Showing 99001 words to 102000 words out of 176055 words
da wanda nakeyi dan shiba ya sani balle yasan na tsanesa, zuwa yanzu ba zuciyar fushi bace a ƙirjina Lubna, ta ɗaukar fansace, wannan dalilinne yasani zuwa gareki domin mu haɗa hannu wajen maida murtanin bashin gaba. Badan Basiru zai gagareni bane ba, sai dan nasan irin tabon daya barmin kema shine ya barmiki, kenan ya dace mu haɗa ƙarfi da ƙarfe wajen tabbatar masa da mata ba hularsa bace da zai ɗauka a sanda yaso yakuma aje a lokacin da yaso, amma in babu ra'ayin hakan a tare dake karki damu zan koma, na ida cikar burina, na gode da tarbar mutunci da kikaimin sosai, sai gani na biyu.......”
“Indai wannan shine burinki nima shine nawa, dan nayi alƙawarin sai Baseeru ya ƙwankwaɗi madarar baƙinciki fiye da wadda ya bani na ɗanɗana, na tsani cin amana, hakama yaudara”. Lubna ce mai maganar a fusace.
hakan ya saka Suhailat dakatawa daga shirin fitar da takeyi, ta juyo gaba ɗayanta tana kallon Lubna fuskarta shinfiɗe da murmushi, ƙaramin ɗan yatsanta ta miƙa mata, Lubna ta tako har gabanta suka ƙulla tareda sakarma juna murmushi.
Komawa sukai suka sake dasa hiran basiru da rayuwar da kowa tayi dashi, anan ma Lubna ke sanarma Suhailat ta haihu da Basiru ita, yarinyar tana nan Amal.
Sosai Suhailat ta tausayama Lubna da yarinyar kanta da batai dacen mahaifiba.
Sun yanke hukuncin yanda zasu samo Fannah itama, dan daga baya bayan rabuwar Lubna dashi itama takejin ya auri Fannah, a tarema ya sakesu.
⚡⚡⚡⚡⚡⚡⚡⚡⚡⚡⚡
Tunda ta fito daga lecture ta hangesa tsaye jikin motarsa, sai dai ta yauma ba irin ta shekaran jiya bace, sanye yake cikin suit kalar sararin samaniya, ƙyaƙykyawane ajin farko, sannan ɗan gayu, yau kwanaki huɗu kenan daya fara bibiyarta, sai dai sam taki saurarensa, amma bawan ALLAH yaƙi yin zuciya.
Ta ɗan sauke numfashi tareda cigaba da takowa inda yake, dan yau taji a ranta zata sauraresa taji da wacce yazo shikuma.
Sanye take cikin atanfa ruwan fauda siket da riga, sai hijjab ɗinta da kaɗan ya wuce cinyarta mai hannu shikuma ruwan madara, tayi ƙyau sosai dukda kamar kullum babu kwalliya a fuskarta.
Tunda ta dososhi murmushi ya faɗaɗu akan fuskarsa, yarinyar ta haɗu ta ko ina, kallo ɗaya ta wuce da dukkan tunaninsa, gata da jan aji, dan itace mace ta farko a rayuwarsa da zaice yanata bi tana yarfashi amma yakasa yin fushi......
“Assalamu alaika” zazzaƙar muryarta ta rangaɗa masa sallama.
Eyeglasess ɗin fuskarsa ya zare yana murmushi, “Wa'alaikissalam gimbiyar mata, Wannan juma'a tazo min da babban alkairi, ga farin wata gab da ni yana haska min hanya”.
Basarwa Ummukulsoom tai tamkar bata fahimcesaba, sai ma cewa da tai, “Wai kai bakayin zuciyane?”.
“Zuciya kuma Babie? Ai akanki ki ɗauka banida zuciya irinta fushi”.
Murmushi Ummukulsoom tayi ba tare da ta shirya ba, ta ɗauke kanta gefe kawai tana faɗin, “Nifa bana zama inuwa ɗaya da maza”.
“Babie aini kece inuwa ta, dan ALLAH a tausaya mini abarni na shiga daga ciki, zafin rana na gasani, sanyin kuma da ya kasance ba na inuwarkiba cutarwace a gareni, aji dani raɓar ƙankara tana neman daskarar da jinina”.
Ɗan kallonsa tayi kafin ta ɗauke idanunta, “Zan duba naga idan ka cancanta”.
“Yeeees!” yafaɗa yana dunkule hannusa.
Hakan sai ya bama Ummukulsoom dariya, tai murmushi mai kayatarwa da har ya bayyana jerarrun haƙoranta farare tas.
Duk yanda taso ƙin binsa saida ya kalameta da daɗin baki ta amince ta shiga motarsa.
Suna tafiya yana janta da hira game da kanta, a taƙaice taita bashi amsa, yayinda shikuma yake sanar da ita wanene shi kai tsaye.
A gate ɗin farko tace ya ajiyeta, dan tasan baza'a barsa ya shiga Barrack ɗinba.
Fitowa yay da kansa ya buɗe mata ta fito, harda wani ɗan sunkuya mata irin na girmamawa, hakan ya sata sakin ƴar siririyar dariya......
Cak numfashin Amaan dake tsaye a ƙofar gate ɗin ya nemi ɗaukewa, tsaye suke shida Attahir da wani abokinsu a wajen, da alama wani abun sukeyi, Attahir ne kawai sanye da complet Uniform a jikinsa da ɗayan abokin nasu, Amaan kuwa wandonne kawai sai dark green ɗin t-shert data kamashi sosai.
Attahir da yaga Amaan ya tsirama waje ɗaya ido fuskarsa na kuma tsukewa sai abin ya bashi mamaki, dan haka ya kalli inda ya ke kallo shima.
Ummukulsoom ya gani tsaye da ƙyaƙyƙyawan saurayi tana zabga murmushi waya a hannunta tana dannawa, yayinda saurayin shima yake murmushin hakoransa waje yana kallonta, ta mika masa wayar dake tabbatar da tasace, da alama Number ɗinta ta saka masa.
Attahir ya janye idanunsa daga kansu ya maido kan Amaan da Abokinsu ke tambayar lafiya?, sai dai sam da alama hankalinsa bama ya wajensa.
Taɓasa Attahir yayi, ya lumshe idanunsa ya buɗe batare da ya kalli Attahir ɗinba, zuciyarsa wani irin zallo take tamkar zata fito waje, ga kansa yay masa wani irin masifaffen nauyi, sam baya fahimtar jawabin abokin nasu.
Sarai Ummukulsoom taga su Amaan tun lokacin da zata fito a motar Umar, hakan ne yasata biye masa dan ganin yanda gaba ɗaya hankalin Amaan ya dawo kansu, saboda ta sake ƙular dashi harda ɗagama Umar hannu da zai tada motar, bata bar wajenba sai da taga motarsa ta hau titi sannan ta saita kanta ta tako a hankali cikin nutsuwarta zuwa gate ɗin.
Sai da tazo saitinsu sannan ta kalli inda suke, da Amaan ta fara haɗa ido, amma tsabar wulaƙanci sai catai “yaya Attahir barka da yammaci”.
Murmushi Attahir yayi yana amsata da faɗin “Yauwa autan Ummi, an dawo lafiya?”.
“Lafiya lau yayana”. Ta faɗa tana yin gaba abinta tareda watsama Amaan harara, Abokinsu kuwa yabar wajen tunkan ta ƙaraso.
Ko motsi Amaan kasa yi yayi, dan tabbas ba'a taɓa masa irin wannan rainin ba da Ummukulsoom ta masa yau, shi bama wannanba, Ubanwaye wanda ya sauketa a mota? Dolene ya takama wannan yarinyar birki, inba hakaba wlhy zataja yayta karya ƴaƴan mutane a gabanta....
Yanda yake fidda numfashi da sauri-sauri ya saka Attahir kallonsa, fushi da tsantsar fusata ya hanga a cikin ƙwayar idanunsa, “Ajiwa lafiya kuwa?”.
Ƙin takama Attahir yayi, saima yabar wajen gaba ɗaya.
Attahir yay ƴar dariya yana girgiza kansa, zuwa yanzu kam yagama yarda Ajiwa yagane Ummukulsoom, tsabar miskilanci ne ya hanasa nuna hakan...........✍🏻
NO. 35
...........Tun daga wannan ranar abubuwa suka nemi rikicema Yaa Amaan, yay bala'in sakama Ummukulsoom ido, yayinda ita kuma ta samu hanyar muzgunama zuciyarsa da salo kala-kala, ita duk tana yine saboda fahimtar kamar ya ganeta, duk dama yana yawan tafiye-tafiye shida Attahir, amma dukda haka kowanne motsinta ana sanar masa ba tare da ita tasan ana bibiyar rayuwar taba.
Karatu kam ta maida hankalinta sosai, fatanta ta samu dukkan nasara, ƙawayenta kam basa wuce abokan karatun ta, duk wanda kuma ya tareta da kalmar so takan nuna masa karatune ya kawota. Ita da Umar kam, kamar wasa sai soyayya da shaƙuwa ta shige tsakaninsu, ita Ummu ma tun tana masa komai da wasa har lamarin yafara shiga jikinta, sai dai wanda ya nutsune kawai zai fahimci shaƙuwace a ranta ba soyayya ba.
Sai wani lecturer ɗinsu Abdul-wahed shima fa ya kafa ya tsare, Bahaushe ne amma girman lagos, kuma saurayi da dukkan mace tagani saita ƙyasa, sam shima mutum ne da baya harkar mata, ko a makarantar ƴammata suna shakkar kaimasa wargi harma da mazan, amma tunda ya ƙyallara idonsa akan Ummukulsoom sai labarin ya canja salo, tun ana ƴar kallo hardai ranar yasa aka kira masa ita taje ta samesa har office.
Ita kanta sai da abin ya bata mamaki, dan shi mutum ne da mafi yawan ɗaliban kance yanada shegen girman kai, ita kanta ta jefesa da wannan sunan, amma a yau sai gashi a gabanta yana fara'a da jaddada mata kalmar wai yanason ta zama wata sashe ta rayuwarsa, gaba ɗaya kuma ya ɗaureta da jijiyar wuyanta akan zai jirata har sai ta kammala, sannan kuma bazasu ringa wani mu'amula a cikin makarantar ba, idan yana buƙatar ganinta zaizo har gida ya sameta, shima zuwa gidan ba yanzu ba, sai sun gama sabawa ta waya tukunna.
kasa koda motsi tayi, harya ɗauki wayarta ya saka Number sa ya kira tasa shima yaga tata.
Har Ummukulsoom ta dawo gida abin na dama mata lissafi, guy ɗin yakai dukkan yanda mace bata zato, dan harga ALLAH itadai anata tsarin ya haɗu, kuma sai akai sa'a zuciyarta take kai kawo akan lamarinsa.
Bily dai kasa daurewa tayi saida ta takura mata ta sanar mata damuwarta.
“Ummukulsoom kuma ke kina sonshi kenan?”.
Ajiyar zuciya Ummukulsoom tayi, “To ni Bily mizan ce, danfa haɗuwa bawan ALLAHn nan ya haɗu......”
“Mtsoww, duk haɗuwarsa yakai Yaa Amaan ne, ke nifa ko wannan Umar ɗin haushinsa nakeji, nifa kullum fatana ki koma gidan Yaa Amaan, dan shine yafi dacewa dake ƴar lukutar Ummi”.
Duka Ummukulsoom ta zubama Bily a cinya, “Kefa banza ce, Amaan ɗin mi, wlhy Abdull ya fisa komai ni a wajena. aini yanzu na wuce da saninsa wlhy, kuma kibar kushemin Umari na, inason kayana, ni saurayi nakeso yanzu ba bazawari ba”.
Bily ta taɓe baki tana barin wajen, “gwara da kikace a wajenki, Umar wannan kuma matsalarki ce, insha ALLAHU babu wani mai kai kamar kwakwa dazai mallakeki sai Yaa Amaan, da kike ce masa bazawari kema ai itace”.
Haushi kamar zai kar zuciyar Ummukulsoom, da bily tasan ko sunan mutumin nan batason ji da wlhy bata sake ambatarsa a gabanta ba, sam ta tsanesa fiye da zaton kowa, ganin bily zata fice sai tai saurin maida murtani, “Koda nake bazawara duk wanda ya aura zai tabbatar da sabuwace dal a kwali, shiko ko aure yayi sai matar tace ya taɓa aure, babu kuma wani jawabin da zai mata ta fahimcesa”.
Haɓa bily ta riƙe tana bin Ummukulsoom da kallo, “Oh ni wai Bestie yaushe kika fetsare har irin hakane?”.
“Zo na faɗa miki”. Ummukulsoom ta faɗa tana shigewa bathroom.
“A'a nikam kinfi ƙarfina, bazaki iskantani ba wlhy”.
Murmushi Ummu tayi daga cikin bayi saboda jiyo maganar Bily.
★★★★
Da daddare duk suna falo suna kallo, Ahmad na gefe yana Homework saƙo ya shigo wayar Ummukulsoom, wayar bily ta miƙa mata, dan tana hannunta tana tura mata wasu apps.
“K cigaba kawai, maybe ma mara amfani ne”.
“A'a kedai karɓa, dan A-Waheed ne, inba hakaba na goge wlhy”.
Warce wayar Ummu tayi da sauri tana faɗin, “ƴar baƙin ciki ashe rabin numfashi nane”.
Maman Ahmad tai dariya itada Bily, sungafa wannan Abdul ɗin kamar yazo da ƙarfinsa, maman Ahmad batason shiga rayuwarta ne kawai, amma idan san samune kar Ummu tayi soyayya da kowa, fatanta takoma gidan Amaan, amma basuda hurumin cemata hakan, dan yanzu dai tanada ƴancin zaɓama kanta miji ko a addinance.
Ummu kam tashi tai ta bar falon sannan ta buɗe saƙon.
_Duniya babban wajene mai yawan al'umma da wasu halittu, sai dai zuciya ta fita faɗi, soyyayya kuma itace al'ummar zuciya, to ni tawa babu kowa a cikinta sai ke kaɗai gimbiyar mata_
*Naki UMA*.
Ummu ta maimaita saƙon yafi sau goma, sai murmushi take zabgawa, tai kissing wayar tana lumshe idanu, hundred percent A-waheed yayi.
Bata maida reply ba ta share kawai.
★★
Washe gari da taje makaranta koda ya shigo musu class ko a fuska bai nuna yama santa ba balle saƙonsa daya tura, hakan yasa itama ta basar tamkar batama gansa ba, ya gama ya fita abinsa.
Tun daga sannan Abdul-wahed yazama abokin hirar Ummukulsoom ta hanyar turo mata saƙo a kowane dare, ko fashin hakan bayayi, kullum kuwa akwai salon da massege nashi ke zuwa dashi, kafin aja wani lokaci yagama saye dukkan zuciyarta, sai dai sam maganar fatar baki bata haɗasu idan taje school, kuma bai sake kiranta Office ɗinsa ba, hakama a waya bai taɓa kiranta ba sai dai masseges da kullum baya gajiyawa.
Da farko abin ya fara damun Ummukulsoom, amma daga baya saita zauna ta nutsu, tareda da yimasa uzuri akan shikuma nasa salon soyayyar kenan, to aiko zata tabbatar masa ta fisa ƙwarewa.
Duk yawan masseges ɗin da yake mata bata taɓa masa reply ko sau ɗaya ba, hakan kuma baisa ya gajiya ba. Tsakaninta da Umar kuwa suna tare abinsu.
★★★★
Ɓangaren Amaan kuwa zuwa yanzu ko haɗuwa sukai da Ummukulsoom ko kallon inda take ba yayi, dan yakula raini na neman shiga a tsakaninsu, ya maida hankalinsa gaba ɗaya ga aikinsa, bama sa haɗuwa sai lokaci-lokaci, dan makaranta kan hanata yini a Barrack ɗin itama.
Yau ta kasance litinin, kamar yanda ya saba bakinsa ɗauke da azumi, tun 4pm ya baro office ya koma gida.
Sanin da Desmond yayi duk mafi yawan irin waɗanan ranakun yakanyi azumi sai yake tambayarsa miza'a masa na shan ruwa.
Yana falo kwance tunda ya dawo daga sallar la'ar, ba barci yakeba amma idanunsa na lumshe, desmond da tun ɗazu ya ke tsaye yana masa magana ya sake maimaitawa,
“Boss miza'a girka maka na buɗa baki?”. Yay maganar a ɗarare, dan ya lura a kwanakinnan abu kaɗan ke tunzura zuciyarsa ya hau faɗa.
Shiru kamar bai jisaba, sai kuma ya sauke ɓoyayyar ajiyar zuciya tare da furzar da numfashi ya ɗago manyan idanunsa da suka canja launi daga farare zuwa sirkin jaa alamar gajiya na tattare da shi da barci, “Yau kunu nakeso, kaikuma gashi har yanzu ka kasa iyawa, barsa kawai zanje gidan Attahir ”.
“Ok Boss”. ‘Desmond ya faɗa yana barin falon, zuciyarsa cike da mamakin mike damun boss? A gaba ɗaya kwanakinnan yakuma zama shiru-shiru, rashin son maganarsa ya ƙaru, ga faɗa abu kaɗan zai fara juyema mutum masifa.
Waya ya ɗauka ya kira Attahir akan yau zaizo nan yasha ruwa, amasa kunun shinkafa da ƙosai na wake.
Attahir yay murmushi, cike da neman tsokana yace, “ALLAH sarki, wlhy harka bani tausayi, matsalar gwauro kenan ai”.
Tsaki Amaan yayi yana fadin, “Banza kawai magananne”.
Attahir ya kwashe da dariya, “Gwarani a magana na tsaya, wanda ya haɗa abubuwan da sukafi nawa fa? Shi minene sunansa?”..
“Kasa micrephone mana saika tambaya”. Yay maganar yana yanke wayar tareda jan tsaki.
Dariya Attahir ya kuma sanyawa yana janye wayar a kunnensa, ya kira maman Ahmad ya shaida mata danshi yana office bai koma gidaba.
Yamma lis Ummukulsoom ta dawo daga makaranta, lokacin su Bily na kicin suna haɗa abinci buɗa bakin Amaan da itama kanta Ummu ɗin, dan tana azuminne itama, amma na ramadan ne da bata rama ba sai yanzu takeyi.
Bata nemi kowa ba ta shige ɗakinsu itada bily, ruwa ta fara watsawa sannan ta fito, bata wani zaman kwalliya ba, sai mansu mai ƙamshi taɗan shafa sama-sama da ƴar khumra tasa wando da riga masu taushi marasa nauyi, sam kayan basu kama ta ba, dan Ummi ta hanasu saka ƙananun kaya masu bayyana jiki, sai akai sa'a ra'ayin Ummi dana Attahir yazo ɗaya.
Tana shirin fitowa Yaa Zaid ya kirata, murmushi kawai tai tareda ɗagawa suka gaisa, har tazo falo ta zauna suna wayane, dama ƙa'idane kullum saiya kirata suyi hira, wani lokacin hirar tai tsawo wataran kuma Ummu ta gajarta ta da cewar zatai karatu.
Ahmad ne da yadawo daga islmiyya ya shigo yana kuka, Ummukulsoom ta yanke wayar tana kallonsa, “Oga Amadi lafiya shigowa gida da kuka kuma?”.
Zuwa yay jikinta ya zauna, “Aunty”.
Ta amsa da “Na'am Amadi angon Ummi”.
“Kinga dai Chizober ce ta dakeni, wai danna bi takan wasansu”.
“To banda neman rigima Amadi inakai ina taka musu wasa? Kaida ka dawo daga islamiyya maimakon kai maza kazo gida ka kawo ladanka saika tsaya ƙofar gidan su chizober, hakan babu ƙyau kajiko, karka sake, ita kuma zanje na kaima Momynta kashedi idan ALLAH ya kaimu gobe kaji”.
Cike da murna Ahmad yace, “Eh auntyna, ALLAH ya kaiki maka