Showing 45001 words to 48000 words out of 158267 words
wajen (pool). Daga tsakiya ya ke, a gefensa rumfa ce aka sanya kujerun zama, wani murmushi ta yi don sosai wajen ya burgeta.
Ta rufe jin kamar motsi ana saukowa daga bene. Tana shirin barin wajen suka yi kici6us da Adnan. Kowannensu ya saki fuska.
"Lah, daman dake aka zo?" Ta yi dariya.
"Eh, kana murnar ganin Mami baka lura ba."
Ya dara shima. "Bari kawai, ai nayi kewarku wallahi. Ina za ki ne?"
"Kaga hanyar na rasa, Anti Aisha ce ke nemana."
Yana dariya ya soma tafiya.
"Ke kam ba dai saurin mantuwa ba, biyoni ki gani."
DAN ADAM
@RUFAIDA OMAR
45
Yana saukowa daga bene, tana tahowa, ta ji numfashinta na barazanar daukewa tsabar had'uwar da ya yi. Ya gama hadewa cikin kufta bak'i wanda ya sha aiki dinkin riga da wando, ya sanya hula, sanyawa na musamman don kuwa ya zauna dabas a kansa. Takalminsa bak'i sai shek'i yakeyi. Bak'in gilas ne a idanunsa bazaka iya tantance inda ya ke kallo ba, saidai jikinta ya bata ita din ya ke kallo shima.
Kamar kuwa tasan hakan, domin babu abinda Faruk ke kallo irin tsarin halittarta. Yarinya cikakkiya, da ace ta samu jin dadi fiye da wanda ta ke ciki da babu abinda zai hana tsantsar zubin halittarta fitowa fili. Ya kai kallonsa ga le66anta masu surkin bak'i da ja wanda hakan ba karamin k'awata siririyar fuskarta ya yi ba, ya lashi nasa le66an gami da kauda kai daga kallonta. Itama ta yi niyyar wuceshi sai kuma ta hango rashin dacewar hakan, wannan yasa ta tsayawa har ya karasa saukowa sannan ta durkusa ta gaisheshi.
Ya amsa yana mai kai hannu da niyyar kar6ar Tahir. Ba musu ta sakarmishi shi. Cillashi sama ya hau yi yana mishi wasa, nan yaro ya hau dariya. Ita kuwa batasan ya akayi ta tsinci kanta da sakin baki tana mai dubansa ba. Wani irin kyau ta ga ya yi mata musamman yanda fararen hakoransa suka fito yana dariya.
Ganin zai kallota ne yasa ta saurin sunkuyar da kanta. Babu kowa awajen domin gaba daya suna can wajen taro, ya durkusa kamar yanda itama ta ke a durkushen. Gabanta ya cigaba da lugude har da surfe(lol), wani kamshi na turaruka ke bugun hancinta wadanda suka kashemata jiki.
"Kinyi kyau." Kasa gaskata abinda kunnuwanta suka ji ta yi, hakan yasa ta dago ta dubeshi, ya cire gilas din idanunsa, ya zubamata ido da murmushi a saman fuskarsa. A rud'e ta ke waige-waige babu wanda ta gani domin dai ba'a fiye zuwa wajejan ba matukar ba wani abu babba ne ya taso ba, sai ko su din dake kwana a dakunan wuraren. Mikewa ta yi niyyar yi ba zato ta ji ya rik'e hannunta ya maidata durkuson sannan ya saki hannun yana jifanta da kallo fuskarsa dauke da mamaki.
"Wai ban hanaki wannan tsoron ba? Na lura ni kadai kike tsoron ma, ko bakyaso ina shiga harkarki? If yes ki sanarmin sai na daina."
Ummi fa kiris ya yi saura ta saki fitsari, ta dubeshi da idanunta wadanda suka kawo ruwan kwalla amma basu kai ga zuba saman fuskarta ba, sai kuma ta kasa jure kallon kwayar idanunsa mai k'ara jefeta cikin tsaka mai wuya.
Ya mike tsaye.
"Rik'eshi." Da sauri ta kar6i Tahir a hannunsa domin dai Allah-Allah ta ke kira a ranta don ya kyaleta ta wuce. Ta rasa sabon lamarin da ke shirin 6ullowa tsakaninsu. Ya maida gilashinsa, ya dubeta da murmushi saman fuskarsa.
"Ke kam ko ni saurayinki ne sai haka. Bansan sadda tsoro da kunya ya shiga tsakaninmu ba alhalin ba shiga harkarki nake yi ba. Yanzun ma dalili ne ya yi dalili."
Ta dubeshi cikin neman karin bayani, ya daga mata gira yana murmushi da gefen kumatu. Kamar mai rad'a, ya furta "Bye." Daga haka ya k'ara gaba.
'Meyasa ya na jin kansa mai aji idan yana gabanta ne wai?' Wannan ne tambayar da ya cillawa zuciyarsa alokacin da ya ke nufar can bayan inda ake taron domin shiga motarsa ya bar gidan, duk iyakar tunaninsa, ya kasa tunano komai, sai lokacin ya ke jin haushin abinda ya ke yi, ya ja guntun tsaki ya bude motar ya shiga gami da barin gidan.
Acan kuwa Ummi ta shiga yanayi mai wuyar fassaruwa, wai yau itace Faruk ke yiwa haka? Kodai yana jin yanda ta ke ji ne? Tasan ba wani so bane, kawai dai jikkunansu da zuciyoyinsu na chanja yanayi duk sadda suka ga juna ba don wani abun ba, hakanan kawai dai. Shine abinda ta ayyana a ranta.
Koda ta koma Amina ta nemi sanin dalilin jimawarta, fakewa ta yi da fadin dakyar ya yi shiru. Har taron nan ya watse, babu wani chanji daga yanayinta na sanyin jiki da yawan tunanin abinda ya kere ta, yafi karfinta gaba daya ma.
*** *** ***
KADUNA
Zaune suke tare da Munira suna faman hira, a haka Deen ya sanyo kai ya iskesu, kamar yanda Munira ta saba, mik'ewa ta yi ta isa gareshi ta taroshi, ya bata kyakkyawar runguma da sumba a kunci. Wani abu ya tokarewa Dija wuya, abin kuma kamar da gayya Deen keyi don ta tabbatar koda bata furta ba, to fa ya fahimci manufarta akansa. Ganin basu ko kula da ita ba, yasa ta amfani da hannu ta tunkude kofin tangaran din dake saman tebur, ji kake taratsatsa. Hankalinsu ya yi saurin zuwa gareta, ita kuwa ta hau salati tana fadin "Wayyo, ina shirin mik'ewa ne bansan na ta6ashi ba."
Munira da sauri ta karasa gareta.
"Sannu yar uwa, ba ki ji ciwo ba? Lanto! Lanto!"
Ta juya ta soma kiran yar aikinta domin ta tattara wajen, Deen kuwa wani kallo na kina sani ya hau watsawa Dija, wani murmushi ta sakarmishi, ya hade girar sama da ta k'asa ya bar wajen zuwa dakinsa.
Tun daga wannan ranar ta ke faman tsiro da sirfa kala-kala musamman ma idan dare ya yi ta ce bata da lafiya Munira ta yita zirga-zirga kenan zuwa wajenta itama da bata gajiya.
A gefe kuwa, ga Raihana wacce ta matsamata da waya da kuma ta whatsapp akan zata iya rasa rayuwarta muddin bata amince da bukatarta ba. Akwai sadda ta budemata wuta ta nunamata ita yanzu haka akwai namijin da take mutuwar so amma ta kasa shawo kansa ya kaunaceta. Raihana ta aikomata audio tana dariya. Ta tabatar mata ko waye shi muddin ta amince da ita to ita mai yi mata komai ce don ta mallakeshi kuma ya aureta a sauk'ak'e.
Jin haka yasa Dija kiranta kai tsaye bayan ta rufe dakin gam.
"Me kike nufi?"
Acan Raihana dariya ta yi.
"Wallahi muryarki dadi."
Banzan tsaki Dija ta ja, batasan ya akayi ta bawa yar uwarta mace wannan damar ba, fatanta dai a yanzu ta samu Deen don gaba daya idanunta a rufe suke.
"Kinga don Allah ki sanarmin idan da gaske kike."
Ganin haka yasa itama ta nutsu.
"Wallahi muddin za ki amincemin babu abinda za ki rasa a duniya Dijat. Kedai ki yarda na zo inda kike kigani."
Dija ta girgiza kai.
"Ki soma yimin aiki akan Deen idan na aureshi na rantse miki da Allah komai kikeso kin samu." Ta karashe a tsorace.
Wani ihun dadi Raihana ta saki gami da mannawa kan wayar kiss.
"Angama wallahi, Zahraddeen sunansa ko? Karki damu, yau dinnan zan kira Malamina na ji yanda za'ayi."
"Dakata (please), ki san sunan da za ki kai, kada ki cutar da ni ta hanyar asiri."
Raihana ta marairaice murya tamkar da wani saurayi ta ke maganar.
"Ba cuta tsakanina da ke don ina sonki. Ki rike wannan." (Wa'iyazubillah)
Dija ta murmusa ji ta ke yi inama Deen ke gayamata hakan ba jinsinta ba.
"Nagode sai na ji ki."
Daga haka suka rabu.
A sati daya kuwa komai ya kammala, Raihana ta aikomata sak'o ta hanyar wata abokiyar ashararancinta da ke a Kadunan. Itama ta so ta latsa Dija ta ga ba fuska sannan Raihana ta gargadeta akanta kafin ta zo. Koda Munira ta tambayi Dija wacece, cewa ta yi kawarta a yanar gizo. Munira sam hankalinta bai kwanta ba da budurwar don da gani kasan yar duniya ce, haka ta yita yiwa Dija nasiha akan ta kula da wadanda zata dunga kulawa a yanar gizo, wasu da yawa 6ata gari ne. Ta amsa da to kawai. Ta kudurta a ranta sai ranar weekend zata soma amfani da turaren, na wanka kuwa a daren ta yisu. Na zubawa a abinci shima sai ranar da ba aiki.
*** *** ***
ABUJA
Ranar da ya kama na yini da(mother's day) ranar akayi sanya ankon atamfa mai fari da bulu. Sunyi kyau matuk'a. Gaba daya abin ya burge, sai bayan magriba kowa ya soma shirin tafiya wajen fatin. Abin nasu ya yi kyau matuka, su Ummi a gida aka barsu rainon yara, har saida suka yi hira suka gaji suka soma gyangyadawa sannan suka soma dawowa. Alokacin suka koma dakinsu suka kwanta.
Washegari kuwa tun asuba basu koma bacci ba, suna kicin suna dirkar aiki na hada karin kumallo. Sai wajejan tara suka kammala komai suka mik'amusu.
Wajejan sha daya na safe sunyi wankansu tsaf, Aisha ta hada Ummi da wankin Tahir. Haka ta kar6a don ba ma su yawa bane sosai.
DAN ADAM
@RUFAIDA OMAR
46
(Sadaukar ga shafin nan gareki sisna...forgive me... Meena Yoruba)
Wajen garden inda ta ga anan suke wanki da shanya ta zagaya ta soma yi. Tare suke da Amina suna hira inda Amina ke labartamata batun aurenta da ya taho, Sa'a ta zo ta sanarwa Amina kiran Hajiya Mama. Wajen ya rage Ummi kadai cike da tunanin duniya.
To ita meyasa bata ta6a jin son wani ba ne? Ga dai maneman suna tururun zuwa har da yaran manyan dake layin makarantarsu masu son ta kulasu saidai ko kad'an babu wanda ta ta6a saurara, maganar Antinta ta fad'omata a rai.
"Kema auren nan ya dace kiyi Ummi, shi kadai ne jin dadinki, ki tara zuri'ar kanki."
Abinda tace mata kenan a wannan hirar da sukayi. Ta girgiza kai tana duban wani dan lilo dake a wurin.
'Babu wanda nake so a raina yanzu Anti.' Ta ayyana a ranta. Haka ta k'arasa wankin ta mik'e ta nufi wajen shanya, tana cikin shanyar ne ta ji sallamar mutum agefenta. Da sauri ta dubi wajen jin muryar namiji. Ta gane ko wanene duk da batasan sunansa ba, amman cikin bak'in Adamawa ya ke. Kana ganinsa shima kaga bafulatanin usuli, ta gaisheshi ya amsa da harshensa mai sirkin yare biyu(Hausa fulani).
"Sannu, ina daga can ina ganinki tun dazu ai, ya sunanki ne?"
Mamaki karara ya bayyana saman fuskarta, baiyi kama da saurayin arziki ba, yafi yin kalar 'yan duniya. Ta k'ara kare kirjinta da ya zubawa ido don kuwa doguwar rigar jallabiya ce jikinta kusan duk ta jik'e agarin wanki. Murya na rawa batare da ta k'ara kallonsa ba ta amsa.
"Ummi."
Ya lura da abinda ta yi din sai kawai ya yi murmushin duniyanci ya shafi ha6ansa.
"Wow, kina da suna mai dadi fa. Ni sunana Kabir but you can call me KB. Ke 'yar uwar su Daddy na Baraka ce?"
Ta girgiza kai don ta k'osa ya bar wajen.
"Aa, ni 'yar aiki ce."
Ya zaro ido da mamaki.
"Yar aiki? Kike da wannan kyan?" Ya ta6e baki
"Gaskiyar magana bebi kin fi karfin zama yar aiki. Idan za ki ban had'in kai to zakiji dadin rayuwa son ranki."
"Innalillahi..." Ta karashe a fili. Zaiyi magana, Amina ta katse hirar ta hanyar gaisheshi. Suka dubeta don basusan ta iso ba, ya amsa ba don yaso zuwannata ba, ya wani tamke fuska gami da fadin.
"Sai wani time din bebi, zan nemeki."
Daga haka ya fice, da sauri Amina ta nufota gami da rike kafadarta a tsorace.
"Mene hadinki da Kb? Kinsan kuwa ko wanene?"
Itama Ummi duk sai ta k'ara rud'ewa.
"Wallahi shi yazo nan yanamin magana." Ta zayyanemata yanda sukayi. Amina ta numfasa.
"Nagode Allah da ba ki ce komai bayan wannan ba, ki yi kokarin nisantarsa, yaron dan iska ne fiye da tsammaninki. Akwai sadda ya ta6a zuwa gida Hajiya Mama basunan sai ni kadai, wallahi Allah ne kawai ya kwaceni daga hannunsa, ya so 6atamin rayuwa. Ki kiyaye Ummi, nasan halinki, ki k'ara akan wanda nasanki na tsare mutunci."
Ummi ta dubeta.
"In sha Allah Anti zan kiyaye."
Ta taimakamata wajen k'arasa shanyar sannan suka nufi ciki. Da gudu Sa'a dake la6e ta koma ciki. Kai tsaye dakinsu ta nufa kicin ta nufa inda Binta ke goge-goge ta fesamata yanda Kb da Ummi sukayi harma da nasihar Amina gareta. Binta ta ja tsaki.
"Banza da ita, ta samu damar da muke nema ta yi watsi da shi, ji dai yanda ya nemeki sau d'aya kuma ya dawo ya juyamaki baya sai zagi idan ya zo kamar gidan ubansa."
Sa'a ta yi kwafa cike da jin takaici.
"Bari kawai, ni su Ummin ma sunfi ban takaici su basu yarda ba masu tsoron Allah. Gulma ce dai, ta ciki na ciki."
Binta ta ajiye tsumman hannunta.
"Ke, ga hanyar samun kudi wajen Kb. Mezai hana tunda ya ganta ya kyasa, mu kai mishi ita kinga kuwa ba karamin kud'i zai bamu ba."
Sa'a ta yi shiru tana nazari, tasan Kb akwai sakin aljihu musamman akan mace. Ta dubi Binta suka kyalkyale da dariya sannan suka cafke.
"Shegiya, kina ja wallahi. Bari zan sameshi a 6oye mu ji yanda zaayi."
Cewar Sa'a, Binta ta jinjina kai cikin gamsuwa.
Da yamma kuwa duk ana ciki ana shan kid'a da rawa kasancewar an daura aure kuma ba wani(event) da suka shirya zasuyi sai dinner wanda Ango ya shirya kayansa. Sa'a ta yi nasarar ganin Kb a farfajiyar gidan yana amsa waya can gefe, da sauri ta karasa wajensa tana fadin. "Yalla6ai." Ganinta yasa ya ja guntun tsaki ya daure fuska, saida ya kammala waya ita kuwa na waige-waige bata hangi wani mai ganinsu ba.
"Lafiya?" Ta dubeshi tanq murmushi.
"Lafiya kalau, daman wata magana na zo maka da ita."
Ya daga kafada.
"Ta mecece?"
"Dazu na ganka kana magana da Ummi, nasan kuma ka kyasa dw ita ne. Idan babu damuwa ni zan kawomaka Ummi, idan har ka yarda za ka biyani."
Wani sanyi ya ji a ransa, sai lokacin ya sakarmata wani shu'umin murmushi ya sosa kai yana duban farfajiyar gidan, babu wani mai kallonsu sai tsirarun ma'ikatan gidan dake harkokin gabansu.
"Idan kudi ne, kinsan bani da matsala da su. Kedai ki cika alkawari."
Ya kara dubanta fuska babu wasa.
"Kada kuma ki kawomin rainin hankali idan ba haka ba kinsan sauran. Ki zauna cikin shiri, yau da zarar kowa ya tafi wajen(party) ki yi yanda zakiyi ki kawomin ita sashenmu, zan iya biyanki ko nawa ne."
Daga haka ya fiddo dubu biyu ya damk'a a hannunta.
"Ga wannan ki sanyawa wayarki kati, ai kina da lambata ko?"
Ta gyada kai farinciki ya cikata ganin dubu biyu, wanda idan ta yi wayasan ko nawa zai bata.
"Eh akwai." Daga haka suka yi sallama fuskar kowanne a sake.
Faruk dake daga sama yana dubansu ta windo, mamaki ya cikashi, shi yasan wanene Kb, yasan kuma illarsa ga diya mace. Babban abin daure kan menene hadinsa da Sa'a? Ko har ita din ma akwai abu tsakaninsu? Ya girgiza kai cike da jin tsanar Sa'ar domin ita ta bada fuska. Ya juya ya koma falo cikin yan uwansa kusan sa'anninsa kuma bak'in Adamawa aka cigaba da hira kafin duk su fito waje don shan iska.
Misalin takwas duk an soma tafiya wajen party da zaayi a Nicon, su Ummi dai na tsaye a farfajiyar wajen sai kallon kwalliya sukeyi. Kowacce ka gani ji takeyi da kanta, duban kanta takeyi a had'add'iya. Wajen sai kamshi kakeji, matasan ma kuwa da alama har da samarin wasu cikin yanmatan. Duk wadannan ba su suka damu Ummi ba face ta inda zata ga 6ullowar Faruk. Shi kadai zuciyarta ta kwadaitu da gani batare da tasan tak'amaiman dalili ba.
DAN ADAM
@RUFAIDA OMAR
47
Daga gefensu ta ji Ikram na balbale Ihsan da fad'a.
"Wallahi zakiyi asarar fatin yau matukar kika kafe sai tare da Yaya Faruk za ki je, idan ma kin shirya tafiya gwara tun wuri ki taho mu tafi don wallahi a yanda nasa halin Yaya Faruk zai iya cewa ya fasa. Mun tafi na daukarmaki komai a waya." Daga haka ta yi gaba.
Ihsan ta yi saroro, ganin dai dagaske Ikram take yasa ta bin bayanta da gudu-gudu, abin sai ma ya bawa Amina da Ummi dariya.
"Wallahi yanzu lamuran Ihsan dariya sukeban." Cewar Amina.
Ummi ta ta6e baki.
"Ato, tunda ta maida kanta wata tsiya ba."
Saida suka ga tafiyar kowa amma basu ga na Faruk ba. Hankalin Ummi ya tashi, ranta ya sosu, ta so kwarai ta ga tafiyarsa, ta kwadaitu matuka da ganin kalar wankansa. Haka suka koma falon, iyayen daga Hajiya Babba sai Inna da wasu dattijai mata yan Adamawa ya rage, suna sama, suka tattara komai sannan suka wuce 6angarensu.
Suna zaune anan sai ga Sa'a ta shigo.
"Ummi, ki zo Adnan na nemanki."
Da mamaki ta dubi Amina.
"Na dauka Adnan ya wuce."
"Tabbas nima naga shigarsu mota."
Sa'a ta yi yak'e.
"Dawowa ya yi, wai ki zo sak'o zai ba ki daga Mami."
Basuyi tunanin komai ba don babu wanda ya kawo Sa'a zatayi hakan cikinsu, Ummi ta mike da sauri yana gyara zaman daurin dankwalinta na atamfa, don sauri ko hijab bata tsaya sanyawa ba ta zura takalmi tana fadin.
"Bari naje."
Amina ta kishingida tana fadin.
"Wash!" Gami da lumshe ido, Sa'a ta kunce gefen zaninta ta yi amfani da hodar da Kb ya bata ta wuce sadaf-sadaf ga Amina ta shek'a mata a hanci, Amina kafin ta yi wani yunkuri bacci ya sureta. Da sauri Sa'a ta bi bayan Ummi.
Ita kuwa Ummi kai tsaye waje ta nufa saidai bata ga mota ba, hakan yasa ta zuwa wajen fakin motoci nan ma bata ga mota ba sai guda daya, da alama da mutum ciki sakamakon kidan da ke dan tashi amma zuwanta aka kashe. Zata nufi wajen Sa'a ta karaso tana kiranta. Ta tsaya gami da juyowa.
'Yauwa ina Adnan din?"
Sa'a ta dubeta.
"Yanzu na ganshi ya nufi sashensu, shima nemanki yakeyi."
Ummi ta jinjina kai.
"Munyi sa6ani kenan, bari na je."
Da sauri ta nufi hanyar sashensu Adnan, Sa'a ta saki dariya yanda ba zata ji ba, ta bi bayanta.
"Adnan?" Ya furta a hankali, a iyakar saninsa Adnan baya nan sai Kb wanda ya bari yana shiryawa amma don tabbatarwa ya dauki waya ya dannawa Adnan kira,