Showing 66001 words to 69000 words out of 158267 words
kwashe kyaututtukansa."
Girgiza kai ta yi.
"Ki taimakeni ki je ke kadai babu inda zan je."
Dariya Binta ta saka.
"Kekam ban ga irinki a fagen tsoro ba."
Ummi ta bi ta da kallo kawai har ta fice.
Haka shagalin ya k'are kowacce budurwa jiki a sanyaye don ba'a samu shiga ba ta ko'ina.
DAN ADAM
@RUFAIDA OMAR
63
Misalin tara na daren, falon Hajiya Babba babu kowa sai matasan yaranta da matansu, sai kuma su Ikram.
Fadila ta kar6i hoton zanen daga hannun Jidda tana mai kuramishi ido itama. Jidda ta dubesu.
"Nikam kaina ya k'ulle ai, nayi iyakar yi na na kasa gane wacece wannan wallahi. Kai na karfen baka kyauta mana ba, yanda muka ci burin yau mu ga hoton matarka?"
Ta karashe tana duban Faruk wanda abincinsa ya ke ci babu ko alamun damuwa a fuskarsa.
"Ke dai bari kawai Jidda, ni kaina ya soma sarawa ma don kallon zanen." Cewar Fadila. Sukayi dariya, Hajiya Babba ta mike tana fadin.
"Um, idan dai Sadauki ne kadan daga aikinsa, a komai sai ya bada mamaki."
Daga haka ta barsu suka bita da kallo. Faruk ya dubi Haidar.
"Broda, ina fa da magana da kai."
"Bakasan hanyar gidana ba?"
Ya yi murmushi.
"Sau daya fa na ta6a zuwa gidanka tun kafin tariyarka, kaga kuwa na mance."
"Aa Lil, baka kyauta ba kam." Cewar Dakta.
Babban Yaya na murmushi ya cafe.
"Kuyi mishi uzuri, aikinsa babu hutu sosai."
Haka sukayita hirarsu, a karshe bayan duk sun tafi, Ikram ta mike rike da takardar zanen zuwa dakinsu.
Ihsan na kwance har kanta ya soma sarawa sanadin kukan da ta ci. Ta mike zaune gami da kar6ar takardar.
"Duk iyakar tunani ban gane wacece wannan ba Ikram, saidai na rasa dalilin da yasa jikina ke bani kamar na santa, kuma na ta6a ganin kwayar idanun nan."
Ikram ta jinjina kai.
"Ni kaina nakasa hakura da kallon zanen wallahi, gani nakeyi kamar nasanta."
Ihsan ta ja tsaki gami da wurgi da takardar.
"Me zan amfana da shi a saninta ma? Ni yanzu gaba daya na gaji da zaman Abija, gida zan koma."
Ikram ta dubeta.
"Kada kiyi saurin karaya ina kara baki shawara, ni nasan taimakon da zan miki."
Ihsan ta dubeta cikin rashin fahimta.
"Ban fahimceki ba."
Murmushi Ikram ta yi.
"Kedai ki bani lokaci."
Jin hakan yasa Ihsan ta dan samu nutsuwa.
A daidai gaban motar Haidar suka tsaya, Intisar na ciki tana jira su kammala. Haidar ya dubeshi.
"Ina jinka."
Faruk ya gyara tsayuwa.
"I am serious fa, wacce na zana dagaske ita nake son aure, saidai ni a wajena ban dauki hakan matsala ba kamar yanda ku ma bana tunani za ku k'i farincikina."
Haidar ya daga kafada kadan cikin rashin fahimta.
"Me ya kawo duk wadannan? Yarinyar musulma ce?"
"Eh."
"Tana da asali?"
"Kwarai kuwa."
Murmushi ya yi gami da dafa kafadarsa.
"Idan akwai hakan, a ganina babu wata matsala, gayamin a ina ta ke?"
Faruk na murmushin shima ya shafi sumarsa.
"Zan zo gidanka gobe daga ofis."
"Dayake taka ce zata kawoka ko? Ai yanzun na ga kafarka."
Sukayi dariya sannan sukayi sallama ya shiga motar suka wuce.
*** *** ***
KADUNA
Munira tana zaune ta kurawa talabijin ido, saidai gaba daya hankalinta baya tare da kallon, Tasleem da Haris sai wasa da keke sukeyi ko kusa basu da wata matsala. Babban damuwarta bai wuce na auren da Deen ya sanarmata zaiyi ba da macen da sai su share awanni uku cikin dare suna waya, har yau batasan wacece ba saidai babu irin cin kashin da bata gani daga gurinsa tun soma soyayyarsa da yarinyar. Tunaninta ya katse sa'ilin da wayarta ta dauki k'ara. Ganin lambar yar uwarta Atika mai aure a Ringim yasa ta rage k'arar talabijin gami da dauka. Bayan sallama ko gaisawa Atika bata bari sunyi ba ta soma magana.
"Wai kuwa Munira kinsan abinda ke shirin samunki kuwa?"
Munira ta kara gyara zamanta kafin ta saki murmushi mai ciwo.
"Na sani Yaya, to ya zanyi? Aure kaddara ce ai, shi ya sani."
Atika ta saka salati.
"Ikon Allah, oh ni Fatima, ba dai kema sun shanyeki kamar yanda suka shanye Deenin ba? Wallahi na tausayawa rayuwarki Munira, cab!"
Munira ta ji gabanta na dukan tara-tara. Daman ya lafiyar giwa....
"Yaya wai me kikeson cewa? Ko kina da labarin wacce zai aura ne? Ni wallahi nan da kike gani ko sunanta bazan iya kawomiki ba don a Yanzu bai daukeni wata abar ba yanzu ballantana ya sanarmin."
"To wallahi Munira bacci bai ganmu ba, tashi tsaye ya dace muyi da addu'a, Deeni ba kowace zai aura ba face Dijar Baba Yahuza."
Jin zancen ta yi tamkar saukar aradu, wani salati ta saka da karfi kafin kuma ta yi wurgi da wayar ta zube anan ta hau kuka.
A guje yaranta suka yo kanta tare da Asiya mai tayata aiki.
"Lafiya Hajiya?"
Ta kasa barwa cikinta, ta sanarwa Asiya matsalar da ta ke ciki yanzun. Asiya ita kanta hankalinta ya tashi ainun, daman ta zargi hakan tsakanin Dija da Oga, ita take ganin yanayin muamalarsu a gidan. Ta yi ta bawa Munira hakuri, karshe dai ganin yaranta sun shiga damuwa ta mike ta dauki wayarta da ke faman ruri ta yi daki. Atika ce, nan ta shiga bata baki da nunamata addua kadai ce mafita
"Yaya ai ni na hakura da zama da Deen ma."
"Me kenan kikayi idan kinyi hakan Munira? Ashe ma ta ci galaba kenan, kada ki soma wannan bahagon tunanin."
Daga haka sukayi sallama. Munira ta cigaba da kuka har ta gode Allah, lallai DAN ADAM butulu ne, kayi mishi alheri ya sakamaka da sharri, ko a mafarki bata ta6a hangen haka ga Dija ba, bata ta6a kawowa zata ci amanarta har haka ba. Wannan rayuwa da me ta yi kama?
Ta jima cikin wannan hali har dawowar Deen daga wurin aiki bata iya komai ba. Daman ba wani nemanta ya ke yi ba yanzun, taso zuwa ta sameshi saidai kuma ta ga rashin alfanun hakan. Wannan yasa ta zuba ido ganin yanda lamuran zasu cigaba da kasancewa, mik'awa Allah lamarin shi yafi kamar dai yanda Yayarta ta ce.
*** *** ***
ABUJA
DAN ADAM
@RUFAIDA OMAR
64
ABUJA
Intisar sanye cikin riga doguwa 'yar kanti, ta ci kwalliyarta daidai misali ta fito daga kicin dauke da kwanukan abinci ta jera saman tebur inda Haidar da Faruk ke zaune. Ta gaida Faruk ya amsa shima ya gaisheta. Abin ma ya basu dariya.
"Ba dariya, matar yaya ta ke ai."
Haidar ya harareshi da wasa.
"Sai yanzu ka sani?"
Dariya kawai ya yi, Intisar dai bata saba irin wasan da Faruk ba don bai fiye sakarmusu ba, murmushi kawai ta danyi. Bayan ta gama(serving) dinsu ta bar wajen. Saida suka kammala ci sannan suka wuce masallaci bayan dawowarsu ne suka zauna a falon Haidar. Haidar ya dora kafa daya kan daya.
"Ina sauraronka."
Faruk ya mik'a mishi waya. Haidar ya kar6a yana kallo, ido waje kuma ya ke kallonsa.
"Wannan kamar Ummi yar aikin Mami."
Faruk cikin jin zafin yar aikin da ya kirata ya jinjina kai.
"Yes itace, a wurina ba 'yar aiki bace, budurwar da nake shirin aure ce, ita kuma nake son ta zama surukarku."
"Kasan abinda ka ke cewa kuwa?"
"Kwarai kuwa, Ummi nake so da aure."
Haidar ya dan yi jim kafin ya girgiza kai cikin sauyin yanayi,
"Bazai yiwu ba."
"Saboda ita ba mutum ba ce?"
Faruk ya jefamishi tambayar rai a 6ace.
Haidar ya dafa kafadarsa.
"Cool down mana, ba nufina wai wani abin daban ba, saidai matsayinku ya bambanta, wannan abu ba mai yiwuwa bane, ka chanja tunani Faruk, da kamar wuya su Daddy su yarjemaka."
Faruk ya murtuk'e fuska.
"Haka kake gani?"
Haidar da mamaki ya ke kallonsa.
"Kai baka gani?"
Ya girgiza kai gami da kwantar da kai jikin kujera.
"Ban ta6a hangen hakan ba, ban kuma sani ba ko don na riga na yi nisa a kaunarta ne yasa ban gano ba? Ni yanzu kai na zo ka ban shawarar wanda ya dace na soma tunkara tsakanin Hajiyarmu da Daddy?"
Haidar ya shafi goshinsa yana kara duban hoton Ummi sannan ya dubi Faruk.
"Ka sanarwa dukkansu alokaci guda. Ni a raayina, banga aibu a auren Ummi ba, na lura yarinya ce nutsastsiya sannan tana da kyawun hali da na fuska. Matsalar dai iyayenmu, idan sun amince shikenan, bansan raayin Babban Yaya da Dakta ba."
Faruk ya dan ta6e baki.
"Nifa zan zauna da ita. Shawara kawai daman na zo nema awajenka, ka kuma tayani adduar samun nasara akansu."
Haidar ya gyada kai yana dan murmushi.
"In sha Allahu, mai Ummi, zan tayaka. Amma wacece H din da ka zana?"
Faruk ya dan dara gami da kashe ido daya.
"Hasiya, real name dinta ne. Sunan mum dinta ta ci, amman ta rasu yanzu."
"Kai Nawan." Cewar Haidar gami da ba shi hannu suka cafke kamar wasu abokai.
"Wato komai nata ka sani? Duk ta yaya?"
Faruk ya gutsira mishi labarin Ummi, ya dora da fadin.
"Tausayinta ne ya soma rinjayar zuciyata har na soma jin sonta a raina."
Shi kansa Haidar ya tausayamata.
"Allah Sarki, rayuwa kenan, kowa da inda Allah Ya ajiyeshi, babu wanda yafi wani a wajenSa sai wanda yafi tsoronShi. Allah dai Ya datar da mu."
"Ameen broda. Ni bari na k'arasa, waya nakeson zuwa na siyo."
"Na wa kenan?"
Murmushi Faruk ya yi, Haidar ya dafa kafadarsa yana tayashi murmushin.
"Lallai na yarda da Dakta ke cewa irinku da bakwa soyayya idan kun tashi yi to zakuyi mai ban mamaki."
Abin ma sai ya bawa Faruk dariya, har wajen mota ya rakashi sannan sukayi sallama da zummar duk yanda Faruk sukayi da iyayen zai sanarmishi.
Hajiya Babba ta ajiye wayarta a gefe bayan ta gama amsawa ta dubi Ikram wacce ke zaman jiranta ta kammala.
"Ina jinki."
Ikram ta yi gyaran murya ta soma magana.
"Hajiya daman akan Ihsan ne."
Cike da mamaki ta dubeta.
"Meyafaru da Ihsan din? Ko ta gaji da mu ne?"
"A'a, daman..." (Ta kwashe tun farkon sadda Ihsan ta soma son Faruk har zuwa jiya da ta shiryamishi party na taya murnar ranar haihuwa.
Hajiya Babba bayan gama sauraronta ta numfasa fuskarta dauke da damuwa.
"Tun ba yau ba nasan yarinyarnan tana son Sadauki, saidai banga alamun Sadauki yana sonta ba."
Ikram itama ta jinjina kai, tasan gaskiya ne.
"Amma Hajiya bakya ganin a haka ya aureta idan yaso son ya shiga a hankali?"
"Kina ganin zai yarda? Banason abinda za'a zo zumunci ya lalace, matukar akayi aure ba da son ran daya ba to shakka babu zai shafi zumuncinmu abinda bazan ta6a fatan naga ranarsa ba kenan."
Ikram ta yi mamakin abinda Hajiyarsu ta ce, duk da tasan gaskiya ne, amma ai ya dace ta duba alak'a. Ita shaida ce akan yanda Hajiya ke tsananin kaunar dannata, batasan 6acin ransa tun yana karami kamar yanda ta samu labari daga yayyunsu. Ta bude baki zatayi magana Hajiya ta dagamata hannu.
"Ya isa hakanan, sai naji ta bakinsa, banason yi mishi katsalanda a lamari irin haka. Musamman lamari irin wannan na aure."
Jiki a sanyaye Ikram ta mike zata fita daga dakin, ta dakatar da ita.
"Maganar ta tsaya iyaka nan, ban yarje miki sanarwa Ihsan ba."
Ikram da ta rasa bakin magana, kai kawai ta gyada sannan ta fice har lokacin mamakin Hajiyarsu bai saketa ba, ko babu komai naka ai naka ne, saidai batasan hukuncin da zata yanke ba.
Mintuna k'alilan da yin hakan, Faruk ya dawo gidan a gajiye, kai tsaye sashensa ya nufa ya yi wanka ya sanya doguwar jallabiya ruwan madara da wando kafin ya dauki wayar da ya siyowa Ummi na kamfanin HTC ya sanyata a chaji. A karshe ya nufi sashen Daddy.
Acan ya iske Hajiya, suka gaisa kafin su shiga hira da iyayennasa. Can Daddy ya dubeshi.
"Son shekarunka talatin a duniya, ya ci ace zuwa yanzu ka soma tunanin aure."
"Ai ina jin ya samu matar aure, bai kai da fad'amana wacece ba ko Sadaukina?"
Murmushi ya yi yana mai shafar sumar kansa.
"A ina take?" Fadin Daddy kenan yana mai gyara zamansa don yasan dagasken ne don dannasu koda wasa bai ta6a zancen kowace mace ba.
"Ba ta yi nisa da mu ba sosai Daddy."
Hajiya da Daddy suka dubi juna, kafin su dubeshi.
"Ko 'yar gidan Alhaji Hamza? (Makwafcinsu)"
Ya yamutsa fuska.
"A'a, asalima ita ba 'yar garin nan bace."
"Wacece kenan?" Hajiya ta tambaya.
Ya yi shiru can kuma ya sunkuyar da kai.
"Zan kawomuku ita ku ganta cikin satinnan In sha Allah."
Suka gyada kai lokaci guda.
"Allah Ya kaimu." Fadin Daddy. Faruk da Hajiya suka amsa da amin, ita kuwa Hajiya ta soma tunanin kodai Ihsan ce?
DAN ADAM
@RUFAIDA OMAR
64
Washegari Ummi ta kammala aikinta, tana shirin barin wajen Hajiya ta shigo, bayan ta gaisheta ta dakatar da ita da fad'in.
"Ina jin zuwa Asabar zaki koma fa, ba don naso hakan ba sai don Madina da ta takura da zama ba mai tayata wasu hidindimun, ta ce yanzu ba wata matsala. Zuwa gobe za'a kawomin wata."
Gaban Ummi ya fad'i, jikinta ya yi sanyi matuk'a. Shikenan ta kusa rabuwa da ganin sanyin idanunta. A fili ta k'irk'iro murmushi wanda ya yi kama da na yak'e.
"To Hajiya, Allah Ya kaimu."
"Amin."
Daga haka ta bar wajen da saurinta, tana zuwa (garden) ta zauna a kujerar da ta saba zaman wanki, ta ajiye bokitin mai dauke da tsummokarai, shiru ta yi tana tunani kafin ta daga kanta tana duban barandar dakin Faruk, shikenan ta kusa daina sakashi a ido koyaushe? Hawaye suka zubomata, ta jima tana shararsu kafin ta daurewa zuciyarta ta cigaba da aikinta. A ranar haka ta wuni jiki babu kwari, daidai da Binta ta lura da hakan, tambayar duniya ta yi mata saidai amsar daya ce.
"Babu komai."
Koda dare ya yi, ta taimakawa Binta da shirya tebur har lokacin bata da wani kuzari, abincin ma kasa ci ta yi sosai. Binta sai kai loma take yi, can ta dubeta.
"Wai menene matsalarki ne?"
Ta numfasa.
"Na fadamaki babu komai, kaina ke ciwo."
Daga haka ta dan ja guntun tsaki ta mike.
"Ni na k'oshi ma."
. Binta na kallonta ta wanke hannu ta bar kicin din zuwa daki.
"Um, ai shikenan idan ta yi wari ma ji."
Daga haka ta cigaba da cin tuwonta. Ummi na tafe a sanyaye, wasa takeyi da jelar dankwalinta, yayinda ta fad'a duniyar tunani, ko kadan bata san inda take jefa kafarta ba, tasan dai hanyar dakinsu ta nufa. Babban damuwarta bai wuce Faruk ba, da kuma irin yanda take tunanin ko aurensu mai yiwuwa ne ko kuwa dai kawai iyakar soyayyar ce?
Bata ankara ba ta ji ta yi karo da mutum har goshinta na ta6a kirjinsa, ta yi saurin ja baya a tsorace, sai kuma ta yi ido hud'u da hasken rayuwarta. Wani hadadden murmushi na gefen kumatu ya sakarmata. Sanye yake da riga marar hannu mai hula da wando(3quarter).
Ta sauke idanunta kasa sannan ta russuna cikin rawar murya ta gaisheshi ya amsa sannan ya dubeta.
"Zo, ke na fito nema daman, na lek'a daki ban ganki ba."
'Gwara da Allah Yasa ka ganni a hanya.' Ta ayyana a zuciyarta.
Ya soma tafiya zuwa samansa.
"Biyoni."
Ta yi sakato tana dubansa. Har ya taka matattakala uku, ya juyo yana dubanta. Tana tsaye cak, ya dan yi jim yana karemata kallo, ita dinma shi ta ke kallo a sace, can kuma sai ta daga kafafunta da sukayi mata nauyi ta soma bin bayansa. Ganin haka ya murmusa ya cigaba da tafiya tana biye da shi tana waige, cikin sa'a Binta ta zo wucewa da sauri ta sauka ta nufeta.
"Ina zuwa don Allah, Yaya Faruk ke kirana, ki rufamin asiri."
Ta yi maganar cikin rad'a, Binta ta gyada kai tana dariya ciki-ciki don wannan soyayya tasu burgeta take yi, daga haka Ummi ta juya. Tuni gogan ya shige, a falo ta iske baya nan, tun da take bata ta6a yiwa sashensa kallon tsanaki ba, ko sadda Sa'a ta yaudareta ta kawota wajen KB, sam ba'a cikin nutsuwa ta ke ba. Falon adon fari da bulu ne, ya tsaru iya tsaruwa. Anan kasan (tiles) ta durk'ushe kamar yanda kowace yar aiki ta saba a gaban masu gida. A haka ya fito rike da kan waya da kwalinsa ya iso ya zauna saman kujera. Da hannu ya yi mata nuni da gefensa.
"Dawo nan Malama, saikace ba dakinki ba?"
Ta saci kallonsa kawai ta dan yi murmushi kafin ta mike cikin tausayawa rayuwarsu, shikenan sun kusa yin nisa da juna duk da hausawa kance garin masoyi ba ya nisa. A kasa ta zauna saman kafet, shima ya zamo ya zauna a k'asan ta dubeshi saidai babu abinda ta ce.
"Kamar kina cikin damuwa Ummina, sanardani abinda ya faru."
Mamaki ya kamata yanda har ya fahimci yanayinta. Ta girgiza kai.
"Bakomai."
Ba don ya yarda ba ya gyada kai sannan ya mik'amata wayar.
"Rik'e."
Ta bude tafin hannu ya dora mata a kai.
"Naki ne."
Ga mamaki ta dubeshi.
"Ai..ai ni ban iya amfani da waya ba."
Ya gyada kai da murmushi saman fuskarsa.
"Nasan da hakan shiyasa na kiraki don koyamiki."
Ji ta yi ranta ya yi wani mugun sanyi, saidai fa haduwar wayar ya tsoratata, bata ta6a ganin irinta ba.
Jin kamshin turarensa ta yi daf da ita, hakan yasa ta dagowa a razane ta dubeshi, ya matso gefenta hankalinsa naga wayar, ya kar6a daga hannunta ya soma nunamata da yacce zata cire (pattern) wanda ya sakamata saboda tsaro. Sannan ya shiga ya soma da gwada mata budo sak'onni, da amsa waya, har gwada kiranta ya yi ta ga sunan "Hubbyna." Ya fito, bata san dai yanda zata fadi sunan a baki ba. Amma tasan wani abun ya ke nufi na soyayya.
Sun dauki kusan mintuna fiye da talatin a haka har saida ya tabbatar ta iya yanda yake so, har (whatsapp) saida ya nunamata yanda zata amsa sak'onshi da mayarmishi da amsa, lambarsa kadai ce a wayar