Showing 162001 words to 165000 words out of 176055 words
babu labarinsa, to da farko dai iyayen basu damuba sosai, dan kinsan ya taɓa irin wannan ɓatan kusan shekara biyar ba'asan inda yakeba, sai daga baya kuma yazo wai ashe yabi matarsane wai ko faransa oho dai, to tundai zuwan da yay yace sun dawo tunda ya tafi bai sake zuwaba, da yake ƴar gidan gwamnan katsina daya sauka yake aure, baba ado ɗin ance sunata zarya gidan an hanasu ganinsa, sai daga bayan nan ne labari yake fitowa wai wani ya kashe aka kaishi firizina, ammafa ashahadu a wuyan masu faɗa tunda nidai ba agabana akaina alkur'an”.
Sosai Ummu ta girgiza da wannan batu, sai maimaita kalmar kisan take a ranta, harta cire zancen a ranta sai kuma ta kasa daurewa tai gajeren saƙo ta turama Amaan akan zataje wani gida ta duba mara lafiya.
Kusan mintuna biyar yay mata reply akan saita dawo, amma ta jira ko Abbas kaɗaine yazo ya kaita.
Sake tura masa saƙo tai akan basai Abbas ɗin yakaita ba, nan kusane.
Ok
Kawai ya sake turo mata, ita da Murja suka zare jiki suka fita zuwa gidansu basiru.
Hankalin Ummukulsoom yayi masifar tashi ganin yanda gidansu Basiru yay masifar lalacewa, bata sake ruɗewa ba saida suka shiga ciki sukaga halin da inna da baba ke ciki, sai talatu dake jiyyarsu su duka biyun, hawaye suka sulaloma Ummukulsoom, fitowa tayi ta kira Amaan, gaskiyar abinda ke faruwa ta zayyane masa, da farko faɗa ya kamayi saboda jin wani kishi da takaicinta, amma yanda take masa kuka da nuna masa ba abinda basiru ya aikata zai dubaba mutuncin iyayensa da tausayinsu.
Yanke wayar yayi batare da yasake tanka mata ba, Ummu ta tsirama wayar ido ranta na suya, tana son Amaan, amma wani lokacin murɗaɗɗen halinsa na bata haushi, sam baka isa gane kansa ko yanke hukunci akan halinsa ba, idan yaso sauki yay maka, idan kuma ya murɗe ita kanta bata isa shawo kansa ba, sai ya gadama ya sauka dan kansa.
Jitai kawai an rungumeta ta baya ana share mata hawaye, tai saurin juyowa ta kallesa dukda taji ƙamshin turarensa, sai dai batai zaton zaizoba, sai kawai ta faɗa ƙirjinsa ya rungumeta.
Su murja wannan lamari ya birgesu, hakama yaya Auwalu da Hambali da suka masa rakkiya zuwa gidan, sai sojojinsa da suka tako masa baya dan aƙafa yazo saboda ance babu nisa, kuma yanason ganin gari shima.
“To kukan ya isa shagwaɓaɓɓiya, kimin iso”.
Hawayenta ta share tana murmushi, ta sumbaci gefen kumatunsa kafin ta shige saboda rashin kunyar da tayi gabansu yaya hambali da suka saki baki suna sake kallonsu.
Amaan ko, ko a jikinsa, dan wajenma ya shafa yana sauke numfashi kaɗan, sai dai yaƙi kallon kowa dukda yasan bashi kaɗai bane a wajen.
Mintuna kaɗan Ummukulsoom ta fito, nuni tai masa ya shigo. Tana gaba yana biye har cikin gidan, shi kansa jikinsa yayi sanyi da ganin halin da tsoffin suke ciki, yanda talatuwa ta sake masa bayani tana kuka sai zuciyarsa ta karye, a take yace talatuwa ta shirya su baba yanzunan zasu wuce dasu kd asibiti.
A tare suka fito shida Ummukulsoom daga gidan, tafiya suke a jere da juna kowa fuska cike da damuwa, sai kallonsu ake, yayinda tuni har zance yafara fitowa, dan suna isowa ma su murja suka fara baza maganar cikin ƴan biki.
Sai sakama su Ummukulsoom albarka akeyi, maimakon 5pm da suka shirya komawa sai ta cabja zani, a lokacin suka wuce dasu Inna da aka fitar ranga-ranga daga gida, talatuwa nata sharar ƙwalla.
Sun taho jama'ar ɗilau na sake jinjina dattako da ƙyaƙykyawar zuciya irinta Ummukulsoom da mijinta, kafin kace mi gari yafara ɗaukar zance, harda masu cewa Amaan atake yayma gwamna waya wai asaki basiru (kai ƙauye akwai iya canja zance😂).
★★★★★
Taimakon gaggawa aka shiga bama baba da inna, dukda Ummukulsoom bata da isashshiyar lafiyar itama haka ta daure, sai da Amaan yaga tayi laushi da yawa yaja hannunta sukabar asibitin, bayan ya bar yaransa biyu tare da talatuwa, akan duk abinda ake buƙata suyi.
Ba gida suka wuceba, kiran Ummi Amaan yayi ya tabbatar tana asibiti, abin ya bama Ummu haushi, wai dannmi Amaan zai kira Ummi yace zaizo a dubata, koma kunyar Ummi bazaiji ba kenan. Shi dai bai tanka ba, dan wannan saurin fushin nata shikam zuwa yanzu ya fara mata uzuri a kansa.
Gwajin farko da Ummi taima Ummukulsoom aka gano ciki ɗan wata biyu maƙale a mararta, kasa motsi Ummukulsoom tayi, dan itafa ko kaɗan batai tunanin cewar maganar mutane na batun cikin gaskiya baneba, catake surutune kawai, Ummi na fita fuskarta washe da murmushi Amaan ya jawo Ummukulsoom jikinsa ya hau kissing ɗinta, yama rasa yanda zai musalta farin cikinsa a yau, shima zai zama uba, ALLAH yay masa ƙyautar abinda babu mai bakashi a faɗun duniya, kuɗi ko mulki ballantana gata.
Abu yayi daɗi, kafin kace mi zance ya baje dangi, musamman da suka koma gida Momcy sai nan nan take da Ummukulsoom, tamkar zata maidata ciki, shi kansa Dad yana cikin farin ciki matuƙa, ALLAH ya amsa addu'arsa kenan, dan kullum fatansa kenan da addu'arsa ALLAH ya bama su Fodion sa rabo suma, to gashi yazo lokacin da ba'ai zatoba.
Tunda zancen cikinnan ya fito tattalin da Amaan kema Ummukulsoom saiya ninku, motsi kaɗan hannunsa nakan cikinta, ita harma sai ta fara fushi wai kowa harya fara daina sonta.
Duk dauriyar Amaan akan kar yayi dariya saiya kasa, saida ya murmusa saboda ya fahimci itafa tsakaninta ga ALLAH take kukan akan anfi son ciki yanzu fiye da ita...
“ALLAH idan bakimin shiruba murƙusheki zanyi, bar ganin baki da lafiya”.
Muƙut ta haɗiye hawayenta saboda a ƴan kwanakinnan babu abinda tafi gudu irin Amaan yace zai kwanta da ita.Yay murmushi yana mikewa ya nufi bayi dama wanka zaiyi.
Tun a daren Amaan ya fara bincike akan komai na Mahaifin Meenal, da ita kanta meenal ɗin, itama Ummukulsoom ta fara barci yafi karfinta, dole ta ajiye ta ɓingire barci, Amaan yay guntun murmushi yana ɗaukar lap-top ɗinta ya duba abinda ta samo itama, ya daɗe baiyi barciba, washe gari kuma tunda safe Ummukulsoom ta roƙesa akan ya barta ta fita wani waje, bai hanata ba, sai dai ya haɗata da Abbas.
Saida suka fara biyawa asibiti taga yanayin jikin baba da inna sannan ta kuma sake ma talatuwa wasu tambayiyi kafin ta fice, ita ta amshi driving ɗin a hannun Abbas tana bin address ɗin da ta samu da taimakon ɗan gidan innar basiru na zariya, dan a waya ta kirasa sukayi magana, shima tace kome yake yazo kd a yau, dan tanason ta binciko komai da wuri, tunda tasan zata koma lagos da wuri saboda tarun ayyuka dake a kanta.
Ummukulsoom ta ɗan sha wahala wajen abinda taje nema, har saida Amaan yama kirata yanata faɗa akan ta dawo gida hakanan, tunda yasan itama bawani lafiyane cikakkiya da itaba.
So take ta lallaɓashi akan case ɗinnan, dan haka bata ja ba tasa Abbas ya tuƙota ya maidota gida, tana dawowa kuwa ta kwanta saboda zazzaɓin daya rufeta ruf, hakan ya sake ɗaga hankalin Amaan, gashi a yau yake son komawa Abuja, yasan kuma bazata yarda ta bisa ba a yanda dukkan hankalinta ya raja'a akan wannan zancen na basiru.
Su inna suna samun kulawa ta musamman, dan haka a cikin sati ɗaya kacal suka murmure, sai dai damuwar rashin ɗansu, kuma yanda sukaga Ummukulsoom da Amaan harma da Dad da Abba da suka shiga cikin zancen suma sai suke kawaicin dannewa a gabansu.
Har su Ummukulsoom suka cinye sati ukun da zasuyi babu wani labari game da basiru, dole suka tarkata suka koma dan tanada cases a gabanta da suke shari'a a kansu, ga laulayin ciki da dauriya kawai takeyi kasancewarta jaruma, da kuma son aikinta data kwallafa ma rai, dan duk wanda Ummukulsoom zakaga ta kare a gaban alƙali to katabbata shi aka zalinta, sannan kuma talakane mara karfi, shiyyasa abokan aikinta lauyoyi da yawa kejin haushinta, gashi kuma ALLAH ya bata ƙwazon aiki da jajircewa, sannan bata da tsoro sam, a ƙanƙanin lokacin data fara aiki har sunanta ya fara shiga bakunan lauyeyi da mutane, karanta ya fara kai tsaiko wajen karawa da manyan lauyoyin da ake shakkar haɗa shari'a dasu, ta fara ajiye tarihin nasarori.........✍🏻
............A gajiye ta shigo cikin Barrack ɗin, dan jan motar take tamkar wata ƴar koyo, tai horn ɗaya daga sojojin dake tsaron gidan nasu ya buɗe mata gate ta shiga, tunda tai fakin idonta ya sauka akan motocin Amaan, hakan ya tabbatar mata ya dawo gidan, dan kusan kwana uku kenan yana mai-duguri.
Da hanzari ɗaya a cikin sojojin ya zo zai karɓar ƙatuwar rigarsu ta lauyoyi data fiddo a sit ɗin baya da handbag ɗinta, kanta ta girgiza masa tana ɗan dafeshi da hannu, dan kanta ke mata ciwo saboda fafatawar da sukai yau a kotu da wani shegen lauya mai masifar naci, amma dukda haka ta nuna masa *Mai laya kiyayi mai zamani* dan an yanke hukuncin kuma tayi nasarar kwatoma yarinyar da akaima fyaɗen haƙƙinta.
Amaan dake jikin Window yana kallonta ya fito cikin takunsa na bajinta da lafiya, yanda take tafiya kamar mara ƙashine yasa harya fito bata ƙaraso ƙofar falonba, gabanta ya tsaya yana maijin tausayin jarumar matar tasa.
A hanki ta ɗago idanunta da sukai mata nauyi, hannu ya buɗe mata ta shige jikinsa tana sauke ajiyar zuciya, shima nannauyan numfashi ya sauke yana sumbatar kanta, jikinta ringim da zazzaɓi kuwa.
“Sannu da zuwa Sweet Fodio na, shine baka kirani ka sanarmin zaka dawo yau ba?” Ummukulsoom ta faɗa a hankali tana ɗagowa daga jikinsa.
Baice komaiba ya janyeta a jikinsa yana amsar kayan hannunta, itama ya kama hannun nata suka shige ciki.
Saida suka shiga bedroom ɗinsa da suke amfani dashi ya zaunar da ita sannan yay ɗan durƙuso a gabanta yana kafeta da mayun idanunsa, “Beauty ki ɗauki hutu haka mana”.
Fusaka ta narke masa, “Dan ALLAH Yaa Amaan kayi haƙuri kaikace haka, idan na aikata haka cases ɗin mutane fa? Ni yanzu ciwon jikine kawai ke damuna, suko jikkunansu da zukatansu duk ke ciwo, karka kalli halin dani nake ciki dazai zama naɗan lokaci, ka kalli su yanda suka tsinci kayinsu”.
Numfashi ya sauke yana mikewa, kusa da ita ya koma ya zauna ya jata jikinsa ya rungume, hawayen da take maƙalewa tuni sun fara gudu a fuskarta, bai hanata ba, baikuma ce mata komaiba, sai bayanta da yake ɗan bugawa kaɗan-kaɗan, saida tayi mai yawa sannan ya ɗagata ya cire mata kayan jikinta, da kansa yay mata wanka, ta ɗauro alwala suka fito.
Tunda cikin ya bayyana bata iya girki, dan ko tayi bata iya ci, Amaan kuma ba zama sosai yake a gidaba, tafiye-tafiyansa yayi yawa, hakan yasa Maman Ahmad ta juri kawo musu a kowanne lokaci, yau ɗinma itace ta aiko ma Amaan abinci.
Fita Ummukulsoom tai zuwa kicin ta haɗo musu fruit salad, dan tafi ƙaunar shansa fiye da komai, saiko tuwon Amala ko na dawa, a cikin firij ɗin dani ta saka ta wuce ɗaki danta gabatar da sallar la'asar, dan Amaan ma ya fita sallar.
★★★★
Yanda take shan fruit salad ɗin hannu baka hannu ƙwaryane ya saka Amaan kallonta cike da tausayawa, ya amshi spoon ɗin yaci gaba da bata da kansa yana faɗin, “Beauty yunwa kikeji, amma bazakiji abinci ba sai baƙin tuwo, ni wannan Friendy n nawa bansan da wane salo tazo ko yazo ba” yay maganar hannunsa akan cikinta daya fara tasowa.
Murmushi kawai tai masa ta zare cokalin tana cigaba da shan kayanta ganin yana ɓata mata lokaci.
“Sweet Fodio kasan wane tunani nakeyi kuwa akan zancennan na basiru?”.
Kallonta yay ba tare daya amsaba, amma hakan yana nufin hankalinsa na a kanta. Ta haɗiye abinda ke bakinta tana kuma dai-daita murya, “inaga ya kamata mu fidda maganarnan duniya ta sani, mutumin nan ɗan siyasa ne, bazaiso sunansa ya ɓaciba, da yaji zancen zai karaɗe duniya zai fara ƙokarin binne case ɗin, mukuma ta wanna hanyarne zamu kamashi dumu-dumu”.
Kansa ya shiga jinjina mata idonsa kafe a kanta, tabbas ya aminta da zancenta, dan abubuwansu na kamanceceniya da juna musamman ta fannin bincike. Ganin ya fahimceta saita ƙara faɗaɗa masa bayani akan shirinta, a daren ranar kuwa suka saki bayanai ta hanyar wani abokin Amaan baban ɗan jarida dake da gidan tv nasa na kansa.
A safiyar washe gari kuwa labari ya fara fita
⚡⚡⚡⚡⚡⚡⚡⚡⚡⚡⚡
Hankali tashe Meenal da taci karo da zancen a social network ta samu mom nasu, dan matakin farko dasu Ummukulsoom suka fara bi kenan, sanin mafi yawan al'umma sun raja'a da social network yanzu, a take Momin su Meenal ta kira dadinsu dake can yana fafutukarsa ta ƴan siyasa, dan an kadashi ne a wannan zaɓen bayan ya kammala shekara huɗunsa, zuwa yanzu kuma soyake ayi hannun karɓa tsakaninsa da gwamnan daya kadashi bayan ya gama burin yin shekara takwas, daganan ya fito takarar shugaban ƙasa.
Lamarin ya girgizashi, a take ya nema wani alƙali amininsa akan ayi duk yanda za'ayi case ɗin basiru ya canja salo zuwa wani abun daban, dan shifa har zuwa yanzu bai taɓajin zai yafema basiru ba saboda dukan da yayma meenal wanda ya barmata ƙaton tabo a fuska da duk sanda suka gani sai sun tuna da abinda yayi.
Dama idonsu Ummukulsoom akansa suke, dan haka sukai amfani da wannan damar wajen yima baba mahaifin basiru jagora ya shigar da ƙara a wata babbar kotu dake nan kaduna da taimakon Abba da Dad.
A daren ranar aka miƙama mahaifin Meenal sammaci daga kotu, sannan aka saka police binciko dukkan prison dake cikin katsina neman basiru.
Har dai washe gari babu wani labari dangane da samun basiru, sai da akabi wasu manyan matakai kafin ai nasarar ganosa cikin gaggan ɓarayi, a yanda shirin mahaifin Meenal yakema saura kwana ɗaya kacal a kashe su basiru.
A yanayin da aka ɗakko basiru daga jail abun babu daɗin gani, dan dolema aka zarce dashi asibiti daga nan, ashe dukan tsiya yaci hannun gayun da suke tare a daren jiya.
Su Ummukulsoom suna lagos aka sanar musu da samunshi, dayake dukkan komai hannun Abba da Dad ya koma, dan hakama Abba yace Ummukulsoom tabar maganar shiga case ɗin a nemi kwararren lauya daya daɗe a aiki, amma sai Ummukulsoom taita roƙonsu akan zata iya.
Ummi ce ta bada shawarar su barta kowa ya bita da addu'ar samun nasara, kar a sare mata gwiwa.
Inna da baba sosai hankalinsu ya kara tashi ganin yanda ɗansu ya koma, ko mai fama da ciwon HIV iyakar lalacewar da zaiyi kenan, banda ƙwala-ƙwalan idanu babu abinda kake gani a jikin basiru, ya rame iyakar ramewa, fuskarsa kam tayi baƙi duk ya koje tayi tabbuna na raunikan duka saikace wani tsohon ɗan daba, ga wasu ƙuraje da duk suka bata masa jiki harma fuskar masu shegen wari dan ƙazanta, duk mai imani ya gansa saiya tausaya masa.
Kwana biyu da samo basiru Ummukulsoom da Amaan da Attahir harma da a maman Ahmad suka dira kd da daddare, dan washe garine za'a fara shiga shari'ar su basiru.
Kallo ɗaya Ummukulsoom ta iyama basiru dake barcin wahala ta fito abinta, jarumta sosai ta nuna wajen danne kukanta dan kar zuciyar Amaan ta sosu saboda kishinsa data gama fahimta akan lamarin, dukda da yarjewarsa take komai hakan bai hanashi yawan nuna ɓacin ransa ba idan ya ga ta cika yawan magana akan case ɗin, dan haka saita iya takunta, dan ita harga ALLAH bada wata manufa take hakanba, sam babu wata soyayyar basiru a ranta tun shekarun da suka shuɗe kafinma tasan kanta, tausayin iyayensa ne kawai ya jagoranci damuwarta akan lamarin.
★★★★★★
Duk da ta tashi babu jin daɗin jiki haka ta nuna jarumtarta wajen dannewa aka shiga kotun, a wannan zaman maida kanta sakara tayi a kotun, lauyan da ke kare baban Meenal yanata murna akan ashema shashasha suka samo, danshi kam gaba ɗaya ya rainama Ummukulsoom wayau akan shari'ar, gashi dama a haife zai iya haifarta, danshi shirinma ritaya yakeyi nan kusa kaɗan.
Jikin su Abba saiya fara sanyi akan yanda Ummu ta nuna sanya a kotu, shiko Amaan dama baima halarci shari'ar ba sam, sai Attahir ne kawai yaje.
Ummukulsoom guduwa tayi, dan kar kowa yay mata maganar abinda tayi a kotu, dan ita tasan minene a ranta,