Showing 42001 words to 45000 words out of 158267 words

Chapter 15 - Dan Adam Book 1 Complete Hausa Novel

ce jallabiya. Ummi ta dubeta taba daga rigingine saman katifa 
"Anti ashe duk tsaruwar gidajen su Mami bai kama rabin k'afar na Hajiya Babba ba?"
  Amina ta murmusa yayinda ta zauna gefenta.
"Haduwa ma ba daya ba kedai, na ji ance fa har wajen wanka akwai(swimming pool)."
  Ummi ta zaro ido.
"Haba?"
"Wallahi a bakin su Anti Intisar na ta6a ji, ba don ma kada muyi laifi ba da mun zagaya gidan."
Ummi ta amsa.
"Wallahi kam, zanso ganin wajen wankan kuwa."
  Haka sukayita hirarrakinsu, Amina na son yi mata magana akan abinda ke gudana tsakaninta da Faruk, tana kuma tsoron kada ya kasance zarginta ne kawai, wannan yasa ta barwa zuciyarta. 
    Sun sakankance suna hira har Ummi ta soma lumshe ido na jin bacci, ganin haka Amina ta kyaleta. Cikin baccin kuma ta ji ana tashinta, ta mike zaune tana murza idanu. Ta yi mamakin ganin lokacin Magriba ya taho.
"Ki tashi magriba fa ta yi, an turo a kiramu ma sai ni na je nayi aikin." Cewar Amina wacce ke kokarin gyara hijabinta bayan dauro alwala da ta yi. Da sauri ta mik'e ta fita zuwa bandaki domin dai bandakin yan aiki mata guda daya ne kuma ba cikin dakuna ya ke ba, yana daga dan lungun dakunan. Ta iske yan aiki biyu na alwala, ta gaishesu.
"Kece Ummi?"
"Eh." Ta amsa da murmushi. Suka saki baki.
"Kema kuma yar aiki ce?"
Ta gyada kai don ta soma mamakin tambayar. 
  Daga haka ta wucesu ta shiga bandaki. Tana jiyo hirarsu, daya na fadin. "Kinsan Allah Binta, da ace ni na samu kyawun wannan ba zan bautawa wasu a aikatau ba, na gwammace na ci duniyata da tsinke."
  Bintar ta ja tsaki.
"Kedai matsalarki Sa'a kina da son maza kamar wata karya wallahi. Nayi zaton ma batun aure zakiyi."
  Sa'a ta ta6e baki.
"Aurena biyu ban ji da dadi ba, don haka ko marmarin k'ara yi bana yi."
  Lokacin Ummi ta fito sukayi shiru, ta isa ga famfon dake a gefen garden din inda suke tsaye ta soma alwala suna kallonta, suka saki baki ganin har wata suma take da a goshinta ga gashi daidai misali, ita dai ta samu ta kammala a gaggauce, ta yi musu sallama ta tafi da tunani hali irin na wasu mutanen da suke da karancin godiya ga Allah, wasu suna can ma basu samu koda rabin yanda su suka samu ba.
  A haka ta shiga ta tarar har Amina ta idar da sallar tana addu'o'in da ta saba. Itama ta zura hijab ta tayar, bayan idarwarsu suka yi zaman hira anan take ji daga bakin Amina cewa su Haidar ma sunzo.
"Mai yiwuwa suma sauran ki gansu." Amina ta karasa.
  Ummi ta bata labarin hirarsu Sa'a akanta, Amina ta dara.
"Mata kenan, muna da matsala wallahi. Mudai mu kama kanmu babu ruwanmu da harkarsu idan ba gaisuwa ba da hirar da bata shafi kowa ba. 
    Suna nan Sa'a ta lek'o.
"Ummi, Anti Aisha na kira."
"Toh."
Ta mike cikin sauri ta gyara zaman hular kanta. 
   Ta fito tana waige-waige don har ga Allah ta mance yanda tsarin gidan yake. Ta karasa wajen doguwar baranda wacce akwai bene daga wani loko, ta yi shiru, ta cigaba da tafiya, wata kofa ta gani makamanciyar wacce suka shigo, hakan yasa ta bude kofar, kawai sai ganinta ta yi a wajen (pool). Daga tsakiya ya ke, a gefensa rumfa ce aka sanya kujerun zama, wani murmushi ta yi don sosai wajen ya burgeta.
Ta rufe jin kamar motsi ana saukowa daga bene. Tana shirin barin wajen suka yi kici6us da Adnan. Kowannensu ya saki fuska. 
  "Lah, daman dake aka zo?" Ta yi dariya.
"Eh, kana murnar ganin Mami baka lura ba."
  Ya dara shima. "Bari kawai, ai nayi kewarku wallahi. Ina za ki ne?"
   "Kaga hanyar na rasa, Anti Aisha ce ke nemana."
  Yana dariya ya soma tafiya.
"Ke kam ba dai saurin mantuwa ba, biyoni ki gani."
 DAN ADAM
@RUFAIDA OMAR

   44
  Ta bi bayansa kuwa, ta yi mamakin ganin ashe ba wata doguwar tafiya bace, ya bude kofa suka shiga babban falon Hajiya Babba. Wani kamshi sassanya ya bugi hancinta har tana sauke numfashi, kunya da nauyi suka cikata domin falon babu kowa sai samarin da su Baraka da matan yayyun ana hira da dariya. Tun shigowarta ya jefeta da kallo daya ya kauda kansa duk a kokarinsa na yak'i da zuciyarsa game da ita. Ya maida hankali ga Ihsan wacce ke faman yi mishi surutu ko kusa bai fahimtar inda ta dosa ma. Ta russuna ta gaishesu da tattausar murya, suka amsa. Anti Aisha bata falon, hakan yasa ta yi karfin halin tambayar Ihsan.
"Ihsan, ina Anti Aisha?"
Ihsan ta yi tamkar bata ji ba don haka kawai ta tsani ganin Ummi awajen yaran Hajiya Babba, ta rasa dalili don ko Amina bata jin hakan akanta sai ita Ummin. 
  Faruk ya zubawa Ummi fararen idanunsa, ta kauda kai. Alokacin ne Adnan ya bata amsa.
"Tana sama ina ji, jeki ki duba."
Ta dubi hanyar saman, to wane dakin zata dosa ne?
  "Tashi ki rakata." Ta tsinci muryar Faruk sadda ta ke kokarin mik'ewa, sauran yayyun hankulansu naga hirar da sukeyi suna tuntsirar dariya. 
  Ta soma tafiya ta ji Ihsan ta bangajeta ta yi gaba da fadin.
"Ki biyoni."
  Ta jinjina kai ranta na suya saidai babu halin tankawa, haka tayita binta tamkar rak'uma. Ya kasa kauda kai daga gareta har saida ta 6acewa ganinsa kafin ya juyo kansa sukayi ido hud'u da Jidda matar Dr Ridwan. Ta daga mishi gira kadan 
"Ya akayi? Akwai fa wani abu."
Faruk ya yamutse fuska.
"Kefa matarnan kin samin ido wallahi."
  Yan uwan sukayi dariya. Jidda ta dubesu.
"Na gayamaku ai akwai wani abu tsakanin wannan kanin naku da Ihsan kun k'i aminta, bakuga irin kallon da ya bita da shi ba yanzu."
Faruk ya dubeta duban rashin fahimta.
  "Ihsan kuma? Please karki jawomin raini mana."
  "Wane raini anan? Kaidai fadi gaskiya Malam, irin wannan kallon ba'a yinsa sai ga wanda ake tsananin so. Da idona fa na kamashi."
  Haidar ya kai mishi naushi a kafad'a yana dariya.
"Kyalemin kanina Maman Ma'aruf, idan ma hakan ne da bakinsa zai fad'a ai."
 Takaici ya ishi Faruk, ga shi a gaban kannensa ne kada su rainashi, ya watsawa su Baraka wani kallo, ba shiri suka mike har Intisar sukayi sama. Ai kuwa yayyun suka kwashe da dariya.
   "Aa, ya zaka korarmin matata?"
Faruk ya shagwa6e murya.
"Wai ni menene haka don Allah? Kun ta6a ganina da wata nace ina so ne da za a takuramin?"
  "Munfi kaunar ka ce din ai k'anina, akan ka zauna kana kallonsu tamkar wani dutse."
  Cewar Haidar cikin rad'a. Faruk ya lumshe ido ya bude alamar gajiyawa da jin zantukansu, mikewa ya yi tsaye.
  "Please stop this, ku rufamin asiri ma kada ta ji  raini ya biyo baya."
  Daga haka ya bar wajen. Suna kiransa amma ko waige. Adnan dake kallonsu ya riga ya gano wacce bestinnasa ke kallo ya kuma fahimci lallai akwai abinda Faruk ke 6oyewa a ransa, watakil ma bai fahimci komai ba har zuwa yanzun. 
     
    Acan kuwa Ummi goyon Tahir aka bata, daga nan aka hadata da kayan wankinsa ta sauko. 
   Babu wanda ya damu da kallonta haka ta wucesu zuwa sashensu goye da Tahir a bayanta wanda baikai ga yin bacci ba. Tazo wucewa ta hanyar da ta biyo ne ta hangi kofar nan ta wajen pool a bude.
"Ya akayi na manta ban rufe ba?"
Fadin haka yasa ta nufar wajen don rufewa. Ta hangi Faruk zaune saman kujerar wajen ya jingina kansa jikin kujera, jin alamun mutum yazo wucewa ne yasa shi waigowa batare da ya raba kansa da jikin kujerar ba. Ya dubeta, da sauri ta saki kofar ta juya don barin wajen.
"Kina neman wani abu ne?" Ya kira sunanta a hankali, gabanta ya hau dukan tara-tara ta juyo a gigice ta amsa da "A'a, kayi hakuri na dauka dazu ban rufe ba shine nayi niyyar rufewa yanzun."
  Ya tsaya kawai yana k'are mata kallo, itama kuma ta juya har lokacin bata da nutsuwa ta fice da sauri. Ya numfasa gami da shafar sumar kansa.
"Ya Allah, wannan wane irin yanayi ne? What's about to happen?"
  Ya fada a fili....

Duk iyaka tunaninsa bai fahimci komai ba hakanan ya share zancen, bai mik'e daga wajen ba sai da ya ji ansoma kiraye-kirayen sallar isha'i.
  Bayan an idar suka ci abinci da yan uwansa sannan kowannensu ya kama hanyar gidansa bayan an gaisa da Daddy. 
  Washegari 'yan Adamawa da wasu da yawa daga dangin Daddy na Kano suka iso. Gidan ya cika kwarai kasancewar wannan ne bikin 'ya mace na fari a gidan, sauran duk maza ne. Su Ummi kam babu ta hutu, sune wancan sune wannan, haka suke wuni aiki. Daga rainon yaran su Rahila sai taimakawa wajen wanke-wanke.
   Ranar Asabar aka soma biki inda aka sanya Baraka a lalle. A ranar dai kuma za'ayi kamu, a katon filin farfajiyar gidan akayi, wajen ya tsaru matuk'a sai ka rantse cewar ba a gidan bane. Kwalliyar fari da golden aka yiwa wajen, Amarya Baraka ita kuwa ta fito cikin farin leshi, nad'in kanta kuma kalar golden. Yanmatan kaf din su doguwar riga sukayi (golden), iyaye ne kowa yasa ra'ayinsa. Ummi ta had'e itama cikin wani jan leshi da Mami ta yi mata kyautarsa acikin kayan Ihsan, ta yi kwalliyarta daidai misali har da kwalli a idanunta, duk da hakan ba k'aramin kyau ta yi ba. Amina ita kuwa yadi kore ta saka mai adon fulawoyi. Suna daga can kujerun baya, Ummi na rungume da Tahir tana aikin raino. A haka suke kallon komai. Babu abinda ya burgeta kamar(step-dance) wanda Ihsan, Maryam (mai bi wa Intisar 'ya ga Hajiya Mama), Rukayya (mai bi wa Maryam) da kuma Ikram sukayi na wata wak'ar turanci (Looku-looku) sukayi. Sunyi shigar riga da wando, Ihsan da Maryam kuwa a maza suka fito. Abin ya yi kyau matuka kuma ya burge har ihu da tafi ya cika wajen, ga baibayesu da akayi ana daukar hotuna da bidiyo. 
   Ifice-ificen ne ya hana Tahir nutsuwa, ya hau canyara ihun kuka. Duk iyakar rarrashin da sukayi mishi ita da Amina ya k'i nutsuwa. Amina ta dubeta.
"Ko za ki kaishi wajen Mamanshi?"
Ummi ta hangeta can sai harkar gabanta ta ke yi, ta girgiza kai.
"Bari na dauko zani na goyashi mugani."
  Amina ta harareta.
"Haba dai goyo, kinga kyan da riga da siket din ya yi miki kuwa? Don Allah kar ki soma goyon nan za ki 6ata kwalliyarki."
Ummi ta yi dariya, ita bata ga wani kyau da ta yi ba da suke faman zuzutuwa. Yanda Tahir ke zillewa yasa ta maida hankali gareshi.
  "Oh  Allah, Anti bari mu dan bar wajennan ko zai nutsu."
  Amina ta maida dubanta ga abinda akeyi.
"Jeki ina nan kallo bazai wuceni ba tunda ke kam bakya jin shawara."
  Da murmushi saman fuskar Ummi, ta yi gaba ta kyaleta. 
   Can wajen(garden) ta nufa tana faman jijjigashi, har lokacin bai gama rufe baki ba, zama ta yi a daya daga cikin kujerun dake a lambun. 
"Oh Tahir, don Allah ka yi shiru kaga kallo ya barni saboda kai ko?"
   Kamar ya ji abinda ta ce, ya hau kallonta yana faman sheshsheka irin na wanda yaci kuka, ganin haka yasa ta nufi hanyar dakunansu don 6ulla zuwa kicin ba shi ruwa. 
DAN ADAM
@RUFAIDA OMAR

43
   Yana daga samansa yana dubansu da murmushi, ya karasa ga Adnan wanda bayan karin safe ya yi wanka ya cigaba da bacci ya kai mishi duka.
"Tashi kaga wani abu." Adnan ya mike da sauri yana dubansa ido waje.
"Sun iso?"
  Faruk na murmushi ya ja hannunsa zuwa barandar. Ihu ya saki wandq har saida su Mami da suka riga suka fito suka kallo shi, dariya suka sanya. Da gudu ya fira ya sauka garesu. Shima Faruk ba shi da za6in da ya wuce na bin bayansa. 

Adnan ya kama hannun Maminsa tamkar ya rungumeta don murna. 
   Baraka da Ikram a guje suma suka fito har Hajiya Babba wacce ta kasa hakurin k'arasowar yan uwannata ciki. Ta rungume Innarta, su Amina da Ummi suka zagaya domin kwasar kaya. 
  Tana janye da katuwar jaka, idanunta ya sauka akan Faruk, yana gefe ya hard'e hannuwansa yana zabga murmushinsa mai burgewa. Sanye ya ke cikin kananun kaya, riga bak'a anyi rubutu da farin abu, wandonsa ma bak'in ne, ya yi kyau har ya gaji da had'uwa. Cikin sa'a idanunsa ya kai kanta sa'ilin tuni sauran sun kama hanyar cikin gidan. Murmushi ya sakarmata, itama ta tsinci kanta da mayarmasa da martani har(dimple) dinta na dama  na bayyana. Ya ji wani abu da bai ta6a ji ba na tsirgashi, ya kauda kansa gami da soma tafiya zuwa ciki. Tana jan akwatin tamkar bata so sanadin kallonsa da take yi, namiji mai aji kenan, ina ita ina shi? Ta sauke ajiyar zuciya ta dubi gefenta jin alamun mutum. Amina ce itama rik'e da katuwar jakar Hajiya Mama tana dubanta cikin nazari, sai kuma bayan sun hada ido ta sakarmata murmushin yak'e.
"Muje mana naga bakya daga kafa ne."
Ummi ta gyada kai ta k'ara sauri. Amina mamaki kwarai takeyi na irin kallo da murmushin da ta ga Faruk na jifan Ummi da shi, da kuma kallon da Ummi ke bin bayan Faruk din da shi har ya illata tafiyarta. Ta numfasa, 'Idan ma akwai wani abun ya zama dole nasa ido na gano, bazan bari Ummi ta jefa kanta cikin matsala babba ba, ina mata kallon kanwata kamar ta jini.' Ta ayyana a ranta. Da taimakon yan aikin Hajiya Babba aka shishshigar da kayan gaba daya ciki. 
  Tsarin gidan Hajiya Babba wane sauran gidajen yan uwanta, iyakar haduwa ya had'u. Kayan duk ansaka a inda ya dace, Ummi da Amina daki guda aka hadasu wanda duk na yan aiki ne, yana daga can bayan(garden) din gidan. 
    Hira ta k'i ci ta k'i cinyewa tsakanin yan uwan, dakyar sukayi wanka suka chanja kaya sannan aka gabatar da sallar la'asar akayi zaman cin abinci. Alokacin kuma Haidar da Intisar suka shigo. Da gudu suka rungume juna ita da Ihsan sannan ta koma ga iyayen kowanne ta hau rungumarsa don dadi. 
  "Wai ke bakya girma ne?" Cewar Hajiya Mama kenan alokacin da ta rungumota. 
  "Kema dai kya fad'a Sadiya, yau kam dole kiban mijina tunda na iso." Cewar Inna kenan.
  "Ahaf, mai zuwa gidanmu sai ya shirya fa." Fadin Haidar kenan, akayi dariya gaba daya. Su Faruk na daga falo suna jiyo caftarsu, shima Haidar bayan gama gaisuwa ya komo wajensu ana hira. Faruk kusan hankalinsa ya kasu biyu, hakanan ya ji yana d'okin ganin daga inda Ummi zata 6ullo, fatansa ya k'ara cin karo da kyakkyawar fuskarta. Da zarar ya soma tunaninta, sai ya yu saurin kwa6ar zuciyarsa, aganinsa babu wani dalili da ya ke da shi da zai dunga tunanin wata can. Abu ne da tun da ya ke a rayuwa bai ta6a faruwa gareshi ba. 
    Ita kuwa baiwar Allah, suna can tare da Amina suna cin abinci, saida suka kammala suka kai komai kicin. Alokacin ta fita wanka, bayan dawowarta itama Amina ta tafi wanko jikinta. Doyuwar riga ta sanya na kanti marar nauyi na yawon gida, itama Amina doguwar rigar ce jallabiya. Ummi ta dubeta taba daga rigingine saman katifa 
"Anti ashe duk tsaruwar gidajen su Mami bai kama rabin k'afar na Hajiya Babba ba?"
  Amina ta murmusa yayinda ta zauna gefenta.
"Haduwa ma ba daya ba kedai, na ji ance fa har wajen wanka akwai(swimming pool)."
  Ummi ta zaro ido.
"Haba?"
"Wallahi a bakin su Anti Intisar na ta6a ji, ba don ma kada muyi laifi ba da mun zagaya gidan."
Ummi ta amsa.
"Wallahi kam, zanso ganin wajen wankan kuwa."
  Haka sukayita hirarrakinsu, Amina na son yi mata magana akan abinda ke gudana tsakaninta da Faruk, tana kuma tsoron kada ya kasance zarginta ne kawai, wannan yasa ta barwa zuciyarta. 
    Sun sakankance suna hira har Ummi ta soma lumshe ido na jin bacci, ganin haka Amina ta kyaleta. Cikin baccin kuma ta ji ana tashinta, ta mike zaune tana murza idanu. Ta yi mamakin ganin lokacin Magriba ya taho.
"Ki tashi magriba fa ta yi, an turo a kiramu ma sai ni na je nayi aikin." Cewar Amina wacce ke kokarin gyara hijabinta bayan dauro alwala da ta yi. Da sauri ta mik'e ta fita zuwa bandaki domin dai bandakin yan aiki mata guda daya ne kuma ba cikin dakuna ya ke ba, yana daga dan lungun dakunan. Ta iske yan aiki biyu na alwala, ta gaishesu.
"Kece Ummi?"
"Eh." Ta amsa da murmushi. Suka saki baki.
"Kema kuma yar aiki ce?"
Ta gyada kai don ta soma mamakin tambayar. 
  Daga haka ta wucesu ta shiga bandaki. Tana jiyo hirarsu, daya na fadin. "Kinsan Allah Binta, da ace ni na samu kyawun wannan ba zan bautawa wasu a aikatau ba, na gwammace na ci duniyata da tsinke."
  Bintar ta ja tsaki.
"Kedai matsalarki Sa'a kina da son maza kamar wata karya wallahi. Nayi zaton ma batun aure zakiyi."
  Sa'a ta ta6e baki.
"Aurena biyu ban ji da dadi ba, don haka ko marmarin k'ara yi bana yi."
  Lokacin Ummi ta fito sukayi shiru, ta isa ga famfon dake a gefen garden din inda suke tsaye ta soma alwala suna kallonta, suka saki baki ganin har wata suma take da a goshinta ga gashi daidai misali, ita dai ta samu ta kammala a gaggauce, ta yi musu sallama ta tafi da tunani hali irin na wasu mutanen da suke da karancin godiya ga Allah, wasu suna can ma basu samu koda rabin yanda su suka samu ba.
  A haka ta shiga ta tarar har Amina ta idar da sallar tana addu'o'in da ta saba. Itama ta zura hijab ta tayar, bayan idarwarsu suka yi zaman hira anan take ji daga bakin Amina cewa su Haidar ma sunzo.
"Mai yiwuwa suma sauran ki gansu." Amina ta karasa.
  Ummi ta bata labarin hirarsu Sa'a akanta, Amina ta dara.
"Mata kenan, muna da matsala wallahi. Mudai mu kama kanmu babu ruwanmu da harkarsu idan ba gaisuwa ba da hirar da bata shafi kowa ba. 
    Suna nan Sa'a ta lek'o.
"Ummi, Anti Aisha na kira."
"Toh."
Ta mike cikin sauri ta gyara zaman hular kanta. 
   Ta fito tana waige-waige don har ga Allah ta mance yanda tsarin gidan yake. Ta karasa wajen doguwar baranda wacce akwai bene daga wani loko, ta yi shiru, ta cigaba da tafiya, wata kofa ta gani makamanciyar wacce suka shigo, hakan yasa ta bude kofar, kawai sai ganinta ta yi a

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login