Showing 39001 words to 42000 words out of 158267 words

Chapter 14 - Dan Adam Book 1 Complete Hausa Novel

wacce aka dauka a hoto. Gaskiya Allah Ya baka."
  Faruk ya share maganar ta hanyar jefomishi tambaya.
  "Wace k'asa ka za6i zuwa ne?"
Adnan ya baro wajen zanen ya dawo, ransa ya sosu don ya tuno abin haushi. Ya dan daga kafada.
"Bar wannan zancen my best, ni nafasa anan zanyi."
  Faruk ya lura da wani abu, kawai sai ya share. 
                  ***   ***   ***
                     KADUNA
DAN ADAM
@RUFAIDA OMAR
   41
                     KADUNA
   Dija gaba daya ta sauya, daga mai surutu da zafi zuwa marar son hayaniya da kuma sanyi. Komai takeyi muddin Deen zai shigo, to fa zata mance komai ta shagaltu a kallon dukkan wani motsinsa. Tun Deen bai lura ba har dai ya soma tsarguwa da yawan bibiyarsa da takeyi da kallo. 
    A yau juma'a, Munira batanan ta wuce gidan wata aminiyarta da ta haihu, saida ta dauko yaranta daga makaranta suka wuce tare, gidan babu kowa sai Dija wacce ganin Denn a gida yasa fir ta k'i binsu ta fake da ciwon jiki. Misalin karfe uku da mintuna, Deen yana kwance a falonsa yana duban talabijin, ya ji sallamar Dija. Da mamaki ya dubi hanyar falon, yana mai amsawa. Ganin da ya yi mata cikin shigar mutunci marar mishkila sosai yasa ya dan ji nutsuwa a ransa. Ya mike zaune yana murmushin yak'e.
  "A'a Dija, k'araso mana." Ta dubeshi ta sauke ajiyar zuciya, komai nashi burgeta yakeyi. Ita kuwa ko zata mutu sai ta sace zuciyarsa, shekarunta sun kai munzalin da ya dace ace tana gidan miji ba yawon gidajen yan uwa ba. Itama fa mutum ce ba dutse ba, tana da sha'awa, koda dai takan biyewa k'awarta wacce waya ta hadasu, mai yawan yi mata hudubar banza akan ta amince ta je Kano su had'u don d'ebewa juna kewa, ta k'i yarda amman takan ta6a hirar banza da ita a waya(Wa'iyazubillah). 
     Ta samu wuri ta durkusa gami da gaisheshi. Ya amsa batare da ya kalleta ba yana mai wayancewa da chanja tasha.
  "Ashe sai kai kad'ai, ga abinci can an jera tun dazu."
  Ya dan dara.
"Eh yanzu zan taso na ci."
Ta narkar da fuska.
"Haba Deen, don Allah ka zo muje, ni kaina sai yanzu zan ci. Na riga na saba da ci da ku ana yi ana hira, yanzu da basunan bazan ji dadi ba."
  Ya jefeta da wani irin kallo har saida ta ji gabanta ya fad'i, tsoro ya cikata, sai kuma ya numfasa gami da maida dubansa ga talabijin.
  "Jeki ina zuwa."
Ya bata amsa a gajarce ta mike jiki babu kwari ta fita. Har ta cire ran zai zo sai kuma gashinan, wani sanyi ta ji a ranta ta mike zata zubamishi. Ya dakatar da ita.
"No barshi, zan yi da kaina."
Ta girgiza kai.
"Ban ta6a ganin kunyi haka da Munira ba, nima bazan bari ka zuba da kanka ba kada nayi laifi awajenta."
Jin haka ya kauda kai, ta zuba tana murmushi ta tura gabansa sannan ta zauna saitinsa tana cin nata. Idanunta a kansa, da zarar ta ga zai kallota sai ta yi sauri dauke idanun. 
  A ransa ya ji yana mai jin haushinta, da ace yar uwarsa ce da tuni ya korata gidansu, saidai ba yanda ya iya, baya son ran Munira ya 6aci ya lura sosai take kaunar Dija hakanan tana tausayinta wai adalilin har yau bata samu mashinshini ba.
  Ya rigata mik'ewa ya bar wajen, ta bishi da zazzafan kallo gami da k'ara cin alwashin ba fa zata barshi ba sai ta cika burinta na aurensa. Babu wacce ta fad'omata a rai sai Baba Habiba, ta tabbatar ita daya ce zata iya yi mata kokarin shawo kan Deen ko ta wane hali. Idan ma da hali ya saki Munira ya aureta. (Kun ji butulcin DAN ADAM)

                  ***   ***   ***
   Bikin Baraka ya iso, komai na shirye-shiryen Mami, ita da kanta ta yi bata saurari Abba ba balle ta tambayi wani abu a aljihunsa har ya samu damar cin zarafinta. Ta yiwa Ihsan anko, hakan ta siyawa Fahad shadda tare da Adnan aka dinka musu. Ummi kuwa ta yi mamaki da Mamin ta bata kudi suka je da Amina bayan isarsu gidan Hajiya Mama ta siyo 'yar kanti da kuma wani abin idan tana so. Ta yi murna matuka duk da tasan ba da ita zasu je ba.
   Hajiya Mama ta jajantawa yar uwarta kwarai na abinda ke faruwa da ita. Ta kuma yi mata fada sosai akan dalilinta na rashin sanar da ita tun wuri. A karshe tace zata sanya ayi rokon Allah, suma kuma ba kwanciya zasuyi ba, su dage sosai da addua da sadaka har Allah Ya kawo makarin koma menene. 
    Bayan Amina da Ummi sun dawo daga shago suka biya gidan Innar Aminar. Mace mai mutunci kwarai, ta yi murna da ganin Ummin da duk sadda Amina ta zo saitq bata labarinta. Sun jima anan sannan suka lek'a gidan Anti Hauwa yayar Amina daga nan suka kamo hanyar gida. A hanyar ne ma Ummi ke labartawa Amina yanda suka ta6a yi da Hajiya Binta. Amina sosai ta tsorata, hankalinta ya dan kwanta jin Ummi bata bi turbar shaidan ba ta aikata. Ta k'ara fahimtar da ita lallai mai yiwuwa yanzun ma da sa hannunsu cikin lamarin Abba da Mami. A karshe ta kara shawartarta akan ta dage da addu'a akan Allah Ya kareta daga sharrinsu. 
    Ashe kuwa dai sharrin na tafe, domin a daren da suka koma gida daga gidan Hajiya Mama, Abba ya kira Mami ya ke fadamata ta gaggauta korar Ummi daga gidansa don labari ya iso mishi cewar tana biye-biyen maza tana fakewa da zuwa makaranta. Acewarsa, yaransa basu jawomasa abin kunya ba, to babu 'yar wata can da zata janyomasa. Mami ranta ya 6aci, cike da mugun 6acin rai ta dubeshi.
"Wannan kuma ba halin Ummi bane, da ace Ummi na yi kasan kafin ka gane ka koreta, da tuni na yi hakan don bana zama da maci amana. To Ummi babu inda zata je, zamanta daram a gidan nan!"
  Ta yi maganar cikin daga murya har kirjinta na bugu da sauri-sauri saboda tsananin 6acin rai, ba wai don kwatarwa Ummi yanci kadai bane, aa, har ma da gajiyawa da jin zafin yanda ya ke bayar da ita gaban kishiyoyinta, don a wannan karon ma har hadasu ya yi gaba daya a falon yana mata korafi akan Ummin. Abin ya soma isarta.
  A fusace ya ce. "Sai mu gani idan gidan ke kika ginashi Madina! Amma wallahi kinji rantsuwa ta musulunci babu yar iskar da zata zauna a gidana, saidai ko ki bita."
  Hankalin Mami ya tashi, su kansu matan sun razana da furucin Abba, Anti Amarya wacce bil hakki ta tausayawa Mamin, ta saka baki.
"Haba Alhaji, ya kake..."
"Kiyimin shiru Malama, bansaka dake ba, daman na taraku ne don na gargadeku da ku jawa yan aikinku kunne, banaso and iskancin banza da wofi. Ke kuma ki tattara taki ki maida inda kika amso ta, bazan lamunci iskanci ba."
  Takaici ya sa Mami jan tsaki batare da tasan sadda ya fito ba.
"Sai kayi, na gayamaka babu inda Ummi zata je, sa'arka d'aya zan je Abuja da na soma gwadamaka gaskiyar abinda nake fad'a tun yanzun. Naga ai wasu ma nasu cikin suka ta6a yo wa aka zubar aka cigaba da zama da su a gidan."
  Hajiya Binta ta fahimci da yar aikinta Sa'ade take wacce ta ta6a yo ciki suka zubarmata. Ta fusata ta yi kwafa batace uffan ba.
   Kafin Abba yace wani abu, Mami ta zura silifas dinta ta fice cikin kunar rai.
  "Ummi! Ummi!!"
Ummi dake daki ta ji Mami na kwalamata kira cikin daga murya. Ta fito a kidime ta russuna.
"Naam."
  Ta tamke fuska.
"Ki shirya kayanki, dake zan tafi."
  Ummi gabanta ya fadi don bata ta6a zato ba,  ta mike ta wuce bayan ta amsa da toh kawai. 
   Shigarta da mintuna biyar Fahad yazo ya kara kiranta wai inji Mami. Ta mike ta isa gareta a can daki. Mamin na zaune gefen gado ta yi jugum tana tunani, bayan Ummi ta durkusa ta dubeta fuska daure.
  "Ki gayamin tsakani da Allah akqn dukkan abinda zan tambayeki Ummi."
  Ummi a tsorace ta ce. "Toh."
Mami ta zubamata ido, ita tasan sharri aka yiwa Ummi, saidai dole ne ta tambayeta don amana ce ita a hannunta. 
DAN ADAM
@RUFAIDA OMAR

42
"Dagaske ne kina...."
Sai kuma ta yi shiru, haka kawai ta tsinci kanta da jin nauyin maganar, ta daure ta karasa.
  "Labari ya iso ga Abba na kina bibiyar maza, ki gayamin gaskiya Ummi."
  "Innalillahi wa inna ilaihir raaji'un!"
  Abinda Ummi ta furta kenan a fili kafin wani kuka ya tahomata, kuka sosai harda sheshshek'a. Mami na kallonta bata katseta ba, bata ta6a jin tausayin Ummi ba aduk zaman da suke sai a yau, k'azafi abu ne mai matukar cin rai, tasan yanda Ummi ke ji irinsa Adnan ya ji a sadda aka mishi sharrin sata, hakanan itama irinsa ta ji alokacin. Maganar Ummi ta katse tunaninta.
  "Wallahil Azim ban aikata abinda ake zargina akai ba Mami, ban ta6a koda tsayuwa na saurari wani d'a namiji  ballantana har ya kai da ta6a jikina ba, ki yarda da ni wallahi Allah ban aikata komai ba. Na shiga uku."
Ta k'ara fashewa da wani kuka wanda ke k'arawa Mami jin wani mugun tausayinta. Ta numfasa muryarta a sanyaye.
  "Ya isa, nasan ba ki aikata ba daman, kawai don kiyaye amanar da aka ban naki ne yasa ni tambayar. Na riga nasan kazafi ne na mahassada amma babu komai wataran sai labari. Kiyi hakuri, kina iya tafiya ki soma shiri, dole dake zamu wuce."
  Ummi ta mik'e ta fita, a hanya suka ci karo da Ihsan ta bita da kallon mamaki ganin ta fito daga dakin mahaifiyarsu kuma tana kuka, da sauri ta karasa dakin don duba Mami. Sai ta tarar ta yi shiru ta zuba tagumi. Ta karasa gareta. "Mami lafiya? Naga fitar Ummi daga nan ta na kuka."
  Mami ta murmusa.
"Bakomai, kin gama shirye kayanki?"
Fuskarta cike da damuwa ta amsa da eh. Bata kaunar ganin Maminsu a wannan yanayin, Allah-Allah takeyi su bar garin su shiga cikin yan uwansu ko zuciyarsu zata sanyaya. Ta kasa hakuri saida ta k'ara tambayar Mamin dalilin da yasa Ummi ke kuka. Haka dai ta sanarmata don ta k'i jinin 6acin ran yarannata. Ihsan duk da tana k'in Ummin itama ta ji babu dadi musamman jin cewa a gaban kishiyoyin Maminnata Abba ya gasawa Mamin magana. Ta yi kwafa.
"Ai Allah Ya fisu, munanan mugun abinsu zai juye kansu."
Mami ta jinjina kai. Tabbas ayanzun ta soma zarginsu duk da zato zunubi, tana yi musu kallon munafukai masu fuska biyu. 
    Ummi ji ta yi duniya ta mata zafi sosai, ta riga tasan makircin Umma ne, ita kadai ce matar da ta ci alwashi akan lalata rayuwarta, ta barta da Allah domin bata da karfin yin fad'a da ita, koda tana da shi, bata jin zata iya ramuwar gayya. Allah zai mata sakayya, saukinta ma Mami bata gaskata hakan ba.

                  ***   ***   ***
Ta dubi 'yarta tana mai zaro ido.
"Me kike nufi ne? To wallahi babu inda zakije. Na rabaki da wannan shegen yaron ba kiji, idan ba kiyi a sannu ba zan mugun sa6amaki."
   Iklima ta turo baki ta mike daga saman kujera.
"Wai don Allah inace ni zan zauna da shi? To ni gaskiya ina sonshi kada ki yi yunkurin rabani da shi. Kuma meye idan naje Abujan? Baraka fa k'awata ce, ana bikinta don kawai wani kishi naki kice..."
  Bugun le66anta da ta yi ne yasa ta yin shirun dole tana sosawa don zafi. 
A fusace Umma ke magana.
"Kinyi kadan! Wallahi iklima kinyi kadan, ban haifi 'yar  da zata fi k'arfina ba nan duniya. Biki ne kuma babu inda za ki taka kije, mu zuba ko ni ko ke a gidannan."
  Daga haka Umma ta nufi dakinta a fusace kasancewar ranar ba aikinta bane. Kai tsaye layin bokonsu ta nema ta sanarmishi akan tana so ya raba zuciyar 'yarta da soyayyar Faruk. Ya sanarmata abu ne mai sauki amman sai ta zo ta amshi wasu magunguna. Ranta ya yi sanyi ta bishi da godiya gami da tabbatar mishi da zuwanta a goben da kuma kudin aikinsa. Daga haka suka rabu.

   Washegari Iklima tana ji tana gani su Mami nata shiryen-shiryen tafiya. Rahila da Aisha suma nan suka zo, dan Aisha, Tahir ya yi wayo sosai. Rahila da yaranta biyu itama, Bintu da Samir wanda shine karami yana da wayo sosai, cikin ikon Allah bai mance fuskar Ummi ba, hakanan ya yarda ya je hannunta. Ko kusa Ummi bata da matsala da Rahila da Aisha, babu ruwansa, sannan basu fiye zuwa gidan ba face da babban dalili. Wannan ne dalilin da yasa basu san wainar da ake toyawa ba, a wannan zuwannasu ne ma ta tsincesu a dakin Ihsan tana faman labartamusu komai harda tafiyar Adnan Abuja. Aisha da mamaki tace "Haba, shiyasa kwana biyu banga keyarsa a gidana ba, ashe baya garin. Bakomai, komai zai wuce."
  Abinda ta tsinkaya kenan ta dauki kayan Fahad da Mami ta aiko ta dauka ta fice daga dakin. 
  Nan su kuma sukayita jajantawa har saida Mami ta gaji ta soma fadan zata tafi ta barsu sannan suka fito. 
   Kai tsaye gidan kakansu suka nufa wato Alhaji Atiku Modibbo inda anan zasu hadu har Hajiya Mama da iyalanta su wuce Abujan. Tafiyar har da Innarsu. Suka yi sallama suka bar dan tsoho daga shi sai yan aiki da wani dan uwansa na Adamawa suka kama hanya. Ummi na rike da Samir a gefen Antinta Amina suna shan hira, kowa a Bus din abinda ya shafeshi yakeyi, Mami kuwa su uku ne a mazauninsu, ita da Hajiya Mama da Innarsu sai hira sukeyi. Nan ma Ummin ke labartawa Amina kazafin da akayimata, Amina abin ya yi mata ciwo saidai fadan da yafi karfinka... 
Har dai suka isa kowa da abinda yasa gaba kafin a karshe a gaji ayi shiru.
   Amina da Ummi wadanda basu ta6a takowa Abuja ba, suka saki baki suna kalle-kalle. Har suka isa gidan Gen. Ahmad Danzaki inda anan kallo ya koma sabo dal. Suka saki baki suna k'arewa haduwar gidan kallo. Wannan ko a Turai ne sai hakan.
"Aljannar Duniya." Abinda Amina ta fada kenan cikin rada yanda Ummi kadai ce zata ji. Sukayi 'yar dariya.
"Bari Anti, basu da matsala a fannin kudi."
  Amina ta jinjina kai. "Tabbas."
Direban ya hau hon, maigadin da sauri ya budemusu kofa yana washe baki gami da dago hannu yana musu lale marhabin. 
DAN ADAM
@RUFAIDA OMAR

43
   Yana daga samansa yana dubansu da murmushi, ya karasa ga Adnan wanda bayan karin safe ya yi wanka ya cigaba da bacci ya kai mishi duka.
"Tashi kaga wani abu." Adnan ya mike da sauri yana dubansa ido waje.
"Sun iso?"
  Faruk na murmushi ya ja hannunsa zuwa barandar. Ihu ya saki wandq har saida su Mami da suka riga suka fito suka kallo shi, dariya suka sanya. Da gudu ya fira ya sauka garesu. Shima Faruk ba shi da za6in da ya wuce na bin bayansa. 

Adnan ya kama hannun Maminsa tamkar ya rungumeta don murna. 
   Baraka da Ikram a guje suma suka fito har Hajiya Babba wacce ta kasa hakurin k'arasowar yan uwannata ciki. Ta rungume Innarta, su Amina da Ummi suka zagaya domin kwasar kaya. 
  Tana janye da katuwar jaka, idanunta ya sauka akan Faruk, yana gefe ya hard'e hannuwansa yana zabga murmushinsa mai burgewa. Sanye ya ke cikin kananun kaya, riga bak'a anyi rubutu da farin abu, wandonsa ma bak'in ne, ya yi kyau har ya gaji da had'uwa. Cikin sa'a idanunsa ya kai kanta sa'ilin tuni sauran sun kama hanyar cikin gidan. Murmushi ya sakarmata, itama ta tsinci kanta da mayarmasa da martani har(dimple) dinta na dama  na bayyana. Ya ji wani abu da bai ta6a ji ba na tsirgashi, ya kauda kansa gami da soma tafiya zuwa ciki. Tana jan akwatin tamkar bata so sanadin kallonsa da take yi, namiji mai aji kenan, ina ita ina shi? Ta sauke ajiyar zuciya ta dubi gefenta jin alamun mutum. Amina ce itama rik'e da katuwar jakar Hajiya Mama tana dubanta cikin nazari, sai kuma bayan sun hada ido ta sakarmata murmushin yak'e.
"Muje mana naga bakya daga kafa ne."
Ummi ta gyada kai ta k'ara sauri. Amina mamaki kwarai takeyi na irin kallo da murmushin da ta ga Faruk na jifan Ummi da shi, da kuma kallon da Ummi ke bin bayan Faruk din da shi har ya illata tafiyarta. Ta numfasa, 'Idan ma akwai wani abun ya zama dole nasa ido na gano, bazan bari Ummi ta jefa kanta cikin matsala babba ba, ina mata kallon kanwata kamar ta jini.' Ta ayyana a ranta. Da taimakon yan aikin Hajiya Babba aka shishshigar da kayan gaba daya ciki. 
  Tsarin gidan Hajiya Babba wane sauran gidajen yan uwanta, iyakar haduwa ya had'u. Kayan duk ansaka a inda ya dace, Ummi da Amina daki guda aka hadasu wanda duk na yan aiki ne, yana daga can bayan(garden) din gidan. 
    Hira ta k'i ci ta k'i cinyewa tsakanin yan uwan, dakyar sukayi wanka suka chanja kaya sannan aka gabatar da sallar la'asar akayi zaman cin abinci. Alokacin kuma Haidar da Intisar suka shigo. Da gudu suka rungume juna ita da Ihsan sannan ta koma ga iyayen kowanne ta hau rungumarsa don dadi. 
  "Wai ke bakya girma ne?" Cewar Hajiya Mama kenan alokacin da ta rungumota. 
  "Kema dai kya fad'a Sadiya, yau kam dole kiban mijina tunda na iso." Cewar Inna kenan.
  "Ahaf, mai zuwa gidanmu sai ya shirya fa." Fadin Haidar kenan, akayi dariya gaba daya. Su Faruk na daga falo suna jiyo caftarsu, shima Haidar bayan gama gaisuwa ya komo wajensu ana hira. Faruk kusan hankalinsa ya kasu biyu, hakanan ya ji yana d'okin ganin daga inda Ummi zata 6ullo, fatansa ya k'ara cin karo da kyakkyawar fuskarta. Da zarar ya soma tunaninta, sai ya yu saurin kwa6ar zuciyarsa, aganinsa babu wani dalili da ya ke da shi da zai dunga tunanin wata can. Abu ne da tun da ya ke a rayuwa bai ta6a faruwa gareshi ba. 
    Ita kuwa baiwar Allah, suna can tare da Amina suna cin abinci, saida suka kammala suka kai komai kicin. Alokacin ta fita wanka, bayan dawowarta itama Amina ta tafi wanko jikinta. Doyuwar riga ta sanya na kanti marar nauyi na yawon gida, itama Amina doguwar rigar

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login