Showing 144001 words to 147000 words out of 158267 words

Chapter 49 - Dan Adam Book 1 Complete Hausa Novel

kallo, duk duniya Gidado biyu ta sani. Da wani kawunsu na Adamawa wanda tsoho ne, sai kuwa Gidadon wajen su Ummi. 
  "Wane Gidadon ki ke magana akai?"
Ta hau kame-kame, bata yi zato ba ta ji Hajiya ta zare wayar daga hannunta, kafin ta yi wani yunk'urin ta budo. Ta yi shiru tana duban hoton kafin ta dubi Ikram cikin sanyin murya mai nuni da karaya ta ce. 
"Shi Gidadon ne ke sanyaki rama da tunani dama? Kinsan waye Gidado wajen Ummi kuwa?"
  Shiru Ikram ta yi babu amsa ga kunya da ta cikata, wani murmushi na manya Hajiya ta yi. 
  "Saidai kuma na ji ance yana da mata, kina da tabbacin za ki iya aurensa ki zauna a Jar Kwami? Sannan za ki iya hakurin zama da matarsa?"
  Sai lokacin  ta iya dago kanta ta dubi mahaifiyarta idanunta na zubda ruwan hawaye. 
  "Duk abinda ki ka lissafo Hajiyarmu, babu daya da ba zan iya jurewa ba, ni nasan harda hakkin Ummi ya kamani, saidai wallahi a yanda nake ji a zuciyata, kamar ba zan iya auren wani ba bayan Yaya Gidado."
  Ta karashe cikin kuka, zuciya irin ta *MAHAIFIYA* nan take ta ji tausayin diyarta ya mamayeta, ta share mata hawayen gami da mikawa mata wayarta tana murmushi. 
  "Allah Ya za6a abinda yafi alheri gareku."
  Daga haka ta juya ta fice, Ikram murmushin jin dadin ta saki, ko babu komai ta ji dadin kyakkyawar adduar da ta fito daga bakin Mahaifiyarta. Ta karasa saman gadon ta zauna sannan ta bud'o sak'on. Sallama ce da gaisuwa, nan take ta ba shi amsa, ai ko babu komai samun lambarsa da ta yi cikin wayarta, abin alfahari ne, zata cigaba da janyo hankalinsa da dabara hakanan zata cigaba da tsananta addu'ar neman za6in Allah. 
    
   Tun daga wannan ranar sai ta ja shi da hira, abinda ya burge Gidado bai wuce ganin yanda koda wasa bata sanarmishi cewar tana sonsa ba, hakazalika babu ranar da bata tambayar Hafsa, har Anti ta lak'aba a farkon sunanta. Ya yi mamaki matuk'a don ya yi zaton zata dunga kishinta ko don ma yanda ya ke yawan yi mata zancenta, abin daure kan ma ita da kanta ta nemi ya bata tarihin farkon haduwarsa da Hafsa inda ya kirata suka dan ta6a hira kafin ya bata.
  Kishi fal ya cika kirjinta jin yanda ya ke kod'a Hafsa a zuciyarsa, saidai ya zata yi tunda ita ta nemi da ya bata labarin.
  "Ya ki ka yi shiru?"
Ta yi murmushin yak'e.
"Bakomai, kwarai soyayyarku ta burgeni, ina fatan nima Allah Ya bani miji wanda zai yimin irin wannan son da ka ke yiwa Anti Hafsa, ko fiye da hakan ma."
Ransa ya sosu, ta kuma ba shi tausayi, anya yana kyautawa yarinyarnan? Ya tuna ya cewa Abubakar suna hira sosai da ita, saidai ya 6oyemishi cewar bai yi mata wata magana da ta danganci soyayya ba.  
   "Hello." Ta fada muryarta a sanyaye. Sai lokacin ya tuna ashe waya ya ke yi.  Ya numfasa. 
  "Allah Sarki, Allah Ya ba ki fiye da ni."
   Ta gyada kai idanunta cike taf da kwalla, shakka babu Gidado fa ba sonta ya ke yi ba. 
  "Um, da wuya na samu hakan, koda zan samun ma bana bukata, nafison daidai kai din a komai da komai."
  "Kamar ya?"
Sai alokacin ta fahimci lallai su6utar baki ta yi. Ta yi saurin gyara furucinta.
"Eh idan na samu fiye da kai ai inajin mata ba zasu barni na huta ba, inada kishi kuma, banajin zan iya jure waccan ta kiraka waccan ta zo."
  Cikin dariya da muryar zolaya ya ce.
"Kuma gashinan kina shiga lokacin wata ko?"
  Itama dariyar ta yi.
"To ai ni kanwa nake wajenka."
Ya yi murmushi mai sauti.
"Hakane."
  Suka kara ta6a hira kafin su yi sallama. 
   Ta k'urawa wayar idanu kafin ta hau ambaton 'Innalillahi wa Inna ilaihirraajiun', wannan ba karaalmar musiba bace ace kana son wanda ba ya sonka. 
   Ta k'ara daukar alkawarin zage damtsenta wajen kyautata mishi da yawan hira da shi da kuma danne soyayyarta, watakil a haka Allah Ya taimaketa ta ci galaba ya soma sonta.
   
      ***    BAYAN SATI UKU   ***

                GIDAN FAR HAS
Faruk ya jima da komawa bakin aikinsa, yayinda ya cikawa Ummi alkawari inda ya daukomata matar da zata koyar da ita karatu kafin zuwan lokacin da zata soma shiga aji. 
   Koyaushe soyayya suke zubawa, a wannan lokacin har Hajiya sun kaiwa ziyara, hakanan ya dauketa zuwa gidan yayyunsa, nan ma ta yi mamakin ganin chanji daga su Jidda duk kuwa da cewar bata iya ta saki jiki da su ba tunda basu saba da hakan ba.  
   A ranar wata laraba Faruk na tsaka da aiki ya tsinci kiran Ummi, a take ya ajiye biron hannunsa ya daga.
  "Assalamu alaikum Ummina."
Ta amsa da fara'arta kafin ta tambayi lafiyarsa. Ya yi murmushi. 
"Ganinan sai afkin tunaninki kuma ga ayyuka sunmin ca."
Ta yi murmushi mai sauti kan ta dora da fadin.
"Allah Sarki, Ummi ma ta kasa rabuwa da tunanin Faruk dinta."
Ya lumshe ido gami da jinginar da kansa jikin kujera yana murmushi.
"Kasan meyasa na kiraka?"
"Saikin fad'a tawan."
  Cikin shagwa6e murya ta ce.
"Fura nakeson sha."
  Ya yi dariya.
"Yau kuma gida ki ka tuno?" 
Itama ta dara.
"Dagaske wallahi, na kasa cin komai, shi kawai nakeson sha."
  Ya mike zaune.
"Ya Salam, meyasa tun dazu ba ki gayamin ba kuma ki ka zauna da yunwa? Bari nasa a kawomiki."
   "Yauwa FAR HAS."
  Tunda ya ke bai ta6a jin ta ce hakan ba, ya yi saurin jefamata tambaya.
"Me kenan?"
  Dariya ta yi ta katse kiran ta barshi sakato da waya a hannunsa ba tare da yasan tak'amaiman manufarta ba.
Tunawa da ya yi da furucinta na bata ci komai ba yasa shi saurin katse wannan gami da kiran Ado direban gidansu da zummar ya bashi aike. 
  Cikin mintuna da basu gaza ashirin ba ya je ya siyo damammiyar fura mai dadi ta cikin roba har guda biyar bayan ya kar6i kudin a hannun Hajiya daga nan bisa umarnin Faruk ya zarce ya kaiwa Ummi. Ai kuwa shi ta wuni a wannan ranar tana sha. 
Koda ya dawo suna zaune, yayinda ya ke cin abinci ita kuwa tana faman sha fura tana kallon talabijin, ya k'uramata idanu yana k'aremata kallo cikin lura. Ta tsargu, hakan yasa ta dubansa.....!
   DAN ADAM
@RUFAIDA OMAR

124

"Meyafaru?"
Ta fada cikin sanyin muryarta, ya dagamata gira yana mata murmushi. 
"Zo nan."
Ba musu ta ajiye robar furarta ta mike ta nufi inda ya ke gami da zama a gefensa, sanye take cikin riga iyaka gwuiwa da dogon wando(tight).  Ya janyota jikinsa. 
"Gaba daya kin chanja, anya babu ajiyata anan?" Ya karashe yana mai kai hannu cikinta gami da shafa. 
  Ta yi shiru, ita daman wata nada sati daya ta tare a gidan yanzu gashinan har watan ya cinye bata ga komai ba. 
Ya zungureta.
"Answer me."
Ta shagwa6e fuska.
"Nidai bani da komai."
Ya yi murmushi.
"Anya kuwa? Ji fa yanda ki ka k'ara girma a komai." 
Ta lumshe idanu jin yanda ya kasa tsayar da hannunsa wuri guda, da sauri ta zame ta koma gefe tana fadin.
"Kai FAR HAS abinci fa ka ke ci."
Ya yi mata duban rashin fahimta.
"Af, kinga na manta ko? Inason tambayarki ma'anar wannan FAR HAS din na manta."
  Dariya ta yi wacce ke burgeshi, bai iya 6oyewa ba saida ya furta, don Faruk sam bai iya 6oye abinda ya yi mishi, ko girki ta yi sai ya yaba balle idan idan ta ci ado, hakazalika duk sadda ya shigo gidan sai ya yaba da gyaranta, wannan ba karamin kara mata sonsa ya ke ba, babu macen da batason a yabawa kokarinta, wasu mazan nasu tunanin su kadai zasuyi ana yabawa, su ba zasu yaba naka ba, basusan cewa yabo na kara soyayya tsakanin maaurata ba,  koda ta yi ba daidai ba idan ka fada bazata ji haushinka ba saboda tasan ka yabawa kokarinta kafin haka. 
  "Har kullum bana gajiya da ganin dariyarki."
Ta rage dariyar tana murmushin jin dadin kalamansa.
  "Nagode FAR HAS."
Ta fada cike da zolaya, ya basar gami da maida kansa ga faranti yana murmushi. 
   Bai kara magana ba hakanan itama kowanne na bawa cikinsa, ita kuwa saida ta shanye robar fura tas. Lokacin shima ya kammala cin abincin ta dauke kwanukan sannan ta dawo ta zauna kusa da shi kamar yanda ya nunamata yafi bukata idan suna zaune. 
   Ya ja yatsun hannunta.
"Fadamin ma'anar FAR HAS."
Ta saki k'ara kad'an kafin ta turo baki.
"A kyauta?"
Ya na murmushi ya girgiza kai.
"Fad'i bukatarki."
  Ta kanne ido daya.
"Gobe a karomin fura."
Ya janyota ta yi filo da cinyarsa.
"Mai sauki kenan daga abinda za ki samu, just tell me."
   Ta lumshe ido tana murmushi.
"Faruk da Hasiya nake nufi."
Sai lokacin ya dan tsaya nazari kafin ya dubeta da mamaki ya na murmushi.
"Sunan ya burgeni ya kuma ban mamaki ta yanda har ki ka yi tunanin hadawa."
  Ta rufe ido da hannu tana murmushi. Ya sunkuyo da fuskarsa zuwa nata....!
              
                ***    ***     ***
                      KANO
  Kwance ta ke tana duban hotunan da suka shigo wayarta ta (whatsapp) don bisa al'adarta duk dare idan ta gama komai sai ta bibiya ta ga ko akwai wadanda basu dace ba ta goge, kamar abinda ya shafi gawarwaki da hatsari. Karaf, idanunta suka kai ga wani hoto wanda yasa ta mikewa zaune babu shiri. 
  Hoton Abubakar ne tare da wata 'yar ajinsu Rukayya Tsigai, ai ba shiri ta hau online ganin wacce ta aiko,  Zahida Taskira ce daya daga cikin yan ajinsu wacce suka sanyamata sunan sanadin surutunta da tone-tone don ba a sirri da ita. Inda ta yi mata bayani kamar haka.
  "Aslm, Ihsan please ba batun gulma ko hada husuma ba, inace wannan shi ki ka ta6a nunamin matsayin wanda zai aureki? Magana ta gaskiya guy dinnan na sanshi tare da Tsigai, saidai ban gayamaki ba time din kada ki ji haushi, idan har dagaske shi ki ka za6a matsayin mijin aure zan baki shawara ki chanja tunani saboda wallahi guy din yana da son mata, Rukayya ba wajen Partyn wata cousin dinta sukayi hoton nan kuma na tabbatar suna chatting."
  Kan Ihsan ya yi dum, ta rasa meke mata dadi a duniya, batasan lokacin da ta soma hawaye ba tana ambaton Allah, saidai me? Ko kankani bata ji soyayyar Abubakar ta ragu ba sai kishi mai zafi da ya turnuketa, ba don tana sonshi ba babu abinda zai hana a yau ta rabu da shi. 
  Bata maidawa Zahida amsa ba don tasan zai iya komawa kunnen Rukayya Tsigai, kawai sai ta kira Abubakar ta ce ya hau online zata mishi magana. 
  Badiyya na kallonsa yana waya yana tambayar ko lafiya duk ya rikice saidai bata ce uffan ba, banda murmushi, idan da sabo ai ta saba da halin Abubakar na hira da yanmata balle kuma ta tabbatar cewa wannan Ihsan ce don duk cikin yanmatansa tana da yakinin ita ya ke yiwa so na aure tunda har ankai da sanya rana. Mikewa ta yi ta bar falonnasa shi dinma bai tsaidata ba don hankalinsa ya tashi jin muryar Ihsan din ba'a hayyaci ba. 
   Nan ta aikamishi hoton, duk sai ya ji jikinsa ya yi sanyi, shakka babu wannan hoton ya jima, yanzun ma ba ya tare da Rukayya sun rabu akan zafin kishin Rukayyar kan yanmatansa, shi kam kullum adduarsa bai wuce na Allah Ya yaye mishi wannan mugun hali ba. 
  Ranar kam Ihsan ta yi kwanan bakin ciki, dakyar bacci ya saceta don idanunta saida suka kumbura. 
Washegari da ciwon kai ta tashi, koda Mami ta tambayeta sai ta ji bakinta ya yi nauyi ta kasa fadamata, tsoronta kada a fasa auramata Abubakar don Allah shaida tana sonsa yanzun musamman yanda ya ke kasheta da soyayyarsa mai tsayawa a rai wanda ta tabbatar da shi ya ke yaudarar yanmata sai kuwa kudi. 
  Ikram kadai ta sanarwa, Ikram da ranar ta tashi da farincikin jin Hafsa matar Gidado ta haihu da kuma dan kishinta a kasan rai duk sai ta ji nata 6acin ran ba komai bane idan an hada da na Ihsan. Ta hau salati, tasan tabbas Abubakar yana da kula yanmata don tasan wata kawarta wacce tasan shi saidai batasan har zuwa wannan lokacin ba, nan ta shiga bata baki da nunamata ta cigaba da adduar neman za6in Allah, katse wayar kawai ta yi. Abubakar ranar ya kira yafi sau biyar saidai ta k'i dagawa, ya bita whatsapp hakanan ya yi mata text saidai ko kusa bata maida amsa ba.  
    A ranar dai suka shirya don kuwa bata iya dogon fushi da shi, abin mamaki Zahida ba ta daddara ba ta turo wani, ai kuwa ta sha zagi kafin a karshe ta rufeta yanda babu damar da zata k'ara shiga sabgarta. 
                 ***    ***    ***
        A KWANA A TASHI....!
DAN ADAM
@RUFAIDA OMAR

   125

Tun Ummi na zuba idon ganin 6atan watanta, har dai ta ji shiru, wannan ya daga hankalinta, ga wani haske da ta kara hakanan komai nata ya k'aru, watarana suna kwance da Faruk ya dubeta. 
  "Ummina ban yarda ba, anya babu ajiyata a wannan cikin naki? Kwadayinki ya yi yawa, yau kice magwaro, gobe ki ce bakyason kamshin turarukana."
  Ta kwanta jikinsa tana mai turo baki.
"Nifa bani da komai."
Ya ja karan hancinta.
"Zamu tantance yanzu. Taso muje."
Ta mike zaune idanu a waje ta ke dubansa.
"Ina?"
"Asibiti mana."
Ta yi narai-narai da fuska. Ya yi saurin toshe bakinta da hannu.
"Shii..karki soma rok'ona don kuwa sai munje."
Ta langa6ar da kai tana sosa idanu.
"To ai..ai yau babu aiki."
Cikin muryar rarrashi ya ce.
"Wajen Dakta zamu je, bamu jima da waya ba ya cemin yana asibiti." 
Ta turo baki.
"Please FAR HAS, allura fa zasu yi min."
  Ya matso da ita yana ji kamar ya hadiyeta. Saitin kunnenta ya yi magana.
"Ba wanda zan bari ya soka maki karfe a jiki, tashi ki chanja kaya kinji?"
  Ba musu ta mike, daman sanye ta ke da riga wacce ko k'ugu bata karasa ba sai kuwa wando shima da bai kai gwuiwa ba, ta kai kofa ya kira sunanta. Ta juyo fuska a turnu6e.
"I love you."
Furucinsa yasa ta murmusawa gami da lumshe ido ta budesu akansa. 
"Love you too." Ta furta a hankali ya sanya yatsunsa cikin sumar kansa yana murmushi gami da sauke ajiyar zuciya, wasu kance soyayya na raguwa bayan aure, shi kam ya rasa dalilin da yasa koyaushe soyayyarta gaba ta ke k'ara yi a zuciyarsa, Allah Ya sani kauna fisabilillahi ya ke yi gareta, tun dora idanunsa da ya yi akanta, bai ta6a hutawa daga tunaninta ba har saida ya mallaketa. Mikewa ya yi shima ya fad'a bandaki don kimtsawa. 
   Lokacin karfe hudu ta kusa, Ummi ta kammala shirinta cikin wani koren leshi dinkin riga da siket, ta yafa farin mayafi ta sanya takalmi flat mai kalar fari da baki. 
   Saida sukayi sallar la'asar kafin su fito kasancewar ranar bata da lesson don daga litinin zuwa juma'a sukeyi, kwarai Malamar na yabawa da kokarin Ummi don har mamakin kaifin basirarta ta ke, ko wata basuyi da somawa ba, ta iya abubuwa da dama.
   Gogan kananun kaya ya sanya, wandon 3quarter ne fari k'al, sai kuwa t-shirt dinta mai layi-layi fari da bak'i. 
  Idan ka gansu dole ka k'ara daga ido ka kallesu don kuwa sunyi matukar dacewa da juna. Saida ya budemata 6angarenta ta shiga ta zauna kafin shima ya shiga, maigadi ya budemusu gate suka fita. 
   A asibitin suka iske Dakta Ridwan, yana duba wasu kasancewar yawanci ranakun hutu, manya yafi gani, saida ya sallami wasu kafin suka shiga.
  "Ango na Amaryarsa." Ya fada yana dubansu fuska dauke da murmushi. 
Suma murmushin sukayi Ummi na sunne kanta, Faruk ya kara matse hannunta cikin nasa.
"Ya son ranka?"
Sukayi dariya don tsakaninsu babu wani zancen raini, sun dauki junansu tamkar abokai musamman su ukun nan idan an cire Babban Yaya wanda ba koyaushe ya ke biyewa shiriritarsu ba. 
   Ummi ta gaisheshi ya amsa tana tambayar su Muhsin. 
"Suna nan lafiya."
"Ai ba'a kyauta ba, ya dace a kawo mana su koda ran Friday ne." Cewar Faruk. 
  Dakta ya yi dariya.
"Karku damu, duka yaranku zasu zo hutu, ai (second term) din ya kusa k'arewa."
  "Wai me? Noo, kar a kawosu duka, ba zasu takura min Bebina ba."
Dariya Dakta ya yi.
"Oh, har ka tabbatar da ka samu bebin? Toh ai sai ku tashi ku je Allah Ya raba lafiya." Ya karashe yana mai daure fuska da wasa.
Faruk na murmushi yana mai dafe goshi.
"Please ka yi hakuri, dubamin ita yau wata biyu kenan bata ga period dinta ba."
Saida gaban Ummi ya fadi ta dan dubeshi, ya dagamata gira yana murmushi.
"Eh ko?"
Ta kauda kanta a kunyace. Dakta murmushi ya yi ya ce.
"Lil kenan."
Daga haka ya janyo takarda ya yi rubuce-rubuce bayan gama yiwa Ummi tambayoyi daga haka ya mikawa Faruk takardar.
"Sai ka je a auna fitsarinta."
Ba musu ya kar6a suka fita, bayan fitarsu ta dubeshi.
"Kai FAR HAS, ko kunyar Dakta ba ka ji ba ka ke magana haka?"
Ya daga kafada kadan yana yamutse fuska.
"Don bakisan ma waye Dakta ba shiyasa ki ke fadin haka, sa'ar da na ci yana jin kunyar idanunki da sai na koma ni ke jin kunyarsa."
Dariya kadan ta yi kawai batare da ta ce uffan ba. Bayan angama auna fitsari an basu sakamako suka koma ga Dakta. Ya bude takarda ya karanta yana murmushi kafin ya dubesu kadan, Faruk ji ya ke kamar ya warce takardar, cikin zakuwa da son sanin meke faruwa ya ce.
"Wai don Allah ka yi magana mana."
Dariya Ridwan ya yi. 
"Bani goron albishir."
Ya fada yana mai mikamasa hannu. Faruk ya wawuro na'urar auna jini (Sphygmometer) ya dora saman hannunsa. Har Ummi saida ya bata dariya, shi kansa dariyar ya yi. 
  "Toh nagode dai na tausayamaka tunda naga ka damu."
Ya dubi Ummi fuskarsa a sake.

"Congratulations, you are two months pregnant."
Sunkuyar da kanta ta yi, ta fahimci me ya ke nufi, wato dai tana da ciki wata biyu. Faruk mikewa ya yi ya karasa ya rungume Yayansa suna dariya. 
  "Congratulations my lil, Hajiyarmu zata yi farinciki da jin hakan."
Sukayi dariya. Tunda Ummi ta sauke kanta bata k'ara dagoshi ba har zuwa sadda Faruk ya dawo ya zauna gami da lalubo hannunta yasa cikin nasa, idanu ta lumshe ta saci dubansa, shima ita ya ke kallo. A hankali bakinsa ya motsa. 
"I love you." Ta fahimci hakan ya fada, ta kauda kanta tana murmushi gami da damke hannunsa alamun ta amsa. Hankalin Ridwan ba ya kansu, ya gama rubuta magunguna kafin ya mikowa Faruk. 
  "Sai a kula banda yawan aikace-aikace. Yau za ka shiga Gida ne?"
 

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login