Showing 3001 words to 6000 words out of 158267 words
cikin da batasan iyaka zurfi da yanayinsa ba.
Amina ta kammala kwashe komai ta wanke na wankewa, tayi mamakin yanda bata nemi tayinta ba. Suka zauna suka ci tuwo da miya sukayi nak, a karshe suka sha ragowar romon kifi wanda duk an jagwalgwalashi da k'ayoyi, haka suka dan tsinci na tsinta suka zubda sauran.
Bayan sun kammala, Amina ta rufe kicin din bayan ta kashe fitila, ta rage fitilun falon sannan suka shige dakinsu suma.
"Bazasu dawo falon ba?" Cewar Ummi.
Ta gyada mata kai. "Ai kuma shikenan, acan babban falon Hajiya suka fi zama, matukar kinga sun shige, toh sai kuma wata safiyar, don daga nan kowa makwancinsa yake nufa."
Ummi ta jinjina kai kawai.
DAN ADAM
@Rufaida Omar
05
Bayan shigarsu Amina ta dubeta.
"Idan kika bi shawarwarin da zan baki, toh lallai zaki zauna da kowa lafiya a gidannan. Yanzu na lura kina tattare da gajiya, ki kwanta ki huta, gobe ma yi maganar idan Allah Ya kaimu da rai da lafiya. Kinji ko?"
Ta gyada kanta tana murmushi, haka kawai ta ji tana kaunar Amina.
"Toh Anti." Antin da ta kirata da shi ya sanyaya ranta sosai, itama ta ji tana kaunarta kamar yar uwarta ta jini. Tana mamakin uwar da ta haifi yarinya kyakkyawa har haka, ta juma iya barinta ta fito aikatau. Kodayake, rayuwa ce ke sanyawa wani lokacin, ba don rai yana so ba. Ita ta ta6a zaton zatayi wani aikatau? Ko a mafarki a'a.
Ta barwa Ummi katifa; ita kuwa tayi amfani da bargo ta shimfida a gefenta ta kwanta. Ummi na jin sadda take zuba ruwan addu'o'i, abin ya bata sha'awa. Daga nan bacci ya kwasheta batare da ta shirya ba.
■●♣♣♣♣♣▪▲♥♥♥★★★★★
Washegari dakyar ta iya mik'ewa saboda dad'in baccin da ta ji. Amina ta jima tana tashinta, har daga karshe ta hakura tayi sallah sannan ta k'ara dawowa ta tasheta. Sai lokacin ne kuma ta farka. Ummi harda su miyan bacci.
Bayan ta idar da sallah tana shirin komawa ta kwanta Amina ta dubeta tayi dariya kad'an.
"Lallai Ummi kinaso Hajiya ta bud'emiki wuta. Ai muddin yaranta zasu makaranta to bacci fa ya k'are mana. Sai an had'a musu shayi an dafawa Fahad indomi don kuwa kullum da shi yake tafiya. Sauran kuma wani sa'in shayin ma ba shansa sukeyi ba haka suke tafiya basu damu ba. Sannan akwai gyaran dakunan yara da Hajiya. Sauran ayyukan da ya shafi kicin da falo da tsakar gida, duk ba namu bane, yana cikin aikin Ramma, sai da daddare ne ma tattara falo da kicin yake dole a kanmu. A yanda nasani kenan yanzu, bansani ba ko kema haka zata d'oraki akai ko kuma zata chanja tsari."
Ummi dai tayi shiru kawai tana sauraronta. Suka fita falon. Amina ta kunna fitilu wanda ta tabbatar ita da ta kashe d'in, ita ta kunna don babu wanda zai fito. Adnan ko zai tafi masallaci, zagaye yakeyi ta k'ofar waje ta d'akinsa. Ummi 'yar mik'omin wannan da wancan ce, tana lura da abinda Amina keyi. Haka kuma tana biye da ita da fahimta.
Komai suka hada, Amina ta zuba Indomin a filas din Fahad na makaranta, ta had'a shayin sannan suka fito. A falon suka iskesu, kowannensu na shiri. Ihsan ta shirya Fahad tsaf cikin riga ruwan goro da bulun wando na makaranta. Itama ta shirya cikin riga fara da siket ruwan toka, sai farin hijabi da safa fara, ta saka bak'in takalmi. Shima Adnan irin kayan Ihsan ne saidai wando ne nashi dogo, da farar hula (Face cap) wanda aka buga tambarin makarantar daga gaba. Shima bak'in takalmin ne sai farar safa, wanda hakan ya kasance tsarin makarantar.
Ba karamin kyau da burge Ummi sukayi ba, gaba d'aya sai ta shagaltu a kallonsu tana murmushin inama itace ta samu wannan gatan na zuwa makaranta. Tana son karatu sosai saidai bata da mai mata gatan nan.
Adnan na kokarin zura (belt) na wando ya ankara da ita. Ya dubeta batare da ya cigaba da abinda yakeyi ba, bai kai ga magana ba, tayi sauri ta durkusa ta gaisheshi, ya amsa sannan ta juya ga Ihsan wacce take zura littafi cikin jakarta ta makaranta, itama gaisheta tayi. Ihsan ta amsa tana hura hanci cike da jin ita d'in ta isa ta kai. Adnan ya girgiza kai ya ja karamin tsaki. "Na gayamaki ki daina gaisheta ko? Kodayake don kanki zaki bari ai."
Ihsan ta turo baki. "Nidai wallahi broda kana ban kunya a gaban 'yan aiki. Kaga banason irin haka, wannan jawomin raini ne fa."
Harararta kawai yayi baice uffan ba. Ta dubi Amina. "Ki zubomin shayi."
Amina ta juya bayan ta ajiye na Fahad a gabansa da biredi da bota. Can sai gata ta fito da kofuna biyu a hannunta. Ta ajiyewa Ihsan d'aya, sai Adnan wanda take yace bazai sha ba. Ta ajiyewa Fahad filas d'in abincinsa sannan ta ja Ummi suka fad'a d'akin da Ihsan da Fahad ke kwana. Karamin daki ne sai gado mai hawa biyu na yara. Saman an saka zanin gado kalar ruwan hoda mai zanen (Barbie), na k'asan kuwa an saka bulun zanin gado mai zanen (spider-man). A gefe kuwa, kwabar kaya ne guda biyu, shima d'aya ruwan hoda da fari, dayan kuma bulu da fari. Sai kafet mai duka kaloli ukun da aka kawata tsakar dakin da shi, da kuma k'arami na takawa a daidai hanyar bandaki. Daga can kuwa, karamin madubi ne, sai kwaba da abu mafi yawa akansa, kayan kwalliyar Ihsan ne. Fanka ce kawai a d'akin, sai bada wadataccen iska take. Ba k'aramin burge Ummi dakin yayi ba. Ta saki baki tana kallo.
"Ummi ki dunga lura kina rike abubuwan da nakeyi fa, don kuwa gobe zai iya kasancewa ke d'aya zakiyi. Da zarar Hajiya Mama ta dawo zan tafi."
A sanyaye Ummi tayi magana. "Yaushe zasu dawo?"
Tana murmushinta na sabo ta amsa. "Hausa nayi miki, ni kaina bansan sadda zasu dawo ba amma na tabbatar ba zata kaisu da nisa ba tunda an koma makaranta, yara zasu je. Nufina yau idan ina nan gobe bana nan, kece zakiyi."
Ta jinjina kai. Tare sukayi aikin, har inda ake daukar sabon zanin gado idan na kai sunyi datti saida Amina ta nunamata. Suka fito, tuni yan makarantar sun tafi lokacin takwas ma ta wuce, saidai sam Hajiya bata lek'o ba. Saida suka shiga dakin Adnan nan ma suka gyarashi tas, shima madaidaicin daki ne, da katifa babba wacce bata da bukatar katakon gado. Komai na dakin adon fari da bulu ne, babu wani tarkace a dakin sosai. Amina ta barta da gyaran gado don taga yanda zatayi, sai kuma ta bata mamaki don tayi kokari ba laifi. Ta dan gyaggyara inda baiyi ba sannan Ummi ta share dakin, anan kam ko Amina ba zata nunamata iyawa ba. Bayan sun fito, shayin suka zuba suka sha da sauran biredin sannan suka maida komai kicin suka koma dakinsu. Suna daga kwance Amina ta soma magana.
"Zanso kafin na fad'amaki halayen mutanen da zakiyi zama tare dasu, na soma gayamaki tsarin gidansu don ya dace kisan da wadanda zaki zauna."
Ummi ta muskuta tana dubanta gaba daya ta tattara hankali da nutsuwarta ga Aminan. Ganin haka Amina ta soma.
DAN ADAM
@Rufaida Omar
(03)
"Assalamu Alaikum." Cewar Yaha alokacin da ta murd'a k'ofar falon ta sanya k'afa. Wata dattijuwa wacce ke zaune, wata budurwa mai kimanin shekaru sha shida. Tana zaune a k'asan lallausan kafet tana daddanna mata k'afa. Ta nutsu sosai, kamar kace arr! Ta arce.
Ummi dai kallonsu take, daga yanayin yanda ta ga Hajiyar na dubanta, ta sha jinin jikinta, da alama dai matar ba ta da mutunci don kuwa fuskarnan nata babu ko alamun fara'a.
"Ranki ya dad'e baya goya marayu, barkanki da hutawa."
Hajiya tayi wani murmushi, da alama ta ji dadin wannan kirari na Yaha. Ummi dai kallon ikon Allah take, yanayin shigarta da komai ma, sun isa shaidar tana cikin rayuwar daula. Wani kallo da Yaha ta watsa mata ne ya sanya ta ba shiri russunawa sosai gami da rankwafar da kanta ta gaisheta. Hajiyar bata ko amsa ba, saidai ta k'ura mata ido tana k'are mata kallo. Can kuma ta yamutse fuska ta rausaya kai gami da maida dubanta ga Yaha.
"Wannan ce?"
Yaha ta washe baki tana jinjina kai.
"Kwarai kuwa ranki ya dad'e uwar gida ran gida, itace, sunanta Hasiya amma Ummi ake kiranta."
Ummi dai sai zazzare ido take kamar shege a rabon gado, Hajiya Madina tayi murmushi, ko babu komai takan ji dadin wannan kirari da Yaha ke mata.
"Tayi sosai, na tabbatar, zata iya dukkan ayyukan da na na bata. Ince dai bata da son jiki?"
Yaha har lokacin bakinta ya k'i rufuwa don ji take kamar ta shid'e don dad'i domin kuwa ta sha kawowa Hajiya Madina yara, basu yi mata ba.
Ta janye k'afafunta, gami da kallon budurwar batare da tace uffan ba, ta mik'e ta wuce don ko Hajiya batayi magana ba, ta karanceta, wato dai ta basu guri.
Bayan komawarta ciki ne, Hajiya Madina ta dubi Yaha.
"Yahanasu, ina fatan kin shaida mata cewar banason wasa, ba kuma na son son jiki. Dukkan wasu ayyuka da na sanyata, inaso ta kammala su alokacin da ya kamata. Ba kuma na son k'azanta, ta kula sosai don kuwa naga yanayinta, da alama k'azamar ce."
Ummi ta sunkuyar da kai tana sosa gashin kanta wanda amosani ya bi ya takura mata, idan ma ance da kwarkwata lallai babu musu don bata da gatan da Saude zata wanke mata kai.
"Kiyi hakuri, na tabbatar ba zaki samu wannan matsalar ba. Sau daya aka gwada mata yanda zata gyara jikinta, na tabbatar babu wata matsala da zata biyo baya."
Hajiya Madina ta jinjina kai alokaci guda ta yamutse.
"Yauwa, don kinsan banason abinda wadancan shirmammun zasu samu damar zagina. Ko kusa banason wani mishkila ya fito daga d'akina."
Dariya Yaha tayi, ta gane Hajiya Madina tana nufin kishiyoyinta, Hajiya Rakiya da Hajiya Munira.
"Ai kin wuce nan Hajiyata, baya goya marayu. Kar kiji komai, yarinya ce mai kaifin basira. Zata bi dukkan umarninki batare da kin 6ata rai ba.
Kwarai, ta ji dadin kalaman Yaha. Daga nan ta mike da nufin zuwa gabatar da sallar la'asar, bayan ta umarci budurwar nan da ta ambata da Amina, da ta nunawa Ummi wajen kwanansu.
Amina a gaggauce ta bi umarnin Hajiya. Suka wuce tarr har Yaha wacce zata d'auro alwalar sallah itama. Ummi ta dubi d'akin, katifa d'aya ce sai filo, a gefe kuma jakar kaya ne. Sai kofa daya wacce ta ga Yaha ta shiga ciki, wannan ya tabbatarwa Ummi, bandaki ne. An malale dakin da ledar tsakar daki. Fentin dakin mai wani kyalkyali ne, fari da ruwan hoda, saidai babu komai na more rayuwa ciki.
Acan kusa da jakar kayanta, ta ajiyewa Ummi nata da murmushi saman fuskarta ta dubi Ummi, haka kawai ta tsinci kanta da murna sosai, ko babu komai ta samu abokiyar hira.
"Nan zaki dunga kwana."
Ummi ta mayarmata da martanin murmushin, saidai har lokacin bata saki jiki ba don kuwa ko k'arar k'ofa ta ji sai ta firgita. Ta riga da ta saba da hakan.
Yaba ta fito ta shimfida dardumar dakin ta tayar da sallah. Itama Ummi ta shiga, saidai tayi turus don kuwa bata saba da bandakin yan gayu har haka ba.
"Bari na nuna maki yanda zakiyi."
Cewar Amina daga bayanta, wannan yasa Ummi matsawa, ta shigo.
Nan ta gwada mata komai, Ummi tayi godiya cikin muryarta sassanya sannan ta shiga ta d'an kara k'ofar don ta tsorata, bata so ta rufe ta kasa bud'e kanta.
Bayan tayi alwala, irin yanda ta saba ganin mutane nayi don kuwa ko alfarmar zuwa makarantar islamiyya, Ummi bata samu ba. Tayi yanda ta iya sannan ta fito ta tayar da sallar. Tasan ana yin sallah raka'a hud'u a lokacin nan hakan yasa ta soma babu wani karatun kirki don babu abinda ta iya. Ta idar ta zauna tana motsa baki sannan ta yi jugum tana kalle-kalle.
Bayan Yaha ta kammala suka fita, Ramma ta basu abinci, nan suka ci sannan Hajiya ta sallami Yaha ta tafi da abin arziki
DAN ADAM
06
Maigidan, sunansa Alhaji Muhammad Modibbo. Shi d'an asalin garin Adamawa ne, bafulatani ne. Hajiya Madina 'yar uwarsa ce, saidai ita mahaifinta anan Kano ya rayu, anan ya tara zuri"arsa. Soyayya ta kullu tsakaninsu har ta kaisu ga aure lokacin shi Alhaji Muhammaf ya dawo Kano da karatu ya kuma kama aiki anan. Yana da mata biyu bayan ita, Hajiya Binta itace wacce kika gani rannan, sannan amaryarsa Hajiya Lubna, ita 'yar Maiduguri ce, yanzun ma da baki ganta ba, taje biki can Maiduguri da yaranta su hud'u gaba d'aya.
Hajiya Madina tana da yara takwas kamar yanda na fadamaki, ita kuwa Hajiya Binta yaranta shida. Iklima itace babbar budurwar 'yarta sannan Hanif, Sadiya, Nafisa, Usman da Jabir.
Ita kuwa Hajiya Lubna, yaranta biyun farko 'yan biyu ne mace da namiji. Hassan da Hussaina, sai Adam da Hajara.
Bar ganin gidannan kamar ba shi da girma Ummi, sai kin shiga can 6angaren zaki k'ara tabbatar da girmansa. Sashe hud'u ne har na Alhajin.
Saidai duk haduwar sashen matan bai kai na maigidan ba, da girma da komai.
Hajiya Madina duk ta fisu fada a wajensa, ko don tana ganin ita din 'yar uwarsa ce kuma tana da daurin gindi wajen mahaifiyarsa Gwaggo ne? Bani dai da masaniya. Amma tabbas Gwaggo bataso ko kusa Hajiya ta kai k'ararsa wai ya 6ata ranta, yanzun nan zata bud'emishi wuta. Shiyasa daga Hajiya Binta har Hajiya Lubna, basu kaunar zuwan Gwaggo Kano, kawai saboda bambancin da take nunawa tsakaninsu da Hajiya Madina. Hakanan tafi zuzuta kaunar 'ya'yan Hajiya Madina har yakai ma bata iya 6oyewa.
Bada son ranta akayiwa Hajiya Madina kishiyoyi ba, saidai kawai don Hajiya Madina ta nunamata tafison kwanciyar hankalin mijinta akan tashin hankali da damuwarsa.
Gaskiya Ummi a wani 6angaren, Hajiya Madina tana da mutunci duk kuwa da cewar bata kama k'afar Hajiya Mama ba. Hajiya Mama ciki d'aya suka fito, saidai ita bata da raina 'yan aiki kuma yaranta sunsan girman ★DAN ADAM★ basu rainashi ko yaya ne. Toh yanda Hajiya Mama take, hakanan itama babbar yayarsu, Hajiya Fatima take. Su uku daman cif a wajen babansu, daga su bai kara haihuwar wasu ba kuma matarsa daya, Baba Ummahani.
Ita a Abuja take zaune. Tana da yaranta hudu samari manya, sai yan mata biyu. Ta aurar da yaranta maxa biyu na farko, matan da ragowar mazan biyu sune dai basuyi aure ba. Mijinta tsohon soja ne kafin daga baya yayi ritaya.
Amina ta d'an tsagaita sannan ta d'ora tana duban Ummi wacce gaba daya kacokam ta maida hankali gareta tana sauraro.
"Hajiya tana da saukin hali idan kika zama mai bin umarninta kan lokaci, sannan tafiso kafin tayi korafi akan bakiyi aikin da kika san kina yi ba toh ki kammala shi. Ko kusa bata son kazanta, hakanan bataso kice zaki wulakanta abinda ta haifa. Batason kuma shigen d'akunan abokan zamanta, idan kika kiyaye bakinki daga daukar magana ki kai wani dakin toh fa zaku d'asa da ita. Ba ruwanki da shishshigi a lamuranta matukar ba ita ta so ki tanka ba. Ki kiyaye kawo mata gulma, nan ma zaku 6ata da ita. Sannan ko wani abu marar dacewa kikaga ta yi, bataso ki tanka mata, nan kuwa zaku 6ata. Batason ta kamaki da cin amanarta.
Yaranta suna da saukin hali Ummi, matukar kika kama kanki ba zasu rainaki ba. Ihsan ce ma mai matsalar, ita kuma kiyi kokarin fita harkarta. Idan dai ta sanyaki aiki kada ki k'i, kiyi hakuri kiyishi hakan saboda itace ma musabbabin da yan aiki basujin dadin zaman gidan.
A duniyar nan, kawai dai ki tsare abinda za'a ci mutuncinki ko yayane, kedai ki tsaya matsayinki baruwanki da cusa kai kinji ko?"
Ummi ta danyi murmushi alokaci guda hawaye suka zubomata ta sharesu, wai yau itace da samun mai bata shawara a lamarin rayuwa? Itace ta samu wannan gatan har haka? Wani irin kaunar Amina ya k'aru a zuciyarta.
Amina da mamaki ta mike zaune.
"Ummi kukan kuma na menene?"
Ummi ta girgiza kai.
"Bakomai."
Amina ta ji wani tausayi ya dabaibayeta. Tasan akwai wata matsala a rayuwar Ummi, tafi kuma tunanin bata da iyaye. Ta numfasa, batason ta matsa mata da tambaya, ta tabbatar wataran don kanta zata gayamata tarihinta.
"Komai yayi zafi maganinsa Allah Ummi. Ki bar damun kanki da lamuran rayuwa har haka kinji ko? Ki rik'i addu'a da karatun Alkur'ani da sallar dare. In sha Allah komai zakiga ya wuce."
Ummi da fuskar tausayi ta dubeta.
"Nifa bansan komai na Addini ba wallahi. Kawai dai ina yin sallah idan naga lokaci yayi mutane sunayi."
Mamaki karara ya bayyana saman fuskar Amina, batasan ya akayi ta jefomata tambaya ba.
"Wai Ummi, iyayenki basu raye ne? Shekarunki nawa yanzu?"
Ummi tayi k'as da kanta ta soma hawaye.
"Mahaifiyata ta rasu tun ina jaririya, babana yana raye. A hannun matarsa na taso."
Kwallah ta cika idanun Amina, ta gano bakin zaren.
"Idan ba damuwa ki sanarmin tarihinki mana."
Tiryan-tiryan ta sanarmata da irin rayuwar kuncin da ta rayu ciki. Cikin muryar kuka tace.
"Kalmar da ta kasa ficemin a rai bai wuce da babana yace wai ko birnin sin ne na tafi ba shi ba damuwarsa bace. Babana baya sona yanda yakeson kanwata Mariya."
Kuka sosai takeyi, itama Amina tana tayata. Wani kaunar Ummi ya k'aru a ranta, ji takeyi tamkar kanwarta ce ta jini. Dakyar Amina ta rarrasheta tayi shiru sannan ta dubeta da kulawa.
"Karki damu Ummi, ki cigaba da hakuri sa mik'awa Allah lamuranki. Komai kika gani, daga gareshi ne. Watarana zaki ga komai kamar ba'ayi ba, nan gaba zakiji dadi a rayuwa in sha Allah. Kada kiyi bakinciki da zuwanki gidan Hajiya, na tabbatar ko a kwana d'ayan nan da kikayi, kinga chanjin