Showing 9001 words to 12000 words out of 176055 words

Chapter 4 - Wutsiyar Rakumi Book 1 Hausa Novel Complete

07 Jan 2025

855

Tunda Ummukulsoom tadawo bata sami zaman yini ko ɗayaba a gidansu na Babban gida, kullum cikin yawon gaida ƴan uwa da abokan arziƙi take da yayyenta da ƴan uwanta na ma'auri, harma da dangin mahaifiyarta dake garin.
Yau dai gidan Murja taje, suna tsakar gida itada surukarta suna ɓarar gyaɗa Ummu tai sallama.
Idanu Murja ta gwalalo na mamaki, kafin ta miƙe cike da zumuɗi tana faɗin “A'a a'a lale marhabun da manya-manya maganin ƙanana-ƙanana, maraba marhabun lalale”.
Murmushi Ummukulsoom tayi tanamai jin takaici a ranta, Murja dukta canja ta fara komawa tsohuwar ƙarfi da yaji, shekara uku kacal da aure, wai ahakanma ita tanajin daɗi saboda mijinta yana zuwa neman kuɗi legas, kuma yana iyakar ƙoƙarinsa wajen yimata abu, dan bashida wani nauyi mai yawa a kansa, babansa ya rasu, mamarsace kawai a gidan sai Murja da yaranta biyu saikuma ƙannensa mata biyu suma duk sunyi aure. Ummukulsoom ta ƙarasa gaban Lamunde surukar Murja ta durƙusa har ƙasa ta gaidata.
Da fara'a Lamunde ta amsa tareda mata bangajiyar gama karatu.
Ummukulsoom tace, “Alhamdulillahi” tana miƙewa.
Kamar idon Lamunde zai faɗo haka tabi bayan Ummu da kallo, tana ganin sun shige Lungun Murja dake a katange saita riƙe haɓa tana faɗin “Ohni Lami, yarinya tazama Uwar mata a gida babu aure, kanada wannan agabanka ai ko barci mai daɗi kabar yinsa”.
Su dai su Ummu basusan tanayiba, sunacan hira ta ɓarke a tsakaninsu bayan murja ta ɗeboma Ummu ruwan tulu mai sanyi, tareda ɗaukar ƙalli ƙaƙau ɗinta na saidawa da takeyi ta ajiye gaban Ummu wai tasha iya shanta.
Dariya Ummu tayi tana ajiye kofin silba datasha ruwa, “wato tawajena kina nan da hali baki sauyaba ko? Yo nama wannan abun cin tuwo ai yau a hanyar bayi zan kwana, wai ina yaran nawane?”.
“Shi wannan ɗan (ɗanta na fari, bata faɗar sunansa saidai tace wannan ɗan😂) yana gidan innarsu karime, da yaranta sukazo ɗazu ya bisu, Amadu kuwa yanzunan su Lance suka fita fashi gidanmu”.
“Ok ƙwarai na gamu dasu, kuma naga Rayya da goyo amma dayake hijjab ta saka nama zata ko ɗan Hadiza ne”.
“A'a Amadu ne, kuɗin ƙalliƙaƙau dasukaimin talla suka kawo, yanzu mikike so na dafa miki? Kinsan ku ƴan gayune ba komai za'a bakuba”.
Hararta Ummu tayi tana faɗin “A'a ƴan mayu ba ƴan gayuba, ni kinsan komi kika bani cizanyi wlhy”.
“To shikenan bara afara sayo miki awara gidan tinenen haruna, dan awararta akwai daɗi, dama yau fate muka tashi da sha'awaryi na tsaki, amma tunda kinzo bara adafa hinkafa”.
“A'a wlhy kuyi fatenku, ni namafi sonshi ai, to kodai munsamu na ukune?”.
Harar Ummu Murja tayi tana shafa cikinta, “Na Ukun lafiya Umma, duka watan Amadu nawa? Dana bani ai, wlhy banida komai, kawai dai sha'awace jiya naje gidan sunan Safare aka wawashe faten bamu samuba, nikuma na saka abin araina shiyyasa nace yau saimuyi, Inna kuma tace itama tanaso”.
“ALLAH sarki, haihuwa ta nawa Safare tayi kuwa?”.
“Ta huɗuce, kinsan ɗanta na biyu komawa yayi ai, yanzu Ukune a raye”.
“Wayyo ALLAH ya amfana waɗannan ɗin”.
“To amin, bara na leƙa nan maƙwafta naga ko ade na nan tasayo awaran”.

Yini guda yau Ummu a gidan murja tayisa, sukasha hirarsu ta zuminci ga fate mai daɗi datai musu, sai bayan isha'i Ummu tabaro gidan.
Tazo tasha masifa wajen baba Yalwa, wai tatafi yawo batazo ta tayata aikin tuwoba bayan tasan batajin daɗi yau da atini ta tashi.
Itadai Ummu haƙuri tabata tai shigewarta ɗaki, babama yana zaune yana saƙar tabarma Uffan baiceba.

Ummukulsoom tacigaba da zaman jiran dawowar Basir, yayinda aketa mata surutun girman datayi, abun na damunta da bata haushi, shiyyasa Gwaggo hinde kullum cikin nema mata maganin baki take, shi kansa baba abun na damunsa, dan haka yasamu mahaifin Baseer akan su tsaida magana a saka rana kodan surutun mutane.
Baban basiru bai musaba, suka kuma kawo kuɗin sallama aka tsaida biki wata takwas, amma idan komai ya kimtsu kafin wata takwas ɗinma za'ayi a huta kawai, yanzu dai dawowar Basiru ake jira.
Hankalin Ummukulsoom daduk wani mai ƙaunarta ya kwanta saboda saka ranarnan, baba ma yasamu ya fara shirin tattarawa zai koma kaduna wajen sana'arsa.
Ummu ta naniƙe akan zata bisa taje ta gaisa Innarsu ƙanwar baba dake kaduna tana aure.
Bai musaba yace ta shirya, itama ta huta da surutan mutane.
Wannan tafiya ta saka su baba yalwa takaici, har suka kasa jurewa saida sukayi tsegumi.
Basu sami amsaba daga baba, ya ɗauke ƴarsa suka nufi kaduna abinsu...........✍🏻

4

...........Kasancewar basuyi fitar wuriba sai gab da magriba suka isa cikin kaduna, koda mota ta ajiyesu a kawo sai suka hau napep zuwa Tudun wada anguwar su Inna Harira ƙanwar baba.
Ita dai Ummu babu abinda take sai kallon hanya, dan wannan shine zuwanta na uku da wayonta dai.

Gidane madaidaici mai jan murfi baba ya tsaya, ya tura ƙofar suka shiga, a soro ya tsaya yace Ummu tashiga sannan.
Da sallama Ummu tashiga gidan, budurwar dake a tsakar gida tana kwashe kayan shanya ta amsa mata, duhun magriba ta rufa, gashi babu wuta shiyyasa bata fahimci waneneba, tace,
“Wacece dan ALLAH?”.
Murmushi Ummu tayi, dan ta fahimci Azizah ce ɗiyar Inna harirah, dukda dai taɗan jima bata gantaba tun bikinsu Azima. Cikin tsokana Ummu tace, “Ƴar yankar kaice”.
Maganar saita bama Aziza dariya, dan haka ta sagale kayan da tafara kwashewa a igiyar tare da takowa inda Ummu take a hanyar shigowa.
Wani ihun murna Aziza ta saka tana faɗin “Kan bala'i Ummukulsoom! Tab wlhy badan fuskarki bata canjaba da ban ganeki ba, sannu da zuwa keda wa?”.
“Nida Baba ne”. ‘Ummu tafaɗa tana nuna zaure da hannu’.
Inna Harirah data idar da salla ta leƙo tanama Aziza faɗa, “Wai Aziza kanki lafiya kuwa? da mangaribar ALLAH kiringa kira mana bala'i a cikin gida? Keda wace Ummukulsoom ne?”.
“Yi Haƙuri mama, wlhy daɗine yasani faɗa ban shiryaba, Ummukulsoom fa ta ɗilau, hardama baba buhari”.
Da sauri Inna harirah ta ida fitowa daga ɗaki tana gyara ɗaurin zani, “Da gaske ɗiyatace yau agidan? Ina yayan shima?”.
“Aiko dai itace wlhy mama”.
Ummu dai dariya taketa musu, yayinda shima baba yay sallama ya shigo.
Murna sosai takuma kaurewa, dan Inna harira taji daɗin zuwan Ummu, dama kullum cikin yima baba tsogumi take akan rashin barin yaransa zuwa wajemta sosai, mazan sunfi zuwa.
Alwala baba yayi yatafi masallaci, Ummu ma haka tayi tata agida.
Sai da suka nutsu bayan baba ya dawo da malam ɗanjuma baban Aziza sannan aka samu nutsuwar zaman gaisawa da taɗin zuminci. Ummu dai bata iya saka baki sai an sakota, saima Aziza dake zungurinta idan taji tayi shiru.


⚡⚡⚡⚡⚡⚡⚡⚡

Ɓangaren Baseer kam Alhmdllh shima yagama jarabawarsa, a yanzu haka satinsu ɗaya kenan, amma yaƙi tafiya ɗilau, wai sai yayi bautar ƙasa (NYSC) ɗinsa sannan yahuta gaba ɗaya kenan.
Innarsa bataja maganarba, ta shirya taje ɗilau ta sanar musu da yanda sukayi da Baseer, aiko mahaifinsa ya shirya da kansa yabita zaria n, saida yayma Baseer tsiya ta fitar hankali sannan yashirya suka koma ɗilau da baba, babban baƙin cikinsa ma baiyi sallama da Suhailat ba saita waya.
Abin mamaki tunda Baseer ya dawo ɗilau ya nane a gida baya fita balle kai tunanin zai nemi hanyar gidansu Ummu yaje ganinta. Hakan da iyayensa suka ganine ya sasu zaunar dashi sukai masa bayani gameda aurensa da Ummukulsoom da har an tsaida rana.
“Baba an tsaida ranafa? Miyasa ba'a bari nadawo anji ta bakinaba? Wlhy ni zanmafa cigaba da karatunane na mastas (masters)”.
“Kai kasan wani masta basiru, aure dai mun ajiye rana kuma babu fashi, tun watan jiya ma an fara ginin gidanka a faƙon amare”.
“Inna ban ganeba, ni aka farama gini a garinnan? To na ƙasa kona siminti?”.
Wane shege kabama kuɗin sayen simintin da za'ai maka ginin bulo da bulo? Basiru wlhy karka kaini wuyafa, bar ganin muna lallaɓaka, kai bazaka dawo cikin hankalinka bane waishin? Wane irin ruɗi duniya da ganga sheɗanne ke buga maka? Banda rashin hankalima inakai ina yarinya ƴar birni ƴar masu kuɗi? Kai kanama ganin iyayenta zasu bakane......?”
“ALLAH baba zasu bani, naga idan na auri Suhailat kumafa zakuji daɗinnan, dan ɗaukeku zanyi na maida binni.”
“dalla rufama mutane baki shashasha kawai wanda baisan ciwon kansaba”.
Shiru basiru yayi yana ɓata ƙyaƙyƙyawar fuskarsa fara tas.

A ranar da yamma ya shirya yaje gidan su Ummukulsoom, bawai dan taji daɗiba kodan shi yana ɗokin ganinta, a'a soyake yaje yaja mata dogon gargaɗi akan tace ta fasa aurensa, dan yasan hakanne kawai zaisa iyayensa su barsa, soyakema yakoma zaria gobe bazai iya zaman ƙauyennan ba wlhy.
Koda Baseru yaje ya aika yaro kiran Ummukulsoom sai yaron yace ai bata nan, jiya suka tafi kaduna itada Baba.
Shiru Basiru yayi takaici na cinsa, haka yabaro ƙofar gidan yanata wani ɗaɗɗaure fuska shi adole mai aji, ko magana wani yay masa a hanya sai dai ya ɗaga hannu yana wani basarwa. Can yakoma bayan gari tafkin da jama'ar ƙauyen ke ɗibar ruwa, yasamu waje ya zauna yana tunanin mafita, ganin wankin hula zai kaishi dare ya yanke shawarar shiryawa yaje zaria koda yini ɗayane ya gana da abokansa su Areef.
Da wannan shawarar yadawo gida yana shaidama innarsa ashe Ummu taje kaduna?.
“Au kaduna taje? Ko shiyyasa ɗazun a gidan raɗin sunan Amina Rashida ke cemin ƴata antafi birni?”.
“Aiko dai inna, nima duk sainaji babu daɗi daban sametaba, inaga gobe idan ALLAH ya kaimu zanje kaduna na yini da yamma saina dawo?”.
”A gaskiya ina bayanka kaje, yanda kusan shekara ɗaya kenan baku haɗuba yakamata kaje, itama zataji daɗi”.
Kallon Inna yayi a kaikaice yana murmushi kawai dashi kaɗai yasan fassarar kayansa, kafin daga bisani ya amsa mata da “to inna”.
Washe gari kam kamar gaske Baseer yay shiri yace musu yaje kaduna, baba harda bashi kuɗin mota, nanko zaria ya yada zango, ko gidan innarsa baijeba yanufi gidansu Najeeb abokinsa.


⚡⚡⚡⚡⚡⚡⚡

Ummukulsoom taji daɗin zuwanta kaduna sosai, balle ga Aziza da suke kusan sa'anni, komai tare sukeyi abinsu, Baba ma washe gari yabar gidan, dan dama ba'anan yake zamaba idan yazo, yanada masaukinsa saidai ya leƙo su gaisa.
Kwanan Ummukulsoom tara a gidan ranar Aziza take ce mata gobe zata koma gidan aikinta, iyalan gidan Alhaji Sufiyan sun dawo daga tafiyar da sukayi.
Ummu dake kwance tana karatun novel ta tashi zaune tareda ajiye buk ɗin, “Ban ganeba Aziza, aikinmi kuma kikeyi?”.
Murmushi Aziza tayi tana cigaba da gugar kayanta da takeyi da dutsen guga na gawayi, “Ummukulsoom kinsan rayuwa irinta yanzu ba'a zama, ballemu rayuwa ta birni bakamar taku ta karkara ba, nauyi yayma baba yawa shiyyasa bayan munyi candy naga da zaman banza gara ko wani abun naɗanyi, akwai makwafciyarmu tana nema ma yara gidan aiki shinefa namata magana ta samarmin gidan Alhaji Sufyan, da ƙyar baba ya yarda nafara, itama mama saida naita roƙonta wlhy, nakan musu share-share da goge-goge sai kula da yaransu, duk wata dubu goma sha biyar”.
Cikin zaro idanu Ummu tace, “Aziza dubu sha biyar fa? A waɗannan ƴan ayyukan kawai?”.
“Wlhy kuwa Ummu, shiyyasa suma su baba suka barni, kuma ga alkairi da wataran haka kawai za'ai miki, yanzu haka ɗan anko da ƴan abubuwa na kwalliyar ƴa mace basai na takurama su baba suminba, da kuɗina nakeyi”.
“A to nima kam ba'a barina baya wlhy Aziza, ni ɗinnan da kina gani an saka ranar biki, ga baba nauyi yamasa yawa shima kuma bawani ƙarfine dashiba, kinga insha ALLAH kafin dai na koma gida wlhy nasamu abin taimakonsa”.
“Hakane wlhy Ummukhoolsum, kuma tundama bikin ansaka da nisa basai kiyi zamankiba har sai lokacin ya matso, kinga ƙya tara ko yayane”.
Haka sukaita tattauna maganar, Aziza nakuma wayar mata dakai gameda aikin. Daga ƙarshe suka sanarma Inna harira.
Shiru Inna harira tayi tana nazarin maganar tasu, dan wannan kam dole ta tuntuɓi yayanta, idan ya amince babu komai sai Ummu ta fara zuwa.
Da daddare Baba yazo gidan bisaga kiransa da Inna harirah tayi masa a waya, bayan sunyi hirarsu ta zuminci saita zayyano masa zancen aiki da Ummu tace zatayi.
Da farko dai cayay a'a, saida Inna harira tai masa bayani na gamsuwa sannan ya fahimci maganar, saima ya amince kai tsaye, yace “Harira to babu laifi, yanzune na fahimci zancen naki, idan ita Ummukhoolsum ɗin taga zata iya sai tayi, fatana dai ALLAH ya karesu daga sharrin wasu ƴaƴan manyan na rashin tarbiyya”.
“To amin yaya, ai lamarinnema yanzu basai ƴaƴan manya ke lalata yaraba, ƴaƴan talakawanma taƙadirane, fatanmu dai ALLAH ya karesu aduk inda suka tsinci kansu”.
“To Amin ya rabbi harira”.

***********

Washe gari inna harira da kanta tashiga gidan Rahine taimata bayani a samawa Ummu gidan aiki dan ALLAH, amma na mutanen kirki irin gidan da Aziza ke nata.
Baki Rahine ta washe tana faɗin, “Wlhy faɗuwa tazo dai-dai da zama, dama maƙwaftan gidansu Alhaji Sufiyan ɗin suna neman mai aiki kuma budurwa kamardai Aziza, kuma suma basuda damuwa, aiko yau ɗinnan ta shirya sainaje na nunata, ALLAH yasa a dace, ina mai tabbatar miki maman Aziza yarinyar zataji daɗin zama gidan Alhaji Mahmud Ajiwa, tsohon sojane mutumin kirki wlhy”.
Murmushi Inna harirah tayi tana cewa “To Alhamdulillahi, babu damuwa bara na tura miki ita kuwa”.
“To tayi maza tazo kuwa mutafi, dan ba'a sakaci da irin wanga dama kar wasu su rigamu”.

Sosai Aziza tai murna dajin gida kusa da kusa zasu ringa aiki, koba komai zasuga juna kullum.
Itama Ummu taji daɗin hakan, dan haka tafara shiri kamar yanda Inna harira ta sanar mata.

★★★★★★★

Ummukulsoom na zuwa ta iske har Rahine tagama shirinta itama, dan haka suka fita zuwa gidan aikin.
Tunda mai napep ya tsaya Ummukulsoom ta saki baki da hanci da idanu tana kallon katafaren gidan, “Oh ALLAH mai rahama mai jinƙai, kiga gini tamkar baza'a mutuba, saima ka ɗauka ba hannune ya ginaba”.
Dariya Rahine tayi saboda a fili Ummukulsoom tayi maganar, “Kinga muje ciki, keda zakiyi aiki acikinsa miye na santi tun yanzu?”.
murmushi Ummu tayi tabi bayan Rahine.
Sai da suka gaisa da mai gadin soja sannan sukai ciki, Duk tsoro ya kama Ummu ganin soja, arayuwarta tana bala'in tsoron soja da ɗan sanda wlhy, kuma batasan daliliba, itadai suna mata kwarjinine kawai.
Rahine ta katsema Ummu tunani da faɗin, “Kinga Ummukulsoom zauna a gaban Fulawarnan nashiga na shaidama hajiya zuwanki sannan”.
Ummukulsoom ta amsa da to.
Kusan mintuna talatin da shigar Rahine saigata taleƙo ta yafito Ummukulsoom da hannu alamar tazo. Tashi Ummu tayi ta nufeta, dama zaman dukya gundureta saboda sojan mai gadin can da take hangowa.
Da ƙyar numfashin Ummu ya daidaita saboda ganin daular dake cikin falon da suka shiga, ga wata hamshaƙiyar mace dukda shekaru sunja gareta hakan bai hanata cake gayuba tamar zata biki. Duk zumuɗin Ummu na zuwa gidan aiki sai taji jikinta yayi sanyi, ta zauna a ƙasa tamkar yanda taga Rahine tayi. Muryarta har ƴar rawa take tace, “Hajiya ina yini, mun sameku lafiya”.
Jitai ba'a amsaba, saita ɗago kai ta kalli hajiyar azatonta bataji baneba. Amma sai tayi karo da idon Hajiya na ƙare mata kallo sama da ƙasa. Kanta ta maida ƙasa ta sunkuyar.
Cikeda isar masu ƙasaita Hajiya Jamila tace, “Minene sunaki?”.
Ummu ta haɗiye wani yawu daya daskare a maƙoshinta kafin tace, “Ummukulsoom”.
Kusan minti biyu kafin hajiya

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login