Showing 57001 words to 60000 words out of 158267 words

Chapter 20 - Dan Adam Book 1 Complete Hausa Novel

hakanan Ihsan sam bata da hakuri, ga saurin fushi. A raayin Hajiya Babba, bata kaunar abinda zai damu 'ya'yanta, kusan halinsu daya da Mami na son 'ya'ya.

   Acan kuwa Ummi tana isa ta zauna saman kujera gami da zubawa famfo ido, hankalinta gaba daya ba a wajen ya ke ba, ya tafi gaba daya ga tunanin Faruk.
'Dagaske fa ya ke.' Shine abinda ta fad'a a ranta, tabbas Faruk dagaske ya ke, asalima babu wani alama na tsoro ko fargaban abinda zai biyo baya. Yanzu ya zata yi? Bai bata damar cewa ba zata zo ba, ya riga ya yanke cewa lallai kawai ta zo ta sameshi. Ta riga tasan duk ranar da wani a gidan ya gano to fa tashin hankalin da zata shiga ba k'adan bane. Tagumi ta zuba tana tunano da Antinta, yau ne rana ta farko da ta soma jin bukatar waya a rayuwarta, ayau inda ace tana da  waya, tuni zata yi kiranta ta bata shawarar da ta dace. Ta ja guntun tsaki sannan dakyar ta mike ta soma aikin da ya kawota, saida ta kammala ta shanya sannan ta koma ciki.
    Misalin biyar na yamma tana zaune a k'asan bishiyar mangwaro tana wasa da ganyen, hankalinta gaba daya ya tafi ga tunanin Faruk, banda murmushi da wani annuri, baka ganin komai saman fuskarta. Ita tasan tana sonsa, bata ta6a son wani d'a namiji ba sai shi, saidai kawai bambancin dake tsakaninsu, shi kadai zai hanasu aure. 
   Ta jima kafin ta sauke ajiyar zuciya ta maida dubanta ga inda ta ji sautin dariyarsu. Ihsan ce da Ikram dukkansu sanye da kananun kaya, riga da siket, sun nad'e kansu da karamin dankwali. Hira sukeyi abinsu da dariya har suka iso wajen motar da tun zuwansu Abuja, Faruk tasan yana hawanta. Suna hada ido da Ihsan ta maka mata harara, Ummi ta kauda fuskarta. 'Kanki ake ji.' Shine abinda ta fad'i a ranta. 
  "Har kun fito?" Tattausar muryarsa ta ratsa dodon kunnenta. Ta so ta jure kada ta kalleshi, saidai hakan ya k"i yiwuwa, ji ta yi tamkar bazata nutsu ba idan bata ga tasa shigar ba. 'SubhanAllah!' Shine abinda ta fad'i a ranta. Riga tshirt ce yasa kalar(golden, long sleev) mai mannuwa a jiki, sai (blue jeans) ya sanya gilas dark brown, agogonsa na k'a'ida yana daure a hannunsa sai zobunansa da baya rabo da su. Ji ta yi tamkar numfashinta zai dauke tsabar kyawun da ta ga ya yi mata a idanu. 
  To ba Ummi kadai ba, Ihsan kanta baki ta bud'e tana kallonsa, ji takeyi tamkar ta dora hannu a ka ta ce wayyo Allah, kamar ta matsa bakin Faruk ya furta yana sonta. 
   "Wow Yaya Faruk, kayi kyau wallahi." Muryar Ikram ya katse Ummi da Ihsan daga tunanin da zukatansu suka lula. Ya dan rankwashi kanta yana dan murmushi.
   "Ko?" Ta yi dariya.
"Allah kuwa."
  Ya jinjina kai sannan ya zagaya zuwa mazaunin direba ya bude motar, Ihsan da sauri ta bude gidan gaba ta shiga, hakan bai wani dameshi ba, don shi bai dauketa wata aba ba face k'anwa. 
   Ya bud'e motar kenan yana shirin shiga idanunsa ya kai gareta. 
DAN ADAM
@RUFAIDA OMAR

57

Ita dinma har lokacin shi ta ke kallo, batasan tana da kishi ba sai a yanzun, Faruk ne da Ihsan wacce ta riga tasan tana tsananin sonshi, babu walwala a fuskarta hakanan bata daureshi ba, ta mik'e da sauri ta bar wajen ta nufi ciki. Ya
 dan dubesu.
  "Ina zuwa. Zo ki tayar da motar kafin na zo." Ya karashe zancensa da duban Ikram. Ba musu ta kar6i muk'ullin, basu kawo komai ba don babu wands zai yi tunanin wai Faruk zai dauki Ummi wata aba. 
   Shi kuwa da sauri ya nufi hanyar da ta yi da zummar komawa sashensa saidai ya zarce kai tsaye wajen dakunansu da zummar kwankwasa mata. 
Hawaye ta ke fitarwa da batasan dalilinsa ba, tasan dai tana jin zafi ne cikin zuciyarta na ganin Ihsan a gaban motar Faruk. (Ji karfin hali!) Tana shirin lek'ensu ta windo, ta ji bugun kofarsa yana kiran sunanta. A rude ta saurara ta ji, tabbas shi dinne, ta share fuskarta da sauri sannan ta bud'e k'ofar. Ya fidda gilashinsa yana dubanta, bata yarda ta kalleshi ba.
  "Kar kiji shiru Ummina, zan kai yaran nan siyayya amma bazan jima ba kinji?"
  Kai kawai ta gyada cike da jin haushi, da tana da iko da ta ce ya fadawa Ihsan ta koma baya saidai yin hakan wani nuna karfin hali ne wai 6arawo da sallama. Ita da ke cin arziki?
  "Ko za kije?"
  Ta girgiza kai a tsorace.
"Sai kun dawo."
  Ya daga kafada yana mai wani shagwa6e fuska kamar wani yaro.
"Allah kuwa idan kina so ki zo muje."
  "Don Allah kayi hakuri." Itama tayi maganar cikin marairaice murya don gaba daya tsoro ya cikamata ciki, bata so wani ya zo ya gansu tare. 
  "Shikenan, me kikeso na siyomiki?"
  Hankalinta ya tashi ga shi ya tsare bakin hanya babu damar ta duba hanyar ta gani ko wani ya taho. Ta dubeshi gaba daya a rude ta ke.
"Ko menene."
  Ya fahimci duk a rude ta ke, murmushi ya saki yana mai juyawa.
  "Bari na tayaki duban hanyar."  
Ya dan kalla sannan ya dubeta har lokacin bai bar murmushin ba, kafada ya daga gami da daga gira kadan.
   "Karki damu, idan don Binta ce, tana tare da Hajiya, can na barota. Bazan tafi ba sai kin gayamin abinda kike so na kawo miki."
   "Na shiga uku." Ta yi furucin da bata shirya fitowarsa fili ba, ga mamakinta sai ta ga yana dariya har yana dan jijjiga kafada. Ta yi sakato tana kallonshi, bai ta6a yi mata dariya har haka ba, sai taga ya k'ara yi mata kyau matuk'a. Hon din da suka ji ya katse su, tasan su Ihsan ne. Ta dubi windo kafin ta juyo ta dubeshi. Ya dan daga gira.  
  "Kina 6atamusu lokaci."
  Ta rasa ya zatayi.
"Ka siyomin alawa." Ta fada kamar zata fashe da kuka. Ya kwaikwayi muryarta.
  "Guda nawa?"
  Ta yi mishi nunin biyu da yatsa. Ya murmusa.
  "Bye, sai na dawo."
  Kanta kawai ta gyada, ya juya ya tafi. Ta lek'o ta na kallonsa har ya maida gilashinsa, murmushi ta saki gami da juyawa ciki ta rufe kofar. Wajen windo ta k'arasa da saurinta tana lek'ensa, tana ganin yanda ya had'e musu gira tamkar ba shine ya gama yi mata murmushi harda dariya ba yanzun. Akan idanunta ya bude motar ya shiga, daga haka ta daina ganinsu sakamakon gilashin motarsa mai duhu ne. Sauke ajiyar zuciya ta yi gami da rike kirji tana dariya marar sauti idanunta a lumshe, dariyar Faruk kawai ta ke gani ta ke jin sanyi, yanda ya nunamata tsantsar kulawa har mamaki abin ya bata, ashe ire-irensu sukan ji dadin duniya? Da ace wannan farincikin zai dore da ta fi kowa sa'a a rayuwa. Ta numfasa gami da bin lafiyar kafet ta kwanta. Sauranta jiran dawowarsa da ganin da wacce ya zo, duk kuwa da tsantsar fargaba da ke cin kasan ranta. Bata so wani ya san alaka'ar da ke tsakaninsu...

  Ba su suka dawo gidan ba sai bayan Magriba. Yana fakawa suka fito kowacce hannunta rik'e da leda wanda kayan mak'ulashe ne zalla. Ihsan bayan sun danyi gaba ta dubi Ikram.
  "Wai duk wancan kayan zak'in da Yaya Faruk ya loda na shi ne sho d'aya?"
  Ikram ta harareta.
"Meya hanaki tambayarsa?"
  Ta yi dariya.
"Mezai kaini gangancin nan?"
  "Wai ma, kina ganin dai ya mik'o mana na Hajiya, kinsan dai nasa ne ko? Amma dai bansani ba ko anjima zai je hira."
Ta k'arashe cikin zolaya. Ihsan ta buga tsaki gami da k'ara d'aga kafa.
"Ke dama ai ba'a hirar arziki dake sai kin kwafsa a wani 6angaren."
  Ita dai Ikram da dariya kawai ta bita. 
        
Shi kuwa gogan kai tsaye sashensa ya nufa, saida ya yi sallah ya fito ya lek'a su Hajiya kafin ya koma sashensa ya fito rike da ledar Ummi wacce ya yo mata siyayya. 
   Daidai lokacin da ya kwankwasa mata, Binta ta fito daga bandaki, zaro ido ta yi domin mamaki da ya cikata. Me Yalla6ai ke yi a bakin k'ofar dakin Ummi har yana kwankwasawa? Ta so ta yi magana saidai ta kuma la6ewa don ganin wannan abin Al'ajabin.  
  Ummi ta shafa adduarta, idar da sallar isha'in ta kenan, mik'ewa ta yi ta nufi k'ofar gami da bud'ewa. Suka dubi juna ta gaisheshi, ya amsa fuskarsa dauke da murmushi. Ledar ya mik'amata.
  "Ajiye wannan sannan ki zo ki sameni."
  Gabanta ya fad'i, ta dubi ledar sannan ta dubeshi. 
"Kar6i mana." Jiki a sanyaye ta kar6a.
  "Nagode."
Ya yi gaba gami da fadin.
"Ina jiranki." 
  Ta juya ta koma ciki har lokacin jikinta babu kwari.
  "Anya batayi wauta ba? Meyasa ta kar6a batare da tunanin kada wani abin ya biyo baya ba?"
   Ganin dai babu wanda ya ganta, yasa hankalinta ya dan kwanta.
"Anyi na farko, in sha Allah shine na karshe." Ta fada a fili, sanin da ta yi babu wani aikin da bata yi ba ne ballantana wani ya nemeta yasa ta saurin mik'ewa bayan ta daga hannu sama.
  "Ya Allah ka taimakeni yau wannan bawa naKa ya fahimceni."
  Daga haka ta shafa sannan ta fice. 
    Akan idon Binta, Ummi ta fito ta wuce, ganin Ummin na shirin waigowa ne yasa ta saurin komawa baya yanda bazata ganta ba, saida ta tabbatar ta bar wajen sannan ta shiga tafa hannuwa tana salati.
  "Tabdijam! Ashe dai duk jirgi daya ya kwasosu da Kb? Duk wannan shiru-shirun na wofi ne? Kuma wai Ummi?!" Tayi maganar a fili cikin nuna tsananin mamakinta. Lallai DAN ADAM mai wuyar gane hali ne.
DAN ADAM
@RUFAIDA OMAR

  58
  Ba su suka dawo gidan ba sai bayan Magriba. Yana fakawa suka fito kowacce hannunta rik'e da leda wanda kayan mak'ulashe ne zalla. Ihsan bayan sun danyi gaba ta dubi Ikram.
  "Wai duk wancan kayan zak'in da Yaya Faruk ya loda na shi ne sho d'aya?"
  Ikram ta harareta.
"Meya hanaki tambayarsa?"
  Ta yi dariya.
"Mezai kaini gangancin nan?"
  "Wai ma, kina ganin dai ya mik'o mana na Hajiya, kinsan dai nasa ne ko? Amma dai bansani ba ko anjima zai je hira."
Ta k'arashe cikin zolaya. Ihsan ta buga tsaki gami da k'ara d'aga kafa.
"Ke dama ai ba'a hirar arziki dake sai kin kwafsa a wani 6angaren."
  Ita dai Ikram da dariya kawai ta bita. 
        
Shi kuwa gogan kai tsaye sashensa ya nufa, saida ya yi sallah ya fito ya lek'a su Hajiya kafin ya koma sashensa ya fito rike da ledar Ummi wacce ya yo mata siyayya. 
   Daidai lokacin da ya kwankwasa mata, Binta ta fito daga bandaki, zaro ido ta yi domin mamaki da ya cikata. Me Yalla6ai ke yi a bakin k'ofar dakin Ummi har yana kwankwasawa? Ta so ta yi magana saidai ta kuma la6ewa don ganin wannan abin Al'ajabin.  
  Ummi ta shafa adduarta, idar da sallar isha'in ta kenan, mik'ewa ta yi ta nufi k'ofar gami da bud'ewa. Suka dubi juna ta gaisheshi, ya amsa fuskarsa dauke da murmushi. Ledar ya mik'amata.
  "Ajiye wannan sannan ki zo ki sameni."
  Gabanta ya fad'i, ta dubi ledar sannan ta dubeshi. 
"Kar6i mana." Jiki a sanyaye ta kar6a.
  "Nagode."
Ya yi gaba gami da fadin.
"Ina jiranki." 
  Ta juya ta koma ciki har lokacin jikinta babu kwari.
  "Anya batayi wauta ba? Meyasa ta kar6a batare da tunanin kada wani abin ya biyo baya ba?"
   Ganin dai babu wanda ya ganta, yasa hankalinta ya dan kwanta.
"Anyi na farko, in sha Allah shine na karshe." Ta fada a fili, sanin da ta yi babu wani aikin da bata yi ba ne ballantana wani ya nemeta yasa ta saurin mik'ewa bayan ta daga hannu sama.
  "Ya Allah ka taimakeni yau wannan bawa naKa ya fahimceni."
  Daga haka ta shafa sannan ta fice. 
    Akan idon Binta, Ummi ta fito ta wuce, ganin Ummin na shirin waigowa ne yasa ta saurin komawa baya yanda bazata ganta ba, saida ta tabbatar ta bar wajen sannan ta shiga tafa hannuwa tana salati.
  "Tabdijam! Ashe dai duk jirgi daya ya kwasosu da Kb? Duk wannan shiru-shirun na wofi ne? Kuma wai Ummi?!" Tayi maganar a fili cikin nuna tsananin mamakinta. Lallai DAN ADAM mai wuyar gane hali ne.
  Saida ta lek'a dakin ta gama bud'e ledar ta ga kayan mak'ulashen da ke ciki sannan ta fita tana had'iyar yawu.
  "Ina yarinya, wannan kam dole nima ki bani rabona."
    
  Acan kuwa Ummi ta iske Faruk durkushe gaban ruwa yana sanya tafin hannunsa na dama yana wasa da shi, fuskarsa a sake. Jin shigowarta yasa shi kallonta, ta kauda idanunta ta karasa bayan ta rufe k'ofar. 
   Mikewa ya yi ya koma ya zauna, itama ganin haka ne yasa ta zama a dayan kujerar kamar yanda sukayi wancan karon saidai a wannan karon ya sanya kujerun suna kallon juna, hakan yasa shi bawa k'ofa baya ita kuwa tana fuskanta. 
   "Na yi zaton bazaki zo ba ai."
Babu abinda ta ce sai wasa da gefen hijabinta da ta ke. 
   "Ummina."
  Ba ta amsa ba sai kirjinta da ke lugude. 
  "Wai meyasa ne kike kasa sakin jiki da ni? Idan da magana a bakinki ko fad'a."
   Ta ga dama ta samu, hakan yasa ta daurewa ta dubeshi.
"Don Allah Yaya Faruk ka yi hakuri ka kyaleni." Ta sauke idanunta daga kansa kafin ta cigaba da magana a raunane.
"Wannan abu ne da ko a mafarki ban ta6a ganin ya faru ba, 'yar aiki da auren d'an masu gida, kayi hakuri domin Allah, komai dake a ranka game da ni ka ajiyeshi gefe. Ni bazan iya abinda ka ke so ba, banason saka kaina cikin kowace matsala. Ka gafarceni amman idan akwai inda na kuskuro a maganata."
 
  Tun soma maganarta ya zubamata ido hannayensa biyu dunk'ule wuri guda. Ya lura iyakar gaskiyarta ta ke fad'a ba kuma don bata sonshi ba. Ya girgiza kai.
  "Meyasa ni ban ta6a hangen matsalar da kike yawan ikrari bane Ummi? Kina da tsoro, nasan kuma abinda ke tsorata ki wanda sam bai dace ba. Na farko dai nasan iyayena ba zasu hanani aurenki ba matukar na nuna musu ke ce za6ina, su din sun kasance maso abinda nake so, haka kuma yan uwana na tabbatar ba zasu hanani rayuwa da ke ba Ummi, koda ace kuma basu yi na'am da ke ba, to fa hakan ba zaisa na k'i aurenki ba muddin iyayena sun yarjemin.
Batu na gaba, ni ban daukeki daban da ni ba, Allah ne Ya haliccemu duka, ina yi miki kallo daidai da matsayina, ki ture dukkan wadannan kananun matsalolin Ummi, ki sauk'ak'awa zuk'atanmu, nasan kina jin abinda nake ji duk da cewar ba ki kama koda rabin k'afata ba."
  Shiru ya dan biyu baya, ya rankwafo kadan ya soma magana cikin rad'a.
  "Kin yarda kin amince na sanarwa Hajiya..."
  Bai kai ga karasawa ba ta hau girgiza kai tana dubansa da idanunta wadanda suka ciko da kwalla.
"A'a, a'a, don Allah kada ka fadawa kowa idan ba haka ba zan gudu."
  Ya dan hade gira jin kalmarta na karshe. 
   "Saboda kada ki aureni ne za ki gudu?"
  Ganin yanda muryarsa ta chanja da kuma yanayinsa yasa ta yin shiru gami da duk'ar da kai. Ya lumshe ido.
  "Shikenan, tashi ki tafi."
  Ta kasa motsawa, sai ta ji bata kyauta mishi ba, shi kuwa har lokacin bai bude idanunsa ba, dagaske bai ji dadin furucinta ba, kenan akan ta aureshi, ta za6i guduwa? 
    "Ka yi hakuri don Allah."
  Ya tsinci muryarta, da sauri ya bude ido don kuwa muryar ta nuna alamun kuka takeyi.  Kukan kuwa takeyi, ya girgiza mata kai.
"No Ummi please, banson hawayenki fa. Ni na hakura."
  Faruk ya cigaba da kasheta da dad'ad'an kalamai wadanda nan take suka kashemata jiki suka sukurkuta ta. Allah Ya mishi baiwar iya lafuzza masu dadi da saurin sace zuciya wanda shi kansa bai sani ba sai a yanzun da ya fad'a cikin soyayyar Umminsa. A wannan zaman da sukayi saida Faruk ya ci galaba don kuwa Ummi ta dan saki jikinta sun yi hira mai dadi har da dariya. Kowannensu yana jin zuciyarsa sakayau, gaba daya ji sukeyi tamkar a duniyar babu sauran bil adama sai su biyu tallin tal! A karshe ya duba wayarsa da ta soma k'ara, yayansa Likita ne(Ridwan). Ya dauka. Bayan sallama ya tambayeshi inda ya shiga, ga shi kuma a falon Hajiyarsu bai ganshi ba.
  Ya dubi fuskar Ummi wacce ke dan satar kallonsa, murmushi ylm    a yi ganin ta kauda kanta.
"Hira nake yi da surukarku amma ina nan zuwa."
   Daga haka ya katse kiran ya bar Ummi da sakin baki.
"To sarkin tsoro, rufe bakin."
Yana fadin haka ya mik'e tsaye.
"Bari na wuce Dakta ya zo. Sai mun hadu gobe kuma in sha Allahu ko?"
  Ta girgiza kai alamar aa. Ya ja dan guntun tsaki. "Kinga dadin waya kenan, da sai mu sha hira, amma dai ba wani abu."
  Daga haka ya yi mata sallama ya wuce, itama barin wajen ta yi da saurinta. Tana shiga dakin ta fidda hijabinta ta zauna, a yau ji take dukkan shawararwarin Antinta babu daya da ta iya dauka, ji take kamar ana k'ara rura mata wutar kaunar Faruk. Ta matso da ledar ta bude, ta yi mamakin ganin kayan kwalam har da su meatpie nad'e a jikin tissue guda uku, ga wani kullin leda karami wanda tana budewa ta ci karo da alawoyi kala-kala. Harda su cake da robar ice-cream manya biyu. 
   "Assalamu alaikum." Da bude kofar da sallamar nata duk lokaci guda ne
DAN ADAM
@RUFAIDA OMAR
  60
"Ya Salam, haba Ihsan, meyasa haka?"
  Ihsan ta mike zaune idanunta jage-jage da ruwan hawaye. Ta ja majina.
"Kinga lokaci ya k'uremin ko Ikram? Da ace na bi shawararki da banga wannan rana ba."
  Ikram tausayinta ya mamayeta, ta dafa kafadarta gami da girgiza mata kai.
"Aa, lokaci har yanzu da sauransa Ihsan. Na fadamiki ki cire kunya ki sanarwa Faruk abindq kike ji game da shi koda ta hanyar  kafar sadarwa (whatsapp)ne. Kada ki karaya da wuri."
   Haka ta yita lallashinta sannan ta fita wajen yan uwanta. Tana fita Ihsan ta dauki waya ta kira Maminta. Ko sallama bata iya yi ba ta fashe mata da kuka gami da labartamata abinda ake ciki. Mami ta shiga damuwa ainun.
  "Ihsan kina kyautatamasa kuwa kamar yanda nace?"
   "Babu abinda bana yi Mami, har gyaran dakinsa hana Ikram nayi na ke yi, amma

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login