Showing 111001 words to 114000 words out of 158267 words

Chapter 38 - Dan Adam Book 1 Complete Hausa Novel

Bayan an gaggaisa, ta ke tambayar Malam Balarabe sadda ya dawo, a kunyace ya bata amsa ya kara da neman gafara. Ta yi kamar bata ji ba don kuwa kokusa bata da rikeshi ba. Mariya dai an zama yan kallo sai rarraba idanu kamar shege a rabon gado. 
   Ranar Ummi dai ra rasa inda zata sanya kanta don dadi, haka ta wuni cikin yan uwa, dangi sai zuwa akeyi rututu ganinta. Wasu sunfi danganta kamanni da yanayinta da Inno Zahra data rasu saidai ita tana da yawan barkwanci da dariya, wasu kuwa sun fi karkata ga Hasiya. 
  Ranar fura da nono har saida ta ture, ga cima kala-kala da aka kawo musu. Mariya tana samun yaran abokan wasa shikenan kuma ta saki jiki har ta fice tare da su. 
  Ranar Ummi ta mance dukkan wasu bakkan cikinta. Kwanan Malam Balarabe biyu suka juya tare da Dan uwansa da kuma Mariya wacce itama ya ke son kaita ganin dangin mahaifinta wadanda bata sani ba, ba kuma yaso nan gaba azo baya raye ta tambaya ba wanda ya sani. 
   Ummi ta zama 'yar lele, kullum cikin hira, idan ta jima wajen Inna Boddo, nan kakanta zai nemeta, nan ma ba jimawa sauran matan musamman uwa ga Inno da Binta, Danejo itama zata shiga nemanta, don tunda ta ga Ummi ta ji kamar Innonta ce ta dawo. Rayuwa kenan, bayan wuya sai dadi idan har mutum zai jure ya yi hakuri da dukkan lamura, Allahu Ya bamu ikon juriya da hakuri ba don isarmu ba, Amin.
    Ranar talata da misalin biyar na yamma, Ummi da wata yar uwarta Abu wacce itama jika ce a gidan suna tafe a hanyarsu ta zuwa gona kaiwa baban Abun abinci. Ummi na sanye da doguwar riga bulu mai adon fulawoyi bakake, ta tufke gashinta wanda tun tsifar da Dada ta yi mata bata yi kitso ba, fuskarta fayau, ta yafa mayafi akanta bata ko daura dankwali aciki ba, sai gashin ya yi tudu a tsakiya kadan, tana wasa da karar dake a hannunta. Suka tsinci muryar yayan Abu, Gidado yana kwalamusu kira ta bayansu. Tsayawa sukayi gami da juyawa, gaban Ummi ya yi wani mugun faduwa ganin wanda ke tare da Gidado. Murmushi tattausa ya ke jifanta da shi da kallon dama na fadamiki...
DAN ADAM
@RUFAIDA OMAR

  99

Kasa kwakkwarar motsi Ummi ta yi, ya hade cikin farin yadi wanda ake ganin farar singiletinsa ya dora bak'ar hula hakanan takalminsa bak'i ne. Ya yi kyau kwarai duk ya chanjamata. Abu  ke tambayar Gidado abinda ya faru. Daidai lokacin da suka karaso wajensu ya kasa dauke idanunsa daga Ummi. 
  "Bak'o ki ka yi, tare da Mai sunan Baffa(Usman kanin Malam Balarabe) ya zo, bayan an gaisa kuma ya ce bazai jira ku dawo ba na yi mishi rakiya." Duk wannan dogon bayanin da Gidado ke yi gareta ita gaba daya jikinta ya yi sanyi, Yaya Faruk? Ina ya baro aikinnasa? Yanzu babu kunya ya cewa su Daddy zai zo wajenta? Wayyo, wannan abu akwai kunya. Saida ta ji Abu ta gaisheshi da hausa ne ya amsamata da fulatanci har Abu na dariyar mamaki, itama ta dawo hankalinta, ta tuna ashe fa shima bafulatanin ne. 
  Ta durkusa ta gaisheshi da girmamawa kamar yanda ta saba. Ya amsa, Gidado ya dubesu.
"To, za ku juya ne ko mu wuce tare?"
Faruk ya dubeshi har lokacin fuskarsa da walwala.
"No ku karasa, ta nan za ku biyo ko?"
"Eh." Abu ta amsa.
"Idan kun zo nan sai mu koma tare."
Suka amsa da to kafin su soma tafiya, shi kuwa baice uffan ba ya soma tafiya ya nufi wajen wani dutse ya sanya hankicif gami da zama. Garin babu rana sai ma hadari da ke haduwa. Ya dubeta, ta sunkuyar da kanta ta soma takowa don ta fahimci manufar kallon, gefe ta dan zauna. 
  "Sai ki ka ga Faruk ko?"
Ta murmusa.
"Ai na yi mamaki, naga kuma yau ranar aiki."
Yana binta da kallo ya amsa.
"Kar ki yi mamaki, kina da daraja da matsayi babba awajena wannan yasa ni daukar hutun sati kawai don na zo na ganki. Na horu da yawa fa Ummina, ji yanda na ajiye k'ashin wuya sadda ke ki ke mulmula k'iba har wani tumbi ki ka ajiye."
Ya karashe a shagwa6ance kamar yana gaban Hajiyarsa. Kunya da dariya ta kamata lokaci guda. Ta dan ja mayafinta da ya zamo har ana ganin kwantaccen gashin goshinta wanda ya kusan haduwa da gira. Tabbas tasan ta yi k'iba saidai bata hango tumbin da ya hanga ba. Ya dan daga gira.
"Dagaske nake."
"Um, ya akayi ka zo nan?"
"Garin masoyi yana nisa ne?"
Bai saurari amsarta ba ya cigaba.
"Zuciyata ce ta kasa samun nutsuwa, rashin ganin mahadinta kwana biyunnan ya jefata cikin tarin damuwar da ba za ki gane ba. Da naga ina neman mutuwa kawai na yanke shawarar biyo jirgi na taho Gombe. Ina isa kai tsaye na kira Babana, shi kansa ya yi mamakin jin wai ina Gombe, ya fadamin sunan unguwar ya ce idan na shiga tasi na hadashi da direban. Ya mishi kwatance, Alhamdulillah, don kuwa Ummina yan uwanmu sun min kyakkyawan tarba sannan sun ji daga bakin Baba cewa ni ke son aurenki. Jiya na iso Gombe, sai yau na taho nan. Kin gane dagaske Faruk bai iyawa babu Hasiya?"
  Ta rufe idanunta tana murmushi, har cikin ranta wani wutar kaunarsa ke kara ruruwa. Bata ji tashinsa ba sai bude ido da ta yi ta ganshi durkushe gabanta ya kuramata idanu yana murmushi, yayinda ya tokare hannun damansa saman dutsen. Sunkuyar da kanta ta yi. 
     "Mu godewa Allah da Ya amsa mana addu'armu ya sadaki da farincikinki, na tayaki murna ainun Ummina. Abu daya ya rage mana."
  Ta ji sarai abinda ya ce sai ta basar.
"Nagode Yaya Faruk."
  "Dayan fa? Ba za ki yi tambaya akansa ba?"
  Ta dan saci kallonsa yanda ya ke maganar cikin rad'a-rad'a. Ya kashemata ido daya, ta yi kasa da kanta da  sauri.
  "Ko bakyaso ki ganki a gidana matsayin matata?"
  Da sauri ta karkata  ta kauce daga saitinsa tana mai ambaton Innalillahi a fili don ji ta ke kamar ta dora hannu a kanta don kunya. Dariya sosai Faruk ya shiga yi adaidai lokacin da iska ta yi awon gaba da mayafinta, ta rike kannata tana mai da na sanin fitowa ba dankwali, tunda suke da Faruk bai ta6a ganin gashinta tsirara har haka ba, ya yi mata kallo daya yana mai kauda kansa da sauri alokaci guda ya na mai tsintar yanayinsa da chanjawa, ita kuwa da sauri ta janyo mayafin ta rufe gashinta sannan ta mike tsaye, muryarta ba rawa ta ce.
"Yaya Faruk mu tafi kada ruwa ya riskemu anan kaga har yanzu ba su tahowa."
Ya sanya hannuwansa cikin aljihun wando, yana mai shakar daddad'ar iskar da ke kadawa, kafin ya juyo ya dubeta sannan ya yi kasa da kansa.
"Muje." Ya fada cikin yanayi na mutuwar jiki. Ta fahimci kamar yana niyyar barin hankicif dinnasa anan, shi kuwa yana sane ya yi hakan, ta dan saci kallonsa, ganin ba ya kallonta yasa ta dauka da sauri ta cusa a riga, ya yi kamar bai gani ba sai ma juyar da kan da ya yi yana murmushi ya soma tafiya. Suna cikin tafiya suka ji yo muryar su Abu da Gidado, hakan yasa suka tsaya suka jera tare suna tafiya da dan sauri-sauri ganin yanda ake iskar sosai, don ma a dazun ba wani nisa Ummi da Abu su ka yi ba ya taddosu. 
   Suna dab da karasawa aka soma yayyafi, cikin taimakon Ubangiji ruwa bai tsuge ba sai bayan isarsu gidan. Suka yita godiya ga Allah. 
   Faruk bisa jagorancin Gidado ya koma dakin Dattijo Manu, wanda a yan kwana biyunnan ne ya dan ji saukin jikinsa don yana fama da hawan jini. 
    Bayan sunyi sallar Magriba, Faruk ya sanya (jacket) sakamakon sanyin da garin ya yi, sannan suka shiga hira da harshen fulatanci, Faruk ya daukeshi tamkar Modibbo, Dattijo Manu na watso mishi tambaya game da ko su fulanin ina ne yana amsawa dalla-dalla. Kafin shima ya labartamishi nasu, ya ji dadin hira sosai da Faruk din, shima Faruk din ya sake da shi ainun don bai ji nauyin sanarmishi yanda ya ke kaunar Ummi ba wanda hakan ba karamin dadi ya yi masa ba. Cikin tsokana ya ce.
"Saidai fa banason kara yin nisa da amaryata."
Dariya Faruk ya yi.
"Karka damu, akai-akai za ka dunga ganinta, idan ta kama ma ai sai mu daukeka mu maidaka Abuja."
"Kayya, barni inda nafi wayo, nan Buba ma ya yi da ni akan na koma can birni Gombe wajensa na k'i." Duk suna maganar da fulatanci suna dariya. 
  "Nima inaga mun kusa zuwa Adamawa, amma fa da Amaryata."
  Cewar Faruk cikin wasa da dariya har ya bawa Dattijon dariya. Saida ruwa ya tsagaita sannan Inna Boddo ta umarci Ummi da kai musu abinci, ta yi tsuru da ido saidai ganin ba yanda ta iya ta ja Abu suka wuce tarr kowanne dauke da kwano bibbiyu don har kaza aka soyawa Faruk, gaba daya dattijan ke haduwa su ci abinci tare saidai ruwa yanzu ya hana hakan ita kuwa tunani ta ke yi Faruk dan gayu dan hutu da shi anya zai iya cin cimarsu? Haka dai suka karasa da sallama, bata kallesu ba, kai a kasa ta gaida Dattijo Manu, ya amsa yana fadin.
"Amaryata ki yi zamanki anan kinji? Sai kin iya fillanci."
Murmushi kawai ta yi, duk yanda Faruk ya so su hada ido ta k'i, saida suka kawo musu komai har ruwan wanke hannu da na sha na randa mai sanyi sannan suka fita. 
    Ummi kuwa kowa a gidan cewa ya ke ta yi sa'a ga shi mutumin kirki ga shi kuma bafulatani shima, murmushi kawai ta ke yi ba ta cewa komai. 
  Tana kwance a dakin Inna Boddo, Innar na cikin sange(mosquito net) an lullu6eta da bargo mai kauri sosai saboda sanyi. Bayan ta tabbatar Innar ta yi nisa a bacci ta fiddo hankicif din ta rufa a fuskarta tana mai shak'ar kamshin idanunta a lumshe, murmushi saman fuskarta. Wayarta ta soma k'ara da sauri ta zarota daga k'asan filo ta danna kada Inna ta farka, Faruk dinne kuwa. Ta dafe kirji kadan, a hankali ta sauka daga gadon ta fito waje ta zauna. 
  "Ummina."
"Um."
"Na yi mantuwa fa a wajen dazu." Ta zaro ido gami da hadiye miyau na fargaba.
"Mantuwar me?"
Ya danne dariyarsa yana duban Dattijo wanda munsharinsa ya hanashi runtsawa kwata-kwata. 
"Hankicif dina, ko kin ganshi?"
Idanunta ya yi kwal-kwal, to ta ce me? Ta ganshi yana wurinta? Me zata yi da shi da bata mayarmishi ba?
"Kinyi shiru."

((Afuwan..ni kaina na qagara na kammala muku saidai haka Allah Ya nufa labarin zai fi yanda na zata a tsawo...not much..lol))

DAN ADAM
@RUFAIDA OMAR

100

Ta runtse ido gami da dan mak'e wuya kamar wacce ake shirin kaiwa mari, ba ta ce komai ba.
  Ya kasa rike dariyarsa saida ya dara kadan.
"Ummina kenan, ki rikeshi na bar miki."
  Ta zaro ido kawai saita kashe wayar don kunya, ashe daman ya ganta? Ya k'ara kira bata daga ba, karshe ma ta kashe wayar.
    Washegari misalin takwas na safe, tana zaune tana shirin karyawa suna waya da Amina wacce ke labartamata cewar itama za su je Nijar dangin mahaifinsu su dawo, ta tayata murna a karshe ta sanarmata Faruk yana nan. Amina ta yi dariya kwarai.
"Oh wannan soyayya ta ku? Kedai ki yi ta godiya ga Allah da wannan babbar kyautar."
Murmushi kawai Ummi ta yi mai bayyana hakora. 
   Sun sha hira sannan su ka yi sallama. 
   Kwanan Faruk biyu ya soma shirin komawa bayan zuwan Malam Balarabe garin an zauna an tattauna inda ya yi musu bayanin karatun da Ummin ta soma a Abuja, sun ji dadi matuka saidai basu aminta da komawarta gidan surukai ba, haka dai ba don ya so ba ya hakura da raayinsa, yasan idan ya turo su Daddy to watakil su amince ta koma can. 
  A zaure suka tsaya suna sallama, Faruk ya dubi Ummi gaba daya ji ya ke kamar ya zubda hawaye, ita kuwa kanta a k'asa, ya fiddo wayarsa ya kara daukarta hoto, sautin camera yasa ta fahimci abinda ya ke. Ta ja hijabinta tana fadin.
"Kai Yaya Faruk na kusan goma kenan fa."
  "Ke an fadamiki ina gajiya da kallon hotunanki?"
   Murmushi kawai ta yi mai bayyana hakora kafin su yi sallama, a sanyaye ta mishi adduar isa lafiya suka yi sallama ran kowannensu cike da jin kewa. 
   Saida Ummi ta yi sati biyu a Jar Kwami, kawarta ta islamiyya, Husna A Rashid har ta gaji da tambayar ranar dawowarta makaranta ganin lokaci ya ja bata dawo ba. A wannan sati biyun har Kwami ta je ta ga dangin kakarta wadanda wasu da yawa sun rasu, kwananta biyu ta dawo sannan ta wuce birnin Gombe gidan su mahaifinta. 
    Kwanakinta uku da zuwa ta lura da sauyin da aka samu tsakanin mahaifinta da Dada don zuwa yanzun ta sake da shi ta nunamishi komai ya wuce abin ya bata mamaki ya kuma yi mata dadi don har hira sosai suna yi. 
  Kamar yau juma'a da yamma, sun hadu gaba daya tsakar gida ana hira, wayar Malam ta yi kara. Ya saki fuska sosai ganin Malam Yahuza ne. Fadi ya ke. "Yau Yahuza ne ya tuna da ni?"
  Ya dauka da sallama, bayan gaishe-gaishe Malam Yahuza ya soma ba shi labarin bayan rabuwa, ya sanarmishi ya samu ya shirya da yan uwansa ya nemi gafararsu, ya gangara kan labarin da ya ba shi mamaki da al'ajabi har saida ya tashi ya bar wajen yana fadin.
"Innalillahi." Suka bishi da kallo musamman Ummi da ta ji wata irin faduwar gaba don tsoronta ya kasance ko Habiba ce ta gudu daga gidan yari. 
   Bayan ya gama wayar ne ya dawo, anan Haruna ke tambayarshi ko lafiya. Ya dubesu.
"Diyar Malam Yahuza, Dije, 'yar Baba kin santa ko?"
Ta gyada kai don hankalinta ya dan kwanta.
"To itace mijin ya turowa mahaifinta takardar sakinta, aciki ya ke shaidawa mahaifin ya kamata tana mu'amala da yar uwarta mace, ya yi mata duka ya korota tun washegarin faruwar lamarin saidai an tabbatar mishi bata zo wannan yasa yanke turomishi takarda. Bayan haka kuma da kwana biyu labari ya riskeshi cewar an ganta can gidan wata Bokanya ta je tare da abokiyar shaidancinnata har an samu wasu sun k'ona gidan kurmus. Dakyar ita Dijen ta samu arcewa, fitarta kuma ta hau titi da zummar tsallakawa mota ta bi ta kanta."
  Kowa a wajen ya dauki salati.
"Duniya abar tsoro, wannan masifa da me ta yi kama?"
Cewar Baffa kenan, Dada ta ca6e.
"Karshen duk wani mai aikata mummunan aiki kenan matukar bai tuba ba, Allah Ya karemu da al'ummar musulmi ga fadawa halaka irin wannan."
Ummi girgiza kai kawai ta ke yi tana salati, lamarin mutane abin tsoro, wani abin kamar a mafarki, ba don na kusa da kai bane idan ka ji a wani wajen kana iya cewa ba gaskiya bane. 
"Allah Ka sa mu cika da imani." Cewar Malam Balarabe, suka amsa da amin.
      Washegari misalin karfe uku na rana, Ummi kwance a dakin Antinta Abida matar Baffa tana karanta wani littafi na Ahlari da ta taho da shi, ta tsinci muryar Baffa na tambayar Abida ta ba shi tabarma anyi bak'i daga Abuja. Batasan sadda ta mike tsaye ba tana lek'ensu ta windo. 
  "Su waye?" Cewar Abida tana mai mik'amishi tabarmar.
"Maneman auren Ummi."
Ai batasan sadda ta dafe kirji ba gami da komawa saman kujera ta zauna. 
"Su Daddy ne?" Shine tambayar da ta jefi kanta da shi a fili.
"Ina ki ke 'yar nema? Fito nan ki ji labari mai dadi." Cewar Abida tana kokarin shigowa dakin, a guje Ummi ta mike ta 6uya bayan labule tana dariya ciki-ciki. 
   "Au 6uya ki ka yi? Kya ma fito, ai ni tun ganin da na yi wannan saurayin ya kasa hakuri ya biyoki har nan, nasan ba lallai ya iya hakurin barinki ba."
   Ta daga labulen da Ummi ke 6oye, ganin haka ta durkusa tana mai rufe fuskarta da hannu tana dariya.
"Kai don Allah Anti."
Abida ta dara.
"Za ki san Anti, bari mu zo mu soma gyaraki yarinya."
Daga haka ta saki labulen ta koma duba sanwarta. 
  Ummi ta fito ta zauna da saman kujera tana dariya, karatun dai bai samu shiga ba.
        
   Gen. Ahmad Danzaki ne, sai kaninsa Alhaji Aminu Danzaki da babban Abokin Gen. Ahmad Danzaki, wato Major Yusuf Bashir mahaifi ga Sa'ad miji ga Baraka. Sai ko Babban Yaya wanda shi ne ya tuk'osu daga Abuja, bayan shigowarsu da tambaya suka iso unguwar sannan suka yi kiran Malam Balarabe kamar yanda suka tsara ya tura aka taho da su. 
  ((Thanks for your votes on wattpad.... Love you all..))

 DAN ADAM
@RUFAIDA OMAR
    
101

Har la'asar, Ummi na mak'ale wajen Abida ta kasa fitowa. Tana cikin sallah   ya shigo, tana ji suna magana k'asa-k'asa da Abida, sai kuma ta ji Abida ta soma bud'a wanda ya sa Ummi gabanta ya fadi adaidai lokacin da ta sallame. Furucin da Abida ta yi ne yasa ta durkuso a wajen tana salati....!
   "Alhamdulillah, Allah Shi ne abin godiya, amma ya akayi haka ta kasance?" Cewar Abida kenan.
"Wallahi abu na Alllah, da kansu suka buk'aci hakan sai kuma Malam bai musa ba don a farko sun bukaci komawarta Abujan saboda karatun da ta soma amman bamu amince ba, sai suka yanke shawarar kan a daure auren kawai, to shine fa aka daura, tarewa kuma aka barshi nan da wata daya."
   Duk wannan bayanin da Baffa ke yi a kunnen Ummi, ta ji jikinta ya yi mugun sanyi, take ta ji ruwan hawaye na kwaranyo mata, wai shikenan ta zama MATAR AURE? Ta zama mata wajen Umarul-Faruk Danzaki? Allah mai Iko, yanzu komai za ta yi saida izninsa? 
  Tana nan durkushe saman darduma tana hawaye, Abida ta shigo bayan fitar maigidanta. 
   Ta rik'ota.
"Haba Ummi, kukan menene? Godiya za ki yiwa Allah, wannan ikon naSa ne anzo da zummar a sanya rana aka daura aure gaba daya kinga kuwa babu mai yin hakan sai Allah."
  Haka ta ja ta har suka isa dakin Dada, nan sauran jama'ar gidan suka yi mata caa, ita kuwa jikin Dada ta shige tana kuka, kukan da batasan dalilinsa ba. Hakanan ba zata iya tantance yanayin da ta ke ciki ba, farin ciki ko akasinsa. 
   Kiran da Malam ya aiko ayimata ne yasa ta dan nutsu. 
   Har

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login