Showing 21001 words to 24000 words out of 176055 words
ta fasa ƙara da kiran sunanta.
Kafin kace mi matan ƙauyen sun fara turuwar fitowa, hakama tsirarun maza dake a ƙarƙashin inuwa suna hira.
Baban Basiru kasa jurewa yayi, ya sulale yabar wajen yana hawayen da baisan dalilinsuba, yana zuwa gida yace Inna ta shirya subar garinnan.
“Baban talatu kayi haƙuri dan ALLAH, basai munje ko inaba, tafiyarmuce zatasa acigaba da zarginmu akan wannan lamari, narasa mike damunmu nikam yau?”.
Kasa magana yayi yashige ɗaki abinsa.
Koda su Basiru sukaga Ummukulsoom ta faɗi suma sai suka bar wajen, duk dama su su daddyn Suhailat basu san ita bace amaryar, ko gida ƙin komawa yay yabi daddyn Suhailat akan ya karɓo keys ɗin gida dana mota da za'a bashi.
Driver n daya kawo Su Ummukulsoom ne yasa aka sakata amota suka nufi zaria aka kaita asibiti.
Tuni ƙananun magana sun baje ƙauyen ɗilau, yayinda zukatan wasu daga jama'ar gidansu Ummukulsoom tamkar su zuba ruwa a ƙasa susha, har gari ya ɗauki zance, yayinda aka sauya maganar gaba ɗaya daga gidan su Ummukulsoom. Wai ciki tayo a binni shine basiru yace ya fasa bazai auri ƴar iskaba.
Tunfa magana na yawo wasu na ƙaryatawa har tafara tasiri akace Baseru yajiyo zsncen cikin Ummu ne tuni, wai wandama yay mata cikinne ys kawota a mota, shi Basiru bai fallasa asirin zancen bane sai yau da yaga Ummu da ƙwartonta bayan kuma saura kwana uku ɗaurin aure yarage kacal.
Dangin mahaifiyar Ummu wannan magana ta rikitasu iya matuƙa, sai kuka sukeyi, musamman ma Inna laraba, mashin tahau zuwa garin Kudan, dagacan tashiga motar zaria tabisu asibiti bayan takira baba a waya ya faɗa mata asibitin da drivern da su Ummu sukazo dashi ya kaisu.
Alhaji Mahmud yagaji da jiran Isa Driver zasu tafi Abuja, amma shiru babu labarin Isa, gashi lokaci yana ƙurewa, shikuma meeting gareshi na tsoffin ma'aikatan tsaro da za'ai a Abujar domin shawarwarinsu gameda halin da ƙasa ke ciki.
Ransa a ɓace ya ɗauki waya yay kiran Isa yana masa faɗan ina ya tsaya nanda zaria ace har yanzu bai dawoba? Bayan yasan shi yake jira kuma.
“Kayi haƙuri Alhaji, wata matsalace aka samu gameda auren yarinyar dana kawo......” ya kwashe kaf abinda yagani ya shaidama Alhaji Mahmud, ya ƙara da faɗin, “Kuma abinda zai baka mamaki Ranka ya daɗe Alhaji Hussain Abba ne fa”.
Cikin tsantsar mamaki Alhaji Mahmud yace, “Isa Kana nufin Alhaji Hussain Abba dai dana sani na nan anguwarmu?”.
”Wlhy kuwa shi yallaɓai, kasan mutuminnanfa bashida kirki dama, akwaishi da alfahari da dukiya, namarasa ina yaron ya sonsa? Kokuma ƙyawun yaronne ya ruɗi Alhaji Hussain ɗin har yayma ɗiyarsa kamunshi?, ni nama zatafa bashida sauran yarinya mace dukya aurar”.
A tsawace Alhaji Mahmud yace, “Wannan bai dameniba, ina mahaifin yarinyar?”.
“Gasunan cikin tsantsar tashin hankali yallaɓai, dan yarinyar bata farfaɗoba har yanzun”.
Alhaji Mahmud ya dafe kansa zuciyarsa na wata irin tafasa da hanƙoro tamkar zata fito, (damashi akwai baƙar zuciyar tsiya, anan Fodio yay gado tamkar jinin kutare haka suke🙊⛹♀), yace “Haɗani dashi”.
Isa yasan ran maza ya ɓaci, dan haka bai kuma tofa komaiba yaje inda baban Ummu ke tsaye yana sharar ƙwalla a kaikaice yabashi wayar.
malam Buhari bai musaba ya amsa ya kara a kunnensa.
Sama-sama suka gaisa Baba na mamakin wanene....?
Cikin katse tunaninsa Alhaji Mahmud yace, “Nasan baka sanniba bawan ALLAH, amma hakan bazai hanani neman alfarma daga garekaba, kasa a ranka kawai ni ɗan uwankane musulmi wanda aduk inda kake zai kare mutuncinka da kimar ka kasantuwarka mai daraja, ni ne mutumin da yarinyarka tai aiki a gidansa, yanzu driver ke sanarmin komai akan abinda yafaru tsakaninka da mijin da zata aura? Idan har ka amince dani bazan cucekaba balle yarinyarka inason gabani aurenta, kuma banaso a canja ranar ɗaurin auren, kamar yanda kuka tsara wannan juma'ar nakeso ayiɗin”.
Gaban baba ya faɗi, dan dagajin muryar mutumin ba yaro baneba, tayaya zai bashi Ummu kuma, amma dukda baba a tsorace yake dajin muryar Alhaji Mahmud, dan dagaji kasan anyi barden namiji a zamaninsa, sannan yanada matuƙar zafi babu alamar ɗaukar raini a lamarinsa, ajiyar zuciya baba ya sauke, batare da tunanin komaiba yace, “Alhaji na amince, ALLAH ya sanya albarka acikin wannan aure”.
Daga canma sai Alhaji Mahmud ya sauke ajiyar zuciya yana jinjina halin dattako da ƙundunbala irinnan Malam Buhari, yace, “Ɗan uwa nagode da wannan karamci naka ƙwarai da gaske, dukda baka taɓa ganinaba amma ka aminta dani batareda ja'injaba, namaka hakane danna gwadaka dama, amma bani zan auri yarinyarka ba, yarona Fodio nake nemama aurenta dake aiki a garin legos yanzu haka, dan soja ne”.
Share ƙwalla baba yayi wani sanyi na ratsa ransa, dan dama ya amincene saboda bashida wata mafita, ga Alhaji Mahmud ya ɗauresa da jijiyar wuyansa, amma jin bashi bane mai aurenma sai baba yace nikeda godiya Alhaji, dan koba komai dariyar maƙiya zata zama kuka, sannan hawayen marainiya bazasuci gaba da kwaranyaba, ALLAH yasa hakane yafi alkairi”.
“Amin ya rabbi, insha ALLAHU zuwa gobe zan shigo garin, yanzu dai zanje Abuja ne”.
Godiya baba ya ƙara masa sannan suka yanke wayar kawai.
Wannan magana tadan sanyaya ran baba danasu Inna laraba, bayan kamar a wa ɗaya dayin haka kuma Ummukulsoom ta farfaɗo, saidai sunmata allurar barci danta sake samun nutsuwa.
Baba ya sanarma Inna laraba halin da ake ciki, hakanne yasata kukan daɗi itama, koba komai Ummukulsoom zata samu sauƙi, dan kuwa wannan matsalar kaɗai ka iya hanata samun miji a ciki da bai ɗin ƙauyen ɗilau, danma basusan ƙurar data tashiba bayan barowarsu ƙauyen na jifar Ummukulsoom da akeyi da kalmar cikin shege.🤦🏻♀
★★★★
Duk wayar da Alhaji Mahmud keyi hajiya jamila na zaune, hakanne ya saka hankalinta ƙololuwar tashi, jinin jikinta na neman daina zagayawa. Cikin tsantsar firgici ta kalli Alhaji Mahmud daya ajiye wayar, “Abban Fodio nifa ban fahimtaba?”.
Wani kallon banza ya watsa mata, saboda har yanzu ransa a ɓace yake, da ƙyar yabuɗe baki yace, “Ai yanzu zaki fahimta uwar rashin haƙuri, yarinyar datai aiki a gidannan tatafi jiya akan za'ai mata aurene mijin ya fasa, nikuma nace a ɗaura da Fodio...”
Zabura tayi tana dafe ƙirji, “Haba Abban Fodio, karasa wadda zaka zaɓa masa sai ƴar talakawa wadda ta fito daga ƙauye tazo aikatau a gidansu?”.
Baiyi mamakin jin hakan daga garetaba, dan a halayyar jamila sai dai yabama wani labari, kansa kawai ya girgiza ya miƙe, dan idan har yace biye mata zaiyi zaima iya lakaɗa mata duka agaban ƴaƴantane, ya watsa mata harara yana nufar ƙofar fita da faɗin “Idan na aura masa ita kisaka ya saketa take a wajen taron ɗaurin auren”. Daga haka yay ficewarsa kawai.
Saida ta tabbatar yafita sannan tashiga zabga bala'i ɗanta bazai auri ƴar aikiba, banbaminta yajawo hankalin yaranta sukazo suka zagayeta suna tambayarta lafiya?.
Cikin tsantsar takaici da tsanar Ummukulsoom tace, “Wai Dad ɗinkune zai aurama yayan ku yarinyar data bar gidannan jiya?”.
Idanu duk suka zaro waje, Ummayya tace, “To wlhy Asiri taima Dad, kuga munafukar yarinya sum-sum da ita tazo tasha jar miya da shayi, itakuma nata salon cin amar kenan?”.
Aneesa ta karɓe da faɗin, “Yo ai dama ɗan talaka bai iya samun wajeba, mi yaa Amaan zaiyi da wannan karabuti ɗin, wlhy Wutsiyar raƙumi tai nesa da ƙasa, mukaɗaima mun isheta”.
Dariya Bassam ya sanya, duk suka juyo suka kalleshi, ya ɗage kafaɗa da faɗin “Ku miye naku na damuwar?, indai Yaa Amaan ne ubanta zataci a wajensa, saita gwammaci mutuwa tai da zama da wannan”.
Harara hajiya Jamila ta zuwa masa, tana faɗin, “Dalla malam rufama mutane baki, ubanmi kasani daga shu'umancin mace, shi dad ɗinku sauƙinne dashi? Amma ta iya cusa masa hakan a ransa ta asiri. Duk yanda kuke tunanin Fodio baya ɗaukar raini zata iya binsa ta ƙarƙashin ƙasa kamar yanda tabi dad ɗinku ai”.
“Hakane kuma wlhy Momcy”. Cewar Buhayyah.
Aunty Nurse dake zaune tana saurarensu ƙala bataceba, saima cigaba da danna wayarta da takeyi, zuciyarta na mamakin halayyar ƴan gidansu da basa canjawa sai dai ƙaruwa, su dai basu zasu zauna da matarba, amma sunbi sun gallabi ransu, yanzu daka nufi faɗama momcy gaskiya ta nemi ɓata maka ranka, dan hakama ita tazaɓi yin shiru.
Miƙewa Aunty Nurse tayi tana faɗin, “Nidai Momcy shawarar dazan bada shine abi komai a sannu, kunsan dai halin dad, karku jawo abinda zai hana kowa zaman lafiya a gidannan”.
Maganarta duk ta shigesu, dan suma sunsan basu isa ɗaga murya agaban dad ba.
“Momcy maganar Aunty Nurse fa gaskiyace, inaga kawai ki kira Yaa Amaan ki sanar masa kafin dad ya faɗsa masa, ki zugasa karya karɓi auren”. Ummayya yace mai maganar.
Kai Momcy ta jinjina saboda gamsuwa da maganar Ummayya. Ta jawo waya tafara kiran Yaa Amaan amma saitaji busy, tunda taji hakan kuwa tasan yana cikin aikine, dole ta haƙura bata sake kiransaba dan tasan inya zama free zai kirata da kansa. Amma dukda haka saita rubuta text massage ta tura masa duk dan kar dad ya rigata😂😝.
★★★★
Alhaji Mahmud kam wani abokinsa ya kira dake Abuja, yace yasaka abuga masa katin ɗaurin aure yanzu kafin ya iso, ya tura masa abinda za'a saka a katin, yayi hakane saboda yanason fara raba I.V ɗinne tun awajen taron nan nasu.
⚡⚡⚡⚡⚡⚡⚡⚡
*_WASHE GARI_*
Washe gari Alhaji Mahmud yazo Asibiti a Zaria ya samu baba, dan daga Abuja ya wuto nan bai tsaya kd ba, a jiya kuwa yayta raba I.V ga abokansu yana basu haƙuri akan abinne yazo a ƙure, amma dukda haka sunce zasuzo insha ALLAHU.
Ya tausayama halin da Ummukulsoom take ciki, kwana ɗaya dukta zube, babu abinda takeyi sai kuka, danma da likita yaga ta takura kanta saiya danna mata allurar barci, dan taƙi sauraren kowa lallashin da ake mata, ita kaɗai tasan tarin ƙaunar da takema Basiru, a yanzuma sai takejin ƙaunarsa fiye da ko yaushe a rayuwarta.
Baba da Alhaji Mahmud sun gama yanke komai, dan ba karamin ƙwarjini Alhaji Mahmud Ajiwa yayma baba ba, mutum kirki dashi, sai daifa ya lura a kwai tsare gida, dan tunda yazo gurin baba baiga haƙorinsa ba da nufin dariya, fuskarnan sam babu wani fara'a, a sojansa yake na gaske dukda yayi ritaya ma tuni.
Komai na asibitin Ummu Alhaji Mahmud ne ya biya, kafin yay musu sallama ya koma Kaduna dan tsara abinda ya dace. harya zo yatafi Ummukulsoom bata saniba tana barci.
⚡⚡⚡⚡⚡⚡⚡⚡
Tunda ya shigo falon Buhayyah da Bassam dake dariya suka nutsu, Ummayya ta ajiye wayar hannunta itama suka haɗa baki wajen masa sannu da zuwa.
Fuskarnan kamar ko yaushe babu walwala ya amsa, sun ringa sun saba da yanayin mahaifinsu na rashin fara'a da ɗaukar raini, dan haka bamasa damuwa da wannan.
Shima ya tambayesu ya gidan? Tareda batun sunje islamiyya (kasancewar shi bai yarda yaransa su dogara da boko ba kawai) kame-kame suka fara, saboda basuje ɗinba, dama ita Ummayya sai yana gida take zuwa, dan acewarta ta girmi zuwa islamiyya yanzu, saboda ta girma
Dukda ya fahimci basuje ba sai bai ce dasu uffanba ya haura sama abinsa, dan yanzu yanada wani uzirin.
Yasan Hajiya Jamila bata gidan shiyyasa bai nemetaba, dan tace zataje gidansu yarinyar ƙanwarta ta haihu, to ƙila tare da Aneesa suka tafi dan baigantaba.
Saida ya watsa ruwa sannan yadawo falo ya zauna yana shawara da zuciyarsa akan ya sanarma Fodio maganar auren koya barsa saidai yaji an ɗaura?. Tunda dama yamasa gargaɗin ƙarshe akan yakawo matar aure amma shiru kakeji tamkar malam yaci shirwa.
WANENE ALHAJI MAHMUD USMAN AJIWA?
NO. 8
Alhaji Mahmud Usman ɗan asalin jihar katsinane a ƙaramar hukumar Ɓatagarawa, cikin garin Ajiwa aka haifesa, anan ya girma haryay karatunsa na secondary, tun bashida wayo shi mutumne dama maison aikin soja, mutane da yawa sukance yadace da aikin, saboda rashin fara'a da yake da ita tun yana ƙaraminsa. Hakanne yasaka mahaifinsa fatan cika masa burinsa, cikin amincin ALLAH kuwa sai komai ya tafi dai-dai yanda ya kamata, dankuwa Mahmud yazama soja bisaga taimakon wani bawan ALLAH da mu'amular kasuwancin audiga ya haɗa malam Usman mahaifin Mahmud ɗin dashi.
Wannan shine tushen dawowar Mahmud cikin garin kaduna da zama, anan kuma ALLAH ya haɗashi da Jamila ɗiyar Alhaji barau daya taimakeshi, dukda yanayin rashin fara'a na Mahmud tace taji ta gani, haka dama take fatan mijinta ya kasance, koba komai mata saji shakkar kawo masa wargi🤣.
Ilai kuwa sai maganarta ta tabbata, dan komin son da mace kema Mahmud tsoron tunkararsa take saboda fuska babu wasane shi, bayan aurensu a cikin jaji suke zaune, babu jimawa saiga ciki ya bayyana ga jamila, sosai tayi farinciki, amma saitaga kamar Mahmud baiyiba.
Hakan ya tashi hankalinta, takasa daurewa ta taresa da maganar, abunka da zuciya a kusa yako sheƙa mata mari, cikin faɗa yace, ”Amma Jamila bakida hankali da tunani, tayaya ALLAH ya azurtani da kyautar da babu dukiyar dake iya sayenta a duniya ki dangantani da wanda baya farinciki? Shin rawa kikeso nazo nayi agabanki sananm kisan ina murnane”.
Jikinta na ɓari tace, ”A'a” sannan ta durƙushe gabansa tana hawaye da bashi haƙuri, bata taɓa tunanin zancenta zai fusatashi irin hakanba, halayyar Mahmud kulum ƙara bata tsoro take, dan saida sukai aure takuma fahimtar shi murɗaɗɗen mutumne mai bahagon fahimta, kokusa mutumne da bayason wasan banza, gashi magana kaɗan take fusatashi, sannan baka isa canja masa ra'ayinsa akan abinda yay niyyaba, tundaga wannan ranar bata kuma tunkararsa da makamancin maganar nanba, tacigaba da rainon cikinta, gwargwadon iko yana bata kulawarsa, hakama abinda ke cikinta.
A kwana a tashi ALLAH ya kawo watan haihuwarta takoma gidansu cikin garin kaduna. Batafi kwanaki huɗu da komawarba ALLAH ya sauketa lafiya ta santalo ƴarta mace. Mahmud yayi murna sosai, sai dai bazaka taɓa ganin hakan daga fuskarsaba, hidimar dayake da mai jego da jaririyace amsar, dukdama a lokacin bawani ƙarfine dashiba, da ɗan albashinsa ya dogara da taimakon iyayensa kuma.
Ranar suna yarinya taci suna Saliha, amma suna kiranta da (Ummi) saboda sunan (mahaifiyar Mahmud kenan).
Bayan arba'in jamila tadawo jaji suka cigaba da rainon ƴarsu Ummi. Watan Ummi takwas a duniya ALLAH yakawo wani cikin batareda jamila ta shirya zuwanshiba, gashi yazo mata da laulayi sosai, harma yafi cikin farko wahal da ita, ga Ummi bata isa yayeba, hakan saiya tada hankalin jamila ga zugar ƙawaye ƴan bani na iya, tako tada hankalinta akan zata zubar da ciki.
Ran Mahmud yakai ƙololuwar ɓaci ya korata gida ta huta, mahaifinta kuwa ya goya bayanshi yabata rashin gaskiya. Hankalinta yatashi matuƙa, dan biris Mahmud yayi da lamarinta yacigaba da sabgoginsa ma, duk wata kuma zai aika mata da kayan abinci, amma bazataga idonsaba, gashi a lokacin babu zancen waya😂.
Ta gurzu iya gurzuwa wajen iyayenta da kewar Mahmud, (kaji iyayen ƙwarai) saida tai laushi sosai, cikinta ya shiga wata takwas, dama an karɓe Ummi daga wajenta, dan kartasha ciki, tuni an yayetama.
Cikinta na wata takwas Mahmud ya maidata gidansa dake cikin jaji, ammafa takuma ganin canjin da babu ƙofar kawo masa raini. Itama saita kama kanta tana taka tsantsan dashi dan a zauna lafiya, bata fatan kuma komawa gidansu dan tasha baƙar wahala, mamanta batai mata da sauƙiba, ballema baba dako gaisuwarta daina amsawa yayi.
Saida Cikinta yacika wata goma sha ɗaya sannan ta haihu, kowa ya zura ido yaga ƴan biyu saboda uban girma da cikinta yayi amma sai sukaji tsit, sai guda ɗaya aka santalo musu namiji ƙato mai kama da Mahmud tamkar anyi kaki an tofar.
A wannan karonma tasha hidima, dan albashinsa yaɗan matsa saboda girma daya ƙara samu a gidan soja, gakuma kasuwanci dayaɗan fara taɓawa shida wani abokinsa.
Ranar suna yaro yaci Usman, amma saboda sunan mahaifin Mahmud ne suke cemasa (Fodiyo). Sai kuma saboda sauran jama'a sai Jamila ta haɗa masa da *AMAAN!*.
Wannan karon ma bata sauya zaniba, watannin Amaan bakwai shi baima cika takwas ɗinba saiga ciki, lokacin sunje hutun ƙarshen shekara Ajiwa, surukan da masu dattako, iya na ƙyalla