Showing 54001 words to 57000 words out of 158267 words

Chapter 19 - Dan Adam Book 1 Complete Hausa Novel

fahimta da yanayin da muke ji game da juna a zukatanmu?"
  Ta girgiza kai ta daure ta ce. "Babu."

Ya yi wani murmushi.
"Ai nasan zaayi haka." Ba ta ce komai ba, shi kuwa saida ya ja fasali sannan ya cigaba da magana. 
   "Kin sani kamar yanda na sani Ummi, amma mu ajiye wannan a gefe."
Shiru ya dan biyo baya kafin ya dora.
"Bani tarihin rayuwarki idan da hali."
  
'Rayuwata?' Ta yi tambayar a ranta. Ganin ta yi shiru ya k'ara magana.
"Look Ummi, ki saki jikinki da ni please, ba ma ke ba, ni kaina ban yi sabo da hakan ba, sai kin zauna da Faruk za ki fahimci ko waye shi. Ban fiye sakin jiki da mutane na yi hira har haka ba, da dai cikin brothers na ne ko Hajiyata. So please Ummi ki min alfarmar nan, ki saki jiki da ni, ina so nan gaba ma mufi haka kusanci kinji ko?"  Ya k'arashe cikin rad'a gami da yin murmushi mai sauti, baiwar Allah idanunta suka cika da kwalla, ga samu ga rashi. Tana son abinda ba za ta ta6a samunsa ba don a yanzun da ya ke magana ji ta ke yi tamkar ana k'ara rura mata wutar kaunarsa. Bata ba shi amsa ba face ta shiga labartamasa labarinta iyakar wanda ta sani banda wanda batasani ba kuma bata ta6a samun labari ba, wato na zamantakewar mahaifinta da mahaifiyarta. To mai labarta matan ma ba shiga sabgarta ya ke yi, bai dauketa matsayin 'ya ba.
   Tiryan-tiryan ta ke bashi labari tana yi tana zubda ruwan hawaye har ta kai yanda aka kawota aikatau. 
   Tana kaiwa karshe ta cigaba da kuka mai kona zuciya, ba don komai ba sai tunanin rashin gatanta da kuma na son abinda ba zata ta6a samu ba.
   Tattausan hannunsa ta ji a saman kumatunta yana share mata fuska, baki ta saki tana kallonsa, ba kwayar idanunta ya ke kallo ba, kyakkyawan farar fatarta ta ke kallo yayinda ya cigaba da magana yana murmushi mai kama da yak'e, fuskarsa dauke da damuwa da tausayi.
       "Kinzo inda za'a share miki hawaye da taimakon Allah, idan har Faruk na numfashi, in sha Allah zai zame miki haske a rayuwarki. A yanzu ta bakinki nake son ji."
  Sai lokacin ya dubeta, ita kuwa idanunta a lumshe suke sakamakon yatsunsa da ke akai yana sharemata kwalla. Daidai lokacin kuma ya dauke hannunsa daga kanta. Ummi bugun kirjinta k'aruwa kawai ya ke yi, ita dai bata ta6a jin yanayin nan kan kowa ba sai shi, ta kasa dubansa, anya kuwa zata iya daukar shawarar Antinta Amina? Kai, dole ta dauka don Antinta ba zata cuceta ba.
    "Kin yarda kin amince mu k'ulla alak'ar da zata kai mu ga AURE? Ta wannan hanyar kadai zan iya taimakon rayuwarki Ummina."
    Kamar ta tashi ta ruga a guje ta ke jinta, Faruk dama ya muryarsa ta ke wajen sanyi kamar mace ballantana kuma yana cikin yanayi na shaukin so da kauna. Ta dan matsa don rage kusancin da ya yi mata. 
    "Kayi hakuri, ni babu wani abu da nake ji game da kai, ban dauke ka komai ba sai dan uwan Yaya Adnan kuma iyayen gidana, ka yi hakuri, bazan iya jefa zuciyata cikin abinda zan wahala ba."
   Daga haka ta kwashi wayoyinsa ta mik'a mishi, saidai ba shi da niyyar kar6a, asalima idanu ya zubamata yana murmushi. Ganin haka yasa ta ajiyewa a kujerar da ta mik'e zata tafi.
  "Ji mana."
  Ta tsaya cak gami da juyowa. Ya dauke wayoyinsa ya dubeta.
"Dawo ki zauna."
   Ba musu ta dawo ta zauna tana share hawayen saman fuskarta.
  Ya dawo ta gabanta ya durkusa. 
"Hey, kalli tsakar idanuna ki ce ba ki amince ba."
  Ta kauda kanta tana jin tamkar ta fashe da kuka gaba daya ita ta gama tsorata ganin Faruk dagaske ya ke babu wani sassaunci. 
    "Ummi say something please, ki ce wani abu mana."
   Ya fada cikin shagwa6a66iyar muryar da bai fiye amfani da ita ba sai ko a gaban Hajiyarsa. Ta girgiza kai.
  "Ni ban amince ba."
  Ya dubeta na sakanni ya na murmushi.
  "Dagaske ba ki amince ba?"
Ya fad'a yana mai kwaikwayon muryarta, abin ya so bata dariya ta kuwa saki murmushi.
  "Masha Allah, ko kefe. Naji wannan kuma nagode, amsa tuni na sameshi, hirar ce nakeson muyi don bakisan yanda nakejin dadin ganinki bane."
  Shiru babu wanda ya k'ara magana, can kuma ya sauke ajiyar zuciya ya kunna wayoyinsa. 
  "Goma har ta kusa."
  Ya fad'a yana duban wayar, can kuma ya mik'e ya sanya wayoyin a aljihun wandonsa, ya yi amfani da tafukan hannayensa ya dafa gwuiwarsa gami da sunkuyowa yana dubanta.
  "Saida safe."
Ta gyada kai sannan ta gifta ta mike tsaye da sauri don daman tun dazu ta soma jin tsayuwar motoci a harabar gidan ta tabbatar yanzun su Mami sun iso. 
   "Allah Ya tashemu lafiya."
  Daga haka ta yi gaba da sauri, koda ta isa ga kofar saida ta kasa jurewa ta juyo kanta ta dubeshi, shi ba shi ma da niyyar barin wajen don komawa ya yi ya zauna. Su ka yi ido hud'u da shi, ta dauke kanta da sauri-sauri ta bar wajen tana ji yana fad'in.
  "Ko na zo ne?"
Bata ko juyo ba balle ta tanka mishi. Ya yi murmushi karo na ba adadi sannan ya kwantar da kansa jikin kujera, kai tsaye hotonta ya lalubo wanda ya yi mata a wata rana da ta ke zaune tana wanki a (garden) da kuma na zanen da ya yi mata.
  "Ke tawa ce in sha Allah."
DAN ADAM
@RUFAIDA OMAR

55
                      KANO
Mami ta yi mamakin chanje-chanjen da ta gani wajen Mijinnata. Abin mamakin bai wuce yanda ya dage akan lallai su bata girkinta ba. A ranar kuwa suna isa ita ce ta shiga fadarsa. Saboda Fahad, Ramma ta kwana a gidan kasancewar yaranta suna kauye ziyarar dangin ubansu.
     Ta sha rok'o a wajensa akan ta yafemishi har ta gaji domin duk da nunamishin da ta yi komai ya wuce, bai iya sakin jiki ba. Ranar kam komai ya yi lafiya, ya sanarmata haka kawai ya soma tsintar kansa cikin halin tunani da kuma tsananin kewarta.
  Tsakanin mata da miji dai sai Allah, a wannan daren suka dinke har ma ya nemi kiran d'ansa don ya dawo ya soma shirin tafiya karatunsa. 
    'Babu abinda ya fi karfin Allah.' Shine abinda Mami ta fad'a a zuciyarta cikin murmushi lokacin da ta saci kallon fuskar mijinta ta ga annurinsa ya dawo ba kamar da ba.

                     ***  ***  ***
                        ABUJA
    Misalin karfe shida a gaggauce ya kammala shirinsa ya fice zuwa aiki ko karyawa bai tsaya yi ba. 
  Ummi tun misalin takwas suka soma ayyukansu, ta yi gyararrakinta tsaf, Binta itama ta kama nata. Hajiya Babba ta yaba kwarai da gyaran Ummi. Koda ta shigo ta iske falon kyal-kyal tana(mopping) ta kalli wajen kafin ta amsa gaisuwarta da murmushi dauke saman fuskarta.
  "Eh lallai, dole Madina ta so zamanki wajenta, ashe haka kika iya gyara? Lallai kam na yaba miki Ummi."
Wani murmushi ta yi har kumatunta saida suka lotsa, kwarai ta ji dadin wannan yabo da ta samu. Hajiya Babba ta yi dakinta, nan ma an kyalkyaleshi tamkar ba'a ta6a kwana cikinsa ba. Komai tsaf, hakanan ta ga bambancin aikinta da na Sa'a kwarai.
   Ummi duk jikinta babu dadi, duk da cewar tana son gujewa Adnan, rashin had'uwarsu a kwana biyunnan yana damunta, batasan dalilin son sanyashi a kwayar idanunta da ta ke yi ba. Hankalinta ya kai ga tafkekan hoton matasan yaran Hajiya Babba. Dukkansu sanye suke da shadda ruwan k'asa tazarce, ta sha surfani mai tsada. Hularsu mai surkin ruwan k'asa mai duhu da marar duhu, a tsaye sukayi hoton a farfajiyar wani  (hall), daga hotunan bayansu za ka tabbatar cewar a wajen wata walima ne.
  Ta kauda idanunta gami da sauke ajiyar zuciya, duk cikinsu babu wanda yafi haskakawa a idanunta kamar Faruk, ko don shi zuciyarta ke so ne?
DAN ADAM
@RUFAIDA OMAR

  54

A wannan ranar dakyar ya jure suka kammala suka tashi, a hanya Magriba ta riskeshi haka ya karasa gidan ya yi fakin duk jiki a sanyaye. Bai zarce ko'ina ba sai sashensa. Saida ya yi sallah ya watsa ruwa ya sanya bak'ar jallabiya a saman gajeran wandonsa sannan ya yi niyyar shiga cikin gidan.  Hankalinsa ya kai ga Adnan wanda ke kwance saman gado yana danne-dannen waya. Yatsun k'afarsa na hagu ya ja wanda ya tilastawa Adnan yin gefe da wayar yana mai sakin k'ara lokaci guda kuma da dariya.  
  "Kai my best."
  Faruk ya murmusa kadan.
"Baka da aiki sai(chatting) kwanakin nan,  ya dace na soma haramar kora ka makaranta naga ta (chatting)."
  Dariya Adnan ya cigaba da yi. Faruk ya zura silifas dinsa ya fice zuwa sashen Hajiyarsa. 
    Bayan saukowarsa daga bene saida ya tsaya cak yana k'arewa hanyar dakunan yan aikin kallo, yasan Ummi zuwa yanzu ta yi mishi nisa. Ya sauke ajiyar zuciya gami da juyawa ya cigaba da tafiyarsa. 
  A falo ya iske Ikram da Ihsan suna cin abinci suna hira. Ganinsa yasa duk suka dubeshi suna mai amsa sallamarshi. Yana duban Ihsan da mamaki ya jefamata tambaya.
  "A'a, baku wuce ba?"
  Ihsan cikin kashe murya ta ce "No sun wuce, ina nan sai bayan sati biyu zan koma."
    Bai wani ji dadi sosai ba, zaman Ihsan takura rayuwarsa kawai ne, ba yau ba ya soma lura da take-takenta, shi din ya kasance mai saurin fahimtar masu nunamasa so haka. Yana sane da Iklima ma, sai yanzu ne ma ya fahimci ta dan kwana biyu bata mishi koda sallama ba a whatsapp ballantana kuma akai ga kira. 
   "Ok." Shine kawai abinda ya ce sannan ya k'ara gaba. Ihsan ta bi bayanshi da kallo har saida Ikram ta zungureta.
  "Kin shiga uku wallahi kedai, nikam har na daina mamaki."
Ihsan ta yi murmushi.
"Me kike nufi?"
"Ina nufin ki sanarmasa kina sonsa."

  Ihsan ta zaro ido.
"Zubda aji."
   Ikram ta yi kwafa.
"Tsaya kallon ruwa kwado ya yi miki k'afa."
  "Wai kina nufin akwai wacce ya ke so?"
  Ikram ta yi dariya.
"Bani da tabbacin hakan. Amma kada ki sake ki tsaya wani jan aji wallahi. Yayanki ne, koda zai wulakanta kowa banda ke."
  Ihsan dai ta yi shiru ta cigaba da kai loma, maganar Maminta kawai ta ke tunanowa inda ta yita bata shawara akan ta yi kokarin jawo hankalinsa ta kissa. 
         
   Ya dan jima wajen Hajiyarsa har akayi kiran salla tukunna ya fito. Daga masallaci dakinsu.
    Ya dan jima wajen Hajiyarsa har akayi kiran salla tukunna ya fito. Daga masallaci dakinsu ya wuce, can su Ikram suka kai musu abincinsu, har lokacin sam ba shi da masaniya akan Ummi na Abuja. Koda ya shiga wajen Hajiyarsa, bata sanarmishi ba.

                   *** *** ***
                   KADUNA
  Wasa-wasa karamar magana ta zama babba, domin kuwa Deen da Dija soyewarsu sukeyi son ransu, saidai hirarsu ta fi a waya ko kuma idan sun yi sa'ar rana Munira bata gida. Tun ita Munira bata ganewa har ta soma zargin akwai wani abun. Kamar yanda Deen ke damuwa da harkar Dija sosai, abin mamaki har zuwa ta ke ta zauna a hau wasa da dariya da ita har ma su dinga wareta cikin hirartasu saidai ta yi shiru tana sauraronsu. 
    Dija da kanta ta bawa Deen shawara akan lokacin komawarta gida ya yi idan har da gaske ya ke sai ya turo magabatansa. Alokacin ne kuma ya yi dumm, ya dubeta.
"Kina ganin hakan bazai janyomin matsala da Munira ba?"
  Ta ji haushin furucinsa, ta fahimci koda asiri ya ci shi akanta, tofa baisa ya mance da matarsa ba. Ta nunamishi idan ba zai iya aurenta saboda matarsa ba, shikenan. Anan kuma ya hau bata hakuri suka ajiye maganar yanda za'a 6ullowa lamarin. 
  Kwanaki biyu da yin maganarsu ta tattara ta koma Ringim, Munira ta ji dadin tafiyarta don Allah shaida ta soma tunanin akwai wata alak'a tsakaninta da maigidanta wanda bata fatan zatonta ya kasance gaskiya.  Ta rik'i Dija yar uwa haka kuma da zuciya daya ta ke zaune da ita. Koda zasu rabu, tayi mata kyauta ta sutura da abin hannu, idan kuma zaa hada da wanda Deen ya yi mata, to fa ba komai bane. 
                  ***   ***  ***
                     RINGIM
   
  "Lale da 'yan Kaduna. To, saukar yamma ce?" Baba Habiba ta fada tana mai dan tafa hannuwa kamar kawata Bingel a fagen nanaye (LOL). Dija ta sakarmata jakar kayanta ta kar6a da gaggawa tana mai k'arewa diyartata kallo da dumbin mamakin yanda akayi ta chanja, wani k'iba ta k'ara da kyau. 
  Sai da dare bayan sun zauna ne suna 'yar hirarrakinsu, wayar Dija ta k'ara daukar k'ara a karo na biyar tun shigowarta gidan. Baba baki bude ta ke dubanta, ta rasa inda zata tsoma ranta don tsananin murna, ga dukkan alamu dai diyarta ta samu saurayi dan birni, lallai ba zasu yi sake ba.
     Bayan Dija ta ajiye wayar ne ta dubeta.
  "Ya sunansa?" Dariya ma tambayar ta bawa Dija, bayan ta gama kyakyatawa ta ce "Wa kenan?"
  Baba ta girgiza kai.
"Ke bafa za muyi sake ba, fadamin sunansa mu k'ara kamashi a hannu yanda bazai ta6a iya su6uce mana ba kafin zuwa lokacin da za'a tashi aurenku muyi shiri na musamman."
  Wani murmushi Dija ta saki.
"Zahraddeen sunansa."
  Baba ta zaro ido waje.
"Wanne kenan?"
  Babu ko d'arr ta amsa.
"Zahraddeen dai da kika sani, mijin Munira, shi nake so kuma ya ke sona."
   Baba ta yi tsit, Dija tiryan-tiryan ta labartamata ire-iren hidimar da yake mata har da kyautar kudi dubu talatin da ya yi mata da za ta taho ya kuma siyamata sabuwar waya tana nan cikin kayanta. Har ma da yanda suka ajiye magana da shi akan zai zo neman aure. Bayan ta kammala bayanin ta fiddo kudaden ta damk'a a hannun Babarta, ta zaro kwalin wayar shima daga jakarta tana mai nunamata. Baba Habiba ta zurawa kudin ido da wayar kafin ta washe baki.
"Ke Dije! Wadannan yanzu duk mallakinki ne? Shakka babu daman bokanya ta tabbatar min idan mijin aurenki ya zo za muyi mamaki gashinan tun ma ba'a je ko'ina ba na soma. Abun yi yanzu, gobe zan koma gidan bori na ji yanda zamuyi ayi komai cikin salama batare da ansamu matsala ba, don ta ubanki mai sauki ne, sai yanda nace."
  Wani ihun dadi Dija ta saki gami da rungume mahaifiyarta.
"Shiyasa nake bala'in sonki wallahi Baba."
  Suka yi dariya, nan suka soma shawara kan irin k'ulle-k'ullen da zasu sanya ayi bayan auren. Ko kusa Dija bata sanarmata komai akan Raihana ba gudun yanda zata yiwa kallon abin.
                  ***   ***   ***
                      KANO
DAN ADAM
@RUFAIDA OMAR

56
  
    Har Ummi ta yi kwana biyu a gidan, Faruk ba shi da masaniya don gaba daya aiyuka sun mishi ca a ofis. Ba shi ya samu kansa ba sai ranar Asabar. Ranar kam ya sha bacci, bai farka ba sai sha daya. Kai tsaye wanka ya fad'a, bayan fitowarsa ya shirya cikin t-shirt fara tas da wando na (Adidas), bak'i mai surkin fari kadan sannan ya zura silifas ya nufi sashen mahaifiyarsa.
   
    Tafe take a hanyarta ta zuwa wajen(garden) don dauraye tsummokaran da ta kammala gyaran dakunan Hajiya da su. Kallon benen da zata yi ta ganshi yana saukowa shima a daidai lokacin ya bar duban wayarsa ya maida ga hanya alokaci daya kuma yana kokarin sanya wayar aljihun wando. Karaf idanunsa cikin nata, yanda ta tsaya bata motsa ba, shima ya tsinci kansa da mutuwar tsaye. Abu biyu ke yawo a kwakwalwarsa. Buri na son kasantuwar abinda ya ke gani yanzu tamkar mafarki da kuma tambayar daman tana gidan? 
  Dakyar ya yi jarumtar k'arasawa har gabanta, alokacin ita kuwa ta sunkuyar da kanta cike da matsanancin fargabar abinda zai k'ara ce mata.
   Saida ya kai dab da ita har suna jin numfashin juna sannan ya sauke ajiyar zuciya ya matsa, ya tabbata ita din ce ba gizo ta ke mishi ba. A hankali ya matsa baya, cikin rawar murya ta gaisheshi bayan ta durkusa. Ya amsa cikin jin wani irin nishadi a ransa, ta mik'e tsaye, tana shirin barin wajen maganarsa ta dakatar da ita.
  "Daman ba ki tafi ba?"
  Ta dan saci kallonsa, murmushi ta gani dauke saman fuskarsa wanda ya kara fiddo kyawunsa.
  "Eh."
  "Saboda ni?" Ya fada a tausashe bayan ya dan rankwafo da kansa yana kallon fuskarta.
   Ta k'ara satar kallonsa, shi dinma bai kauda nasa idanun daga kanta ba. Ta ji wani iri a jikinta, wai saboda shi. Maganar ma nauyi ta yi mata, ta kauda idanunta.
   "Mami ta ce na zauna zuwa wani lokaci."
   Ya ji dadin maganar, ba zai iya misalta farin cikin da ya shiga sanadin hakan ba. Ya dubi hanya babu wani ko wata da ke tahowa sannan ya dubeta.
  "Ummi, yau kenan za ki tayani hira?"
Ta zaro ido batare da ta dubeshi ba, cikin sauri ta girgiza kai.
  "Kayi haku..."
"Shiit." Ya dakatar da ita ta hanyar dora yatsansa a saman le66ansa.
  "No please, karki hana zuciyarki abinda ta ke so mana Ummi. Ko kina so wani abu ya faru da mu sanadin hana zukatanmu farin cikinsu?"
  Ba amsa sai idanunta da suka kawo ruwa, ya mik'e da rankwafawar da ya yi. 
   "Shikenan, ki tafi, mu had'u wajen pool."
   Daga haka shiru ya biyo baya, karshe ma ya juya ya cigaba da tafiya. Da ido ta bishi, ta tabbatar shi babu abinda ya ke tsoratashi, kamar yanda babu matsalolin da ya ke hangomusu, ita kadai ta damu da duk wadannan. 
  Koda zai shige saida ya juyo domin ganin yanayin da ta shiga, suna hada ido ta juya da sauri ta soma tafiya. Murmushi ya saki kafin ya karasa cike zuciyarsa cike da tsantsar farinciki. Daidai da Ikram da Ihsan sun ga chanji yau wajen yayannasu, don kuwa biyemusu ya yi akayita hira da dariya. Ihsan ji ta ke tamkar ta buga tsalle don murna da farinciki, yau ita Faruk ya dage hira da ita? Tabbas shawo kansa zai zo mata da sauki muddin ya d'ore a haka. 
   A yan kwanakin da ta yi tsaf Hajiya Babba ta fahimci inda ta dosa, a farko bata gaskata Ikram ba da ta sanarmata cewar Ihsan na son Faruk ba, saida ta lura da kanta. Abin ya yi mata dadi, zata so hakan ta kasance, saidai d'annata ne batasan abinda ke ransa ba. A ganinta da wuya ya kaunaci yarinya mai rawar kai irinta,

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login