariya, a ranar yini guda iskancin dataita masa kenan.
Washe gari su Najeeb sukazo musu yawo, yini guda a gidan sukayi suna shan hira, abinci ma sai sawo musu akayi, dan Suhailat dai bayi zataiba, gidanma yau da safe Baseer ne yaɗan gyara inda zai iya, amma dayaga tashiga barci da rana yayta zulama su Areef ƙarya🤣😝.
Washe garima dai baƙin sukai, ƴan uwan Suhailat sukazo su Amrah, ranar dai Baseer sai barmusu gidan ma yayi yafita gararanba agari dan babu inda ya sani, su Najeeb kuma duk ƴan Zaria ne.
A wajen yawonsa yasamo budurwa mai suna Lubna, yarinya ƙyaƙyƙyawa ƴar manya, Number ya amsa amma shi yaƙi bata tashi, yace mata idan ya kirata ta gani.
Sosai Lubna tamutu akan Baseer, shiko sai fankama yake da huruwa yana basarwa.
Sanda ya dawo gida su Amrah sun wuce, hakanne yasaka Suhailat yin fushi tanata masa masifa itafa bazata ɗauki wannan yawonba gaskiya. Haƙuri yayta bata dan daya fara mata ƴar masifa irin shi miji ɗinnan saita ɗauki waya zata kira Daddynta, dole yakoma lallashinta da bata haƙuri sannan ta saukko sukacigaba da ƴar soyayyarsu.

Haka rayuwar tasu take tafiya ba a daidaiba, dan kuwa Suhailat ke acting a gidan like miji, shiko yazama mijin hajiya, sai abinda tace takeso ake a gidan, randa suka cika sati biyu saiga kuku daddynta ya turo mata, abin ya matuƙar sosa ran Baseer, sai dai kuma babu damar magana kan ran Suhailat ya baci.
Ƙiri-ƙiri ta hanashi fita, idanko ma yasamu ya fitan minti talatin yay yawa take danna masa kira ya dawo gida, yaukam ma dazai fitan motarsa babu mai catai yaje yahau napep, dan batada kuɗin bashi yasha mai.
Dole sai haƙura yay da fitar kuwa, dan harga ALLAH bazai je ya hau napep ba da ajinsa da komai😹⛹‍♀............✍🏻


Mungode kwarai da gaske da lamuninku, waɗanda suka kiramu sukai mana gaisuwa da waɗanda sukai mana ta chart, harma waɗanda basu manaba duk mun gode ALLAH yabada ladan zuminci. Shikuma ALLAH ya gafarta masa ya yafe masa da dukkan iyayenmu da al'ummar musulmi tundaga zamanin ANNABI ADAMU har kawo yau😭🙏🏻, ALLAH ya ƙara mana haƙurin rashinsu, Muma ALLAH ya wajabta tsoransa a zukatanmu ya ɗauki ranmu muna masu imani da soyayyar MANZON ALLAH (S.A.W)😿, ALLAH ya gafarta mana baki ɗaya


NO. 16

..........Matan Barrack ɗin sunata shigowa ganin Ummukulsoom amarya, Hausawa da ƙabila, waɗanda basajin hausa iyakarta dasu gaisuwa, saikuma taita murmushi.
Da yawansu sukan ƙunshi gulmar mamaki a ransu, basu taɓa zaton ganin matar Ajiwa yarinya irin hakaba, sun zata zasu gata wata babba irin sa'arsa ɗinnan.
Ummu dai bama tadan sunaiba, damuwar gida da tabon da Baseer ya barmata arai sune maƙale a ranta, duk da dai tana ƙoƙarin cire Baseer ɗin da ƙarfin tsiya.

Yau ma dai bayan ta tashi barci ta kimtsa ɗakinta da jikinta, fes ta fito cikin doguwar riga ta shadda ruwan gwaiduwar ƙwai, kayan sun mata ƙyau dukda babu wata kwalliya atare da ita, daga fauda sai lipsgloss data saka, sai ƙamshinta mai daɗi dake tashi a jikinta.
A falo ta iske A'i na faman Morping, suka gaisa cikin girmama juna tamkar gaske, Ummu dai batada matsala da A'i, saima yabon halayenta da takeyi, girmamata kuma takeyi sosai kasancewar a haifema zata iya haihuwar kamarta.
Bata zaunaba ta wuce dani danta karya. A'i tabita da ido tana wani taɓe baki, itafa harma tafara tsarawa kanta ƴarta zata kawo gidan itama a dama da ita, idan da rabo sai aci wannan daular duniyar da ita tazama matar soja. dan tun randa tazo gidan tai tozali da Amaan taji a ranta sun dace da ƴarta, dan Aina'un tata ƙyaƙyƙyawace san kowa ƙin wanda bai samuba.
Ummukulsoom dai batasan hidimar da A'i keyiba ma ita, anutse tai breakfast ɗinta ta taso tadawo falon da A'i kesa turaren wuta. Kasancewar babu nepa saita kwanta cikin kujera tana tunanin rayuwa da sauyin da take zuwa dashi akowacce rana.
Cike da salon iya bariki A'i tazo ta zauna a falon

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login