Showing 111001 words to 114000 words out of 176055 words
nazo miki matsayin shi saboda maganar aure da baba yay mana, na kiraki yafi a ƙirga muyi magana kinƙi saurarena, saina bincika ta hanyar Bily ba tare da itama tasan manufar hakanba, ita ta sanarmin kina shirin bama Abdul-Waheed dama fa, hankalina ya tashi sosai dan kuskuren danayi shine ban saka Abdul goge Number kiba, kekuma ban goge a nakiba, namanta koda namasa katanga da zuwa wajenki dolene zaku cigaba da mu'amula ta waya fa, kiyi haƙuri Ummukulsoom Please, nasan ni mai laifine a gareki”.
Wani ƙududun takaicine ya maƙale numfashin Ummukulsoom, dama yaya Zaid ne yay ma Abdul-Waheed katanga da zuwa wajenta? Bawan ALLAH tanata zarginsa da wasa da hankalinta ba tare da ta sani ba, da gudu ta shige ɗakinsu ta barsa nan tsaye ko waigowa batayiba dukda kiran da yaketa ƙwala mata kuwa.
Attahir dake tsaye bayansu ya kafe Zaid da ido yanason gano gaskiyar zancensa, Zaid dayaji motsi a bayansa ya waiyo suka haɗa ido da Attahir, ƙasa yay da kansa na jin nadamar abinda ya aikata.
Attahir ya girgiza kansa yana faɗin, “Ya maka ƙyau Zaid, ƙanwarka zakazo kana ma wasa da hankali ko?, ashe dama tun jiya ka shigo lagos amma kamin ƙaryar yaune zakazo ko?”.
“Kayi haƙuri yaya, nayi kuskure, amma nayi nadama, tunda bata sona kuma na barta”.
Ƙala Attahir bai ce masaba yay gaba zuwa ɗakin su Ummukulsoom.
Sai da yay sallama suka amsa sannan ya shiga, Ummukulsoom na kwance jikin maman Ahmad tana kukan takaicin Zaid.
Bakin ƙofa ya tsaya ya tsura mata idanu, kafin ya saume numfashi ya ƙarasa takowa cikin ɗakin sosai, saurin tashi Bily tai ta basa stool ɗin mirror ya zauna.
“Ummukulsoom tashi zaune”.
Babu musu ta tashi zaune tana share hawayenta.
“Wanene Abdul-Waheed ɗin?”.
Kanta a ƙasa tana wasa da yatsun hannunta ta bashi labarinsa, Attahir dake saurarenta sai jinjina kai yakeyi, “Ummukulsoom kin tabbata kinason Abdul-Waheed a matsayin mijin aure?”.
Ƙasa ta kumayi da kai alamar jin kunya, hakan ne ya saka Attahir fahimtar tana son nashi.
Yaɗan murmusa yana miƙewa, “Nima na goyi bayan ki bashi dama, dan nasan da Zaid bai aikata daƙilesa ba da tuni yafara zuwa gidannan, amma nabaki dama kiyi tunanin acikin kwanaki Uku kacal, dan Abba sati biyu nikuma ya bani akanku”.
Kanta ta jinjina masa alamar amsawa.
Yana fita maman Ahmad ta kalli Ummukulsoom da kulawa.
“Ummukulsoom yanzu ke kinason Abdul-Waheed ɗin?”.
Kallonta Ummukulsoom tayi tana guntun murmushi, “Aunty idan nace miki bana sonshi nayi ƙarya, sai dai rashin mu'amulantata azahiri da yake shike sakani jin rauni akansa, tayaya zan bashi dama bayan bansan halinsa ba, sau ɗaya kacal muka taɓa maganar fatar baki dashi, daga nan ko'a makaranta muka haɗu bama magana, sam ban fahimci nasa tsarinba nikam”.
“indai dan wannan ne inaga ba abin damuwa baneba, dan lokaci bai ƙureba a gareku, ayanzu haka zaki iya buƙatar ganinsa, shikuma zaid Abban Ahmad nasan zaimasa magana yaje ya janye gargaɗin da yay masa na hanashi zuwa gareki ko kuwa Bily?”.
Baki Bily ta turo gaba cike da jin haushi, “Nifa wlhy danma tawani dage ne, amma mizai hana ta koma gidan yaya Amaan, itama hankalinta sai yafi kwanciya wlhy”.
Harara Ummukulsoom ta makama Bily, rai a ɓace tace, “Bilkisu idan har bason mu sami matsala kikeba kidaina sakomin mutumin nan a lamarina, ni nace mikine sonsa nake ko buƙatar sake zama dashi? Wancanma umarnin iyayene, kamar yanda yace shi da mahaifiyarsa da ƴan uwansa wutsiyar raƙumi tai nesa da ƙasa a tsakaninmu to nima hakance yanzu a gareni, ko ɗauramin shi akayi saina since shi, Abdul-Waheed ɗin dai da baƙyaso dashi zan rayu insha ALLAH ”.
Baki Bily ta taɓe tama fice daga ɗakin ta barsu tana jan tsaki.
Itama Ummukulsoom tsakin tayi, ita maman Ahmad ma sai suka bata dariya.
★★★★
Gaba ɗaya lamarin yazoma Ummukulsoom da ruɗani, dan ita dai da farko sai taga kamar ba Zaid baneba, amma bayanin da yay mata yasata gazgata maganarsa, musamman data turama Abdul-Waheed massege akan tana son ganinsa. saiya bata amsa da,
*_“Ummuna yayanki yamin shamaki dake, dukda zuciyata na tsananin ƙaunarki, tunda kika turomin maganar aurenki ina cikin tashin hankali mai tsanani, dan ALLAH ki bani damar fuskantar iyayenki._*
Bayan taga wannan saƙon saita sharesa batareda ta masa reply ba, kusan kwanaki biyu da faruwar hakan sai gashi ya kirata, abin ya bata mamaki, dan tunda suke bai taɓa kiranta a waya ba sai yau.
Ɗagawa tayi jiki a sanyaye, su duka sukai shiru na wasu sakwanni, kafin daga can ya ɗan sauke numfashi murya ƙasa-ƙasa yace, “Assalamu alaiki”.
Amsawa Ummukulsoom tai zuciyarta na wani irin harbawa, amma saita danne tana saita numfashinta tana gaidashi.
Yanzunma a taƙaice ya amsa mata, hakan saiya kuma bata mamaki, amma sai ta share itama tai shiru.
A haka suka kuma cinye wasu seconds ɗin, harma ta fara tunanin yanke wayar taji yace, “Insha ALLAHU inason zuwa gareki inhar yayanki ya amince”.
Ɓoyayyar ajiyar zuciya Ummukulsoom ta sauke, maimakon ta amsashi sai kawai tace, “Humm”.
Sosai yaji Humm ɗinnan har cikin ransa, dan itamafa ya kula ba kanwar lasa bace, sai dai jan ajinta ke ƙara wutar sonta a ranshi sosai...
Kuma katse shirun nasu yayi da faɗin, “Ban gane Humm ba?”.
“To mikakeso nace maka nikam? Ni a ganina ya rage naka kazo a lokacin daya dace ko kazo a makare, ni dai a gareni babu fashi wajen bin umarnin iyayena”.
Daga haka ta yanke wayar tama kasheta gaba ɗaya tanajin takaicin halayyar maza, kowa da kai tamkar giginya da tasa matsalar, taja tsoki tana miƙewa daga gaban mirror ɗin domin sanya kaya, dama wanka tayo tanason zuwa wankin kai ne.
A gaba ɗaya kwanakin nan maganar auren nan ta dagula mata lissafi, sam batai niyyar yin aure a nan kusaba, amma bazata iya bijirema iyayenta ba, dan baba yamayi ƙoƙari daya amince mata taci gaba da karatunnan, abinda ba'a taɓayi ba a garinsu, yanzu haka da ansan matsayinta a garin da ko ruwa ba'a barta tashaba saboda surutai da za ai ta mata itada baba.
*BAYAN KWANA BIYU*
Kamar yanda Abdul-Waheed ya alkawarta yay mata massege akan yau zai zo.
Dan kawai ta baƙanta ran Yaya Zaid da har yanzu bai koma ba ta shirya tarbar Abdul-Waheed, harma fatan Amaan ma ya gansu tare take, dukda ma ita a tsakanin nan gaba ɗaya bata ganinsa, taji dai kamar ranar Attahir na faɗin yaje kaduna.
Da taimakon maman Ahmad aka shirya masa abinci mai ma'ana mai kuma sauƙi, dan Bily catai batayi, ita gaba ɗaya batason wani Abdul-Waheed, tafiso Ummu ta zaɓi Zaid ko yaa Amaan, rashin dawowar Umar ma ba ƙaramin daɗi yake mataba.
Shareta Ummukulsoom tayi, suka gama tsaf sannan ta wuce yin wanka, kamar kullum yauma bawata kwalliya ce tayiba, sai dai tayi ƙyau masha ALLAH, ga ƙamshinta mai daɗi tana fiddawa.
Huɗu da rabi dai-dai ya turo mata massege akan ya iso, da kanta ta fito ta sanarma Maman Ahmad.
Maman Ahmad ta kalli bily dake zaune ta saurarensu sai kumbura take, dariyar dake cin ranta ta danne tace, “Yi haƙuri aunty B ɗinmu dan ALLAH ki kaisa falon baƙi kafin ta ƙaraso”.
Kuma kumbura Bily tayi, “Nifa gaskiya Aunty ki.....”
“Yi haƙuri Aunty B ɗinmu, ai har yanzu Bestie ɗinki allura ce cikin ruwa ko”.
“Aunty kuna wani goya mata bayane keda Yaya Attahir za'ace allura cikin ruwa?”.
“Ai komai sonmu data auri Abdul idan ba mijinta bane bata aurensa wlhy”.
Dariyar ƙeta Bily ta sanya tana cewa, “Insha ALLAHU ma bazata ƙulluba wannan igiyar” tai maganar tana yima Ummukulsoom gwalo sannan ta fice.
Hakan saiya soki zuciyar Ummukulsoom, taji a ranta kai tsaye zata bama Abdul-Waheed dama dan kawai ta cusama bily takaici.
Sai da bily ta dawo da kusan minti huɗu sannan Ummukulsoom ta miƙe ta fice ɗauke da tire.
Haka kawai taji zuciyarta na ayyano mata abinda ya faru ranar tsakaninta da Zaid, saurin kauda abun tayi a ranta tareda karanto addu'a sannan tai sallama.
Sassanyar muryarsa dake saka Ummukulsoom shiga ruɗani ta ce ta amsa, ta ɗan rumtse idanunta sannan ta shiga.
Zaune yake ƙafa a harɗe, kansa a sunkuye yana danna waya, ƙamshin turarensa dukta cika falon.
Sai da ta ajiye tiren sannan ta kuma satar kallonsa, yana sanye da farin yadi mai ƙyau harda hula, sosai yayi ƙyau a asalin bahaushensa, Abdul-Waheed ɗintane tabbas, hakan saiya saka zuciyarta samun nutsuwa, sai dai tana mamakin bugun da zuciyarta ke ɗanyi da sauri-sauri.
Kallonta yake ta cikin eyeglasess ɗin fuskarsa mai cike da kwarjinin cikar kamala, sam fuskarsa babu walwala.
Sai dai hakan bai damu Ummukulsoom ba, dan ayanda ta lura dashi haka shima yanayinsa yake kamar Ama..., kasa ƙarasa sunan tayi dukda a zuciyartane kuma.
Ganin kallon da yake matane yasata cewa, “Ina yini”.
Ya janye idanunsa daga kanta yay luu har zai lumshe sai kuma yay azamar buɗewa.
Kaɗan ya rage numfashin Ummu ya ɗauke, dan ba ƙaramin rikita zuciyarta taso shigaba ganin yanda yay da idanu, sai dai buɗewar da yay batare da ya lumshe ba ne ya sa ta saume ɓoyayyar ajiyar zuciya.
Shi kansa ya kula da halin data kusa shiga, yay saurin kauda yanayin da faɗin, “Ko ba'ai murna da ganina bane gimbiya?”.
Murmushi Ummukulsoom tayi kawai, amma batace komaiba.
Ya ɗauke idanunsa daga kallonta yana ɗan furzo iska a bakinsa, “Nasan akwai tarin tambayoyi a bakinki akaina, sai dai nima bazanso kimin suba kulsoom, dama kawai nake buƙata”.
Batare da ta kallesa ba tace, “Miyasa bakason na tambayeka? Bayan kuma waɗan nan tambayoyin sune abu mafi cin zuciyata a tarayyata da kai”.
“Nasan da hakan Kulsoom, sai dai sam bansan taya zan baki kowacce amsaba idan kinmin”. ‘ya ƙare maganar yana ɗan dafe kai’.
Kallon mamaki Ummukulsoom tai masa, dan sosai taga alamun ƙosawa da magana a tattare dashi.
Ta ɗauke kanta kawai zuciyarta na kuma tsunduma a wasiwasi.
Shiru duk sukayi babu wanda ya sake tankawa, zuwa can ya kuma kallonta ya janye idanunsa, “Baki ce komai ba”.
“Humm” ta faɗa kawai tana basarwa, kamar bazata tankaba sai kuma tace, “Bansan mizan ce ba nima, kamar yanda na lura kaima bakinka babu abin faɗa”.
Lallausan Murmushi taga ya saki a karo na farko, sai dai badan kallonsa takeba ma bazata taɓa fahimtar yayiba, yakai hannunsa a saman ido sai kuma yay azamar waskewa ya dafe kansa...
Tsira masa idanu Ummukulsoom tayi tsoro na kuma bayyana karara a fuskarta.
“Ba abin faɗa bane babu, yanda za'a faɗa ɗinne matsalar”. ‘Yay maganar cikin basar da ita’.
Janye idanunta tayi tana sauke ajiyar zuciya a hankali, “Abdul-Waheed kenan, to ni dai yanzu mike tafe da kai?”.
Sai da ya gumtsi iska ya fesar yana mata wani kallon ƙasan ido, kafin yace, “Maganar aure”.
Ta ɗan taɓe baki, “Ai banga alamar hakanba”.
Idanu ya tsira mata yana kuma ƙoƙarin control ɗin face ɗinsa wajen sakinta, “Ban cika son nuna lamarina a zance ba, ki bani dama ta halattacciyar hanya kawai”.
“Miyasa da sauri haka?”.
“Saboda nafi kowa buƙatarki”.
Murmushi Ummukulsoom tai taɗan basar, “Baka tunanin bakai kaɗai bane a filin dagar?”.
“Sanin hakan ne yasani tahowa da ƙarfina”.
“Banda cika baki dai”.
Shiru yay bai amsaba, alamar yakai maƙura.
“Yakai shiru? Ko dai bazaka iya takararba?”.
Bakinsa yaɗan motsa, amma yarasa abinda zaice mata, sai kafeta da idanu da yayi.
“Yawan magana akwai wahalarwa ko?”.
Da mamaki ya kalleta, karfa yazam kallon ƙitse akema juna? Ya faɗa a ransa. A fili kuma saiya jinjina mata kai alamar A'a.
Tai murmushi dan ita haka kawaima saiya bata tausayi, wannan kam da a kd suka haɗu babu abinda zai hanata yarda basuda alaƙa da Dad, dan halayyar tazo ɗaya.......
Katse mata tunani yay da faɗin, “Ba maganar wasa ya kawoniba kulsoom, inason tura iyayena gidanku a satin nan”.
Kasa amsashi tai, sai zuciyarta ke mata kaikawo akan ta amsashi koko ta ƙara jansa?....
“Dan ALLAH karkice A'a”. Ya faɗa a hankali can ƙasan maƙoshi.
“Ai baka ci jarabawa ko ɗayaba”.
“A jinkirta min ita mana har sai na gama nutsuwa waje ɗaya”.
“Minene matsalar?”.
“Mahaifiyata nason na auri watanki, bayan kin mamaye ko ina”.
Kallonsa tai na wasu seconds tare da janye idanunta.
Yayinda shikuma ya dafe kansa saboda tsantsar ƙosawa yana tsoron kar akai maƙura komai ya buɗe.....
“Zanyi tunani”. Ummukulsoom ta faɗa cikin katsesa.
Kansa ya rausayar gefe batare da yace komaiba.
Ganin hakan ne yasata miƙewa tana faɗin, “Bismillah kaci zwani abu ina zuwa”. Bata jira cewarsa ba ta fice.
Nannauyar ajiyar zuciya ya sauke bayan fitarta, ya maida kansa ya jingina da kujera yana lumshe idanu...........✍🏻
*_NO. 39_*
..........Abdul-Waheed dai ya tafi yabar Ummukulsoom da nazari, gashi Bily ce abokiyar shawarar amma ta botsare mata, maman Ahmad kuma yaya Attahir na gida, shiyyasa babu sakewa sosai.
Kiran da baba ya sake matane ya saka hankalinta tashi, dan kuma jaddada mata maganar yakeyi, hakan yasakata fahimta lallai akwai abinda ke faruwa baba na ɓoye mata, anya ba magar bata da aure bane ya fasu kuwa?.
Tasan a bakin murja kawai zata iya samun ƙarin bayani, itakuma sai mijinta na gida suke iya gaisawa. Wayarta ta ɗauka ta kirashi, cikin sa'a kuwa ta shaiga. Bayan ya ɗaga daga can suka gaisa, kafin ta tambayi ƴar uwarta.
Daga can yace, “Kash aiko Umma ansamu akasi, dan jiya-jiya na baro gida yanzu haka ina nan kan hanyar legas, amma itama fa shekaran jiya ta nemeki bamu sameki ba ne saboda natuwak”.
Cike da zumuɗi, Ummu tace, “ALLAH saiki, lafiya dai ko?”.
Jimm yayi kafin yace, “Eh to da sauƙi kam, wata dai ƴar magana ce keta yawo a gari akanki”.
“A kaina kuma? Tami kenan?”.
Shiru yay kamar bazaice komaiba.
“Inajinka, karkaji komai ka sanarmin dan ALLAH”.
Cike da jin nauyinta yace, “Umma kiyi haƙuri, haka aketa cewa wai aurenki ya mutu, randa aka kaiki a washe gari mijin ya sakeki amma shine baba yarufe yaƙi faɗa, kuma wai....”
Hawayene suka cika idanun Ummukulsoom, haba itakam tayi mamakin azalzalarta da baba keyi a tsakanin nan akan batun aure, bata bukatar jin ƙarshen zancen dan haka kawai ta yanke wayar tana haɗiye kukanta, zuciyarta taf da mamakin ya akai wannan maganar ta fito a ɗilau? Gashi harma an canja salon zancen gaba ɗaya.
Zafin da kanta ya ɗaukane ba tare da tunanin komaiba ta turama A-Waheed saƙo akan ta amince ya tura magabatansa kawai.
Tana turawa ta kashe wayarta gaba ɗaya ranta duk a matuƙar dagule.
⚡⚡⚡⚡⚡⚡⚡⚡⚡⚡⚡
A ɓangaren basiru kuwa tun daga wannan ranar Abu yaketa bin duk hanyar da zata sadashi dashi koda suna tare da Meenal ne, ahankali sai shaƙuwa ta fara shiga tsakaninsu, basiru ya fara sakin jiki da Abu, bakomai yasa Meenal ƙyalesu ba sai fahimtar da tayi shima Abu ɗan masu farcen susa ne, ita haka kawai ma sai taji ya kwanta mata a rai, dan shima yaron babu laifi akwai kala.
Yau ma dai tare suka fito yawo a motar Abu, danshi baseeru fa inhar bada Meenal