Showing 15001 words to 18000 words out of 158267 words

Chapter 6 - Dan Adam Book 1 Complete Hausa Novel

ko kusa kada yayi tunanin zai iya da Babban Goro, duk cikinsu babu sa'an aurenki, don haka ki maida maitarki, kurwar kaf dinsu, ta fi karfinki."
   Daga wannan ta sanya kai ta fita tana kwalawa Ramma kira. Iyakar radadi da bacin rai, Ummi ta ji shi a ranta, batasan sadda idanunta suka ciko da kwalla ba, wannan cin zarafi har ina? Kai tsaye an yankemata mummunan hukuncin da ko a mafarki bata yi zaton koda mak'iyinta zai shaideta da aikatawa ba, toh daman ina ita ina ire-iren wadannan mazan? Yaudarar kai ne, koda ta auna cewa Ihsan batasan irin zargin da ya kamata tayi mata  ba, yasa ta yin murmushi mai ciwo, da alama Ihsan bata gama sanin bambancin matsayinta da su ba, tabbas ta cucesu tunda har ta had'asu da ita, watakil da zasu ji da sai sun had'a da kai mata bugu don haushin abinda tayi musu. Ta share batun gami da goge fuskarta sannan ta juya ta koma don ta tabbatar a yanzun Mami ta shiga sallah. Dakinta ta koma itama ta tayar da nata sallar, saida ta idar ta kaiwa Allah kukanta akan Ya ji6anci lamuranta. Bata da kowa sai Shi, Shi ne gatanta. Yayi rahma ga Mahaifiyarta. Haka tayita kwararo addu'o'i har tana fidda ruwan hawaye kafin kuma ta shafa. Bata kai ga mikewa daga wurin ba ta ji Fahad na kwala mata kira adaidai sadda ya murd'a kofar dakin nata.
  "Ummi! Kizo inji Mami."
  Ta mike batare da ta cire hijabin ba ta bi bayansa.
    
DAN ADAM

@RUFAIDA OMAR

15


Anan ta iskesu tsaitsaye ana hira banda babban yaya wato Yaya Usman da ke zaune cikin mota tare da Faruk wanda gaba d'aya ya matsu su koma gida don jinsa yake a gajiye.
Ihsan ta bita da kallon harara, hakan yasa ta kauda kanta.
"Kanki ake ji." Ta fad'a a ranta. Ta dubi wata doguwar budurwa siririya bak'a, bata san itace Ikram ba ko kuma Baraka, don sunayensu kawai Amina ta sanarmata ba ta nunamata su ba a fuska.
"Ga wannan a ina zan ajiye?"
Ta dubeta, sannan ta nunamata motar da yatsa batare da dogon bayani ba.
"Kinga, saka anan."
Ta dubi Yaya Haidar dake nunamata boot wanda yasa hannu ya bud'e. Ta karasa ta ajiye gami da fad'in.
"Allah Ya tsare hanya." Daga haka ta juya ta bar wajen.

"Adnan ina mutuniyata ne? Ban ganta ba."
Adnan ya yamutse fuska yana duban farar budurwar siririya da tayi mishi magana, wato Baraka.
"Wa kenan?" Ya tambaya cikin basarwa kamar bai fahimci ko wa ta ke nufi ba da gaske.
"Abokiyar fad'arka mana, your lil sis."
Ya harareta, ya gane Iklima take magana akai.

"Ai kinsan hanyar gidansu ko? Sai kije."
Baraka tayi dariya.
"Kwarai ma kuwa wallahi, idan ma kana ganin kamar bazan iya zuwa ba zaka sha mamaki. Kada fa ka manta k'awata ce, mun riga mun saba da uta adalilin (whatsapp group) da muke ciki tare. Zo muje Ihsan ki rakani."

Ba musu ta ja Ihsan suka tafi. Hajiya Binta suka soma gani a falo tare da Usman, Jabir da Hanif, gaba daya kallo ya daukemusu hankali. Sallamarsu ce ta sanyasu maido hankali garesu. Ta soma shan kamshi yayinda ta amsa ciki-ciki.
Suka karasa suka gaisheta. Saida ta k'arewa suturar dake jikin Baraka kallo sannan ta numfasa, ta riga tasani iyalan Hajiya Fatima ba su ta6a zama a baya wajen suturu da sauran kayan more rayuwar duniya.
"Baraka ko?"
Baraka fuska a sake ta amsa.
"Eh ni ce Umma."
"Sannu, yanzu kuka zo?"
"Za mu tafi ne dai, ina Iklima?"
Hajiya Binta ta nunamusu hanya.
"Ku shiga tana d'akinta."
Suka shige ta bi bayansu da kallo cike da jin wani tuk'uk'i a ranta, dole Madina ta dunga yi musu wani gani-gani kasancewar daga ita har Lubna, ba wasu 'ya'yan masu kudin azo a gani bane, a komai dangin Hajiya Madina sun k'ere musu, yana daga dalilin da yasa suke matukar kishinta. A gefe kuma tana tak'ama da cewar ita din fa jinin Alhajinsu ce, shi kansa Alhajin koda hira akeyi da ya shafi danginsu, sau da yawa yakan yabawa bajintar mahaifin Madina, da irin yanda ya iya rik'e iyali da sauransu. Wannan yasa ko kad'an acikinsu babu mai kaunar suyi wata doguwar hirar da ta shafi dangin Alhaji Modibbo. Babban burinta yanzu, bai wuce yaranta su kasance wasu shahararru ba a fannin kudi, ta ci buri akan Iklima wannan yasa ta haneta abota da dukkan wani jinin talaka, dukkan abokan Iklima 'ya'yan wasu ne. Koyaushe tana hanyar biki da party. Babu laifi takan samu samarin masu ji da kudi saidai da yawansu ba da aure suke sonta ba, saidai wata manufarsu ta daban. Idanunta sunyi masifar budewa wanda hakan nai ta6a damun Hajiya Binta ba, acewarta, idan bata kasance wayayyiyar ba, a ina har zata samarwa kanta miji dan zamani.
Acan kuwa su Baraka suna shiga Iklima ta rungume Baraka tana ihun murna don sosai kawarta ce, kusan halinsu yazo d'aya na son gayu da samari.
"Shegiyar gari, daman kinzo shine ko ki nemeni?"
Baraka tana dariya tace "Afuwan tawan, kinsan tun dazu na so shigowa Allah baiyiba, ina su Yaks?"
Fad'in haka yasa ita da Ikliman suka tuntsire da dariya ita dai Ihsan ta zama 'yar kallo, ko ita da suke tare da Ikliman basu hira mai tsayi har haka, lallai ba karamin sabo Baraka da Iklima sukayi ba.
"Yana inda yake, kwana biyu munyi fad'a ma, zan baki labari kedai. Ina mijina?"
Cewar Iklima tana mai kashe mata ido d'aya, Baraka ta ja guntun tsaki tana dariya. Ta fahimci Faruk take nufi, tun daga sau daya da ta ga ta dora hotonsa a dp lokacin shi kuwa yana gani ya shigo har dakinsu ya hauta da fad'a har yakai ga mangarinta, yace tayi gaggawar goge dukkan hotunansa a wayarta. Daga ranar bata kara dora hotonsa. Daga ranar Iklima ta makale akan lallai ita fa sai ta hadata da shi, hakuri kawai ta bata ta gwadamata Faruk sam ba irin nasu bane don ba shi da wannan rawar kan akan mata.
"Kedai ki kama kanki baruwana na gayamaki."
Cewar Baraka. Iklima tayi dariya.
"Ina ruwanki? Bazan kama ba sai randa kika bani lambarsa."
Ihsan duk bata fahimci komai ba saida ta ji Baraka na fadin.
"Kizo muje da kanki ki tambayeshi, ga shi can a waje." Ai sai Iklima ta zaro ido.
"Dagaske?"
"Wallahi." Cewar Baraka cikin dariya, tuni ta ja dankwalinta ta rufe kanta, daman riga 'yar kanti ce a jikinta sai siket ruwan madara na leshi da dankwalinsa.
"Muje wallahi na gaisheshi na tambaya."
Suka kamo hanya Baraka cikin dariya ta na fad'in.
"Kamar gaske, bakisan wanene Yaya Faruk ba wallahi."
Gaban Ihsan ya fad'i, me Baraka ke nufi? Wato Iklima batun Faruk take? Aikuwa ba zata sa6u ba, saidai su yi BIYU BABU. Muddin ita bata samu soyayyarsa ba, to babu wata ta jininta da zata samu, ta gwammace ya je ya auri bare akan tana ji tana gani ya auri wata jininsu. A ganinta, itama fa tana da aji, ba zai yiwu ta zauna wani namiji na sha mata kamshi ba, ta tsani dukkan wani namiji mai ji da kansa, baruwanta da kyansa, idan kyau ne, akwai wadanda suka fishi da suka nuna suna sonta tana sha musu kamshi.
Anan kofar shiga sashen Alhaji Modibbo suka ga takalman Mami da Hajiya Babba, wannan ya tabbatar musu suna ciki. Da rawar jiki Iklima take tafiya, Allah-Allah takeyi ta had'u da Faruk ko don shima yasan da zamanta. Ta tabbatar ba kowane namiji ne zai iya dauke idanu daga kanta ba. Haka suka karasa bakin motar, alokacin Haidar da Adnan ne kawai tsaye sai Ikram wacce ta jingina jikin mota tana danne-dannen waya. Iklima suka gaisa da Haidar, Adnan sai dauke kai yakeyi. Itama bata bi ta kansa ba ta dan lek'a motar, kasancewar akwai wadatar haske a farfajiyar gidan hakan yasa ta hangi Faruk dake zaune a mazaunin direba ya d'ora tafin kafarsa akan kujera, kansa jingine jikin kujerar yayinda kunnensa ya sanya (Earpiece) yana shan sauti. Idanunsa a lumshe. Wani wawan ajiyar zuciyar Iklima ta saki, ta ko'ina Faruk ya had'u. Ta gaida su Yaya Usman suka amsa mata fuska a sake kafin tayi ta wajen Faruk tana gaisheshi. Ko kusa baisan ma tana yi ba saida Usman ya cire mishi kunne d'aya na (Earpiece) sannan ya juyo da rinannun idanunsa, da alamu ma bacci ya soma.
"Au bacci kakeyi ma? Ana gaisheka."
"Ina wuni." Ta k'ara fad'a. Ya juyo ya zubamata idanu, ai ji tayi kamar ta saki fitsari tsabar yanda kallon ya kad'ata, duk inda take zaton Faruk a kyau da komai, ya wuce nan. Kansa kawai ya gyad'a mata sannan ya dauke kai. Ji tayi ta kasa koda kwakkwarar magana, to ta ina ma zata iya furta mishi wani abun har ya kai ga tambayar lambarsa? Ba zata iya ba, hakan yasa ta koma ga su Baraka wadanda ke yi mata dariya har Ihsan wacce ba karamin dadi abin ya yi mata ba.
"Wace ne?"
Faruk ya tambaya ba tare da ya bud'e idanunsa ba.
"Iklima, step-sister dinmu." Cewar Adnan. Ya yamutse fuska.
"Har yanzu Hajiya bata fito ba? Wallahi na soma bacci."
DAN ADAM
@RUFAIDA OMAR

16
Kafin waninsu yayi magana, sai ga Mami da Hajiya tafe suna hira, Yaya Ridwan ne yayi magana.
"Ai idan iyayenmu mata suka had'u wallahi har mamaki suke ban, ko kusa basu kaunar rabuwa da juna."
Faruk da Usman suka d'an dara, kamar ba zasu karaso ba haka suke tafe suna hira. Ganin dai da gaske basu da niyyar tahowa ya sanya Faruk dannan hon, wannan ya maido hankalinsu wajensu. Ya koma can gefen mazaunin direba yana fad'in.
"I can't drive wallahi, bacci ya soma kama idona."
Haidar ya bude mazaunin direba ya shiga yana fad'in.
"Ai nayi mamaki ma da ka iya kaiwa war haka, kodayake na dole ne. Mutumin da wani sa'in takwas ma yayi bacci."
Murmushi kawai Faruk yayi ya kara lumshe idanunsa sannan ya budesu. Hajiya Babba ta karaso ta shiga, ganin haka yasa yanmatan sallama da juna, bayan shigarsu Iklima ta zubawa Faruk ido kamar ta had'iyeshi, tsaf ya lura da kallon da take jifansa da shi, wannan yasa a sannu ya zuge gilas wanda ya kasance mai duhu, shi ya yi mata katanga daga dubansa. Ta sauke ajiyar zuciya, ta juya ta kama hanyar ciki bayan ta gaishe da Hajiya Babba, sun kara sallama da Baraka.


"Maganar banza ce kikeyi, wacce ba zata ta6a kasantuwa ba matukar Binta na raye wallahi. Da kinsan yanda nake kishin Madina da danginta, da baki soma tunanin son Faruk ba Iklima."
Cewar Hajiya Binta tana faman hura hanci fuska a murtuke kamar bata ta6a bud'a hakoranta ba don dariya. Iklima ta tur6une fuska tana kunkuni ta mik'e ta barta tana faman bud'e wuta.
"Eh lallai, gwara tun wuri na tashi tsaye kafin kema ki rikita lamurana, shawarar Luba zan bi."
Ta karashe tana daukar wayarta, H
Luba ta dannawa kira sannan ta mike ta fad'a d'aki. Suka gama kulla-kullarsu akan yanda Alhaji zai shigo hannunta sai yanda tayi da shi, da kuma irin nau'ikan muguntar da za'a yiwa Madina a lalata rayuwar 'ya'yanta, itama a dusasar da tauraronta dake haskawa a idanun Maigidan da surukarsu. Haka suka ajiye wayar cike da jin wani nishad'i ko babu komai itama tana dab da samun matsayi babba.

☆☆☆

Haka rayuwa tayita tafiyarwa Ummi, yau dadi gobe babu dadi. Yawanci matsalarta bai wuce Ihsan ba don Mami matukar zata yi abinda ta sanyata to fa babu ruwanta da harkarta. A wannan halin ne wata ranar Asabar ta tashi da ciwon mara marar misali, tun tana dauriya har ta kasa, ko tashi ta kasa yi balle ta kai ga aikace-aikacenta. A wannan hali Ramma tayi sallama ta shigo bisa umarnin Mami da ta dubo ko lafiya bata fito ba har ga Ramma ta rigata zuwa.
Ganinta ba lafiya yasa ta fita ta sanarwa Mami. Kafin su dawo ta soma jin ta da lema, saida Ramma ta d'agata ne suka fahimci abinda ke faruwa. Ramma ta taimaka mata bayan ta kar6o (Always) wajen Mami, ta gwada mata yanda zatayi, saida ta kimtsa sannan suka rankaya kemis da Ramma.
Tun daga wannan ranar Ummi ta fahimci girma ya hau ta, Ramma ta k'ara jaddada mata hakkokin da suke akanta yanzun wadanda ta riga ta sani don a makaranta duk ana koyardasu.
Mami bata yarda da kazantar kunzugu ba, hakan yasa ta bata (pads) cikin na Ihsan wacce ta rigata somawa tuni. Saida tayi kwanaki hud'u sannan tayi wankan tsarki. Daga wannan lokacin ta k'ara kame kanta ta zama mai kula sosai da takatsantsan musamman ma ga sallolinta.
☆☆☆

A KWANA A TASHI...!
DAN ADAM
@RUFAIDA OMAR

17
A kwana a tashi ba wuya a wajen Ubangiji, har ga shi ana sauran kwanaki hud'u bikin Haidar da Intisar. Wannan ya janyo Ihsan komawa gidan Hajiya Mama don taya 'yar uwarta shirye-shirye. Alokacin tuni su Hajiya Babba sun iso Kano don anan za'a yi sha'anin bikin kasancewar mijinta, Gen. Ahmad Danzaki, uba ga su Usman, shima dan asalin Kano ne.
Mami ta yiwa Ramma da Ummi kyautar atamfa turmi d'aya na anko. Ramma ta had'a ta kai musu dinki wanda ya zauna d'as a jikinsu. Ana washegari za'a soma biki, suka ziyarci Hajiya Mama wacce ke fama da shirye-shirye. Amina ta ji dadi kwarai na ganin Ummi. Anan gidan Mami ta barta tare da Fahad suka fita zuwa babban shagon siyar da kayayyakin kicin, hakanan su Ihsan suma sun fita wajen gyaran Amarya.
Ummi ta dubi hannun Amina da suka sha kunshi.
"Anti na kasa dauke ido daga kunshin nan naki wallahi, yayimin kyau sosai."
Amina fuska a sake ta amsa mata sadda take gyara zaman tsintsiyar hannunta wanda take shirin yin shara.
"Idan kina so muje na rakaki sai na dawo, wallahi yarinyar ta iya kunshi, baki ganta ba kuma ba wata babba ba."
Ummi ta zaro ido, ga koshi ga kwanan yunwa.
"A'a, banason fad'an Mami, idan suka dawo basu tarar da ni ba ai nasan ba zata kyaleni ba."
Amina ta dara kadan. "Kedai akwai matsoraciya, ni na fadamaki har babban gida sai sun shiga tunda Gwaggo ta zo (surukar Mami kuma yar uwar mahaifinta). Na tabbatar su da mu gansu a gidan nan sai Magriba. Bari nayi shara na rakaki, keda kike fara tas ma ai sai ya fi yi miki kyau a kaina."
Ummi tayi tsuru da ido bata kara cewa komai ba, tana kallo Amina ta kammala share tsakar falon, ta wanko hannunta sannan ta yafa gyale.
"Muje."
Ummi ta girgiza kai.
"Ai baki isa ba, tunda har kina so wallahi sai kinyi, saidai wani ikon Allahn ya hana. Idan kudin kike ji, kada wannan ya dameki, zan biya."
Dakyar ta shawo kanta ta amince suka tafi. Babu nisa sosai, saida Amina ta ga an soma yi sannan ta taho bayan ta rok'i alfarmar mai kunshin akan ta sanya a raka ta gida. Ba wani mai yawa akayi mata ba, saidai duk kushen mai kushe bazai kalli hannu da kafafun Ummi ba ya ce baiyi kyau ba. Bak'in lalle ne, hakan yasa babu jimawa sosai ya bushe adalilin iskar dake kad'awa. Ta wanke a gurguje, alokacin anyi sallar la'asar, gaba daya fargabanta bai wuce na kada ya zamana su Mami sun dawo ba. Saidai cikin ikon Allah daga su Mamin har su Intisar babu wanda ya dawo. Amina ta rude ganin yanda Ummi tayi kyau.
"Kai amman lallen nan yayi miki kyau sosai masha Allah, sauranki kitso."
Ummi ta murmusa.
"Anti nikam banason kitso wallahi bansan dalili ba."
Amina ta harareta kad'an.
"Eh mana, don kinga kina da gashin ne ai, amma idan kana da kyau saika k'ara da wanka. Gashinan yanzu kunshi yasa kin fito a Mace."
Sukayi dariya. Koda Ummi ta idar da sallah, tare suka shiga kicin tana kallon yanda Amina ke had'a girke-girke. Abin sai ya bata sha'awa matuka, don duk iyakar girkinta a gidan Mami, bai wuce dahuwar kwai da indomi ba. Amina ta bata shawara akan ta k'ara zage damtse wajen lura da yanda su Mami da Ramma ke girke-girke. Anan suka shantake wajen hira, har Amina na labarta mata batun wani saurayinta wanda shi kadai take saurara, har a yanzu haka ya soma matsawa da batun turo magabatansa.
"Allah Sarki, toh Anti ki ba shi dama mana."
Amina ta murmusa.
"Ba anan matsalar take ba, dangin mahaifina ne abun ji, kina ganin yanda suka wancakalar da lamuranmu, ina gudun kada azo a samu matsala ne."
Ummi ta gyada kai.
"In sha Allah babu abinda zai faru, ki gwada ba shi

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login